Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
masa sallama.Cikin izza ya amsa don ya ɗauki muryar. "Lafiya?" Ya ce mata a gimtse yana mamakin kiran Daurewa ta yi ta kawar da muguwar shawarar da zuciyarta take ba ta tana zugata kan ta danna masa ashar, a maimakon hakan sallama ta yi masa, wanda ya amsa kamar mai ciwon baki. "Na san ka gane ni matarka ce ba lafiya tana asibiti." "Ya za a yi na kasa gane ki uwar shishshigi." Ya ce mata yana girgiza ƙafafunsa. Ranta ya ɓace amma sai ta daure za ta yi magana ya riga ta."Ba ta da lafiya sai ta kasa kiran kowa, sai ke dangin dagiro?" "Faruk, don't provoke me. Nasreen tana cikin halin rashin lafiya ɓari ta..." "Ɓari me? A gidan uban wa ta yi cikin?" Tambayar ya yi matuƙar ba su mamaki da haushi, har bai san lokacin da zuciya ta cika shi ba ya gushe wayar ya ce,"Kai wane irin mara mutunci ne? Kana rayuwa da matarka kake tambayar ina ta samu ciki?" Jin muryarsa ya yi ta doki kunnensa "To ɗan iya! Kai kuma a dangin wa? Kuma ba zan tambaye ta ba, tun da ban san da cikin ba?" Ya yi dauriyar faɗin haka duk da cewar muryarsa ta firgita shi. "Kana tsoron Allah kuwa?Anya ka ɗauki aure a matsayin bauta, kana da sanin cewar Allah zai tambaye ka yadda ka riƙeta a ranar alkiyama" "A'a ba na tsoron Allah sai na ka. Kuma da kake mini tambayoyin nan kai a zuwa? Ban san matata na da ciki ba, laifi ne na tambaya?" "Ban yi mamaki ba saboda ba ka da hankali, har za ka iya sanya ƙwanka ba tare da ka sani ba." Zuciyarsa ta tunzura jin bin da ya ce. Zaginsa ya fara yi, amma sai ya dakatar da shi ta hanyar cewa,"Ni ba jahili bane kamar ka. Matarka tana kwance a asibiti kuma jini ake so, don haka sai ka yi sauri ka zo ka bada jinin, saboda an nema babu kalar nata." "Kutumar uba! " Ya ji ya danna ashar. Yana mamakin abin da ya ce, sai kuma ya ɗora da cewa,"Wallahi ko mutuwa za ta yi ba zan bayar ba. Ina tsaka da cin amarci sai a iban mini jini?Wallahi uban kuturu ya yi kaɗan." Ƙit ya kashe wayar yana zagi. Kallon wayar suka yi cikin mamaki. "Marwana irin mijin da take aure kuma take zama da shi kenan?" "Ya za ta yi? Rayuwarta rana zafi inuwa ƙuna. Mahaifinta shi ma rayuwar sa babu dama. Ƴaƴanta daya shine kawai haskenta." "Kira shi ki sanar masa." Ya ce cikin ɓacin rai yana jin kamar ya zama hukuma ya hukunta shi. Cikin sanyin jiki ta danna kira. Ringing biyu ya ɗauka."Hello, ƙanwata, yanzu na karɓo cajin na ke shirin kiran ki." Gyaran murya ta yi ta ce,"Ba ita ba ce ƙawarta ce. Muna asibiti ta yi ɓari." Salati ya sanya jin abin da ta ce,"Don Allah wane asibitin?" Kwatance ta yi masa ya kashe wayar. "Ƴaƴanta yana so ta shi ne gatanta." Shiru kawai ya yi ba tare da ya tanka ba. Bai ɗauki tsawon lokaci ba ya ƙara so. Hankalinsa a tashe ya shigo cikin asibitin. Mamakin kyaunsa asibitin ya kama shi, domin ya dai san asibitin, amma bai taɓa shiga ba. Kallonsu ya yi yana mamakin kyawunsu da haɗuwarsu. A ransa yake godiya ga Allah da ya haɗa ta dasu. "Tun jiya take asibitin nan ta kira wayarka a kashe, sai ta kira ni. Ta yi ɓari jini ake so kuma ba su da jini. Shi ne