mata kama da na Nasreen, amma kasancewar ba ta taɓa ganinta da niƙabi ba, sai ta ɗauka tafiyar ta su ce ta yi kama.
Ta fara tunanin ita ce ganin goyo a bayanta kuma tana dumfaro inda take. Ƙwayar idanunta ta kalla daidai lokacin da ta yi mata sallama.
"Subuhanallahi! Mai ya samu idanunki?" Ta yi mata tambayar, ba tare da ta amsa sallamar ba tana ƙoƙarin cire mata niƙabin
"Ga shi na dawo miki da kyautar ki. Da na san abin da zai faru a dalilin kyautar da ban karba ba. Mijina ya yi fushi kuma ya ce na mayar miki. Ki gaya wa yayanki na gode, zan ci gaba da karatuna ba tare da ina da su ba."
"Nasreen, wai me ya faru? Da ma kyauta yana zamo abin faɗa ne? Shi mijin na ki bai yarda dake bane?" Ta yi mata tarin tambayoyin tare da buɗe fuskarta.
Ja ta yi ta matsa cikin tashin hankali."Nasreen? Mai ya faru da ke?" Kawai sai kuka ta kai hannu za ta kamata.
"Ki fita daga rayuwata na ce!" Ta daka mata tsawa tana faɗin haka, sannan kuma ta ɗora da cewa,"Kin san abin da ya faru a dalilin kyautar nan? Ya ce ina cin amanar sa, kuma ya duke ni ya tozarta mahaifina. Na yi dana sanin karbar kyautar nan."
Tsananin tashin hankali ya bayyana a Kyakkyawar fuskarta. Kuka sosai ta rushe da shi ga in yadda halittun ta suka canza.
"Kina rayuwa da mijin da bai yarda da ke ba and you call this marriage Nasreen? What the hell kike yi har kika yarda namiji ya raina ki kamar haka? Dubi yadda ya canza kyakkyawar fuskarki. Kin san yadda fuskan ɗan adam take da daraja? Ko kin san darajar da Allah ya bawa 'ya'ya mata?"
"Ba na son jin komai daga gare ki, zan bi umurnin mijina saboda shi ne kawai gatan da na ke da shi.
"Namijin da zai duke ki shi ne kike kira miji?"
"Eh, saboda bani da wanda ya fishi. Ina rokonki da ki fita daga rayuwata. Na gode da taimakon ki." Ta ce tare da juyawa.
Ba tare da kula da ije mata da ta yi ba ta bi bayanta.
"Nasreen!" Ta furta daidai lokacin da ta ƙaraso motar.
Tsayawa ta yi ganin har ya tashi motar ya bar harabar makarantar.
Matuƙar mamaki ya kamata ganin mijinta na da mota. Sam ba ta taɓa tunanin mijinta yana da mota ba
Kuma mota mai tsadar gaske. Sannan shigarsa da yanayin sa ya tabbatar mata da yana da kyau da hutu, sannan ya yi karatun boko.
Kanta ya ɗauke wuta, har ta ji yana shirin sara mata. Zama a gurin ta yi cikin tsananin tashin hankali tana tunanin fuskarta.
"Innalillahi wa inna ilahir raju'un! Wannan aure take yi ko bauta? Ace mijin ka bai yarda da kai ba?"
Sosai hawaye yake zuba a ƙuncinta matuƙar tausayinta ya kamata. A maimakon ta fita daga rayuwata kamar yadda ta ce, sai ta ji wani irin mugun sonta da ƙaunarta, ya shiga cikin ranta har tana ji ta san rayuwar ta kuma ta san asalinta.
"Ta ce shi ne kawai gatanta marainiya ce?" Ta yi wa kanta tambayar hakan.
"A'a, ita ba marainiya nace, saboda na ji ta ce a dalilin kyautar ya wulaƙanta iyayenta." Ta bawa kanta amsa.
"To mai yasa take zaman aure a gidansa na ƙangin bauta?" Ta kasa gane dalilin haka.
Dama ta shigo ta je Library ta yi karatu ne. Faruwar abin ya sanya ta juya ta koma gida cikin tashin hankali. A hanya kuka take yi, tana tausayinta da mamakin rashin imaninsa da ya yi mata haka.
