Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da cewar bai ga lamarin da zafi ba, domin saboda Marwana ya yi, kuka ta san a rayuwar sa zai iya komai anything for her." Jikinsa ya ƙara yin sanyi sosai, domin zai iya cewa wannan shine karo na farko, da ya taɓa kai hannu a cikinta. Hankalinsa ya tashi har yana jin ba zai yafewa kansa ba, ga tsohon ciki a jikinta."Kiyi haƙuri bai kamata ki yi mini wannan zargin ba, saboda kin fi kowa kusanci da ni. Ka da ki bari kishi ya rufe miki ido. Wallahi ban taɓa ganinta ba, kuma na taimake ta saboda Marwana." Ya ƙarashe maganar yana ƙoƙarin kamota ganin yadda take cige baki. "Karka taɓa ni! Na tsane ka bana sonka mayaudari kawai." Ta ce masa sai kuka ta dafe cikinta tana nishi da ƙyar. "Please kar kishi ya sa ya ki illata mini kanki da baby. Wallahi na rantse miki ban taɓa son wata ya mace ba, bayan ke ballantana matar aure." "Anty Batula ki yarda da shi kar ji jawowa kanki wata cutar. Kin san a cikin satin nan za ki..." Hajiya ce ta ƙara sauke mata mari."Rufe mini baki shashasha kawai, duk abin da ya faru ba ke kika kawo ba, saboda ba ki da hankali da tunan.." Maganar ta tsaya sakamakon Batula da ta dace cikinta ta ce,"Wayyo Allah!" "Bayana, cikina, marata." Ta furta cikin gigitaccen ƙara. "Please Batula, kar mu yi haka dake. Kar ki yi ƙoƙarin haihuwa kin san C.A sa a yi miki." Ya faɗa yana dakatar da ita da hannu, amma ina ya makaro, domin kafin wani lokacinta fita hayyacinta. Hannu ya kai zai kamata sai ta ture hannun, ba tare da ya kula ba, cikin tsananin tashin hankali ya sungume ta zuwa cikin ofishin likita. Ganin halin da take ciki ya ruɗe yana kallonsa."Ka na sane da aiki za a yi mata, mai ya sa ka bari ta fara naƙuda da kanta?" "Please we don't have time. Intentionally ya faru, don Allah ka duba ta." Ya faɗa tare ɗa ƙara matsawa gurinta daidai lokacin da ta kira sunansa ta ƙara ƙankame. hannunsa. "Wayyo na shiga uku! Mutuwa zan yi!" Ta furta cikin tsananin tashin hankali tana nishin wahala. Jikinta zufa ya jiƙata sosai har ɗiga take. Kafin wani lokaci ta fita hayyacinta. Naƙuda ta taso mata gadan-gadan. "No ba za ki mutu ba, don Allah kar ki haihu ki bari ayi miki aiki." Ya furta yana ƙara riƙe hannunta. Tofa Batula wannan kishi haka?🙄🙄🙄 Wai Allah lamari fa ya rikice har na kasa cewa komai, saboda mai haihuwa akwai tausayi. Allah kawai ya san wahalar da iyayenmu suka sha. Allah ya ba su lafiya. Wannan page ɗin na duk wata uwa ce. Batula Allah ya sauke ki lafiya. WASU MAZAN" Labari ne a kan rayuwar Nasreen wacce ta haɗu da jarrabawar rayuwa. Nasreen tasha jarrabawa a rayuwar aurenta da Faruk. Wanda faruwar haka yana da nasaba da rashin bango mai kyau abin jingina da ba ta samu ba, wato mahaifinta da ya kasa cike gurbin da ya kamata ya cike. Rayuwar aurenta madubi ne ga wasu matan da suke shan wahala ko rashin sama lafiya da mazajensu. Duk da ƙoƙarin su na son su zauna a ɗakinsu don gudun ZAWARCI da kuma fargabar rayuwar 'ya'yansu yadda za su kasance in ba su, da kuma fargabar mijin da za su aura bayan aurensu ya mutu. Wannan