Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yace "Abbakar ina matukar bakin cikin hanaka auran fatima amma kayi hakuri Allah ne bai sa matar ka bace, akwai abubuwa da dama da Allah kan jarrabi bawansa don yagwada imaninsa, idan yajure yayi hakuri sai Allah yamusanya mai da abinda yafi wannan alheri sakamakon hakurin da yayi da abinda Allah yajarrabe shi dashi. Duk kokarin da dr. khalifa yayi na mayar da hawayen da suka taru a idonsa don kada malam ya gani abin yaci tura, domin sai da yadinga sharar kwalla yana jan numfashi da kyar, daga karshe kasa ci gaba da tsayuwa yayi sai durkusawa yayi, hankalin malam yatashi sosai tun yana iya magana har yayi shiru ya zurawa khalifa ido, yaji tausayinsa a wannan lokaci ,tausayi mai tsanani, zuwa can khalifa yatashi yatafi gida ba tareda yakara cewa da malam komi ba. Malam ya jima yna kallonsa sannan yashige ckin gida ya iske inna itama na ta jikin a sanyaye, yazauna yace "kai yaron nan dagaske yana son fatima. "Itama tana sonsa malam ". Inna tafadi tana kallonsa. Yace "wane irin tana sonsa kuma da maganar musbahun a kanta take son wani. Tace "wallahi kuwa fatima ta yi abinda ban taba zato ba a yanayin rayuwarta, tadubi idona tace a yanzu ita khalifa take so tana son mu fasa ba musbahu auranta mu bata shi in bar da tana son sa za tayi haka? tunda tagaya min wannan maganar jikina ke rawa hankali na yatashi sosai, ni dai yin wannan rana na yi shi ne kawai amma zuciyata tana cike da sarkakiya da damuwa, sbda fatima ta ban mamaki ta ba ni tsoro, duk abinda fatima za ta budi baki tayi magana akansa ba karami bane, tana da kunya sosai da zurfin ciki, tunda harta iya magana to da gaske tana son khalifa, yawan kukan datakeyi shi yake dada dagan hankali har na rasa yadda zan bullowa lamarin. Malam yace "amma wannan zancen banza ne, ni za ta mayar karamin mutum, sa rai da ci shi ke kawo jin yunwa in barda ta sa soyayyar ta sa ai ba za ta daga hankalinta akan shi ba, tun yaushe aka sa wa musbahu rai da batun auran ta, ya saki jiki itace matarsa kawai sai ta dawo tace ga wanda take so, a gun nan nafada mata idan ba ta son musbahu ba zan mata dole ba tace ta ami? ce, yanzu ya kike zaton mutane za su daukeni idan nafasa ba musbahu naba khalifa, kwadayi? Babu ta inda zan fidda kaina a gun musbahu da yan'uwansa dasauran jama'an gari na sayowa kaina zagi. Inna tace "wallahi malam ni ma ban goya mata baya ba don na san son zuciya ne karara tazo dashi. Haushi yakara kama malam ya kwalawa fatima kira, tafito tana rabe rabe ta tsuguna ybuga mata harara yace "na fahimci cewa ke ce kika ba khalifa fuskar yazo gdan nan yazo min da batun auranki alhalin kina sane da musbahu, kin ba ni mamaki fatima ban taba shakku akan lamarinki ba sbda biyayyar ki garemu kada ki bamu kunya kada kija abinda zai ja mana damuwa alhali muna zamanmu lafiya. Fatima tayi doguwar ajiyar zuciya tace "kuyi hakuri baba ni ma banyi tsammanin zan wayi gari ckin wannanyanayi ba, ni kam ina son khalifa don Allah ku ba musbahu hakuri.... "Salamu Alaikum Muryar musbahu knan, suka daga kai a razane suka zuba mai ido fuskarsa a cunku she