Tana isa cikin gidan ta yi parking sannan ta fito ta wuce ciki.
Mamaki sosai suka yi ganin ta dawo.
"Marwana, mantuwa kika yi?" Hajiya ta tambayeta cikin mamaki.
"A'a." Ta ba ta amsa tana zama a kan kujerar da take zaune, tare da ture Little Marwana da ta haye cinyarta tana faɗin,
" Anty."
Makaranta innsha Allahu yau zan yi posting safe da yamma a cigaba da surbubuɗo comments ❤️❤️❤️❤️💃💃💃💃
WASU MAZAN" Labari ne a kan rayuwar Nasreen wacce ta haɗu da jarrabawar rayuwa. Nasreen tasha jarrabawa a rayuwar aurenta da Faruk. Wanda faruwar haka yana da nasaba da rashin bango mai kyau abin jingina da ba ta samu ba, wato mahaifinta da ya kasa cike gurbin da ya kamata ya cike. Rayuwar aurenta madubi ne ga wasu matan da suke shan wahala ko rashin sama lafiya da mazajensu. Duk da ƙoƙarin su na son su zauna a ɗakinsu don gudun ZAWARCI da kuma fargabar rayuwar 'ya'yansu yadda za su kasance in ba su, da kuma fargabar mijin da za su aura bayan aurensu ya mutu. Wannan dalilin ya sanya ta jure zaman gidan aurenta don ta samu ta rayu da 'ya'yanta. Sai dai ƙaddara ba ta wuce mutum dole afkuwarsa tabbataciyace tun da Ubangiji ya tsara tun a Lauful Mahfuz. Duk yadda ta so ta kaucewa ƙaddara faruwar hakan ya ci tura. Ta shiga cikin tsananin rayuwa da fidda tsammani. Ta haɗu da wacce ta kira hasken da ya haska fitilar rayuwarta, amma sai dai a garin ta kawo hasken, ta sanya rayuwarta cikin tsarƙaƙiyar da ya zama tsarƙen da ya jefa rayuwar ta cikin tsarƙaƙiyar soyayyar mai kama da ƙiyayya. Sai dai Ubangiji ya faɗa a cikin littafinsa mai tsarki cewar,"Duk tsakani, akwai sauƙin." Haka ta kasance a lokacin da ta fidda tsammani a cikin rayuwarta, sai Allah ya kawo haske mai walƙiya da ya canza tubalin ƙaddararta da ga duhu zuwa haske. Ta kuma sha ruwan zuman da take tunanin ba za ta taɓa shan sa ba, bayan ta kwankwaɗi na maɗaci, wanda ya gauraye dukkan rayuwarta har ta fidda tsammanin shan zuma. A cikin littafin akwai wata irin soyayya mai tsuma zuciya. Masoyana karku sake a baku labarin littafin "WASU MAZAN" Domin na wasa ƙwaƙwalwa ta na zauna na tsara shi ta yadda zai sa ya ku tausayi da nishadi har ma ya zama darasi. Ku kasance masu bibiyar littafin domin jin yadda tubalin ginin rayuwarta zai kasance. Kun san dai alkalamin Jamila lawal Zango ba ya rubuta shirme.
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KusyXgwh9wEAHDTn6dzD43
*WASU MAZAN*
NA
*JAMILA LAWAL ZANGO*
*FIRST CLASS WRITERS*
MARUBUCIYAR
Sakacina ko halin maza
Kura da fatar akuya
Ranar wanka...
And now
Wasu mazan
08144072423
PAGE 10
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
"Marwana, mantuwa kika yi?" Hajiya ta tambayeta cikin mamaki.
"A'a." Ta ba ta amsa tana zama a kan kujerar da take zaune, tare da ture Little Marwana da ta haye cinyarta tana faɗin," Anty."
"Sis, lafiya?" Cewar Damir da yake zaune gefen Hajiya.
Sai kawai ta fashe musu da kuka sosai. Gabakiɗaya suka yi kanta.
"Mai ya faru? Suka yi mata tambayar cikin mamaki."
"Wallahi na fasa auren Ya Ashman in har haka auren yake." Ta ce tana share hawaye.
