Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
da Nasreen take yi ba. Ya sake ta mana rabuwarsu ya fi kawai. Tun da ya yi aure Allah ya ba ta wanda ya fi shi. Da ace ya kula da ita da duk abin da yaru bai faru ba." "Kai innalillahi! Wallahi lamarin bai yi daɗi ba. Kuma da gaske matarsa ta mutu?" "Eh, dama tsohon ciki ne da ita, kuma likitocinsun gargaɗe ta, kar ta sake ta haihu a gida. Da zarar cikin ya shiga watannin haihuwa za a cire mata. Dalilin mijinta ya bawa Nasreen jini kishi ya sanya naƙuda ta tashi. Kamar wasa ta haihu ta rasu." "Kai mutuwar kenan? Rai ba a bakin komai yake ba." Mama ta ce cikin kaɗuwa. "Ki bari kawai Mama yau na shiga cikin tsananin tashin hankali. "Allah ya yi mata rahma, amma babu abin da za mu yi suga farincikimu, kuma ya kamata mu je musu ta'aziya?" "Ai ya zama dole."Ya furta cikin damuwa. Ya buɗe baki zai yi magana, sallamar Faruk ya katse shi. Da sauri ya miƙe ya ƙarasa ƙofar ya dakatar da shi. "Uban me ka zo yi?" "Ban gane ba? Matata na zo gani." Ya ce masa yana harararsa. "Ka san Allah ba za ka shiga cikin ɗakin nan ba, kuma a yau sai ka rubuta saki ka bata." Jin abin da ya ce ya ɗaga murya ya ce,"To sai na ga uban da zai sanya na saki matata. Banza wawa kawai don na taimaka ina zaune da ita. Karka manta amarya na yi jiya, in har na sake ta ita ce da wahala. Yarana kawai na ke tausayawa, amma kai ka san babu abin da zai sanya na ci gaba da rayuwa da bagidajiyar ƙanwarka." Jin a bin yake faɗi sai kawai zuciya ta kai shi ya shake shi. Dabbe suka fara kicikici. Dama Ahmad jiran ranar yake, don haka ya fara aika masa da nushi. Ganin suna shirin illanta juna Mama ta wanka wa Ahmad mari."In har ka ƙara kai masa nushi ban yafe maka ba Ahmad." Ta faɗa cikin Muryar kuka. Cak ya tsaya yana huci, ganin haka Faruk galla masa harara, yana mai da numfashi. Nasreen da ta lallaɓo ta zo gurin da suke faɗan. Rushewa da kuka ta yi tana kallonsa."Laifin me na yi maka Faruk? Ka zaɓi ka cutar da zuciyata? Ka san a rashin ƙular da ka kasa bani halin ƙuncin da na jefa kaina kuma na sanya wadanda suka taimake ni? Saboda me ba za ka iya ba ni jininka ba? Alhalin akwai wani can wanda babu dangantaka zai iya. Yayan Marwana ya ba ni jininsa wanda hakan ya sanya matarsa ta mutu. Mai na yi maka da ba ka sona? Don Allah ka sake ni Faruk. Na gwammce na fuskanci ko wace irin rayuwa, da na zauna da kai ba ka san daraja ta ba." Kallonta ya yi cikin tsananin kishi jin wani ya ba ta jininsa. Hannunsa ya sanya ya shaƙeta ba tare da ya kula da halin da take ciki ba."Kika bari aka sanya miki jinin maƙiyina? Na gaya miki na tsani family ɗin su, a dalilin ƙanwarsu da take son ta ɓata miki tarbiya. Tun ranar da kika hadu da ita na rasa gane kanki. Wallahi kin ji na rantse miki sai na je na ji dalilin da ya sanya ya ba ki jininsa, kuma sai na sanya hukuma ta hukunta shi. Daga yau zan sanya ayi miki tsakani da su, domin na lura in har kina tare da su. Kwaɗayinki ba zai bari mu zauna lafiya