suke son a samu wanda za a ɗiba. Ta gaya mini Faruk kalar jininsu ɗaya." Kansa ya ɗage domin kalar jininsu ba ɗaya ba."Yanzu mai Faruk ɗin ya ce?" Ya yi mata tambayar duk da ya san ba zai yarda ba. Cikin takaici ta ware hannunta ta ce,"Ya ce ba zai bayar ba, ko mutuwa za ta yi." "Hhmmmm!" Ya ce dama ya san za a rina, an saci zanin mahaukaciya. Ɗakin da take ya shiga. Ganin haka suke bishi har da Damir. Damir ya shiga don ya ɗauki Little Marwana su koma gida. Don in bai bar asibitin ya yi baz zuciyarsa za ta iya harzuƙa ya sanya a ɗaure sa. Yana ƙarasawa kan gadon ya hau ya kama hannun ta."Ƙanwata ashe ba ki da lafiya." Kuka ta saka tare da kama hannunsa."Yanzu ina za a samu jinin?" Jin bin da Marwana ta ce sai ta kalle ta. "Faruk ya ce ba zai bayar ba ko?" Shurin da ta yi ya tabbatar mata da hakan. Kuka take yi sosai. Damir ya ɗauki Marwana zai fita saboda kukan damunsa yake yi. A rayuwar sa ya tsani kukan mace, wannan dalilin ya sanya Batula ta gane lagonshi take masa kuka a duk lokacin da take son ya amince da wata buƙata da take da shi. Hannunsa Marwana ta kamo tana kallonsa. Juyowa ya yi yana kallonta ba tare da ya ce mata komai ba. "Jininku iri ɗaya ne, don Allah ka taimaka a ibi naka.." "What?" Ya ce yana zare idanunsa yana kallonta, sai kuma ya ɗora idanunsa kan nata da ta yi ƙasa jin abin da ta ce. Fita kawai ya yi yana girgiza kansa, ba tare da ya ce komai ba. Shi kansa ya rasa gane dalilin da ya sanya shi ƙin amincewa. "Zan je na nemo jinin ko kuma wanda yake da kalar jinin. Mun gode da ƙaunarku gareta." Ahmad ya ce tare da miƙewa. Wai readers kun san me? Labarin WASU MAZAN kamar yanzu aka fara it is just beyond predictable. This part that we are is just like the introduction part. Ku ci gaba da bibiyarsa kuna rikirkitani da zafafan comments akwai ƙura a cikin labarin. WASU MAZAN" Labari ne a kan rayuwar Nasreen wacce ta haɗu da jarrabawar rayuwa. Nasreen tasha jarrabawa a rayuwar aurenta da Faruk. Wanda faruwar haka yana da nasaba da rashin bango mai kyau abin jingina da ba ta samu ba, wato mahaifinta da ya kasa cike gurbin da ya kamata ya cike. Rayuwar aurenta madubi ne ga wasu matan da suke shan wahala ko rashin sama lafiya da mazajensu. Duk da ƙoƙarin su na son su zauna a ɗakinsu don gudun ZAWARCI da kuma fargabar rayuwar 'ya'yansu yadda za su kasance in ba su, da kuma fargabar mijin da za su aura bayan aurensu ya mutu. Wannan dalilin ya sanya ta jure zaman gidan aurenta don ta samu ta rayu da 'ya'yanta. Sai dai ƙaddara ba ta wuce mutum dole afkuwarsa tabbataciyace tun da Ubangiji ya tsara tun a Lauful Mahfuz. Duk yadda ta so ta kaucewa ƙaddara faruwar hakan ya ci tura. Ta shiga cikin tsananin rayuwa da fidda tsammani. Ta haɗu da wacce ta kira hasken da ya haska fitilar rayuwarta, amma sai dai a garin ta kawo hasken, ta sanya rayuwarta cikin tsarƙaƙiyar da ya zama tsarƙen da ya jefa rayuwar ta cikin tsarƙaƙiyar soyayyar mai kama da ƙiyayya. Sai dai Ubangiji ya faɗa a cikin littafinsa mai tsarki cewar,"Duk tsakani, akwai sauƙin." Haka ta kasance a lokacin da ta fidda