yazauna jagwab kusa da malam muryarsa na rawa yace "Baba hakika na ji duk tattaunawar ku da fatima kuma na ji matsayina a gunku, ba ni da abi? da zan ce muku sai godiya, kyautatawar dakuka mini Allah ne zai biyaku domin don shi kukayi. Baba na san ina son fatima soyayyar da tasa nake jin cewa idan na rasata zai wahala in yi aure domin bansan ta yadda za ai in so wata mace ba bayan ita, ko da yike komi na Allah ne amma wannan soyayyar danake mata ba za tasa in aureta alhali na san ba ta so na ba, kayi hakuri baba kaba fatima khalifa... Cikin zafin rai malam musa yace "yi min shiru musbahu, wannan yarinyar bata isa tasauya min ra'ayi ba, tunda tun farko da amincewarta aka sa bikin auran nan kadarra cewa ma ka auri fatima ka gama. Ranar da aka sanya za a daura wannan auran ba fashi, insha Allahu za a daura in dai ka ga ba a daura ba sai dai in ranar ce tariskeni ba na numfashi, za a daura auranku kuma za a kaita gdanka, a ranar tahadiya zuciya tamutu a kawo min gawarta. Musbahu yabude baki zaiyi magana malam yayi mai tsawa yace "in dai kaima ba so kake kabata min rai ba kayi min shiru, idan Allah yakaimu gobe kaje ka amso katunan daurin auran a kaiwa kowa. Yatashi yafice ,musbahu ma yabi bayansa, itama innar tashige daki tabar fatima tana kuka. Tunda take bata taba batawa iyayanta rai ba ballantana suyi fushi da ita sai yau, shin me ya shiga zuciyarta ne tasauya haka, a duk lokacin da ake magana, soyayyar khalifa ce take karuwa a zuciyarta, kamar ana hura mata wuta, idanuwanta suka kada jawur tarasa yadda za tayi da ranta. Soyayyar dr. khalifa ta gama rufe mata zuciya ji take kamar ba xa ta iya rayuwa ba in ba shi, gabaki daya ta watsar da batun ummi ta kanta kawai take, tana ji a ranta in dai ta auri khalifa duk abinda zai biyo baya me suki ne, iyaka dai ummi tadaina kulata ita in dai tana tare da khalifa bukatar zuciyarta ta biya, matsalarta yanzu iyayanta wadanda sun dau zafi dayawa. Ta daga kai ta amsa sallamar musbahu, haushi yakara kamata tabishi da ido har yatsuguna gabanta yace "fatima. Bata amsa ba sai kallo yace "kiyi hakuri. Ta mike tashige ckin daki a zuciyarta tana fadin ai kai hakuri yakama ba ni ba. Musbahu yayi zaman dirshan a gun yazuba tagumi da hannu bibbiyu shin wani irin iftila'i ne yasa me shi haka?da can bai rasa fatima ba sai da yagama sakin jiki bai da mata sai ita, yakasa juriya yabita dakin na su, ya isketa a kwance tana kuka. Yace "fatima baki min adalci ba don Allah ki kwatanta idan ni nayi miki haka za ki so? a ce a irin wannan lokaci in ce na fasa auranki wata zan aura? Ya tsuguna a gabanta kamar mai neman gafara yace "don Allah fatima ki taimake ni wlh ba karamin so nake miki ba, ni ban isa in ce kwadayin duniya ne yasa kike son khalifa ba idan akwai kwadayi ba za ki tsaya akaina ba, masu kudi dayawa sunce suna sonki baki ba su hadin kai ba. Fatima batayi niyyar yi ma musbahu magana ba dan ita kanta ta san ba ta da abinda za tace musa, amma a bisa wannan maganar tasa da taji ya dace tace wani abu a kokarinta na samin mafita. Tace "Nagodewa Allah dayasa da kanka kayi min shaidar ba kwadayi yasa