"Mai ya faru, wani abu ya yi miki?"
"Ya duketa ya fasa ya fasa mata kai, har yana cewa tana cin amanar sa, sannan ya tozarta iyayenta."
"Wa ke nan, ko ya yi aure ne bamu sa ni ba." Hajiya ta yi mata tambayar cikin mamakin kalamanta.
"Mijin Nasreen." Ta furta cikin muryar kuka.
"Nasreen?" Suka yi mata tambayar har da Damir, saboda shi ya manta da ya bawa wata kyauta.
"Nasreen ɗin da ta ke top a ajinmu wacce ka siya mata waya da laptop."
"Ohh," Ya ce tare da tunawa.
"Waye ita Damir?" Hajiya ta ce.
"Wata yarinya ce a ajinsu tana da ƙoƙari shi ne na ce zan yi mata kyauta. Ta ce na siya mata waya da laptop ta samu na karatu. Da na siya mata ta kai mata. Ina ga shi ne mijinta ya zargi wani abu." Ya ce cikin basar da zancen.
"Kuna da hankali kuwa? Dama dole ai ya nuna tashin hankalinsa, saboda yanzu duniya Babu tsoron Allah. Yin zanace-zinace ya yawaita ba 'yan mata ba, ba kuma zawarawa ba har matan aure marasa tsoron Allah suna aikatawa."
"Amma Hajiya kin ga dukan da ya yi mata? Ya fasa mata fuska, ko ina jikinta shafin duka ne."
"Bai kyauta ba saboda bai kamata ya duke ta ba." Cewar Hajiya.
"Kuma in ban da shi mahaukaci ne, iya zaman da suka yi ai ya kamata akwai yarda da amana a tsakaninsu. Ko da ace an gaya masa cewar matarsa na cin amanar sa bai kamata ya yarda ba."
"Abin da nake tunani kenan. In har babu yarda da ita ba. Ban ga dalilin da zai sanya ta zauna da shi ba. Yaran su biyu."
"Haka WASU MAZAN suke sun ɗauki mace kamar baiwa." Cewar Hajiya.
"Kuma abin mamaki she is young. Ba za ta wuce sanata ba, don zan iya girme mata." Ta faɗa tana kallon Damir da ransa ya ɓaci.
"Saboda wannan zai sa ya ki fasa auren Ashman? Ina ba zai taba aikata haka ba, kuma duk ranar da sheɗan ya sanya shi ya aikata. To nine ajalinsa. Ki kwantar da hankalinki matukar ina raye, babu wanda ya isa ya yi miki tsawa ballantana ya ɗora hannu a kanku."
"Na gode Yaya Damir, kuma ina godiya ga Allah da ya ba ni kai a matsayin Yaya. Allah ita ma ya bata Yaya kamar kai."
"Amin," Ya ce yana murmushi.
Ɗakinta ta shiga ta kulle ƙofa tare da zama kan gadon. Ɗan kwalinta ta cire cikin damuwa.
"Anya yana da imani kuwa?" Ta furta cikin takaici yayin da take ji kamar ta je ta rama mata.
A mota kuwa hankalinsa ya tashi matuƙar gaske! Ganin Marwana. Ya tabbata duk inda ta fito ta iyayenta ko mijinta suna da kuɗi.
Harararta ta gefen idanu yake yi cikin jin haushinta.
"Wallahi kin ji na gaya miki matuƙar kika ƙara kula yarinyar nan, sai na yi mugun saɓa miki, saboda daga ganin yarinyar nan, irin matan da suka gagari iyayensu ne."
Shiru ta yi ba ta tanka masa ba hawaye suke zuba a ƙuncinta.
"Wa ya sani ko 'yar lesbian ce, saboda irin wannan kyautar da ta yi miki in dai ba wani abu take buƙata daga gareni ba, to babu abin da zai sanya ta yi miki shi."
Nan ma ba ta ce masa kanzil ba, domin ba ta da abin da za ta ce.
Da suka koma gida wanka ya yi sannan ya fice daga gidan.
Tun da ya fita take kuka kamar za ta haɗiye ranta. Ta yi kukan har ta ji babu daɗi. Dana sani kuwa ya fi cikin kwanon masaki.