dalilin ya sanya ta jure zaman gidan aurenta don ta samu ta rayu da 'ya'yanta. Sai dai ƙaddara ba ta wuce mutum dole afkuwarsa tabbataciyace tun da Ubangiji ya tsara tun a Lauful Mahfuz. Duk yadda ta so ta kaucewa ƙaddara faruwar hakan ya ci tura. Ta shiga cikin tsananin rayuwa da fidda tsammani. Ta haɗu da wacce ta kira hasken da ya haska fitilar rayuwarta, amma sai dai a garin ta kawo hasken, ta sanya rayuwarta cikin tsarƙaƙiyar da ya zama tsarƙen da ya jefa rayuwar ta cikin tsarƙaƙiyar soyayyar mai kama da ƙiyayya. Sai dai Ubangiji ya faɗa a cikin littafinsa mai tsarki cewar,"Duk tsakani, akwai sauƙin." Haka ta kasance a lokacin da ta fidda tsammani a cikin rayuwarta, sai Allah ya kawo haske mai walƙiya da ya canza tubalin ƙaddararta da ga duhu zuwa haske. Ta kuma sha ruwan zuman da take tunanin ba za ta taɓa shan sa ba, bayan ta kwankwaɗi na maɗaci, wanda ya gauraye dukkan rayuwarta har ta fidda tsammanin shan zuma. A cikin littafin akwai wata irin soyayya mai tsuma zuciya. Masoyana karku sake a baku labarin littafin "WASU MAZAN" Domin na wasa ƙwaƙwalwa ta na zauna na tsara shi ta yadda zai sa ya ku tausayi da nishadi har ma ya zama darasi. Ku kasance masu bibiyar littafin domin jin yadda tubalin ginin rayuwarta zai kasance. Kun san dai alkalamin Jamila lawal Zango ba ya rubuta shirme. FOR WHATSAPP: 07072971093 CALL: 00814407242 Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/E9kBdqbI0Yf2hsCTaxPVjg *WASU MAZAN* NA *JAMILA LAWAL ZANGO* *FIRST CLASS WRITERS* MARUBUCIYAR Sakacina ko halin maza Kura da fatar akuya Ranar wanka... And now Wasu mazan 08144072423 PAGE 16 Duƙawa kan gadon da aka kwantar da ita ya yi. Cikin wani irin yanayi yake kallonta, ganin yadda ta fita hayyacinta."Saboda kishi sa ki yi mini asarar rayuwarki." "Ka taimake ni, su cire mini cikin nan mutuwa zan yi, ka taimake ni ka sanya su cire mini cikin." "No, ba za ki mutu ba, saboda inhar kika mutu, ni ma mutuwa zan yi." Ya furta yana tofa mata addu'a. Ganin cikin ƙanƙanin lokaci ta fita hayyacinta. Hakan ya tayar da hankalin likitocin da su Damir. Tun sun ganin lamarin da sauƙi har ya tsananta. A lokacin da Doctor ɗin ya fito yana share zufa. Da sauri ya ƙarasa gunsa."Kana ganin za ku iya ko na yi mata viser?" Dafa kafaɗunsa ya yi,"A halin da take ciki ba za ka iya fita da ita ba. Ka yi mata addu'a domin matarka tana cikin wani yanayi." Jin abin da ya faɗa ya sanya shi daga kansa yana salati. Kansa ya zarga da kuma yarda da ya yi aka ibi jininsa, domin da duk haka ba ta faru ba. Ina ma ace lokacin da ta buƙaci ya zo ya kaita asibiti bai zo ba. "Ku shiga ciki tana son ganin ku." Tsoro ya sanya shi kasa jirgawa har sai da Hajiya ta ja hannunsa suka shiga. "Wayyo Allah!" Ta ce tare da miƙa masa hannunta. Kama hannun ya yi ya ƙarasa kusa da ita."So kike kiyi mini asarar kanki? Wallahi babu abin da ya haɗa ni da ita. Ƙawar Marwana ce, kuma kin san zan iya komai a kanta. Wannan dalilin ya sanya har na ba ta jinina, don na faranta mata." "Ka yafe mini mutuwa zan yi, sannan ka kula mini da Little