ba." Mamaki, takaici, da haushi suka kama su jin abin da ya ce. Ahmad ya kalle shi ya ce,"Kai dabban ina ne ne? Taimakon da suka yi mata sai ka ɗauke shi da mummunar manufa. Idan ka kasa kula da matarka ka ba ta jini, sai aka gaya maka kowa zuciyarsa mara imani ne kamar kai?" "Wallahi ban yarda ba, ai dama tuntini na fahimci tana kula wasu mazan, saboda innba kuka shi take yi ba, babu yadda za a ya rinƙa ba ta kyauta." "Innalillahi wa inna ilahir raju'un! Na shiga uku Faruk ka san babu kyau zargi a aure ko?" "Ke zan gaya ma haka don ki san darajar aurenki." Ya ce mata yana zare mata ido. "Faruk ka sake ni na gaji da zama da kai. Wallahi ka ji na rantse maka ko kai ne autan maza na gama zama da kai. Am done in this hell that you call marriage." Wata 'yar iskar dariya ya saki."Ok, na sake ki don ki je ki auri ɗan iskan nan ko? To da na yi ninyar sakin ki, amma kin ji na rantse miki ba zan sake ki ba, sai na tabbatar da babu abin mora a jikinki. Sai na wulanƙa ta rayuwarki, ta yadda babu namijin da zai iya kallon ki har ya yi sha'awarki..." "Wallahi ba ka isa ba sai ka sake ta yau." Ahmad ya ce yana gyara hannun rigarsa. "To uban da yake iko dani sai ya yi mini dole. In har kuma son na sake ta, sai ku biya ni tas bashin mahaifinku da yake karɓa sannan kuma ku biya ni duk abin da na kashe, domin tun da na aure ta ban mori komai ba, sai uban yara da ta tara mini." Tsananin mamaki ya kama su, ganin tozarcin da yake musu ya sanya suka kasa ce masa komai, har ya fice yana takun taƙama. "Ya Allah ka ɗauki raina don rayuwata babu amfani." "Kar ki ce haka Nasreen ki yi addu'a." Mama ta ce mata Ahmad kuwa ya kasa cewa komai zama ya yi cikin tashin hankali. Jikin Mama ta faɗa ta rinƙa kuka tana jin kamar zuciyarta za ta fito waje. Ƙirjinta wani irin zafi take mata sam ba ta da amfani a cikin duniyar. Faruk na fita kai tsaye ya fara neman gidan su Damir. Saboda tsananin kishi ƙirjinsa har tafasa take masa. Ya san cewa yana sonta tun da ya ganta soyayyarta ta hana shi sukuni, amma mugun halinta da ta kasa bin duk abin da yake so, ya sanya shi wulaƙanta rayuwarta. Kasancewar gidan na su ba ɓoyayye bane, sam bai sha wahala ba. Ɗaya daga cikin ɗan sandar da ya ɗauko ya kalle shi cikin tsananin razana. "Dama wannan gidan ka ce mu zo mu kama mai gidan?" "Eh matata yake bibiya ku kama mini shi, sannan ku yi masa warning na yi alkawarin biyan ku ko nawa ne." Shiru ya yi yana tunani amma jin ya ce zai biya su, sai ya ɗan samu ƙarfin gwiya. Parking suka yi a ƙofar gidan. Ganin taron mutane sai jikinsu ya yi sanyi. Kamar rasuwa aka yi a gidan?" "Ban damu ba ko uwarsa ce ta mutu. Don ayi rasuwa sai ku kasa kama mai laifi? In ɗan kidnapping ne uwarsa ta mutu ba za ku kama shi ba?" Ya yi musu tambayar a fusace yana zare idanu. "No ba haka na ke nufi ba." Ya furta cikin sanyin murya yana kallon da. "To kamar haka ne ka san dai hukuncin wanda yake bin mace da aure?" Ɗaga masa kansa ya yi ba tare da ya ce komai