nace ina son khalifa ba, ka san cewa soyayya ce don Allah, ina son kayi hakuri kayi min adalici, soyayya Allah ne me sanyata a zuciya ba mutum ba. Ya katseta zuciyarsa cike da daci yace "fatima ki fito a gaban ido na kawai ki ce ba kya so na, khalifa kikeso, na gode fatima nagode. Yamike dasauri yafice yana goge hawaye. Fati tace "innalillahi wa inna ilaihir raji'un. A DAREN FARKO 27 izuwa wannan lokaci ummi ta tabbatar fatima ta daina yi mata aikin komai ita takewa kanta, ta fahimci soyayya suke shimfidawa da dr. khalifa ta gaske duk da cewa rigima ake tafkawa a gdansu, ga katunan daurin auren yau an fito dasu har an kawo na Abba gdan, a kalla kwana uku kachal a daura auran musbahu da fatima, har takaici da kishi ya yiwa ummi yawa, yaudara ita take fassara fatima ta yi mata tunda gashi ta fita hanyarta tunda gashi ta fita hanyarta gaba daya ko neman ta ba ta yi lallai mutum abin tsoro ne. Ta iso gdansu da katin daurin auran ta nunawa hajiyarta tace "to ai zance ma ya kare in dai aka mata aure aka kaita dakin mijinta ai dole khalifa ya hakura da ita duk maitarsa . Unmi tace "kayya dai hajiya khalifa yana son fatima in kinga abin da yake nunawa za kiyi mamaki. Tace "duk ihu yakeyi bayan hari shi zai bawa kansa auran na ta? ki kwantar da hankalinki malam yana nan yana buga mana aiki da kafarsa khalifa zai zo gdan nan. Ita dai ummi hnkalin ta ya ki kwanciya son da khalifa ke nunawa dmfatima kadai ya isheta takaici, ita ko kallon ta ba ya yi tamkar ba aiki ake yi a kansa ba. ***** Ummi ce take sha'aninta khalifa bai san an fara rabon katin auran fatima ba sai da yamma daya dawo daga asibitin su dr. hafiz ya iske katin a hannun abbansa, yana gama karantawa yazube a gun. Abba yatashi a firgice yana jijjiga shi tare da kiran sunan sa da karfi ina khalifa ko motsi baiyi ba numfashinsa yatsaya cak, abba yafita dagudu yakira mai gadi yace yazo sudauki khalifa ba lfya, mama da anty sdiya ma suka fito daga daki ganin yanayin khalifa yatashi hankalin kowa sun shiga dimauta, suka nufi wani asibiti mai zaman kansa har suka isa khalifa ko motsi abba salati yake yana fadin "shike nan Khalifa ya mutu akan son ftima na ga takaina. Likitoci suka amshe shi ckin gaggawa suka kaishi wani daki suka fara ba shi taimakon gaggawa, dakyar suka lallashi abba y tsaya a waje dan cewa yayi sai ya shiga dakin, gani yake kamar khalifa ya mutu, mama datake mace ma ta fi abba karfin hali, itatadinga ba shi baki tana nuna masa cewa ba mutuwa khalifa yayi ba, yadinga kai komo a kofar dakin ba likitan daya fito, yagaji yashiga buga kofar yana fadin "ku fito min da gawar khalifa na san ya mutu. Wani bakin likita dogo siriri yafito yaja hannunsa suka shiga dakin yaba shi kujera yazauna daf d gadon da aka kwantar da dr. khalifa yace "Alhaji duba kagani yana numfashi ko? Anan ne abba yayi doguwar ajiyar zuciya, ashafi fuskar khalifa zuwa wuyansa yaji sanyi kalau, numfashinsa yadawo normal amma lokaci daya yarame fuskarsa takara haske. Likitannan mesuna dr. mansur yadan rusuna kusa da abba yace"ka gamsu bai mutu ba ko? Yace "hakane amma nikam likita jikina na ba ni mutuwa