Marwana. Ka tuna da alƙawarin da ka yi mini cewar ko na mutu ba za ka ƙara aure ba. Ina mugun sonka, don Allah kar ka auri ko wace 'ya mace. Ka jira mu yi rayuwarmu a Aljanna." "Ki bar wannan maganar ba za ki mutu ba. Za ki haifa mini yarona kuma ki raine shi da hannunki." "Lokaci ya ƙure ka yafe mini." Ta ce tana kallonsa sai kuma ta fara jijjiga. Kallon lamarin suke kamar wasa, amma sai suka fahimci ya wuce lamarin wasa. Ya ruɗe iya ruɗewa ganin da gaske yana shirin rasata. Yana tsaye a gurin kamar gunki aka canza mata kaya. Miƙa masa takkadda aka yi ya sanya hannu. Idanunsa suka kaɗa suka yi jajir, hankalinsa ya tashi matuƙar gaske! Ya kama hannunta ya riƙe, daidai lokacin da aka gungurata zuwa cikin ɗakin. Tsayawa a gurin ya yi hawaye yana bin ƙuncinsa. Sun yi jugum-jugum har da Marwana, da take jin kamar ta rufe idanunta ta zama lamarin da wasa. Kusan awa ɗaya suke tsaye ba tare da kowa ya fito ba. Ganin haka hankalinsa ya tashe, domin a wancan aikin da aka yi mata, uwar haka tuni an fito da ita. An nuna masa Marwana har ya yi mata huɗuba. Tsoro fargaba da damuwa suka cika masa zuciya. Suna tsaye a gurin har lokacin da likitan ya fito. Ganin yadda ya yi kace-kace da jini gabansa ya faɗi. "Doctor, ya take?" Suka yi masa tambayar cikin tsananin tashin hankali. "Please, ku shiga tana son ku yi bankwana, saboda we tried our best, but unfortunately we couldn't, saboda kafin mu yi mata aikin ta haihu." "No," Ya ce yana matsawa sai kuma ya riga ya shiga ciki, daidai lokacin da su Mommy suka shiga. "Batula," Ya kira sunanta tare da riƙeta ba tare da ya damu da jinin da yake zuba ya ɓata jikinta ba. "Kaga maganar da nake maka na cewar ba za mu rayu tare ba ya tabbata? Mutuwa zan yi! Jikinsa ya ba ni ba zan rayu ba, don Allah ka ɗora mini abin da na haifa a jikina, ka nuna mini shi." Idanunsa ya kai kan jajirin da yake ta kuka yana neman nono. Hannu Mommy ta sanya ta ɗauko.mata, ta ɗora mata shi a saman ƙirjinta. "Kin haifi ɗa namiji." Murmushi ta yi tana kallon yaron."Allah ya yi maka albarka. Za ka rayu cikin maraicin uwa, amma na san mahaifinka zai kula da kai." Ta ce tana nuna alamun a ɗauke shi daga jikinta. "Ina little Marwana? Don Allah ku kawo ta mu yi bankwana." Ta ce tana kallonsa. Matsawa ya yi kawai yana kallon ikon Allah. Tunawa da ya yi mahaifinsa da zai mutu, haka ya rinƙa ba shi wasiyya. Tun yana ganin wasa yake yi, amma tafiyar da ya yi kenan, wanda har yau bai ƙara ganin sa ba. Mommy ta fita cikin kuka tana kuka. Kallon da ta yi mata ya tabbatar mata da sai wani ikon Allah. Little Marwana ta ɗauko ta zo ta ɗora ta kan jikinta. Hannunta ta kama tana murmushi."Allah ya yi miki albarka." Ta ce tana kallonta hawaye yana zuba a ƙuncinta. "Don Allah ku ɗauke sa, ƙirjina zai fashe." Da sauri ya janye ta ganin tana tari. Jini yana ta zuba. Iya ruɗewa sun ruɗe. Kuka suke yi sosai hankalinsu ya tashi matuƙa. Duk yadda suke ɗaukar lamarin ya wuce wasa. Damir da ya ga numfashi yana ƙoƙarin bankwana da gangar jikinta. Ƙara ya saki cikin tashin hankali. Da sauri likitoci