Ganin kukan ba shi ne mafita ba, ya sanya ta share hawayenta ta ɗauki qur'ani tana karantawa.
Sallamar Maman Muwadda ya katse mata karatun da take yi.
"So kike ki kashe kanku Nasreen? Dukan da yake miki bana hankali bane. Wallahi da na zauna da kalan mijinki gara na shiga duniya."
"Ba ni da zaɓi ne, zaman aure a shi ya fi mini kwanciyar hankali."
Ta furta tana kuk,a wanda ya sanya ta yi fushi ta bar mata gidan.
Cikin dare Marwana ta kasa bacci. Da ta rintse ido sai ta ga fuskar Nasreen tana kuka. Miƙewa ta yi ta zauna a tsakiyar gadon.
Tun bayan da ta dawo gida take ta neman layin ta amma a kulle.
Na damu da na ji halin da kike ciki Nasreen. Don Allah ki buɗe wayarki.
Ta tura mata tsaƙo kamar haka sannan ta koma ta kwanta.
Washegari da safe ta shirya don ta je makaranta.
Nasreen kamar ba za ta je makarantar ba, amma saboda gidan da ya yi mata ƙunci ya sanya ta shirya ta tafi.
Bayan ta ka Raihan makaranta ta wuce school.
Ganin ta ya sanya taso da sauri har tana tuntuɓe.
"Wallahi juya sai dai bacci ɓarawo ya sace ni. Nasreen, ban yi miki kyauta don ki samu matsala da mijinki ba. Na so ki bani da ma na yi masa bayani, watakila da ya fahimci nufina."
"Ba zai fahimce ki ba, ina son ki yi hakuri mu yanke alaƙarmu, saboda ya yi mini kashedi mai girma, daga ciki har da yanke igiyar aurenmu"
Zare idanunta ta yi sai hawaye shar suka wanke mata fuska.
"Har cikin raina na ke jin ki kamar 'yar'uwata, amma matuƙar zan zamo sanadin mutuwar auren ki zan yi nesa dake har abada, amma ki sani ya kamata ki gyara zaman auren ki da mijin, saboda mijinki bai yarda da ke ba, matukar da ace akwai yarda a tsakanin ku ba zai yi miki wannan dukan ba. Ina jiye miki gaba matuƙar ba ki gyara zaman aurenki ba, za ki yi dana sani a lokacin da ruwa ya ƙare wa ɗankada. Ina miki fatan alkhairi da zama mai ɗaurewa a rayuwar aurenki." Ta juya za ta tafi sai kawai ta fashe da kuka.
Mamakin kukan da take yi ya kamata ƙwarai. Ita kanta kukan take so ta yi. Ji take kamar ta ɗora hannu aka ta yi ta ihu, tana fadawa mutane abin da ke damunta, watakila ta samu rangwame na raɗaɗin da zuciyarta take yi."
Dama mai shirin kuka ne, aka jefe shi da kashin awaki, sai kawai ta fashe da kuka tare da rungume tana kuka.
"Ina cikin wani hali na fi buƙatar na mutu da rayuwar da nake yi. Duniya ba ta maraba da ni, kullum cikin kurɓar ruwan baƙinciki nake a cikinta. Zaman aurena ya zaman mini tamkar zaman gidan yari ko ƙangin bauta. Mijina bai damu da ni ba." Ya duke ni ya zagi iyayena, sannan babu yarda a tsakanin mu abincin da xanci baƙinciki yake ya bani."
"Innalillahi wa inna ilahir raju'un! Kuma kike zaune da shi Nasreen? Da kyanki da ilmin ki kika zauna baƙincikin ɗa namiji zai kashe ki? Dubi yadda kika rame kika koma duk adalilin ɗa namiji. Wallahi na tabbata kina ɗauke da ciwon depression."
"Ya zan yi? Zaman aure a shi ne kawai gatana da 'ya'yana."
"Ba ki da iyaye ne?"
Murmushin mai ciwo take tana kallonta."Wannan shine dalilin da na gaya miki zaman aure a shi ne kawai gatana. Mahaifina da shi da babu a cikin rayuwata duk ɗaya."