zaiyi, khalifa ba zai yi dogon kwana ba a duniya... Dr. mansur yarufe me baki yace "haba alhaji ya za kadinga wadannan maganganun a matsayinka na musulmi? mutuwa daban ciwo daban, kayi hakuri mun sha kan matsalar khalifa dimuwa ce kawai takai shi ga shiga wannan halin in dai ku? yi kokarin magance masa damuwarsa shi knan komi zai tafi yadda yakamata. Su mama ma an ba su damar shigowa ita da anti sadia, gaba daya suka zubawa khalifa ido cike da damuwa jikinsu ya gama sanyi da al'amarin . Abba yagirgiza kai yace "hajiya wani irin tsari ne haka, shi knan akan mace mutum yadaga hankalinsa kamar zai bar duniya,ni wallahi har na rasa yadda zan bullowa al'amarin na khalifa tunda ga wanda iyayanta suka yiwa kawari na yi na yi yayi hakuri ya ki fahimta,ban taba ganin abinda khalifa ydga hankalinsa akan sa ba sai akan fatima, wacce irin soyayya ce wannan, daga ganin katin daurin aure. Mama tagirgiza kai tace "wallahi abba nima tunda khalifa yafara maganar yana son fatima hankalina a tashe yake, sbda yanayin daya ke nunawa abin fargaba ne, in an yi magana yace wai a kyale shi b a san abinda yake ji bane, to rayuwa za tatafi a haka, wani abun idan mutum yana so yana samu wani abun kuwa duk maitarsa da kaunarsa da abin ba zai same shi ba sai hakuri. To shi khalifa ji yake kamar ba zai ci gaba da rayuwa ba idan bai mallaki yarinyar nan ba,. Suka yi shiru kowanne idonsa kan khalifa, daga bisani abba yaja numfashi yace "wai yaya za mu bullwa lamarin nan ne? Mama tace "to yaya za muyi kuwa abba in barda muyi hakuri dole fa khalifa yahakura da fatima. Abba yace "kai hajiya a irin wannan yanayin, dubi fa yadda yake. Tace "to idan bamuyi hakurin ba ta karfin tsiya za mu ba shi fatima? ***** Ga dai lokacin biki ya zo gadan gadan amma gdansu fatima yanayin babu dadi domin kuwa ango da amaryar suna cikin damuwar dataja jikin kowa ya yisanyi babu mai walwala,Fatima ce zaune kan kujerar zaman tsakar gida da wayarta ta hannu ta kurawa sakon daya shigo wayarta ido zuciyarta na azalzala sako ne daga khalifa yace. Fatima soyayyarki xa ta hallakani bbu wani taimako daza kimin don Allah kiji tausayi na kada ki bari iyayanki su bawa musbahu ke wallahi na fi son ki fatima. Tagoge hawayen dasuka gangaro mata tayi ta maimaita sakon tana girgiza kai, ta tashi tashiga dakinsu tacimma katunan gayyata na biki da musbahu yakawo mata da la'asar din dazu, ganin idon katunan sun tsaru sun yi kyau amma ita bakin ciki ne yakara turnuke mata zuciya data gansu, ganin katunan yakara kusanto mata lokacin bikinta knan kuma lokacin rabuwarta da masoyinta dr. khalifa, kuma idan tayi wasa wankin hula na daf da kai mata dare. Shi kansa musbahun lokacin daya kawo mata katin sai da yabata tausayi, tana sallah yashigo yatsuguna bakin kofa kamar me neman gafara, data idar bata kalleshi ba tajawo pillow ta kwanta, a sanyaye yace "fatima ga katinan gayyatar. Tadube shi wani iri tace "to ajiye anan. Ya matso daf da ita ya ajiye, uace "ko kina bukatar wani abu daya danganci bikin? Ta ki magana sai da yayi ta mata naci sannan tace "Ni fa ba abinda nake bukata. Yace "shi knan sai