tsammani a cikin rayuwarta, sai Allah ya kawo haske mai walƙiya da ya canza tubalin ƙaddararta da ga duhu zuwa haske. Ta kuma sha ruwan zuman da take tunanin ba za ta taɓa shan sa ba, bayan ta kwankwaɗi na maɗaci, wanda ya gauraye dukkan rayuwarta har ta fidda tsammanin shan zuma. A cikin littafin akwai wata irin soyayya mai tsuma zuciya. Masoyana karku sake a baku labarin littafin "WASU MAZAN" Domin na wasa ƙwaƙwalwa ta na zauna na tsara shi ta yadda zai sa ya ku tausayi da nishadi har ma ya zama darasi. Ku kasance masu bibiyar littafin domin jin yadda tubalin ginin rayuwarta zai kasance. Kun san dai alkalamin Jamila lawal Zango ba ya rubuta shirme. FOR WHATSAPP: 07072971093 CALL: 00814407242 Follow the 𝑊𝐴𝑆𝑈 𝑀𝐴𝑍𝐴𝑁 channel on WhatsApp: https://whatsapp.com/channel/0029Vb5xqsd72WTrg772JU2P *WASU MAZAN* NA *JAMILA LAWAL ZANGO* *FIRST CLASS WRITERS* MARUBUCIYAR Sakacina ko halin maza Kura da fatar akuya Ranar wanka... And now Wasu mazan 08144072423 Na buɗe wani group wancan ya cika mai son shiga ya bi link ɗin nan👇👇👇👇👇 https://chat.whatsapp.com/E9kBdqbI0Yf2hsCTaxPVjg PAGE 15 BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM "What?" Ya ce yana zare idanunsa yana kallonta, sai kuma ya ɗora idanunsa kan nata da ta yi ƙasa jin abin da ta ce. Fita kawai ya yi yana girgiza kansa, ba tare da ya ce komai ba. Shi kansa ya rasa gane dalilin da ya sanya shi ƙin amincewa. "Zan je na nemo jinin ko kuma wanda yake da kalar jinin. Mun gode da ƙaunarku gareta." Ya ce tare da miƙewa. Damir da ya shiga cikin mota sai ya kasa tuƙawa. Rintse idanunsa ya yi. Yana jin wani iri saboda hana jinin da ya yi, amma ya zai yi ya ba da jininsa a sanya wa matar wani? Bayan shi mijin da yake morarta ya ƙi ba da na sa? Sakarcin Marwana ya gani da ta yi masa tambayar. Ta san yadda yake matuƙar shan wahala in har aka ibi jininsa. Baya manta wahalar da ya sha a lokacin da aka sanya wa mahaifinsa jininsa. Sai da ya suma har sau uku. Yana da wadataccen jinin, amma duk lokacin da aka ina ba ya sha ta daɗi. Kunna motar ya yi, yana jin ba zai iya wannan taimakon ba, amma kuma sai ya ji ya kasa fara tuƙa motar. Cak ya tsaya yana tunani. Tsintar kansa ya yi, da buɗe motar ya koma cikin asibiti. Saura kaɗan su ci karo da Ahmad da ya fito cikin tashin hankali. Yana tunanin inda zai samu jini. Naira dubu biyu ya tashi da ita, kuma ya ba su Mama su yi girki da shi. Matsawa ya yi yana kallonsa. Marwana ganin ya dawo sai ta ƙarasa gurinsa."Na yarda a ibi jinin." Ya ce mata cikin murya mai sanyi. Faɗawa jikinsa ta yi cikin farin ciki. "Mun gode Yaya Allah ya biya ka." Ba tare da ya amsa ba ya nufi inda ake iban jinin. Ita da Ahmad sun kasa magana, sai kallonsu suke yi cikin mamaki. A lokacin da aka sanya masa allura aka caka masa inda jinin zai rinka zuba. Rintse idanunsa ya yi. Yana jin yadda zafin ke shiga ƙwaƙwalwarsa. "I will do everything for you little sis." Ya ce tare da rintse idanunsa. Ba tare da ya motsa ba har aka gama iban jinin. Yana kwance sai da ya tabbatar da ya huta ya miƙe. Sai bayan an kammala iban jinin, sai tsoro