ba, suka nufi ƙofar gidan jikinsu a sanyaye. Damir da yake ƙofar gida yana karɓar gaisuwa. Tun lokacin da aka yi rasuwar ya zama kamar mutum-mutumi. Kallon mutane kawai yake yi ya kasa ce musu komai. Idanunsa sun canza sun yi jajur. Ganin motar 'yan sandar gabansa ya faɗi. Kasancewar bai taɓa ganin Faruk ba. Wannan dalilin ya sanya shi tunanin dalilin da ya kawo su. Da fari ya ɗauka gaisuwa suka zo, amma bayan sun yi masa gaisuwar sai suka kalle shi." Don Allah nuna son yin magana da kai, saboda wancan ya turo mu don ka zo ayi maka tsaka Ni da matarsa Nasreen. Ya ce yana zarginka da bibiyar matar..." "What!" Ya ce yana zare idanu."Am sorry ba wani babbar magana ba ce. Cewa ya yi so yake kawai a ja maka kunni kar ka ƙara shiga lamarin matarsa." Ransa ya ɓaci idanunsa suka firfito. Hawaye kawai yake yi yana mamakin da ga taimako ya sa ya rayuwarsa cikin tashin hankali. Matarsa ta rasu ranta a dalilin haka, kuka yanzu mijin ta yana zargin sa da bibiyar matarsa. Jiri ne ya ibe shi ya dafe mota da sauri yana karanto duk addu'ar da ta fito bakinsa. Ganin yadda ya birkice. "Please Yaya Damir, take easy bari na je na yi musu magana." Ƙaninsa Fadil ya ce yana ƙoƙarin kama shi. "No, kar ka damu." Ya ce masa tare da ture hannunsa ya nufi inda Faruk yake yana aika masa da mugun kallo. Kallo kallon suka yi wa juna. Kowa tsana ce ƙarara a fuskarsa. Kallo ɗaya suka yi suka tsani juna. Ji suke yi da za a basu takubba don kare kai, ko wane zai iya kaiwa abokin gabarsa farmaka da ninyar kai sa kushewa. Faruk ya bi shi da kallon tsana. Mamaki yake yi har ya kula Nasreen kuma ya ba ta kyautar jininsa. Wani irin kishi ya lulluɓe shi. Sai ya bi shi da wuƙa yana jin tamkar ya sassare shi da wuƙa. Damir kuwa mamaki ya kama shi ganinsa wayayye. Saboda halin da yake ciki sai kawai ya kalle shi tare da ɗauke kansa. "Ba zan iya zuwa ofis ba ina karɓar gaisuwar matata." Ya furta cikin karayar zuciya. "Eh, ku yi masa tsakani da matata." Faruk ya ce yana zare idanu da kumfar baki. "Shi kenan in sha Allahu ba zai ƙara ganina ba, kuma matarsa ba zan ƙara shiga lamarinta ba." Ya ce tare da juyawa. Harara Faruk ya bi shi da shi har ya shige cikin gidan. Damir yana shiga cikin ɗaki kai tsaye ɗakinsa ya wuce. Gilas ya ɗauka ya yi jifa da shi. "Mai ya sa kika shigo rayuwata don ki tarwatsa mini farincikina? Ashe taimakon ki zai zame mini rashin alkhairi? Haƙiƙa kin cancanci a kira ki tauraruwa mai wutsiya. Na tsane ki Nasreen ko a mafarki bana fatan Allah ya haɗani dake." Sai ya fashe da kuka cikin tsananin tashin hankali. Mommy ta kama shi ta riƙe ganin ya ji wa kansa ciwo."Haba Damir ka zama mai imani da hakuri." "Mommy taimako yana zama laifi? Mijin ta ya kawo 'yan sanda ayi mana tsakaninsa ita, wai ina bibiyar matarsa!" "Innalillahi wa inna ilahir raju'un! Wannan wane irin musiba ce? Yarinyar nan wallahi in har Marwana ta ƙara hurɗa da ita sai dai ta nemi wata uwar. Yarinya ta zamar mana baƙar daga tauraruwa mai baƙar