anjima. Yamike yafita yayin da tabi bayansa da ido cike da takaici. Gabadaya dr. khalifa ya sauya mata yanayin rayuwarta, kafin dawowarsa tana zaune lafiya ba ta damuwa da komi babu abinda yake tayar mata da hankali sai daya dawo. Tun randa dr. khalifa yafara cewa yana snta bata kara samun kwanciyar hankali ba, gabadaya ya jefata a ckin damuwa da rudani kullum tunani, ta zamo abar tausayi akan kanta domin yanayin da zuciyarta ke ciki ba dadi, ba ta jin dain halin data sanya musbahu sbda babu abinda yayi mata, ya rayu yana tattalin abin da take so tun tana yar karama yake tattalin rayuwarta har maganar aure ta bullo a tsakaninsu, ya dauki son duniya ya daura mata kullum kamar zai lashe ta, ba ya son abinda zai daga mata hankali, kowa ya shaidi musbahu da kyawawan dabi'u ababan so ga kowacce mce, dari bisa dari ta amince da batun auransa, shi yasa bata tava kallon wani da namiji da sunan so ba, sbda ita dai yardar Allah kawai take nema a rayuwarta, bata taba damuwa da kyale kyalen duniya ba, bbu kwadayi ko son zuciya tsarinta, shi yasa tafiyarsu da musbahu yaxo daya svda shima akan wannan tsarin na ta yake tafiya. kowa yana kyautata zaton za su zauna lfya a dalilin kowannen su ya dauki rayuwa dasauki, iyayanta suna cike da murnar auran ba su da fargabar komi, sai da abin yazo daf dr. khalifa ya bayyana cikin rayuwarta shi knan zuciyarta tasauya. ***** A DAREN FARKO 28 Tana cike da jin nauyin musbahu, soyayyar dr. Khalifa ce take da karfi a zuciyarta shi yasa takasa tuna komi. A bangare guda da ummi, ummi ta taka muhimmiyar rawa a kanta ta hanyar nuna mata kauna da aminci na gaskiya takuma haifar da cigaba a rayuwarta, a daidai lokacin datake kokarin taimakon ummi don ta cimma kufurinta a kan dr. khalifa soyayyar khalifan yakama zuciyarta, wanda a wannan lokacin ne ta fahimci meye so tasan zakinsa da dacinsa kusan wahalar da zuciya ke sha akan ciwon so, tausayin ummi ya yawaita a zuciyarta domin ta dade tana fama da ciwon son khalifa, alhali ba ta da tabbas din komi a kansa, ga misali itama dayake son ta tanayin ciwo me zafi a rayuwarta na son sa ina ga ummi da ta tabbatar ba ya sonta ,kowannansu kam abin tausayi ne, ama dai ita ta fi zama abun tausayi tunda ita tana sa ran samun khalifa wani abu ne yake neman yi mata shamaki dashi, ummi kuwa dama tana sa rai ne tana cire ranta, tunda ta san bai karbi soyayyarta ba. Wannan shi ne tunanin fatima. ***** A bisa wani dan benci dake kofar gdansu fatima,musbahu ne zaune ya yi tagumi lokaci lokaci yana fidda nannauyar ajiyar zuciya wadda ke cike da damuwa da dacin rai,idanuwansa sun kada jawur ,yau so yake yi ma yayi kuka ya kasa, wai shin me ke faruwa dashi ne, da can bai fuskanci matsala da fatima ba sai yanzu, an ya ba mafarki yake ba, fatima ce tadawo ko ganinsa ba ta son yi, a baya ko yaushe in suna magana idan ya kutso mata maganar rayuwa takan bata rai tace ita kuwa me za tayi da wani namijin bayan ga zabin da iyayanta suka yi mata, ta kance k kwantar da hankalinka ba ni da abin da yafi iyayena in dai zuciyarsu za tayi haske to ni burina ya cika ba ni da damuwa . Ire iren wadannan