An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
*WASU MAZAN*
NA
JAMILA LAWAL ZANGO
"JAMSY"
☀️ *First Class Writers Asso* ☀️
Hame of Qualities And Trusted writer's of The Nation
*GARGAGAƊI*
Ban yarda kuma ban amince a juya mini labari ko ta wace siga ba, sannan ban bada lamuni a ɗora mini littafi a kowane kafar sadarwa ba sai da izinina a kiyaye⚠️
JAN HANKALI
Kirkirarran labari ne ban yi shi don wani ba, idan har ya yi daidai da labarin ki/ka to arashi ne.
PAGE 1
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
Cikin tashin hankali take tafiyar tana duba lokaci a wayarta. Duk wanda ya kalleta ya san cewa tana cikin tsananin damuwa! Damuwar da ta sanya canza yanayin fuskarta.
Musaddik ta ƙara gyara goyon da ta yi masa daidai lokacin da wayarta ta fara ringing alamun ana kira.
"Na shiga uku! Har ya dawo ban iso gidan ba." Ta furta tare da dage ƙirjinta hawaye na bin ƙuncinta.
"Hello Abban Raihan, wallahi gani nan na shigo cikin unguwarmu, ka bani mintina ƙalilan zan shigo gidan."
Daga can ɓangaren aka tsaki wani wawan tsaki." Ni dai ba ki ɗauke ni a matsayin mijin ba ko Nasreen? Tun da karatun ki yafi girkin sai na ga uban abin da za ki ci a gidan, domin kin ji na rantse miki yau ke da abinci sai ƙarfe sha ɗaya inna daw..."
"Don Allah ka yi hakuri ko don yaranmu. Ka san horan yunwa ba shi da amfani. Kuma kana ganin ragowar taliyar da muka ci jiya da daddare, shi na sawa Raihan ta tafi makaranta da shi." Ta katse shi cikin rawar murya tana faɗin haka.
"Kin damu da ita ne? In har kin damu da ita tun lokacin da na kira ki, ya kamata ace kin bar duk abin da kike yi kin dawo, tun da na ga karatun bokon ba lahira za ki tafi da shi ba."
"Ka yi hakuri lecturer ɗin ne san ba shi da hakuri ko na ɗauki excuse ba zai lamunta ba."
"Tun da ubanki ne ba." Ya ce tare da jan tsuka ya kashe wayar.
Hawaye ne suka ci gaba da bin ƙuncinta. A yanayin da take ba za ta iya biya wa ta ɗauko Raihan ba, musamman da ya ke jiranta.
Da sauri ta ƙarasa shiga cikin gidan bayan ta buɗe ƙofar get ɗin gidan.
A harabar gidan ta same shi yana ƙoƙarin shiga motarsa. Da sauri ta ƙara da gurinsa dai-dai lokacin da ya shiga cikin motar ya rufe ƙofar.
Ganin ya ta da motar ya sa ya ta ruga ta buɗe masa get.
Sai da ya zo bakin get ɗin ya kalleta ya ce,"Tun da kin fi jin maganar Malaminku sai ki je ya ba ki abinci."
Hawaye shar! Suka zo mata. Yayin da cikinta ya yi wani irin ƙugi na yunwa.
Ganin ya fice daga gidan ya sa taka ƙafa zuwa inda Musaddik yake ta ɗauke shi.
Falon ta shiga ta zauna jabar tana jin yadda zuciyarta ke tuƙuƙin baƙinciki. Cikin rashin dubara ta miƙa zuwa kicin da sauri. A tunaninta ko ya kawo mata cefane, amma babu komai. Ƙofar ɗakinsa ta ja a kulle
Komawa ta yi ta zauna tana jin yadda zuciyarta ke bugawa tamkar za ta fito waje.
Saboda takaici ta kasa fita sai kiran Maman Muwadda maƙociyarta ta yi, ta roƙeta ta turo mata Raihan.
Tana zaune a gurin tana karanta wasiƙar jaki suka shigo.
Da gudu ta rugo ta faɗa kanta." Umma, kin dawo?"
"Eh Raihan, ya makaranta?"
"Lafiya lau kuma an mana karatu sosai. Sai dai abincin da kika bani lalacewa ya yi tunkafin na ci, haka na yi ta wuni da yunwa har sai da na dawo Maman Muwadda ta zuba mini."
"Allah Sarki! Ki yi hakuri ina can ina tunanin zai iya lalacewa saboda akwai wake."
"To,"Ta ce tare da ɗaukar wayarta ta zauna a gefenta.
Tun tana saka ran zai ji tausayinsa ya dawo, har ta cire tun da ba shi ne farau ba. Bayan ta isar da sallar Isha ta yi shafa'i. Wuri kuma ta barshi da ninyar in ta tashi da daddare za ta yi."
Ɗaukar Musaddik ta yi ta shinfiɗar da shi kan gadon bayan ta yi masa shinfida. Sannan ta kama hannun Raihan suka shiga ciki.
"Ummu, har yanzu Abba bai dawo ba, kuma bacci na ke ji ga shi ina jin yunwa."
"Bari na ɗauki miki ruwa kisha ki kwanta in ya dawo na girka zan tashe ki, kin ga Musaddik shi ma ya yi bacci."
"To," Ta ce bayan ta hau gadon.
"Addu'ar bacci fa?" Ta ce mata wanda ya sanya ta ƙaranto sannan ta rufe idanunta.
Ita ma cire kayan jikinta ta yi sannan ta kwanta tana karanta addu'ar bacci ta shafa musu.
