Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya miƙe yana nuna ta da hannu. "Mai ya kawo ki gidan nan? Ki kin zo ki kashe ni ne?" Jin abin da ya ce yana nuna ta ya sanya ta tsaya cak, tare da ɓoyewa a bayan Marwana. "Ya Dam...." "Please shut up!" Ya daka mata tsawa yana faɗin haka sannan ya ɗora da cewa,"Kina tunanin akwai malaman da zai sa ya na ƙara kallonta da tausayi? Marwana a sanadinta na rasa matata wacce na ke so fiye da komai. Mai kike so ki gaya mini?" Shiru ta yi tana hawaye ganin yadda yake magana cikin tsawa tana zare idanu. "Fita da ita kuma ki gaya mata kar ta ƙara shigowa gidan nan, don ko a lahira bana fatar Allah ya haɗa fuskokinmu." Duƙawa ta yi cikin kuka ta ce,"Ka yafe mini na san ce...." "Kar ki ce mini komai! Bana son jin muryarki na tsane ki kar ƙi ƙara fatan ki haɗu da ni, domin kin ji na rantse miki haɗuwarmu ba za ta yi kyau ba." Jin abin da ya ce ta fisge hannunta cikin na Marwana ta juya za ta fita. Mama ta gyara murya ta ce,"Mun san cewa haƙuri da malamai ba za su taɓa goge abin da ya faru ba, amma don Allah mu zama musulmai masu yarda da ƙaddara, Allah ya riga ya ƙudurta a za ta mutu, kuma babu makawa sai ya faru." "Don Allah ku fita daga gidan nan don bamu buƙatar ganinku. Marwana ta haɗa zumunci kuma na yi mata gargaɗi in har ta ƙara zuwa inda take sai na yi mata baki." "Subuhanallahi! Haka ba zai faru ba. In sha Allahu Nasreen za ta yi nesa da ku. Mun gode da abin..." Maganarta ta katse sakamakon jifa da ƙaton gilas ɗin ɗakin da Damir ya yi. Kallonsa suka yi cikin damuwa. Kukan da Little take masa ya isa ya mai da shi ƙaramin mahaukaci. Ga kuma jaririn da ta bar masa yana ta tsotsan hannu. "Mommy ki ce musu su fita daga gidannan, in ba haka ba zan iya aikata abin da zai zama dana sani. Zuciyata zafi take yi mini in na ganta. Bana son ganinta na tsane ta."Ya furta hakan yana dage ƙirjinsa, sai kuma ya ruga da gudu kamar zautacce ya ƙara sa gurunta da dake tsaye tana kuka tamkar ranta zai fita. "I hate you whatever you name. Ki fice daga gidan nan, tun kafin na yi ajalinki. I hate you kar ƙi ƙara fatan ki zo inda na ke, domin duk ranar da kika bari muka hadu sai na yi ajalinki." Cikin tsawa yake maganar yana zare idanu, wanda a dalilin haka ya sanya duk idanu suka koma kansu. Ganin haka Ahmad da sauri ya kama hannunta suka fita zuciyarsa na zafi. Faɗawa jikinsa ta yi tana kuka. So take yi ta yi magana, amma ta kasa sai kallonsa take yi, tana haki tamkar ranta zai fita. Shiga cikin napep suka yi ya kwantar da ita a abaya. Ganin yadda ta jiƙe da zufa sai ya cire mata hijabi. "Don Allah ja napep ɗin mu bar ƙofar gidan nan." Ya ce masa cikin dana sanin zuwa. Da ya sani da ya ji maganar ta, amma ga shi zuwan ya haifar da wata damuwar. Sai da suka yi nisa sannan ya umurce sa da ya tsaya. Ruwa mai sanyi ya siya ya ba ta. Babu musu ta karba sai da tasha leda biyu. Da suka koma gida sun yi jugum-jugum suna kallonta da ta kwanta. Idanunta rufe amma ba bacci take