wutsiya!" Marwana da take bakin ƙafa tana jin abin da Mommy nta ce, sai ta fashe da kuka. Kuka take yi sosai tana tunanin halin da take ciki. Mommy da ƙyar ta rarrashe shi sannan ta fito. Marwana ta gani a tsaye a bakin ƙofar tana ta kuka. Wucewa ta yi ba tare da ta ce mata komai ba. Zama ta yi ta ɗauki Little Marwana da ta samu bacci ya ɗauke ta. Nasreen da aka ba ta sallama Ahmad gida ya wuce da ita. Kuka sosai take yi har suka isa gida. Da suka isa gida ɗaki ta shige ta kwanta. Kanta ke ciwo ga cikinta da har yanzu yana mata ciwo. "Rayuwata ba ta da amfani Allah ka ɗauki rayuwata na huta." Ta ce tana share hawaye. Kafin wani lokaci kanta ya ɗauki zafi sosai, tamkar tukubar mai tsire. "Nasreen, ki sha magani ki samu ki ji sauki, gobe mu je mu yi musu gaisuwa." "Mama, ku je kawai ba zan iya ƙara ƙara hada idanu da su ba. Sun yi mini alkhairi na zamar musu tauraruwa mai baƙar wutsiya." "Duk abin da kika ga ya faru haka. Allah ya ƙaddara. Duk abin da za su ce, ai ya zama dole mu je mu yi musu ta'aziya." "Kai innalillahi wa inna ilahir raju'un!" Ta ce tana rintde idanunta. Da daddare sun kasa bacci sai tunanin lamarin suke yi, musamman ita da take ganin duk abin da ta faru a sanadinta ne. Ahmad kuwa tunanin hayar da zai ɓullo wa Faruk ya sake ta yake yi. Ya san cewar baƙaramin daru za a yi ba, kafin Baba ya amince ta zauna a gidan, amma a wannan karon duk abin da zai faru sai dai ya faru. Ya shirya don ya shanye duk wani wulaƙanci. Ko da ace Faruk zai nace sai ya biya shi, zai je ya samu ko bashi ne ya biya shi, don ya saketa. Da safe Baba ya shigo ɗakin. Tun daren Faruk ya kira shi ya sanar masa da duk abin da ke faruwa. Ya kuma yi masa barazana da ya biya shi kuɗinsa kaf. Hankalinsa ya tashi tunawa da ko wata ba a yi ba, da ya aro naira dubu talatin, kafin ya bashi kuɗin ba kalar tozarta da bai yi masa ba, amma ya haɗiye. Ya je ofis ɗin da ya fi a ƙirga kafin ya ba shi kuɗin. Babu babu irin tozarta da bai yi masa ba, amma ya jure har sai da ya ba shi. A yanzu cikin kuɗin ba ya tunanin ko dubu uku za a iya samu. Barazanar da ya yi masa kan ya dawo da kudin ya tayar da hankalinsa. Fuskarsa babu rahma ya shigo. Mama tana zaune tana ba Musaddik koko da ta gama damawa. "Mai Nasreen take yi a gidan nan?" Ya furta cikin ɗauke fuska ba tare da ya amsa gaisuwar da ta yi masa ba. WASU MAZAN" Labari ne a kan rayuwar Nasreen wacce ta haɗu da jarrabawar rayuwa. Nasreen tasha jarrabawa a rayuwar aurenta da Faruk. Wanda faruwar haka yana da nasaba da rashin bango mai kyau abin jingina da ba ta samu ba, wato mahaifinta da ya kasa cike gurbin da ya kamata ya cike. Rayuwar aurenta madubi ne ga wasu matan da suke shan wahala ko rashin sama lafiya da mazajensu. Duk da ƙoƙarin su na son su zauna a ɗakinsu don gudun ZAWARCI da kuma fargabar rayuwar 'ya'yansu yadda za su kasance in ba su, da kuma fargabar mijin da za su aura bayan aurensu ya mutu. Wannan dalilin ya sanya ta jure zaman gidan aurenta don ta