Zare idanunta ta yi tana mamakin abin da ta faɗa. A iya saninta iyaye sune ginshikin da kuma jigo ga 'ya'yansu. Matuƙar za ta furta haka kenan bai kasance bango abin jingina ba?
"Na san za ki yi mamakin dalilin da ya sa ya na ce miki haka. Mahaifina shi ne dalilin da rayuwata ta koma haka. Sam bai damu da rayuwarmu ba.
"Ina buƙatar na ji rayuwarki. Please mu je wani guri ki bani tarihin rayuwarki." Kama hannun ta ta yi suka shiga mota.
"A halin da na ke ciki ba zan iya ba ki labarina ba, amma na yi alkawarin zan sanar da ke wani lokacin."
Kallonta ta yi cikin tausaya jin abin da ta ce. Jakarta tana kallon Musaddik da yake son ya yi kuka. Hannu ta sanya ta ɗauke shi tana masa wasa.
"Shi kenan, zan jira ki duk lokacin da kika shirya. In sha Allahu zan samu Faruk na yi masa bayani..."
"Ba zai saurare ki ba."
"Zan jaraba saboda ya kamata na fiddaki cikin zargin da yake miki."
Ba tare da ta ce mata komai ba suka fara tafiya.
A maimakon su tafi makaranta su tafi gida ta biya da ita shopping mall ta yi musu soyayya sosai. Mamaki ya kamata ganin yadda ba ta jin ƙyashin kashe mata kuɗi.
Kamar yadda ta yi mata alkawari suka samu lokacinta ba ta labarinta. Mamaki sosai Marwana ta yi. Kallonta take cikin tsananin mamaki.
"Nasreen rabuwa da Faruk shi ne alkhari, saboda dole watarana za ku rabu."
"Bana sonsa na aure shi, amma ba ni da zaɓi saboda yarana. Bana son su samu tarbiyar wata. Uwa ita ce ginshiƙi ga rayuwar 'ya'yanta."
"To saboda yara za ki kashe kanki? Kina da tabbacin in kin ƙi rabuwa da shi zai zauna da ke? Nasreen Allah ba ya ɗorawa bawansa abin da ba zai iya ba, dai sai mu ɗorawa kanmu. Akwai buƙatar ki natsu ki yi tunanin makomar rayuwarki da Faruk. Ki rabu da shi zan ɗauki nauyin karatunki, sannan in kin gama zan sanya Ya Damir ya ba ki aiki a campaninsa. Rayuwarki za ta yi kyau za ki taimaki iyayenki, amma a haka wallahi matuƙar ba ki samar da kanki mafita ba za ki yi dana sani."
Sosai take kallonta yayin da maganganun ta duke yin tasiri a zuciyarta, amma kuma da ta suna a magantarta, dai ta ga zama da Faruk ya fi kan ta ɗora musu ɗawainiiyarta babu dangin iya ba na Baba."
"Na gode da ƙaunar da kike mini. In Sha Allahu zan ci gaba da addu'a, domin duk wanda ya roƙi Allah zai kawo masa mafita. Zan ci gaba da zama da Faruk saboda yarana."
"To shikenan tun da haka kika ce. Allah ya kaimu mu kammala karatun mu zan saya Yayana.ya ba ki aiki."
Kama hannunta ta yi ta riƙe jin abin da ta ce."Haƙiƙa kin wuce matsayin ƙawa a gare ni sai dai 'yar'uwa. Ina fatan Ubangiji ya bar mu tare."
"I will do anything for you Nasreen. Soyayyar ki Allah ya saka mini, saboda yadda na ke jin ki tamkar Hajiya ta haife ki."
Daga nan gida suka wuce sai da ta kai ta har unguwarsu, sannan ta yi parking don ta sauka."Zan yi masa magana domin ba zan iya jure ganin yana dukanki ba, zan gwada watakila ya daina."
Fita ta yi daga motar sanna ta leƙo ta windon motar tana kallonta ta ce,"To shikenan, tun da kin na ce sai na yi miki fatan alkhairi Allah ya sa ya daina, saboda Ni kaina zan so na samu 'yanci a gidan aurena."