yi ba. A ranar ta ita kawai ta san zafin da zuciyarta take yi. Ta yi fatan ace ita mutuwa ta ɗauka ba Batula ba, domin mijinta yana so ta haka dangin mijinta. Sannan duniya ta yi maraba da zuwanta, har ta sanya take kurɓar ruwan daɗi a cikinta, amma ita fa sam babu wanda yake kaunarta. Bayan Yaya Ahmad shi ne ya damu da ita sai mahaifiyarta. Tana kwance cikin damuwa. Ta yi kuka har ta ji babu daɗi. In ta tuna rashin mutuncin da Faruk yake mata, sai ta ji tamkar ta haɗiye kanta ta huta. Tana kwance ta ji sanyi na ratsa jikinta. Ganin ta fara kyarmar sanyi Ahmad ya lulluɓeta. Idanunsa sun ciko da hawaye. A ransa ya ƙudiri ko nawa zai nemo sai ya yi wa Faruk hulɗi ya sake ta. Faruk Ango kasha kanshi kenan. Tun lokacin da ya je gidan su Damir ya yi musu kashedi. Ya wuce hotel kai tsaye. Amarya tana kwance kamar ruwa tana shan baccin gajiya. Da ya shiga ɗakin ya zauna ya kalleta da take jan rago. A hankali ya zauna a gefenta. Bubbuga filon ya yi kamar wanda zai ta shi jariri."Baby na dawo." Ya ce mata yana kashe mata idanu. "Oh darling sannu da zuwa." Ta ce masa tare da miƙa masa hannunta da nufin ya zo su kwanta. Amaimakon ya kwanta sai ya kalleta ya ce,"Ki tashi mu tafi gidanmu." Miƙewa ta yi ta zauna tana kallonsa."Ba ka ce Mahaifiyaarka ta ce sai ka yi mata kayan faɗan kishiya ba?" "Ai ba ta gidan tana gidansu. Bakin shi ya sa ya ta zubar da cikin da take da shi. Ni wallahi murna sosai na yi da cikin ya fita, don ban san tana da shi ba." Jin abin da tace sai ta kalle shi kawai. A ranta mamakin halinsa take yi. Duk yadda take tunaninsa ya wuce haka. Haɗa kayanta ta yi sannan suka bar hotel ɗin. Da suka isa gidan kallon gidan take yi sosai tana ƙara kallonsa. Ta gaya mata Nasreen ƙazamiya ce, amma sam ba ta ga ƙazanta a cikin gidan ba, duk da ya yi gyara. Da ace ƙazamiya ce a gidan dole a ga zahiri. Komai tsaf-tsaf hatta kayan kicin ɗin ta sai da ta yi mamakin tsaftarsu. Abinci ta shirya musu lafiyayyen suka ci cikin farin ciki. Ganin jikin Nasreen ya yi zafi Ahmad ya kaita kyamis. Ƙarin ruwa ya zo ya sanya mata har gida. Ƙarin ruwan da aka yi mata ya samya ta samu sauƙin ciwon da kanta yake yi. Tana zaune bayan an cire drip ɗin tasha magani. Ruwan koko Mama ta dama mata ta samu ta sha. Raihan take ta kallonta cikin tausaawa. Ja yota ta yi ta rungume tana hawaye. "Umma, ki bar kuka za ki samu sauki." Jin abin da ta ce sai ta yi ƙoƙarin tsaida ruwan hawaye dake zuba kamar famfo. Duk bala'in da Baba yake yi, Ahmad ya tsaya kan kaifi ɗaya ba za ta koma gidan Faruk ba. Mamaki ya ke ba shi. Ganin ba ta da lafiya, amma ko sau daya bai leƙo ya gaishe ta ba. Yana mamakin mugun halinsa da ya haife su ya kasa sanin darajar su. Damir Rayuwarsa ta zama abin tausayi domin ya canza kamar ba shi ba. Abin da ya ƙara rikitar da shi. Jaririn da Batula ta bari, cikin dare ya fara zazzaɓi mai zafi bai ɗauki wani tsawon lokaci ba ya koma ga mahallicinsa. Hakan ya ƙara rikitar da shi gabakiɗaya. Ya kasa yarda an yi