samu ta rayu da 'ya'yanta. Sai dai ƙaddara ba ta wuce mutum dole afkuwarsa tabbataciyace tun da Ubangiji ya tsara tun a Lauful Mahfuz. Duk yadda ta so ta kaucewa ƙaddara faruwar hakan ya ci tura. Ta shiga cikin tsananin rayuwa da fidda tsammani. Ta haɗu da wacce ta kira hasken da ya haska fitilar rayuwarta, amma sai dai a garin ta kawo hasken, ta sanya rayuwarta cikin tsarƙaƙiyar da ya zama tsarƙen da ya jefa rayuwar ta cikin tsarƙaƙiyar soyayyar mai kama da ƙiyayya. Sai dai Ubangiji ya faɗa a cikin littafinsa mai tsarki cewar,"Duk tsakani, akwai sauƙin." Haka ta kasance a lokacin da ta fidda tsammani a cikin rayuwarta, sai Allah ya kawo haske mai walƙiya da ya canza tubalin ƙaddararta da ga duhu zuwa haske. Ta kuma sha ruwan zuman da take tunanin ba za ta taɓa shan sa ba, bayan ta kwankwaɗi na maɗaci, wanda ya gauraye dukkan rayuwarta har ta fidda tsammanin shan zuma. A cikin littafin akwai wata irin soyayya mai tsuma zuciya. Masoyana karku sake a baku labarin littafin "WASU MAZAN" Domin na wasa ƙwaƙwalwa ta na zauna na tsara shi ta yadda zai sa ya ku tausayi da nishadi har ma ya zama darasi. Ku kasance masu bibiyar littafin domin jin yadda tubalin ginin rayuwarta zai kasance. Kun san dai alkalamin Jamila lawal Zango ba ya rubuta shirme. FOR WHATSAPP: 07072971093 CALL: 00814407242 Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/E9kBdqbI0Yf2hsCTaxPVjg *WASU MAZAN* NA *JAMILA LAWAL ZANGO* *FIRST CLASS WRITERS* MARUBUCIYAR Sakacina ko halin maza Kura da fatar akuya Ranar wanka... And now Wasu mazan 08144072423 PAGE 18 "Mai Nasreen take yi a gidan nan?" Ya furta cikin ɗauke fuska, ba tare da ya amsa gaisuwar da ta yi masa ba. "Maganar mai tsawo ne zama ya kamata ka yi." Ta ce masa cikin tashin murya. "Na zauna saboda me? Abu ɗaya na sani kishi ya sanya ta dawo, kuma wallahi kin ji na rantse, ba za ta zauna a gidan nan ba. Ai na gaya miki duk yarinyar da na aurar, babu ita babu zawarci a gidana. Ke kishiya nawa aka yi miki? Amma kin mutu ne? Saboda baƙin kishi har ta ɓarar da cikinta." Ba ta yi mamakin abin da yake faɗi ba, don ta san Faruk ya gaya masa ƙarya da gaskiya. "Lamarin nan da kake gani ya wuce wasa. Inda ka san abin da ya haifar da sai ka yi mamaki." "Ta ya ya zan sani tun da ba kwa shawara da ni? Kin mayar da ni mara amfani, saboda ba na ciyar daku." Shiru kawai ta yi, tana girgiza kanta don ba ta san inda za ta fara ba, amma kuma sai ta daure ta ce,"Faruk ba ya kyautawa, a sanadin rashin ƙular da yake ma ta ya janyo matsalo..." "Kin ga ko kai mai za ki ce babu ruwana, abu ɗaya na sani ba za ta zauna mini a gida ba." "Baba, wallahi ka ji na rantse Nasreen ba za ta koma gidan Faruk ba, a wannan karon na fito na shirya zan ja da koma waye, don ya ba ta takaddarta. Ko da ace ba shi zan ciyo sai na biya shi sadakinsa." "Au iyye lailai wuyanka ya isa yanka. Fito na fito za ka yi da ubanka, anya Ahmadu kai ɗan kirki ne?" Ya yi masa tambayar cikin tsanannin mamaki yana kallonsa. "Ka