"Zan gwada kuma zai daina in sha Allahu."
"Ina fatan haka sahibata." Ta ce tare da ɗaga mata hannu.
Makaranta innsha Allahu yau zan yi posting safe da yamma a cigaba da surbubuɗo comments ❤️❤️❤️❤️💃💃💃💃
WASU MAZAN" Labari ne a kan rayuwar Nasreen wacce ta haɗu da jarrabawar rayuwa. Nasreen tasha jarrabawa a rayuwar aurenta da Faruk. Wanda faruwar haka yana da nasaba da rashin bango mai kyau abin jingina da ba ta samu ba, wato mahaifinta da ya kasa cike gurbin da ya kamata ya cike. Rayuwar aurenta madubi ne ga wasu matan da suke shan wahala ko rashin sama lafiya da mazajensu. Duk da ƙoƙarin su na son su zauna a ɗakinsu don gudun ZAWARCI da kuma fargabar rayuwar 'ya'yansu yadda za su kasance in ba su, da kuma fargabar mijin da za su aura bayan aurensu ya mutu. Wannan dalilin ya sanya ta jure zaman gidan aurenta don ta samu ta rayu da 'ya'yanta. Sai dai ƙaddara ba ta wuce mutum dole afkuwarsa tabbataciyace tun da Ubangiji ya tsara tun a Lauful Mahfuz. Duk yadda ta so ta kaucewa ƙaddara faruwar hakan ya ci tura. Ta shiga cikin tsananin rayuwa da fidda tsammani. Ta haɗu da wacce ta kira hasken da ya haska fitilar rayuwarta, amma sai dai a garin ta kawo hasken, ta sanya rayuwarta cikin tsarƙaƙiyar da ya zama tsarƙen da ya jefa rayuwar ta cikin tsarƙaƙiyar soyayyar mai kama da ƙiyayya. Sai dai Ubangiji ya faɗa a cikin littafinsa mai tsarki cewar,"Duk tsakani, akwai sauƙin." Haka ta kasance a lokacin da ta fidda tsammani a cikin rayuwarta, sai Allah ya kawo haske mai walƙiya da ya canza tubalin ƙaddararta da ga duhu zuwa haske. Ta kuma sha ruwan zuman da take tunanin ba za ta taɓa shan sa ba, bayan ta kwankwaɗi na maɗaci, wanda ya gauraye dukkan rayuwarta har ta fidda tsammanin shan zuma. A cikin littafin akwai wata irin soyayya mai tsuma zuciya. Masoyana karku sake a baku labarin littafin "WASU MAZAN" Domin na wasa ƙwaƙwalwa ta na zauna na tsara shi ta yadda zai sa ya ku tausayi da nishadi har ma ya zama darasi. Ku kasance masu bibiyar littafin domin jin yadda tubalin ginin rayuwarta zai kasance. Kun san dai alkalamin Jamila lawal Zango ba ya rubuta shirme.
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/KusyXgwh9wEAHDTn6dzD43
*WASU MAZAN*
NA
*JAMILA LAWAL ZANGO*
*FIRST CLASS WRITERS*
MARUBUCIYAR
Sakacina ko halin maza
Kura da fatar akuya
Ranar wanka...
And now
Wasu mazan
08144072423
PAGE 11
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
Kamar yadda ta yi mata alkawarin cewar za ta same shi. Har ofis ɗin shi ta je. Farouk zaune da waya a hannunsa yana chatting da amaryarsa to be.
Tsaddaden murmshi yake saki fuskarsa ɗauke da annuri. Cikin nishaɗi yake sakin murmushi yana jujjuyawa kan kujerar da irin mai juyawa nan.
Da ya ga chatting ɗin ba zai gamsar da shi ba, kiran wayar ya yi. Daga ɓangaren da ya kira, aka saki wani lallausar murmushi bayan ta yi sallama.
Shi ma murmushin ya sakin mata, yana jin kamar ya zaro ta cikin wayar.
"Ni fa gani na ke kamar da wasa sanya ranar da aka yi mana. Wallahi na zaƙu na shigo gidanka a matsayin mata, na nuna maka tsantsar kula, domin uwargidanka sai ta raina kanta. In ban da shashanci ace ta samu miji kamar ka, kuma ta kasa kula da kai?"