masa rashina lokaci guda. Har yau ya kasa yarda cewa Batula ta tafi ta bar shi. In ya kalli Little Marwana sai ya ji kamar zai fasa ihu, saboda tausayinta. Yana mugun tausayinta sosai, ganin har yau ta kasa yarda cewar ta tafi ta barta. Kullum kuka take yi masa kan ya kaita gurin Mommy. Ya yi kuka har idanunsa sun ƙafe. Baya bacci sai sallama dare yana roƙon mata yafiya. Ya rame ya susuce ya fita hayyacinsa. Ya tara ƙasumba kamar sabon mahaukaci. Ya daina shiga cikin mutane yana cikin ɗakinta rungume da hotonta yana zubar hawaye. Ganin yadda yake son ya takura kansa in ya kalli little Marwana, ya sanya mommy ta dawo gidan kullum taba sashinta. Gabakiɗayan rayuwarsa ta canza. Damir da aka sanshi da haƙuri da tausayi da girmama mutane, sai ya zama mutum mafaɗaci. Sam ba ya uzuri ga kowa. Ko Marwana da ba ya iya mata tsawa bayan rasuwar rasuwar mari biyu ya yi mata. Ganin yadda ya tashi hankalinsa Mommy ta sanya aka kwashe hotunanta. Hatta wayarsa sai da ta sanya aka goge, amma a banza domin ya adana hotunanta a inda ko da an goge zai gansu. Ganin yana shirin kashe kansa Mommy ta sanya shi a gaba cikin kuka. Lamarin ƙara girma yake yi, domin da ya rintse idanunsa sai ya ga batula tana masa gizo. Ganin haka hankalin Mommy ya tashi kan dole suka koma gidanta. "Damir, ba a mutuwa mahaifinka ya mutu? Allah ya halicci Batula kuma ya ɗauke abinsa. Ka tuna kai ma watarana tafiya za ka yi. Rashin yadda da kaddarar da ba ka yi ba, tamkar kana ja da ikon Allah ne.". Rungume ta ya yi jin abin da ta ce,"Ya zan yi Mommy? Na kasa yarda cewar Batula ta tafi ta birni. Ta yi mini nisa da ba zan ƙara ganinta ba." "Ya za ka yi? Haka Allah ya ƙaddara sai ka yarda da ƙaddarar Ubangiji. Ka yi mata addu'a." WASU MAZAN" Labari ne a kan rayuwar Nasreen wacce ta haɗu da jarrabawar rayuwa. Nasreen tasha jarrabawa a rayuwar aurenta da Faruk. Wanda faruwar haka yana da nasaba da rashin bango mai kyau abin jingina da ba ta samu ba, wato mahaifinta da ya kasa cike gurbin da ya kamata ya cike. Rayuwar aurenta madubi ne ga wasu matan da suke shan wahala ko rashin sama lafiya da mazajensu. Duk da ƙoƙarin su na son su zauna a ɗakinsu don gudun ZAWARCI da kuma fargabar rayuwar 'ya'yansu yadda za su kasance in ba su, da kuma fargabar mijin da za su aura bayan aurensu ya mutu. Wannan dalilin ya sanya ta jure zaman gidan aurenta don ta samu ta rayu da 'ya'yanta. Sai dai ƙaddara ba ta wuce mutum dole afkuwarsa tabbataciyace tun da Ubangiji ya tsara tun a Lauful Mahfuz. Duk yadda ta so ta kaucewa ƙaddara faruwar hakan ya ci tura. Ta shiga cikin tsananin rayuwa da fidda tsammani. Ta haɗu da wacce ta kira hasken da ya haska fitilar rayuwarta, amma sai dai a garin ta kawo hasken, ta sanya rayuwarta cikin tsarƙaƙiyar da ya zama tsarƙen da ya jefa rayuwar ta cikin tsarƙaƙiyar soyayyar mai kama da ƙiyayya. Sai dai Ubangiji ya faɗa a cikin littafinsa mai tsarki cewar,"Duk tsakani, akwai sauƙin." Haka ta kasance a lokacin da ta fidda tsammani