yi hakuri da abin da zai faru, amma bana tunanin akwai abin da zai sanya na janye ƙudirina." "Haka kace? To shikenan mu zuba shege ka fasa." Ya faɗa tare da zabga tsaki ya juya ya fita. Cikin takaici ya ƙaraso gurinta da take kuka kamar ranta zai fita."Ki yi shiru ki daina zubar hawayenki. Da yanzu in sha Allahu in har ina raye, na yi miki alƙawarin babu wanda zai ƙara sanya ki zubar hawaye." Ya ce mata tare da kama gefen hijabinta yana share mata hawaye. "Yaya, dole na koma saboda Faruk, ba zai sake ki ba sai an yi masa hulɗi, kuma ka ga bamu da kuɗi." "Kar ki damu da wannan duk inda kuɗi yake zan nemo. Akwai aikin da oganmu yake sanya ran samu a kudi. In sha Allahu zan bi shi don na samo kuɗin." Kallonsa ta cikin tsananin ƙauna."Na gode Ya Ahmad, Ubangiji ne kawai zai biya ka." Murmushi ya yi jin abin da ta ce."Ki samu kisha ruwan koko, sai ki shirya mu je musu gaisuwa." Girgiza kanta ta shiga yi cikin zubar hawaye."Ba zan iya ƙara haɗa idanun da wadannan mutanen ba, domin sun yi mini alkhairi na saka musu da tsiya. Ku je kawai zan kasance ina yi wa matarsa addu'a har tsawon rayuwata." "Nasreen, ki taɓa ganin wanda ya kashe wani ba tare da lokacinsa ya yi ba? Allah kawai yake da ikon ɗaukan ran bayinsa, domin shi ne ya halicce su. Lokacin mutuwar bawa Ubangiji ya riga ya tsara ta tun kafin zuwan mu cikin duniya. Ko wace mutuwa da sanadinta a rayuwa." "Na sani Yaya, amma sam ba za su fahimta hakan ba. Ni ce na yi sanadin mutuwar matarsa. Na san cewa a yanzu ba shi da abin da ya tsana sama da ni. Na zama baƙar daga na sanya rayuwarsu cikin damuwa. Marwana kullum burinta ta sanya ni farinciki, sai ga shi na sanya su a cikin ƙuncin da za su dauwama a cikinsa." Ta ƙarashe maganar tana kuka sosai. Miƙewa ya yi, yana kallon ta ganin rarrashinsa bambaki ba za su yi mata ba."Ko mai za ki ce dole mu je musu gaisuwa, don haka ki gama karyarwa ki shirya bari na yi wanka." Idanun ta bi shi da shi, ta kasa cewa komai har ya fita. Tun da ya gaya mata zuwa gaisuwar gabanta yake faɗi. Kunya sosai take yi, tana tunanin tarbar da za su musu. A ranta ta yi dana sanin haduwa da Marwana ya fi kwando masaki. Cikin mutuwar jiki ta gama shiryawa. Tana cikin uwar ɗakar Mama ta yi zugum hawaye yana bin ƙuncinta. Ahmad ya je ya samu tashar napep suka hau. Tun da suka shiga suka yi shiru. Babu wanda ya yi ko tari, kowa da abin da yake saƙawa a cikin ransa. A lokacin da suka isa ƙofar gidan wani irin faɗuwar gaba ta ji, har sai da ta kama hannun Ahmad ta riƙe. "Innalillahi wa inna ilahir raju'un! 