suka yi kan kanta. "Da gaske mutuwa za ki yi? Don Allah kar ki mutu ki bar ni." Ya ce yana miƙa hannunta. Da ƙyar likitocin suka yi nasarar fita da shi suka rufe ƙofa. Tari ta fara tana faɗin,"Ruwa ku ba ni ruwa zan sha." Na take jikinta ya rikice. Bayan fitarsu Nasreen ta shiga cikin tsananin tashin hankali. Ahmad shi ma tsaye ya yi yana mamakin lamarin. "Ya Ahmad, anya ina da sa'a a rayuwa? Dubi yadda suka shiga cikin damuwa saboda sun taimaka mini?" Ta yi masa tambayar tana zare idanunta kamar taɓaɓɓiya. "Ki yi shiru in sha Allahu, komai zai wuce." Ya ce cikin damuwa yana kallonta. "Wayyo Allah na! Da na sani da ban kira ta ba, wallahi na yi ta kiranka, amma wayarka a kashe. Don Allah ka je ka basu haƙuri su daina faɗa" Kama hannunta ya yi ya riƙe yana rarrashi ganin yadda take ta kuka. Kwanciya ta yi tana ta kuka, tana ganin duk abin da ya faru laifin Faruk ne. Da ace ya kula da ita babu wacce za ta kira. Tausayin Marwana ya kamata tana tunanin halin da take ciki. Duk iya ƙoƙarin su, na son dawo da numfashinta da ya ɗauke sun gaza. Doctor Fadil ya janye mata oxygen da aka sanya mata bayan ya sanya farin ƙyalle ya rufe mata fuska. Kallonsa ya yi kamar zautacce yana faɗin,"No! No doctor, ka da ka furta mini matata ta mutu? Don Allah kar ka ce ta mutu ta bar ni?" Ya yi masa tambayar yana jijjiga shi. "Am so sorry to say, matarka Allah ya yi mata ras..." "I said no! Batula ba za ta mutu ta bar ni ba." Ya furta tare da ƙwala ƙara. Ƙarar da ya ƙwala sai da asibitin ya ɗauka. Nasreen hankalinta ya tashi matuƙa. Zabura ta yi za ta fita."Ba za ki iya fita ba, sam ba ki da ƙarfi." "Don Allah ka bar ni na je, Allah ya sa matarsa ba ta mutu ba, a dalilina." Ta ce masa tana kuka. Kamata ya yi ya kwantar yana rarrashinta. Kuka take sosai kamar ranta zai fita. Tunani take innhar matarsa ta mutu zai yafe mata kuwa? Jin ihunsa ya sanya suka sheƙo da gudu zuwa ciki. Ganinsa zube a ƙasa ya sanya suka fahimci ta mutu. "Innalillahi wa inna ilahir raju'un! 😭 Batula Allah ya jikan ki." Ta furta tare da ƙarasawa gurin ta tana kallonta. Jin abin da ta ce wani irin zabura Marwana ta yi. Hankalinta ya tashi matukar gaske. Gani take yi lamarin kamar a mafarki. Ƙarasawa ta yi inda take kwance babu numfashi."Anty Batula," Ta ce tare da ɗaya ƙyallen da aka rufe mata fuska. "Innalillahi wa inna ilahir raju'un!" Ta furta sai ga ta a ƙasa babu numfashi. Gabakiɗaya sun rufe sun shiga cikin tsananin tashin hankali. Kuka suke yi sosai suna gani kamar za ta farfaɗo. A lokacin da ya farfaɗo ya karasa kan gadon. Tsayawa ya yi yana kallon ta tamkar ya zauce."Yanzu tafiya kika yi kika bar ni? Dama da gaske ne kike gaya mini ba za mu rayu har abada ba? Batula don Allah ki tashi ni da Little Marwana muna buƙatar ki." Ya faɗa yana girgiza ta. Ganin ta ƙi tashi sai kuma ya je ya ɗauko jaririn ya ƙara mata jikinta. "Kin ga yana kuka ko? Ki tashi ki ba shi nono." Kuka suke yi sosai suna kallonta. Lailai rai ba a bakin kowa yake ba. Duniya kenan kana ciki yau babu kai. Ga Batula ta tafi ta bar su a cikin wani yanayi. Jin