a cikin rayuwarta, sai Allah ya kawo haske mai walƙiya da ya canza tubalin ƙaddararta da ga duhu zuwa haske. Ta kuma sha ruwan zuman da take tunanin ba za ta taɓa shan sa ba, bayan ta kwankwaɗi na maɗaci, wanda ya gauraye dukkan rayuwarta har ta fidda tsammanin shan zuma. A cikin littafin akwai wata irin soyayya mai tsuma zuciya. Masoyana karku sake a baku labarin littafin "WASU MAZAN" Domin na wasa ƙwaƙwalwa ta na zauna na tsara shi ta yadda zai sa ya ku tausayi da nishadi har ma ya zama darasi. Ku kasance masu bibiyar littafin domin jin yadda tubalin ginin rayuwarta zai kasance. Kun san dai alkalamin Jamila lawal Zango ba ya rubuta shirme. FOR WHATSAPP: 07072971093 CALL: 00814407242 Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/E9kBdqbI0Yf2hsCTaxPVjg *WASU MAZAN* NA *JAMILA LAWAL ZANGO* *FIRST CLASS WRITERS* MARUBUCIYAR Sakacina ko halin maza Kura da fatar akuya Ranar wanka... And now Wasu mazan 08144072423 PAGE 19 Rungume ta ya yi jin abin da ta ce,"Ya zan yi Mommy? Na kasa yarda cewar Batula ta tafi ta bar ni. Ta yi mini nisa da ba zan ƙara ganinta ba." "Ya za ka yi? Haka Allah ya ƙaddara sai ka yarda da ƙaddarar Ubangiji. Ka yi mata addu'a." Durƙushe wa ya yi, ya saka kuka kamar ƙaramin yaro."Ki yafe mini Batula, saboda son zuciyata. Na taimaki wata can na bar matata ta mutu! Na san cewa abin da na yi ban kyauta ba, amma ki gafarce ni. Na karashe rayuwa ta ba tare da ƙara aure ba, shi zai sanya ki gafarta mini. Mu yi rayuwarmu a Aljanna. Ni Damir ina ƙara miki alƙawarin, ba zan..." Da sauri Mommy ta sa ya hannu ta toshe bakinsa."Kar ka yi alkawarin da ba za ka ci ba, domin rayuwarmu tana hannun Ubangiji. In Allah ya tsara za ka yi aure, babu makawa sai ka ƙara. Sannan dole ka yi aure ka haifa mini wasu yara. Dubi tarin dukiyar da Allah ya ba ka? Nufin ka ba za ka samu ɗa namiji wanda zai gaje ka ba. Dole ka yi kaffara don ba zaka ƙarashe rayuwarka babu aure ba." "Ba zan iya ba, ba zan iya karya alƙawarin da na yi mata ba. Kuma bayan iya ba zan iya auren ko wace mace ba." "Zan nema maka aure dole ka yi aure! Ka manta alƙawarin da ka yi mini na cika family ɗin mu da zuriya?" "I can't mommy ba zan iya ba." "Ka shirya gobe ka je Companyka ka ci gaba da kula da Company. Duniya babu amana mutane cuta ya yi musu yawa." "Ban damu da na rasa komai ba tun da na rasa Batula. "Ya ce tare da shigewa cikin ɗakinsa. "No dole za ka ci gaba da harkokinka haka rayuwa take, duk yadda muke son wani Allah ya karɓe shi. Kuka da alhini muke yi, sannan mu ci gaba da rayuwa. You have to move on, and start a fresh life." Girgiza kansa kawai yake yi, domin ya san da wuya ya manta Batula, har ya yi farin ciki a rayuwarsa. Kan dole washegari ya shirya cikin riga da wando na shadda sky blue, ya tafi aiki. Duk wanda ya Ganshi sai ya yi mamakin yadda ya koma. Sanin cewa shi ɗan gayu ne wanda ya iya ɗaukar wanka. Ƙasumbar da ya tara shi yafi bawa kowa mamaki. Da isa cikin Company Muhsin ya tuka shi. Yana zaune