maganganun suke ba shi cikakkiyar natsuwa da kwanciyar hankali, musamman a bisa la'akari da rayuwar fatima ba mai tsada bace in ban da haka kallonta kadai ya isa hnkalinsa yayi ta tashi sbda kyawun halittar da Allah yayi mata zai dinga jan hankalin mazan zamani kanta, to kuma si gashi abubuwa sun sauya a lokaci guda fatima tajuya masa baya khalifa take so, yadinga jin wani azababban kishi da takaici yana tafarfasa zuciyarsa kamar zaiyi hauka, iyakar tunanin sa bai san yadda zai bullowa al'amarin fatima ba haka zai aureta hankalinta na kan khalifa ya girgiza kai, inama sai da akayi auransu khalifa yadawo, da ba zai ganta bama ballantana yace yana sonta har yadaga mata hankali yadagawa kowa. Yashiga harar kwalla, sai yanzu yaji zuciyarsa ta yi masa dama dama daya samu hawayensa suka zubo, tabbas yana son fatima amma yanzu fati tsoro take ba shi "kukan me kake musbahu? A firgice yadaga kansa yadubi malam wanda yake tsaye a kansa yana kallonsa, yaci gaba da sharar hawayensa ba tre da y ce komi ba, malam yace "Biyoni ckin gida. Ckin sassarfa musbahu yake tafiya suka shiga dakin malam din suka zauna, yakara maimaita mai tambayar "kukan me kake? Muryarsa a dashe yace "baba ban san yadda za ayi in shawo kan fatima hankalinta yadawo kaina ba, ina jiyewa kaina tsoron abubuwa da dama game da fatima. Malam yace "musvahu ni ne fa na haifi fatima ni ne na yarje ma auranta, har a halin yanzu ina dada tabbatar maka da cewa in dai ranar daurin auran nan tazo ina raye ba zan daurawa fati kowa ba sai kai, to meye na tayar da hankalinka kan fatima in dai in dai tana ckin gdan nan tana karkashin ikn mu za a kaita gdanka kuma dole ne tayi biyayya gareka in har tana son zaman lafiya damu, ita kanta ta san ba na kwadayin abun duniya bana son zuciya a kanta kuma ba zan fa ra ba. ***** A son ran ummi tayi zamanta a gdansu kada takoma gdansu khalifa wai a tunanin ta hakan zai sa hankalinta yakwanta, ta huta da bakin ckin dr. khalifa da fatima ke haifar mata amma ina lokacin da dare yayi dare sai taji hankalinta ya tashi sosai khalifa kawai take bukatar gani. Tabdijan ashe dai tana da jan aiki a gabanta ace duk sanda ba ta gdansu hnkalinta ne zai ding tashi haka, knan va za ta iya rayuwa ba sai tana ganin khalifa? ta mike zaune zaman ya gagara tamike tsaye anan ma tashiga sunturi ta dauki wayarta tayi kiran nomban khalifa bai daga ba bata san abinda za tace masa ba amma dai in taji muryarsa watakila tasamu tayi bacci ta huta, in dai a haka xuciyarta za ta tafi tana da babbar matsala. Takira nomban fatima bugu daya fatima tadaga tayi mata sallama da siririyar muryarta, tace "fatima bakiyi barci ba? "Eh banyi ba. "Meya sa? Tayi shiru. Tayi murmushi tace "na san tunanin dr. khalifa ne yahanaki bcci, don Allah haka ne. Fatima tayi ta maza tace "Na san kin san haka ne unmi shiyasa kika fada. Tayi ajiyar zuciya tace "fatima da ma na san ba za ki iya kaucwa soyayyar dr. khalifa ba duk da cewa a baya na mi? ce har ckin zuciyata za ki taimake ni a kan dr. khalifa to sai ga shi kema.... Haushi yakama fatima ta tabbata soki burutsun na rashin abin yi ne yasa ummi