"Hmmmmh! Ni kaɗai na san halin da na ke ciki, saboda matata shashasha ce. Wallahi halin da na ke ciki, da zan gaya miki sai kin tausaya mini. Sam ba ta iya gyara kanta ba, kuma ba ta san yadda ake tattashin miji ba."
"Ba ka da matsala Hubbyna, domin ni zan share maka hawayen da matarka ta kasa share maka."
"In har kika ɗauke mini damuwata, ni kuma zan zamo miki miji abin alfahari, saboda Nasreen sai ta raina kanta. Zan barta da yara ta yi ta fama da ɗawainiyarsu. Ni kuma na kula da ke sarauniyar zuciyata."
"Duk abin da kake so ka samu babyna. Za ta sha kallo, don babu kalar soyayyar da ba zan yi maka ba, ita kuwa sai ta yi ta zama da gidadancinta."
"Kar ki damu masoyiyata, zamu ci duniyar rayuwar aurenmu da tsinke."
Wayar suka ci gaba da yi da musayar kalamai. Kalaman da ya kamata da wanda bai kamata ba, suka rinƙa faɗa wa junansu. Daga bisani suka yi sallama, bayan ta yi masa alkawarin turo masa da zafafan hotunan da ta ce masa ta ɗauka.
Suna gama wayar ta tura masa da hotunan. Kallon hotunan yake yi yana murna da ya samu mace wayayyiya, ba irin matarsa da ba ta san komai ba sai gidandanci.
Yana cikin kallon hotunan, Marwana ta ƙwanƙwasa ƙofar cikin fargaba, don ba ta san yadda za su kwashe ba.
Da sauri ya amsa tare da ba da umurnin shigowa.
Cikin siriyar sallama ta shigo cikin ofishin. Farouk ya miƙe bayan ya amsa sallamar da sauri yana kallonsa.
Miyau ya haɗiya da ƙyar yana mata kallon ƙurulla. Idanu ya zuba mata kamar zai lasheta. A zuciyarsa tunani yake yi kamar ya taɓa ganinta.
"Ba ka gane ni ba ko?"
"Eh, wallahi amma kamar na taɓa ganinki." Ya ce mata cikin tashin murya yana mata wani kallo ƙasa-kasa.
"Da ma na yi tunanin ba za ka gane ni ba, saboda sau ɗaya ka taba ganina."
"Eh, gaskiya ba lailai na gane ki ba. Daga ina baiwar Allah? Saboda da kika shigo na ɗauka 'yan matan hurul ain ce ta faɗo duniya.
Haushi da takaicin abin da ya faɗa suka sanya ta murmushin dole." To ba ita ba ce, domin ni mutum ce kamarka." Ta furta a gajarce tana gyara zamanta.
"To ai dole mutum ya yi tunanin haka, saboda kyawu ki da zubin jikin ki."
"Ƙawar matarka Nasreen ce." Ta furta masa tana kallon sa jin abin da ya ce.
Lokaci guda fara'ar fuskarsa ta kau. Ƙara ɗauke fuska ya yi."Ok, mai ya kawo ki ofis ɗina?" Yadda ya yi maganar, ya sanya zuciyarta harzuƙa don sam ba ta da hakuri.
Faruk kuwa, ji ya yi ransa ya ɓaci matuƙa, domin ya ɗauka tarkonsa ya kama kurciya.
Ganin ya yi shiru, ya sa ya ta ƙara gyara zama ta ce,"Na zo kan kyautar da na yi wa matarka Nasreen?"
"Ke dakata! Ya katse ta yana faɗin haka sannan ya ɗora da cewa,""Nasreen matata ce kuma ina da ikon na zaɓa rayuwar da na ke son ta yi..."
"Ka yi haƙuri ba ni da nufin na yi kutse a cikin rayuwar ku, amma don Allah. Ka ji tsoron Allah, ka san cewa Allah yana ganin rayuwar da kuke yi kai da ita, kuma zaman aure ba zaman bauta ba ne. Wallahi ni na yi mata wannan kyautar, ba tare da ta
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 7 Chapter of 17