ya kamata ganin yadda ya koma. Tunawa ta yi da yadda yake komawa in ka gama. Tsoro da firgice ya sanya ta kusa hauka. Sam ta manta, son ƙawarta da tausayi sun sanya ta manta halin da ɗan'uwanta zai shiga." Ganin yadda idanunsa suka birkice sai ta kalle shi, tare da kama shi da sauri cikin rawar murya ta buɗe baki ta ce,"Ya Da..." Hannunsa ya ɗaga nata yana jin yadda kansa ke juyawa, abubuwa na rabuwa nasa gida biyu."Kar ki damu son ƙawarki ya sanya kika manta da halin da yayanki zai kasance and I will do anything for you." Kallonsa ta yi, yana murmushi daidai lokacin da ya shiga ciki. Abin da ya ce mata kamar magana ya daɓa mata. "Ya Damir, wallahi na manta ba ka sha ta daɗi, in har aka ibi jinin ka." Murmushi kawai ya y, yana jin yadda kan shi ke juyawa, komai na rabuwar masa gida biyu. "Don Allah ka bari na kai ka." Idanunsa ya buɗe ya ɗora kanta sai ya ga kamar uku-uku yake ganinta, amma saboda ƙarfin hali ya ce,"Don't Bother ki kula da ita." Shiru ta yi tana fargabar Allah ya sanya kar wani abu ya faru da shi, domin Allah kawai zai raba ta da Hajiya lafiya. Tana kallon yadda yake tuƙin cikin mutuwar jiki. Ta san abinda lafiya, in har ya ce zai yi, to dole sai ya yi. Wannan dalilin sa ya ba ta ja da tsawo ba. Ganin ya fita daga harabar asibitin, sai ta shiga ciki don ta yi mata sallama, kuma ta yi mata transfer na kuɗi, ko za a bukata kafin ta dawo. A lokacin da ta shiga tana kwance a cikin zuciyarsa, tana girmama karamci irin na su. Tana kwance idanunta rufe hawaye yana ganganrowa Ahmad yake mata wa'azi yana kwantar mata da hankali. "Zan je gida na dawo. Na yi miki tranfer na kuɗi a wayarki, ko ana son wani abu kafin na dawo." Kallonta suke yi sun kasa magana."Mun gode Allah ya ƙara buɗi." Ahmad ya ce mata. Ita kuwa sai hawaye tana kallonta. Ƙarasawo ta yi kan gadon ta shafa kanta."Ki kula da kanki kuma ki ci abinci. Zan je gida na yi wanka na dawo." "Na gode Allah ya saka da alkhairi." "Don't mention." Ta ce tare da juyawa ta fara tafiya. Kallo suka bita da shi har ta fita. A hanya yana tuƙi yana haɗa hanya. Da ƙyar ya samu ya isa gida. Ko parking bai gama ba, ya samu ya ja hannun Little Marwana suka shiga cikin gidan. Batula ta taso ta tare shi tana faɗin,"Ka daɗe fiye da yadda na yi tsammani." Ajiyar zuciya ya ja ya kalle ta cikin rashin hayyaci. Tsoro ya ba ta ganin yadda idanunsa suka dawo. "Lafiya mai ya faru da kai?" Sharab ya zauna kan kujera yana saukar da numfashi. "Ba komai." Ya ce mata yana kallonta. Tsoro sosai ya ba ta ganin yadda ya koma."No, akwai abin da ya faru." "Na ce miki ba komai..." Ya fara maganar cikin fushi zai mike, amma sai jiri ya kwashe shi ya fadi ƙasa. Ganin haka ta sa ya ihu, tana girgiza shi tana kiran sunanshi, amma ina idanunsa sun ƙafe. Jin ihu ta ya sanya Baba Azumi ta sheƙo don ta ɗauka haihuwar ce ta taso. Ganinsa kwance babu numfashi tana girgiza shi sai ta ruga waje ta kira maigadi. Da ƙyar suka sanya shi a cikin mota. Wayarta ta ɗauka ta kira Hajiya ta sanar mata suna asibitin. Hankalinta ya tashi matuƙar gaske! Ta shiga tambayarta. "Lafiya