a baya ya haɗa kai da gwiya. Hawaye yake yi sosai yana jin matsananciyar kewarta. Cikin rashin sa'a suka yi hon a get ɗin babu masu gadin gurin. Damir da zuciya ta tuƙoshi, da sauri ya fice daga motar ya shiga ciki. Daidai lokacin da ɗaya daga cikin masu gadin gurin ya ƙara so. Ba tare da wani dogon nazari ba, ya ƙara sa inda yake ya wanka masa mari, ji kake kau da ƙarfinsa. "Ashe wawaye na ɗauka ban sani ba? Ina biyan ku kudi, amma kin kasa yin aikin ku?" Ya yi masa tambayar yana huci cikin tsananin bacin rai. Da sauri Baba Bala ya kalle shi cikin tsananin mamaki. Ya san wane ne Damir da yadda yake jin daɗin kirkinsa. Matsawa ya yi, tare da dage ƙuncinsa yana mamakin marin da ya yi masa. Yadda ya koma da gashin da ya tara, yansa ya shi matsawa yana tsoro ko rasuwar matarsa ya haukatar da shi. "Ka yi hakuri Yallaɓai." "Ka je na sallame ku duka masu gadin gurin." Ya ce tare da fara tafiya daidai lokacin da Muhsin ya kama hannunsa suka shiga cikin campanin. "Ka yi hakuri Yaya Damir." "Ka tabbatar da ka sallame su." Ya ce masa tare da shiga cikin ofishin nasa. A ranar kowa ya san ba shi cikin hayyacinsa. Duk wanda ya kawo masa aiki zai yi musu fata-fata, duk da cewar daidai suka yi, amma sai ya kafe ba su yi aikin daidai ba. Mari kuwa shi kansa ba zai san mutanen da ya mara ba. Kallon tsoro ya yi ya yi masa a lokacin da ya fatattaki P.A ɗin da yana faɗin,"Nonsense, ka je na sallame ka tun da ba ka iya aikin ba." Kwashe takaddar ya yi cikin tausayi yana kallon sa. Ya san wane ne Damir. Da irin kyautatawar da yake masa. Saboda tausayinsa bai san lokacin da hawaye suka wanke masa fuska ba. Yana fita Damir ya watsa littafin da suke kan teburin."Na tsani kowa da duniyar da na ke ciki. Na fi buƙata na mutu na je na tarar da Batula." Ya ce cikin ƙaranci yana buga kansa da gini. "Ka yi hakuri Ya Damir."Ya ce tare da kama shi."Mu koma gida kawai." Ya ce masa bayan ya kama hannunsa suka fita, domin in har bai koma gida ba, kafin ya tafi zai iya ƙona kampany. Bayan sun koma Mommy hankalinsa ya tashi jin abin da ya ce."Haka rayuwa za ta tafi Damir?" Ta ce masa cikin kuka. Rungume Little Marwana ya yi yana hawaye . Ganin ya ƙi cewa komai Mommynta ce,"Ku shirya mu fita Ƙasar wajen wataƙila ya manta da komai." Shiru ya yi yana kallon ya ji dadin abin da ta ce, saboda yana son ya yi nesa in da hali karya ƙara dawowa. Ya bar ƙasar ya daina tunanin wacce ta kashe masa mata tana nan a duniya tana numfashi. Cikin ƙanƙanin lokaci suka fara shirye-shiryen tafiya. Marwana babu yadda za ta yi dole ta je makaranta don ta yi differing. Jikin Nasreen ya yi sauƙi domin ba karamin kula Ahmad ya ke ba ta ba. Duk abin da take so shi take ci. Hatta yaranta yana kula da su. Ta samu sauki ta warke sosai. Tana jin daɗin zaman gidan, duk da cewar samuwar halin da ta sanya halin Marwana yana damunta. Rikici sosai suke yi da Baba da Ahmad, amma ya rantse ba zata koma ba. Shi kansa Faruk ɗin ko aikinsa don yana can yana cin