kukan ya yi yawa ya sanya Ahmad fitowa. Tsananin ruɗani da tashin hankali ya shige shi. Duk da ba a mamaki da mutuwa, amma sai da mutuwarta ta buge shi. Ɗaki ya dawo ya samu Nasreen tana ƙoƙarin miƙewa."Ki koma ki kwanta sai haƙuri. Allah ya yi wa matarsa...." "No, Ya Ahmad!" Ta furta tana toshe kunninta. "Don Allah don Annabi, kar ka ce mini na zama sanadin da matarsa ta mutu? Kaicona! Ba ni da amfani a duniya. Da ma ni na mutu ba ita ba." Kuka take yi sosai ta kasa daina surutu, sai sumbatu take yi. Ahmad tun yana rarrashinta har ya ga ji ya zuba mata idanu, yana mamakin faruwar lamarin. "Ya kamata Ku ɗauke ta don kuke ku yi mata sutura." Likitan ya furta yana kallonsu cikin tausayawa. Cikin mota aka sanya gawar. Har suka isa gida Damir yana jin lamarin kamar a mafarki. Tamkar mutum-mutumi ya dawo. Babu um babu a'a sai kallo. Ita kanta Marwana ji take kamar ta mutu, ganin lamarin duk ita ta zamo silar faruwarsa. Kuka kuwa tun tana yi har idanunta suka ƙafe. Kafin kace me mutuwarta ta zaga duniya. Yan'uwa da abokan arziki suka fara zuwa cikin tsananin tashin hankali. Masu kuka na yi masu salati na yi. Damir zama ya yi ya tasa gawar da ido yana kallo. Shi har yanzu ji yake kamar ba ta mutu ba. Ya tuna a darenjiya da ta shayar da shi madarar ƙaunarta, da safe ma haka suka kasance cikin farinciki. In ya tun haka sai ya rintse idanunsa yana jin tsanar Nasreen. Ba ita ba hatta mai sunan da ya fara da harafin sunanta, ba ya kaunar ya gani. Ya yi kuka har ya gaji duk dauriyarsa. Bai ƙara shiga cikin tashin hankali ba, sai da aka ce ya shiga ya yi bankwana da ita. Anan ya mike yana mazurai."Na rantse babu wanda ya isa ya fitar mini da matata, saboda ba ta mutu ba, tana numfashi ku lura ku gani." Ya ce yana ƙoƙarin janye likafanin. "Ka yi haƙuri ka ɗauki ƙaddara, amma ta riga mu gidan gaskiya." "Babu wanda ya isa ya ɗaukar mini mata, duk wanda ya ɗauke ta sai na kashe shi." Ya karashe maganar yana kallon abokinsa da ya furta maganar. Kama hannunsa ya yi suka ƙarasa inda take kwance."Ka yi mata addu'a dole a kaita makwancinta." "Nazir, kai ma ka yadda Batula ta mutu?" "Ka yi haƙuri lokacinta ya yi." Ya ce tare da kama hannunsa ya kai shi har gurin. Durƙusawa ya yi ya fashe da kuka."Batula, kin ga ana son a raba mu? Don Allah ki tashi ki gaya masa ba ki mutu ba." Ganin shiru babu magana ya sanya shi sakin kuka." Da gaske kin mutu? Ba za mu rayu tare ba?" Da ƙyar ya miƙar da shi, sannan aka samu aka ɗaga makarar da su fice. Ganin haka Little Marwana ta riƙe tana kuka tana faɗin,"Mommy, ina za ki je? Daddy za su fita da Mommy." Jin abin da take faɗi ya ƙara tayar da hankalinsa. Ya ƙaraso da gudu ya riƙe makarar. Da ƙara aka samu aka raba shi da gawarta, sannan aka fita da shi. Ganin sun fita ya ƙara zubewa haka Marwana. Rayuwa kenan mai canzawa. Suna cikin farin ciki 'yan awannin da suka wuce, amma yanzu komai ya canza musu. Daga farar takadda zuwa baƙa mara daɗin karantawa. Faruk Tun da suka gama wayar ya kashe wayar yana huci. Rashida ta so daga inda take, ta sanya hannunta