mai ya faru? Na kira shi ya ce mini yana asibiti, zai zo gidana in ya dawo. Dama ba shi da lafiya ne? Saboda da na kira shi kamar ya ce mini dubiya za shi." Jin tambaye da take mata cikin ruɗani ya sanya ta ce,"Ni ma ban sani ba, ya dawo mini kamar ba shi da lafiya sai kawai ya faɗi." Ta karashe maganar cikin kuka. "Ina Marwana?" "Tana asibiti ƙawarta ce babu lafiya shi ne suka kaita tun jiya da daddare." "Ƙawarta?" Ta yi mata tambayar cikin tsananin mamaki, tana tunanin wace ƙawar ce. "Eh, ita da shi suka kaita asibiti don ta yi ɓari tana zubar jini." Kanta ya kawo wuta ta tuna da Nasreen. "Ok, ma za ku kaishi asibitin gani nan sai na ji abin da ya faru." "To Hajiya sai kin zo." Ta ce tare da kashe wayar tana kallonsa. Kuka take yi sosai tana girgiza shi. Sun shiga cikin asibitin ta buɗe ido sai kuma ya fara jijjiga ya ƙara sumewa. Tsananin tashin hankali ya ƙara kamata. Dafe cikinta ta yi da yake juyawa. Marwana tana tuƙi zuciyarta na bugawa na halin da yake ciki. Dana sanin iban jinin ya fi kwando masaki. Ta san yau Allah kawai zai raba ta da Hajiya, domin ko mai za ta ce mata ba za ta fita ba, daga ƙarshe ƙalubantatarta za ta yi cewar ƙawa tafi shi matsayi, da har zai sanya halin da take ciki ya sa ya ta manta halin da zai shiga. Tana ƙoƙarin karya kwanar gidansa kiran Hajiya ya shigo. Saboda tsananin tsoro har parking ta yi kafin ta ɗaga wayar. "Marwana?" "Na'am," Ta masa cikin rawar murya jin yadda ta kirata. "Mai ya samu yayanki ya sume kuma wace ƙawarki kuka kai asibiti?" Tambayar da ta yi mata ya tsinkar da zuciyarta."Ya sume?" Ta yi mata tambayar cikin tsananin tashin hankali. "Ya ina tambayarki kina tambayata? Kina ina ne?" "Um, eh, ina kwanar shiga gidansa." Ta ba ta amsa cikin rawar murya. "To ma za ki dawo asibiti don yana can sai ki yi mini bayani." Ta ce tare da kashe wayar. "Innalillahi wa inna ilahir raju'un! Na shiga uku!" Ta furta bayan ta yi jifa da wayar ta yi reverse ta nufi asibitin. A lokacin da suƙa karasa da shi aka kai shi asibitin. "Innalillahi ba yanzu muka ibi jininsa ba?" "Jini?" Batula ta tambaya tana zare ido. Duk da cewar, ba ta san cewa yana shiga cikin yanayin ba in har aka iba, amma ta yi mamakin abin da ya sanya aka iba. Tana ƙoƙarin tambayarsa daidai lokacin da Hajiya ta karaso. "Ina Damir ɗin mai ya faru da shi?" "Ban sani ba yana ciki likitan dai ta ce mini jininsa aka..." "Ji mene ?" Ta yi mata tambayar tamkar zata zauce. Ganin ta firgita ya santa ta ce,"Eh, jininsa aka iba haka suka gaya mini." "Saboda me aka ina mai aka yi da shi?" Ta yi tambayar daidai lokacin da Marwana ta shigo, jin tambayar da take yi wa likitocin ta santa ta tsaya tana zare ido. "Wata petien da suka kawo da daddare wacce ta yi ɓari aka sanyawa jinin Damir?" Mamaki ya cika Hajiya ta juyo tana kallon Marwana da ta gama tsurewa."Petien? Wai mai yake faruwa Marwana? Ko kun fara yin abu ba tare da na sani ba?" Daurewa ta yi cikin rawar murya ta ce," Ƙawata ce Nasreen wacce na gaya miki tana samun matsala.da mijinta. Ta yi ɓari kuma ya yi sabon auren ya tafi ba tare da