😭 Ta tabbata matarsa ta mutu saboda ni." Ta furta tana kallon get ɗin gidan da ya cika da motoci da mutane. Ganin ta kasa fita daga cikin napep.Ahmad ya sa ya hannu ya kamo ta. Da ƙyar ta ƙoƙarta ta fara taku tamkar 'yar koyo. A haka suka rasa ƙofar gidan cikin tsananin damuwa. Tun daga ƙofar gidan Nasreen ta tsinke da dukiyar da suke da shi. Tsananin mamakin ƙawance su take yi, domin ta san ruwa ba a san kwando bane. Duk da cewar jikin Marwana, kawai mutum zai kalla ya tabbatar da hutu da jin daɗi, amma ko kaɗan ba ta taɓa tunanin suna da kuɗi haka ba. Saboda babu wanda suka sani a gidan, sai suka tsaya a harabar gidan suna raba idanu. Marwana da ta fito, za ta raka ƙawayenta da suka zo mata gaisuwa. Cak ta tsaya tana kallon Nasreen da take tsaye kamar gunki. A hankali ta ƙarasa gunta. "Nasreen," Ta furta cikin sanyin murya. Da sauri ta juyo ta kalle ta. A tunaninta kamar yadda danginta, suke kallon ita ta yi sanadin Batula haka za ta yi, amma sai ta ga ta share hawaye ta rungume ta. "Ya jikin ki?" Tambayar da ta yi mata ya sanya ta fashe da kuka. "Marwana ashe za ki ƙara mini magana? Na ɗauka ke ma kina kallona a matsayin ni na...." "Shit! Kar ki faɗi haka." Ta katse ta tana faɗin haka. Ganin ta yi shiru sai hawaye suke ga zuba daga ƙuncinta ya sanya ta ɗora da cewa,"Kin taɓa ganin wanda ya kashe wani? Anty Batula, lokacin ta ya yi, kuma dama can ba lafiyayya bace, tun kafin ta auri Ya Damir Allah ya ƙaddara sanadin haka za ta mutu. Family ɗina sun yi fushi. Zafin rashinta ya sanya sun ɗauki laifin mutuwarta sun ɗora miki." "Wannan dalilin, yansa ya na ce ba zan zo gaisuwa ba. Ina jin tsoron haɗuwa da Yayanki. Na san cewa ya tsane ni babu wacce ya tsana kamar ni." "Haka ne Nasreen, musamman da Faruk ya zo har gida da 'yan sanda ayi masa kashedin ya daina kula matarsa, amma zuwan ya fi rashin zuwan." Jin abin da ta ce ya sanya ta zare idanunta."Anya Faruk na da imani kuwa? Duk da abin da ya faru kan rashin kula da ni ne?" Ta yi mata tambayar cikin muryar kuka. "To ya za mu yi? Lamarin ya riga ya faru." Shiru ta yi tana kallonta ta kasa cewa komai. Yadda Marwana ta dawo kawai zai tabbatar maka da tashin hankalin da suke ciki. Ganin ta kasa cewa komai sai ta kama hannunta. "Ku zo mu shiga ciki ku yi musu gaisuwa." Tamkar waɗanda aka zare musu lakka haka suka shiga ciki. Damir yana zaune da hoton Batula ya riƙe yana hawaye. Hannunsa ɗaya kuma Little Marwana da take ta yi masa kuka tana kiran Mommy. Hawaye yake yi sosai. Ya kasa cewa komai, domin shi kansa da ace akwai wanda zai kwanta a jikinsa ya yi ta kuka yana rarrashinsa hakan zai yi, don ya samu sauƙin zafin da zuciyarsa ta ke yi. Ya san cewa lokacinsa shi ma ya yi, domin ba zai iya rayuwa babu Batula ba. Yarinyar da ya so kamar ransa. Tun tana ƙaramar Allah ya sanya masa tausayinta saboda wahalar da take sha na ciwo. Daga baya ta riƙe ta koma soyayya. Yau ga shi ta yi masa nisa. A sanadin taimakon wata can ya rasa masoyiyarsa. In ya tuna hakan sai ya ji ba zai taɓa yafewa kansa ba. Ya yi kuka har ya ji babu daɗi, in ya tuna cewar da shi da Little Marwana sun zama marayu, sai ya ji duniya da abin da ke cikinta sun gimshe shi. Haka nan rayuwar sa za ta ƙare, domin ya yi mata alkawarin ba zai taɓa aure ba. Zai yi ta zama haka har Allah ya ɗauki rayuwarsa ya koma ga Allah. Jin sallama ya sa shi da Mommy suka ɗago kansu. Zubbur

Chapter 13 of 17