ke mata wannan shiriritar dan haka takashe wayarta. Mamaki yakama ummi ta jima tana kallon wayarta wai yau ita fatima ke ma haka, bata ma da lokacin saurararta, hakika ya zamo dole ta dauki mataki mai kwari akan fatima. Da gari ya waye da sassafe ta tashi tayi wanka ko tunanin cin abinci batayi ba tashirya tace da mahaifiyarta "na tafi gdansu khalifa. Hajiya na zaune a kicin tana suyar wainar fulawa tayi mata wani irin kallo tace "wai me ke daminki ne ummi, abin ci ma ba za kidinga tsayawa kina cinsa ba sbda khalifa? wannan wainar ma sbda ke nake yinta na san kina sonta amma ki ce tafiya za kiyi? Tace "don Allah hajiya barni in tafi hankali na a tashe yake ko barci banyi ba jiya. Tana tuka mota tana wasi wasi a haka har ta iso gdan masu aiki suka tarbeta da mummunar labari a asibiti dr. khalifa yakwana ba shi da lfya, tayi saurin kiran nomban mama tayi mata kwatancen asibitin dasuke tafigi mota ta nufi can. Hankalin ummi yakara tashi ganin yadda taga dr. khalifa mike isa gado, yana wani irin bacci wanda ga duk alamun bai san a inda kansa yake ba, mamane zaune bisa dadduma a kasa sadiya a gfenta abban na zaune kan wata kujera dake gefen gadon khalifa yazuba masa ido kawai. Ta tsyguna ta gayar dashi tare da jajanta masa ciwon khalifa ta zauna kusa da mama tana tambayarta "me ye musababbin ciwon ne? Mama ta tabe baki tace "katin daurin auren fatima yagani. Ummi tafiddo ido gabanta na faduwa tace "don ya ga katin daurin auran fatima yashiga wannan halin? Mama tace "kwarai kuwa tunda muka kawo shi asibitin nan bai farka ba har yanzu, nasarar da akaci dai nu; fashinsa ya dawo dai dai sabanin lokacin da muka kawo shi dan ko numfashi bbu, ni zatona ma ya mutu. Jikin ummi yakara mutuwa murus takoma jikin bango itama tayi shiru har tarasa abin da za tace. Wato wannan soyayyar har ta kai zafin haka, ina aikin da malamin su yace zai musu mai zafi wanda yaci musu alwashin zai raba soyayyar fatima da khalifa da ta duk wata diya mace sai ita ummin,. Amma abin mamaki kamar karawa dr. khalifa soyayyar fatima ake, me malamin nan ke nufi knan, aikain yake musu ko yaudararsu yake" Ta jinjina kai a baya kam ta san dr. khalifa yana son fatima haka yanayinsa yanuna, to amma yau ne yadada tabbatar da soyayyar nan ba ta wasa bace duk inda ake tunanin abin ya wuce nan,fidda soyayyar fati daga zuciyar khalifa abu ne mai wahalar gaske. Tadubi mama tace "to yanzu me likitocin suka ce? Mama tace "cewa sukayi a samar masa da abinda yasaka a ransa yana so din idan ana son rayuwarsa. Tace "to wani mataki aka dauka? Mama tace "har yanzu bamu san abinda za muyi ba. fatima dai tunda ba mu da ikon ba shi ita ai sai hakuri . Ta jinjina kai tace "To Allah ya sawwaka bari inje gda in kawo muku abinci ko zai farka ya bukaci wani abu. Mama tace "ga abin cin nan na asibiti an kawo. Tace "ai khalifa ba zai iya cin abincin asibiti ba bari dai in dafo wani abun. Lallai dr. khalifa ya yi nisa ba yadda za ayi yaji kira, gdansu fatima tafara shiga sai ita kadai a rmfar inna tana fama da waya, inna tana dakin malam suna hiran bikin fatima. Ta amsa sallamar ummi ckin fara'a