ya kula ta ba. Shine ta kira ni ta gaya mini. A daren muka je muka ɗauko ta. Yau likita ya gaya mana sai an ƙara mata jini. Mun kira mijinta ya ƙi zuwa shi ne na roƙi Yaya ya ba da jininsa, tun da kalar jininsa take da shi." Kau ta ji ta wanke mata fuska da mari."Ashe shashasha ce ke? ba ki da hankali. Saboda wata sai ki nemi kashe ɗan'uwanki?" Kuka take yi sosai cikin muryar kuka ta ce,"Hajiya ki gafarce ni wallahi na manta cewar yana shiga cikin wannan yanayin." "Saboda me za ki tuna, tun da wata banza can ta fi shi matsayi." Ta yi mata maganar tana hararar ta Matsawa ta yi zata kara marinta, daidai lokacin da likitan ya ce su shiga ɗakin da yake. Batula da ba ta a cikin hayyacinta jin an ƙarawa wata mace jinin mijinta. Idanun ta suka rine da kishi. Ranta ya ɓaci laifinsu ta gani, domin in har da bai amince ba, babu yadda za a yi a iba. Tuna waya da laptop ɗin da ya siya mata wanda sai Marwana ta gaya mata da suna hira, amma bai taɓa gaya mata ba, duk da cewar sun yi alkawarin ba za su rinƙa ɓoyewa junansu komai ba. "Son matar aure yake yi?Ta yi wa kanta tambayar cikin tsananin tashin hankali! Sai kuma ta ƙara tambayar kanta da cewa," Wannan dalilin ya sanya har ya ɗauki yaranta suka kwana a gidansa, kuma ya kasa bacci ya rinƙa kula da su. Why mijina? Mai ya sa za ka yi ƙoƙarin sanya na daina yadda da kai" Ta ji zuciyarta ya yi mata tambayar da har sai da gabanta ya faɗi. Rintse idanunta ta yi, tare da fita cikin ɗakin zuwa inda ta ji an ce an kwantar da ita. Nasreen tana kwance har yanzu hawaye yake bin ƙuncinta. Kamar yadda ta ga 'ya'yanta dama ba ta yi tunanin mummuna ba ce. Tana kwance tana rintse idanunta har ta gana kallonta ba tare da ta san ta shigo ba. Fita ta yi zuwa cikin ɗakin da yake kwance. Kansa ya dafe yana kallonta sai kuma ya ƙara suma. "Wallahi Marwana in har kika yi sanadin da na rasa Damir sai kin gwammce kin bi shi lahira." Kuka take yi tana girgiza shi tana kira sunasa"Yaya ka tashi don Allah Karka mutu." Hajiya fita ta yi da sauri, zuwa ɗakin da Nasreen take kwance. Ganin haka ya sa ya Marwana ta bita."Don Allah Hajiya kar ki tozarta su, wallahi ba su da laifi kan lamarin laifine. Don Allah kar ki yanke ƙawancen da muke fatar mutuwa kawai za ta raba shi." "Ko mahaifiyarki ce sai na wulaƙanta ta." Da sauri Nasreen ta buɗe ida ita jin abin da matar take cewa.Ahmad shi ma miƙewa ya yi yana zare ido. "Ke ce aka ibi jinin ɗana aka sanya miki ko? Wallahi in har ya mutu sai na ɗauke ki daga ke har dangin ki har sai igiya ta yi rara." Jin abin da ta ce hankalinsu ya tashi. Suna kallon Marwana da take kuka cikin dana sani. Ta yi ninyar alkhairi sai ga shi ya koma ya zama tsiya. Ba ta ƙara shiga tashin hankali ba sai da ta ji Hajiya tana musu zagin fitar arziki. Ta rintse idanunsa cikin kuka ta kama hannunta. "Ki hukunta ni wallahi bata da laifi." Kau ta ƙara kaureta da mari."Ina nan zuwa gunki dama ba kyale ki zan yi ba." Batula ce ta shigo cikin ɗakin tana haɗa hanya, Saboda kishi da ya rufe mata idanu ba ta gani. Kan gadon da take kwance ta ƙara da tana kallonta