amarcinsa. Rashin zuwa ya ƙara ƙular da Ahmad, ganin bai damu da ita ba. Yana nan yana shirin tafiyar da za su yi. Ya sanya ran da dawo zai maka shi kotu ya yi masa hulɗi ya sake ta. Ganin ta samu sauƙi ta shirya ta je makaranta. Haushinta ɗaya Faruk ya ƙi yarda a kwaso mata kayanta. Tun da ta doshi get ɗin makarantar zuciyarta ke bugu. Sam ba ta son ta ƙara ganin Marwana, domin har yanzu tana jin ba ta saka mata da alkhairi ba, amma ya za ta yi? Ya zamar mata dole ta ƙara da karatunta musamman da ta kusa gamawa. Da ta shiga cikin makarantar idanunta na ƙasa har ta ƙarasa kan kujerar ta zauna. A gida ta bar Musaddik don Mama ta ce ta barwa Zainab. Tana zaune tana sauraren darasin har lecturer ya gama suka fita, kafin wani darasin. Zama ta yi a cikin gerden. Marwana ta ƙara so, cikin sanyi ta zauna a gefenta bayan ta yi mata sallama. Da sauri ta ɗaga kanta tana kallonta jin muryarta. Hawaye share suka zubo mata. Miƙewa ta yi za ta bar gurin cikin jin kunya. Hannunta ta kamo ta tsaya tana kallonta. Sai kawai ta fashe da kuka. Idan akwai wanda take jin kunya a duniya, bai wuce ita da ƴaƴanta ba. "Ki yafe mini na ruguza miki farincikin ahalinki. A lokacin idona ya rufe. Tsananin azaba ya sanya na kira ki. Na kira Ya Ahmad..." "Is ok, ban zo nan don na ji uzurin ki ba. Komai za ki gaya mini ba zai canza komai. Anty Batula ta rasu addu'a kawai za ki yi mata." "Allah ya jiƙanta kuma zan kasance har ƙarshen rayuwata ina mata addu'a." Ta ce tana share hawaye. "Na zo na yi miki sallama za mu bar ƙasar. Akwai yiwuwar dawowarmu da wuri ko akasin haka. Tun bayan rasuwar Anty Batula ya canza ya zama tamkar mahaukaci kuma masifaffe. Sam ba ya shiga cikin mutane. Gabakiɗaya rayuwarsa ta susuce."Tsayawa ta yi ko za ta ce wani abu, amma sai ta ga ta share hawaye kawai ta gyara zama. Ganin haka ya sa ta ja numfashi ta ɗora da cewa,"Wannan dalilin ya sanya Mommy ta ce mu bar ƙasar na wani lokaci. Na zo na dakatar da karatuna inna dawo to, in kuma na ci gaba a can shikenan. Ina ta tunanin yadda zan yi miki sallama, cikin ikon Allah sai ga shi mun haɗu." "Eh, yau na fara zuwa. Ya Faruk ya hana ni komawa. So yake ya yi tafiya ya tara kuɗi akai shi kotu, ayi masa hulɗi." "Da kyau Ya Ahmad ya cike gurbinsa na Yaya har masa na mahaifinki. Sam bai kamata ki ci gaba da zama da Faruk ba, domin in har kika ci gaba rayuwarki za ta tagayyara. Faruk ba ya ƙaunarki. " Kanta ta ɗaga ba tare da ta ce komai ba. Hannu ta sanya a jakarta ta ciro maƙudan kuɗi."Ga shi ki kula da kanka. Za ki iya kai shi kotu da waɗannan kuɗin." Girgiza kanta ta yi cikin hawaye."Ki yi hakuri ba zan karɓa ba, na yi wa kaina alƙawarin ba zan ƙara amsar taimako da ga gare ki ba." "Haba Nasreen, wallahi ko kaɗan ban zarge ki kan abin da ya faru ba." "Haka ne na sani amma ki yi hakuri. Ina muku fatan kyakkyawa ra rayuwa, kuma ina neman alfarmarki. Don Allah ki yi ta rokon mini yayanki ya yafe mini. Ki gaya masa akwai wata gangar jiki da jininsa yake yawo a