ta jawo sa jikinsa. "Don Allah ka share su, kar maganar da suka gaya maka ya ɓata mood ɗin ka." "Ki ƙyale ni da su marasa mutunci. Ni na rasa dalilin da ya sanya suke shiga cikin rayuwar iyalina." Shiru ta yi ba ta ce masa komai ba. Ganin haka ya kwanta akan gadon yana mamakin Nasreen na da ciki, amma ba ta gaya masa ba."Kenan ɓoyewa ta yi sai dai ya ganta da shi kenan?" Ya tambayi kansa cikin tsananin mamaki. Kwanciyarsa ya yi suka yi bacci da ba suka ci bashin sa. Sai kusan sha biyu sannan ya tashi ya yi wanka. Kallon Rashida ya yi, wacce ta fito daga bayin tana share ruwan kanta."Baby, bari na je na duba Nasreen, sannan zan yi wa Anty Asiya maganar tarewar mu." "Ai da ka ƙyale su mu yi zamansu anan." Wani banzan kallo ya yi mata jin abin da ta ce."An gaya miki yayo kuɗin na ke yi, da zan yi rayuwar aurena a hotel?" Fita ya yi bayan ya yi mata sallama. Kwanciya ta yi tana tunanin hanyar da za ta ci kudinsa. Jin abin da ya ce sai ta kalle shi kawai, dama ta san shi da shegen maƙo, don da bikin duk abin da ta ce za a yi sai ya rage kuɗin. Tsananin mamaki ya kamata da bai yi mata kyautar kuɗi ba, saboda maganin da Malam ya ba ta ya tabbatar mata da ingancinsa. Ko da ace bai tabbatar mata ba, yadda ta sha wahala a darenjiya ta san cewa yana da kyau. Tsanannin mamakin maƙonsa ya ƙara kama ta, amma a ranta ta sanya za ta yi maganinsa, duk hanyar da za ta fito, saboda ba zata iya rayuwa babu kuɗi ba, watakila kuma don bai san inkiyar sunanta Rashida lashe money ake kira ta ba. Tsakaninta da kuɗi akwai amana domin in har kana dasu sam baka da damuwa. Kudi kenan abokan harka. In har yana tarawa ba ya kashewa. Ita za ta koya masa yadda zai kashe. Wayarta ta ɗauko tana son kiran Malam. Sam zuwa gurin Nasreen da ya ce zai yi, bai dame ta ba, tun da ba ta a gabansa. Asalima ba ta jin kishinta, musamman yadda yake kusheta. Kamar yadda yake gaya mata ƙaddara ya sanya ya aureta, ta yarda da hakan, saboda kamarsa ɗan gayu babu yadda za a yi ya zauna da irinta a yadda yake fasaltata da kalmomi irin kucaka ƙazamiya wacce ba ta iya tarairayar namiji ba. Faruk hon ya rinƙa yi a ƙofar gidan domin a tunaninsa ta dawo. Ganin ba a buɗe ba, ya sanya shi fitowa ya sanya ɗan makullinsa ya shiga. Tsananin mamaki ya kama shi ganin bushashshen jini a ɗakinta. Fita ya yi zuwa falo ya zauna. Wayarsa ya zaro ya kira numbarta. A wannan lokacin tana cikin halin gaba kura baya siyaki. Tun da ta ji Batula ta rasu, sai da ta yi suma.ya fi a ƙirga. Ahmad hankalinsa ya tashi. Shi kansa mutuwar ya gigita shi. Yana rungumeta da ita wacce ta fita hayyacinta. "Yanzu da gaske ta mutu? Innalillahi wa inna ilahir raju'un! Kaicona sun yi mini alkhairi na saka musu da tsiya." Ta ƙarashe maganar da sakin razanannen kuka. "Nasreen, don Allah ki natsu wani bai isa ya kashe wani ba. Lokacinta ne ya yi. Ki duba halin da kike ciki." Ganin duk rarrashinta da yake yi, amma ta ƙi kwantar da hankalinsa ya sanya shi kiran gida. Mama da Zainab suka zo cikin tashin hankali. Fita ya yi daga asibitin cikin tashin hankali. Lamarin ya