cikin tsanannin tsana Tun da take a rayuwarta, ko 'yan mata ba ta taɓa ganin Damir ya kula su ba, sai matar aure wacce take talaka? Kai ina akwai lauje cikin naɗi! Anya ba asiri suka yi wa mijina ba, saboda ta samu ta kashe aure ya sake ta?" Ire-iren waɗannan tambayoyin suka cika mata zuciya, tare da makantar da ita, har ta kasa tuna waye mijinta da abin da zai aikata. "Banza jaka da aurenki kike bibiyar mijin wata, har a rasa jin da za a sa ya miki sai na mijina, wato ga ki mai iya asiri kin yi masa asiri ya zama miki bita zaizai don ki shiga cikin ɗaula ko?" Tsananin mamakin abin da ta furta, ya sanya ta ji tamkar an ɗora mata dutsen dala. Wasu irin zafafan tagwayen hawaye suka sauka a ƙuncinta. Zare idanunta ta yi tana kallon Batula jin abin da ta ce. Hakan ya tabbatar mata da ita ce matarsa. Kalaman ta suka tayar da hankalin Marwana matuƙa gaya! Da sauri ta ƙarasa gabanta ta ce,"No Anty Batula, don girman Allah ƙarki wulaƙanta ta wallahi ba ta da laifi." Ta ƙarashe maganar cikin kuka ta haɗa hannunta tana roƙonta. Tureta ta yi cikin tsananin zafin kishi."Wallahi jinin nan ba zai ƙarasa shiga cikin jikin ki ba, domin ba zan bari jinin mijina ya yi yawo a jikin wata ba." Ta kai hannu za ta fisge sauran ragowar jinin da ya kusa karewa. Damir bayan ya farfaɗo, cikin dauriya ya fito daga cikin ɗakin da aka kwantar da shi, ya nufi inda aka kwantar da Nasreen hankalinsa a tashe. Ya san cewa yadda ran Hajiya ya ɓaci, sam ba za ta yi musu da daɗi ba. Sannan yana kallon irin kallon, da Batula take masa a lokacin da ta ji an ibi jininsa. Yana daidai ƙofar ɗakin ya ji mugayen kalaman da take faɗi. Kansa ya sara, da sauri ya dafa bango jin abin da take fadi."Innalillahi wa inna ilahir raju'un! Ya Allah taimako na yi sam zuciyata babu mugun nufi." Ya furta tare da shiga cikin ɗakin, daidai lokacin da ta yi nasarar fisgo allurar dake soke a hannunta. Wani irin ƙara ta saki tare da rintse idanunta, tana jin tsananin azaba, yadda yake shiga cikin ƙwaƙwalwarta. Da sauri Marwana da Faruk suka yi kan gadon, ganin za ta cutar da ita. Hankalinta ya gusar da tunaninta, burinta kawai ta hana jinin mijinta shiga. Ji ta yi an riƙe hannunta da sauri ta juyo.Ganinsa tsaye yana nishin wahala ya sanya ta fashe da kuka. "Jininka fa ka yarda aka sanya mata zai rinƙa yawo a jikinta?Ni da bana fatar ka kula wata mace, amma sai ka yarda ka bada jinin ka aka sanya mata. Matar auren kake so?" "Kau ya kaureta da mari jin abin da ta ce?" Kina da hankali? Ransa ya ɓaci! Idanusa suka firfito. Gabakiɗaya jijiyoyin jikinsa suka tashi."Kin san abin da kike faɗa? Taimako na zama sharri ne?" Riƙe gurin ta yi tana hawaye jin abin da ya ce. "Marina ka yi, da tsohon cikinka a jikina?" Ta faɗa tana dage ƙaton cikinta da yake barazanar fitowa a kodayaushe. "Kin cancanci fiye da haka Batula in har iya tsawon rayuwar da muka yi babu yadda a tsakaninmu." Dukansa ta shiga yi a ƙirji tana faɗin,"Ka gaya mini ta yaya zan yarda da kai, bayan ka aikata abin da ko a duniyar mafarki ba zan yarda ba?" Jikinsa ya yi sanyi duk

Chapter 11 of 17