cikinta. Ita gagar jikin ta ba shi wani matsayi mai girma, duk da tsanar da ya yi mata." "Zan gaya gaya mishi don Allah ki karɓi kuɗin nan." Girgiza kanta ta yi sai ta juya da gudu ta shige ciki. Marwana ta daɗe, a tsaye tana kallon ta cikin tausayawa. Har ga Allah ta yi kunyar ta taimaka mata. Burunta su gama karatu ta sanya Ya Damir, ya ba ta aiki, amma ƙaddara ta canza komai. Bayan sun gama lecture ta koma gida. Tana kwance a ɗaki suna hira cikin nishaɗi. Ahmad ne ya kalle su ya ce,"In sha Allahu, ina ga cikin sati nan za mu wuce Inugu. Ogana ya ce na kasance cikin shiri a kodayaushe zai iya kirana mu wuce." "Allah ya kaimu kuma ya kaika lafiya ya tsare mana kai." Cewar Mama tana kallonsa. "Amin." Ya amsa tare da ɓallar raken da yake sha. Nasreen ta ƙura masa ido ya cikin tsananin so. Ta san cewa abin da yake mata Allah ne kawai sai biya shi. Inda ace babu shi a rayuwarta, Allah kaɗai ya san halin da za ta shiga. "Ubangiji ya kai ka lafiya ya dawo mana da kai lafiya." Ta ce tana kallonsa. A maimakon su tafi kamar yadda ya ce, sai ba su tafi ba har suka ƙara sati biyu. A lokacin. Nasreen ta kwantar da hankalinta, ba kamar da ba tana ta zuwa makaranta. A daren da za su wuce Nasreen da ka ta ta yi masa wanki. Bayan ta gama ta shanya, da suka bushe ta goge masa, sannan ta shirya masa a jaka. Duk wani abin da ya kamata ya ɗauka ita ta shirya masa. Da ya zo zai yi musu sallama. Ta tsaya yana kallonsu cikin tsananin ƙauna."Mama, Nasreen zan wuce ku yi mini fatan sauka lafiya. Ga wannan kuɗin ku rinƙa amfani da shi kuma cin abinci. Ni ma ba a bani kuɗi sosai ba, in sha Allahu da zarar na fara aiki zan turi muku." "Ubangiji ya kai ka lafiya ya dawo mana da kai lafiya." Ta ce tana share hawaye sai kuma ta kalle shi ta fashe da kuka."Ka yafe mini na ɗora maka nauyin da ba naka ba." Murmushi ya yi jin abin da Mama ta ce."In sha Allahu Mama zan kula da rayuwarki da ƙannina sai baba ya yi nadamar rashin bamu kulawa da bai yi ba." "Allah ya ba ka iko." Cewar Mama. Nasreen kuwa ƙarasawa kusa da shi ta yi ta riƙe hannunsa."Ya Ahmad amma ba za mu daɗe ba ko?" "Eh wata ɗaya kawai za mu yi. Duk abin da Bana zai yi miki kar ki koma gidansa. Da zarar na dawo in sha Allahu zan biyasa duk abin da ya kashe ba." "Faruk ba zai zo gare ni ba, saboda ya samu wacce ta fini. Ina sha Allahu ba zan koma ba." Ta ƙarshe maganar maganarta tana kama hannunsa tana ji kamar karya tafi. "To in zauna mu je mu zauna mu ci ƙasa kenan?" Ya yi mata tambayar cikin tsokana yana harararta cikin wasa. "A'a, Ubangiji ya dawo kai lafiya." "Amin," Ya amsa bayan ya karɓi Musaddik ya riƙe hannun Raihan. Har ƙofar gida suka raka shi. Har ya hau mashin ta ƙwala masa kira."Ya Ahmad, sai ka dawo Allah ya tsare." Ta furta tana ɗaga masa hannu. Shi ma hannu yake ɗaga musu har ya ɓule. Da suka dawo cikin gida. Zama suka yi suna ta hirarsa har aka kira sallar azahar, sannan suka tashi suka yi sallah. A ranar da ya tafi Nasreen cikin dare

Chapter 14 of 17