ruɗa shi. Ofishin likitan ya shiga don ya bukaci ya ba su sallama, domin fitar da ita daga asibitin kawai zai sanya ta kwantar da hankalinta. WASU MAZAN" Labari ne a kan rayuwar Nasreen wacce ta haɗu da jarrabawar rayuwa. Nasreen tasha jarrabawa a rayuwar aurenta da Faruk. Wanda faruwar haka yana da nasaba da rashin bango mai kyau abin jingina da ba ta samu ba, wato mahaifinta da ya kasa cike gurbin da ya kamata ya cike. Rayuwar aurenta madubi ne ga wasu matan da suke shan wahala ko rashin sama lafiya da mazajensu. Duk da ƙoƙarin su na son su zauna a ɗakinsu don gudun ZAWARCI da kuma fargabar rayuwar 'ya'yansu yadda za su kasance in ba su, da kuma fargabar mijin da za su aura bayan aurensu ya mutu. Wannan dalilin ya sanya ta jure zaman gidan aurenta don ta samu ta rayu da 'ya'yanta. Sai dai ƙaddara ba ta wuce mutum dole afkuwarsa tabbataciyace tun da Ubangiji ya tsara tun a Lauful Mahfuz. Duk yadda ta so ta kaucewa ƙaddara faruwar hakan ya ci tura. Ta shiga cikin tsananin rayuwa da fidda tsammani. Ta haɗu da wacce ta kira hasken da ya haska fitilar rayuwarta, amma sai dai a garin ta kawo hasken, ta sanya rayuwarta cikin tsarƙaƙiyar da ya zama tsarƙen da ya jefa rayuwar ta cikin tsarƙaƙiyar soyayyar mai kama da ƙiyayya. Sai dai Ubangiji ya faɗa a cikin littafinsa mai tsarki cewar,"Duk tsakani, akwai sauƙin." Haka ta kasance a lokacin da ta fidda tsammani a cikin rayuwarta, sai Allah ya kawo haske mai walƙiya da ya canza tubalin ƙaddararta da ga duhu zuwa haske. Ta kuma sha ruwan zuman da take tunanin ba za ta taɓa shan sa ba, bayan ta kwankwaɗi na maɗaci, wanda ya gauraye dukkan rayuwarta har ta fidda tsammanin shan zuma. A cikin littafin akwai wata irin soyayya mai tsuma zuciya. Masoyana karku sake a baku labarin littafin "WASU MAZAN" Domin na wasa ƙwaƙwalwa ta na zauna na tsara shi ta yadda zai sa ya ku tausayi da nishadi har ma ya zama darasi. Ku kasance masu bibiyar littafin domin jin yadda tubalin ginin rayuwarta zai kasance. Kun san dai alkalamin Jamila lawal Zango ba ya rubuta shirme. FOR WHATSAPP: 07072971093 CALL: 00814407242 Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/E9kBdqbI0Yf2hsCTaxPVjg *WASU MAZAN* NA *JAMILA LAWAL ZANGO* *FIRST CLASS WRITERS* MARUBUCIYAR Sakacina ko halin maza Kura da fatar akuya Ranar wanka... And now Wasu mazan 08144072423 PAGE 17 Fita ya yi daga asibitin cikin tashin hankali. Lamarin ya ruɗa shi. Ofishin likitan ya shiga, don ya bukaci ya ba su sallama, domin fitar da ita daga asibitin kawai zai sanya ta kwantar da hankalinta. Bayan fitarsa Faruk ya kira wayarta. Mama ta sanya Zainab ta ɗaga wayar.Tambayar da ta ji ya yi mata, ya sanya ta kalleta daidai lokacin da ta gaya masa."Dama wannan mara mutuncin bai zo asibitin ba?" Ta yi mata tambayar tamkar tana asibitin. "Ban sani ba mama, ya dai tambaye ni kuma na gaya masa." "Mai ya sa kika gaya masa?" Ahmad ya faɗa daidai lokacin da ya shigo ya ji abin da take faɗi. Tsuru-tsuru ganin haka ya kalli Mama ya zauna gefenta ya ce,"Wallahi ban ga amfanin zama da Faruk

Chapter 12 of 17