tamkar ba wani abun, tukukin bakin ciki yakara turnukewa ummi zuciya, tayiwa fati kallon sama da kasa lokacin datake ce mata zauna mana anty ummi. Tace "ba zama nazo yi ba zuwa nayi in tamvayeki ina amsar taimakon dakika dauka za kimin a gun dr. khalifa.? Nan fatima tarasa abinda za tace tayi shiru, ummi tace "dama na san bbu abinda za ki iya cewa, tunda ba ki da abin fada din kinyi amfani da damar dakika samu kinja ra'ayin dr. khalifa har soyayyar dayake maki ta kaishi ga kwanciyar ciwo, to yana asibiti bai san inda kansa yake ba a dalilin ya ga katin daurin auranki da musbahu, sai kije ki duba shi kafin yakarasa mutuwa. Tajuya za ta tafi fati tajawo hannunta tace "Don allah ummi kar ki tai zauna ki taimake ni nasamu kaina a wani irin hali. Wani taimako zan maki fatima? ni van taimaki kaina ba wa zan iya taimakawa? in kura na maganin zawo me yasa batayi wa kanta ba?. Fati na kuka tace "ai rai ba ta rasa motsi ummi tasaya kiji. Ta jingina da bango tare da rungume hannayenta a kirjinta tana kallon fatima, fati tace "a wane asibitin khalifa yake? Tace "idan za ki wuce muje. Gaba dayansu sun rasa abinda za su cewa junansu kowacce tana neman taimakon 'yar 'uwarta ne ,unmi tace "tunda baki da abin fadi nima na rasa abinda zan ce miki kisameni a gda zan hadawa khalifan abinci sai muje asibitin, dasauri tfice daga gdan. Yayin da fatima tanufi dakin babansu ta durkusa tashaida musu cewa za su je karbar dinkin tada mama tayi musu na biki da ummi, sukace a dawo lfya. Ta sauya kaya ko wanka batayi ba tafice daga gdan, musbahu na kallonta tashige gdansu khalifa ba shi da ikon yi mata magana sai kallo, fatima ta fi karfin sa yanzu. Ummi na kicin tana ta hada abincin cikin gaggawa, fatima ta yi zaune a falo tana ta kallon hoton khalifa gabanta sai faduwa yake, wani babban hotonsa ne yakewa mutum maraba da zarar ka shigo falon, murmushi yayi a hoton murmushin dayayi matukar kayatar da fuskarsa, takagu ummi tagama su tafi taga halin da masoyin ta ke ciki. Bayan ummi ta kammala komi a mota tashiga dakinta da niyyar yin wanka ganin ta jima bata fito ba a fusace fatima ta bita ckin dakinta tashiga buga kofar toilet din tana fadin 'haba ummi wane irin jan rai ne haka? kinsan fa jiranki nake. Ummi tace "to don kina jira na ba zanyi wanka ba, karki dameni malama asibitin ma ganin damar kaina nayi ko kin sani ne ba sai da na gaya miki ba. Fatima tarasa me za tace da ummi don haushi, kuma karin haushi ne yasa bata kara ce mata komi ba sai da tagama abinda take a toilet,sannan tafito tafara shiryawa,fatima takara fusata a karo na biyu tace "ummi idan ba za ki rakani asibitin nan ba ki gaya min in yi tafiyata. Ummi tarausayar dakai tana murmushi tace "yi hakuri taso mutafi. A cikin mota tafiya suke kamar wasu kurame, kowacce da abinda take fama dashi a zuciyarta, da suka shiga harabar asibitin tasamu wuri tayi parking fatima ta tayata diban kayan abincin suka shiga dakin. Abba ne yakama fara'a yana fadin "fatima ke ce da kanki? Kunya da tausayi suka kamata lallai abba na cikin damuwa ta tsuguna tagayar dasu tare da tambayarsu mai jiki,

Chapter 12 of 19