Tana kwance sai juyi take yi kamar wata maciya. Hawaye ke kwaranya a ƙuncinta yana jiƙa matashin da take kwance.
Cikin dare ta kasa bacci janyo Musadik da yake kukan ta ba shi mama. Duk da cewar babu komai a ruwan nono, amma ihu kukan da yake mata wanda zai iya tada maƙota ya sanya ta saka mishi fatar a baki, wanda ya shiga ja yana ajiyar zuciya.
Tausayin yaron ya cika mata zuciya dai da suka yi nasarar zubar ƙwallar dake idanunta.
"Ka yi hakuri ka daina jan fatar nan babu abin da za ka samu." Ta ce masa da tare da ƙoƙarin janye fatar nonon a bakinsa, wanda ya sanya shi canyara ƙara.
Cikin sauri ta mayar masa ina jijjiga shi. Ganin ya ja babu komai a fatar ya sanya shi saki yana faɗin,"Umma, ci ci." Cikin gwaranci yake daɗi yana dukanta da hannunsa.
Miƙewa ta yi na nufi kicin da sauri tana jijjiga shi duk da ta san cewa babu komai. Ka yi hakuri ka kwanta?" Ta yi masa maganar tamkar ba ƙaramin yaro ba, tana nuna masa kular da babu komai.
Ganin ta miƙa masa kular abincin ya sanya shi turewa yana kuka.
Turus! Ta tsaya ina kallon yaron da bai wuce shakara ɗaya da rabi ba cikin tausayawa
Kukan da yaron yake yi ya sanya ta kasa komawa baccin wahalar da ya ibe ta. Wannan dalilin ya sanya ta kasa yaye shi don na samu rangwame da ga tsotson da yake mata.
Cikinta ne ya yi wani irin ƙara tare da bada sauti. Da sauri ta dafe cikin tana jin yadda kayan cikinsa suke juyawa, tamkar za ta yi aman da ta san kummalo kawai zai fito.
Kaita ta ɗaga tana duba agogon bangon dake cikin ɗakin. Ta san cewa ba ya dawowa da daddare, amma na yau ya fi dadewa. Wani irin juya yake rufe mata idanuna har ba na iya ganin komai na cikin ɗakin.
Ba ta san lokacin da ta fashe da kuka ba tuna halin da ta ke ciki. Zaman aurenta; da ba shi da maraba da zaman gidan yarin! Mijinta Farouk bai san darajarta ba. Ko na ce bai ɗauke ta a wata aba wacce Allah ya yi wa daraja ba. Irin rayuwar da suke gudanarwa ta gwammace gara mutuwata. Sai dai, ba ta da gatan da ya fi nan.
Tunaninta ya katse daidai lokacin da na ji alamun buɗe get tare da shigowar motarsa. Da sauri ta mike jikinta na rawa ta fito ta isa ƙofa ta buɗe masa, tare da fita don ta ɗauko kayan da ya zo da shi.
"Saboda iskanci kin ji na dawo tuntuni ba ki fito ba? Uban wa kike kira ya zo ya kwashi kayan?"
"Ka yi hakuri sankatan ne ya ƙi budewa da wur.."
"Ke tsaya!" Ya daka mata tsawa yana faɗin haka, wanda ya sa ta ja ta tsaya ba tare da ta ɗauki kayan da ta buɗe gaban motarsa don ta ɗauka ba.
"Wallahi kin ji na yi miki rantsuwar ɗan musulmi matukar kika ɓata mini ƙofa sai dai ubanki ya gyara mini "
Da sauri ta ɗago kanta tana kallonsa, yayin da hawayen da take ƙoƙarin maida su, suka shiga turereniya a kyakkyawar fuskarta.
"Eh, kin ji ai ubanki na ce har wani daraja ya ke da shi da ba za a dage shi ba? Mutumin da ya kasa ci daku ballantana ya ba ku ingantacciyar rayuwa?"
"Ka ji tsoron Allah Faruk, ka daina zagin iyayena. Ban san me na yi maka ba, ka auro ki ka kawo ni cikin gida ka, kana gasa mini aya a hannu, sannan ka matar da ni kamar baiwar ka. Rayuwar aure ba kangin bauta ba..."
"A hakan ma ai gata na yi miki, da yanxu kina can kina fama da ƙanzon tuwo da garin kwaki in an samu." Ya ce yana watsa mata mugun kallo.
Ranta ne ya ƙara ɓaci jin tozarci da yake mata ta rintse idanunta tana faɗin,"Innalillahi wa inna ilahir raju'un! Alllahumma ajirni fi musibati!"
"Zagina za ki yi ko ƙarya na yi?" Ya furta yana ƙoƙarin matso ta da shirin zare bell din dake wandonsa.
Matsawa ta shiga yi domin in har ba ta yi watsa ba, sai ya ɗumama mata jiki kafin ya kwanta.
"Ka yi hakuri." Ta furta tare da saurin iban kayan da ya siyo
"No, da ki tsaya ki yi mini rashin kunya tun da ba ki da tarbiyya. Yanzu ki kwana a gidanku da ko gurin kwana ba ku da shi mai kyau. Stupid girl. Har wani baki kike da shi na magana. In mata ne ga su nan birjik a duniya sun yi kwantai ba irin ki ba, kin yi da ƙugu kamar an daurawa taɓarya zani. Wata jemammiya dake." Ya ƙarashe maganar daidai lokacin da ta shige cikin falon.
Kuka ne sosai ya kubce mata har sai da ta duƙa.
"Jiran ki na ke yi ki zo ki kwashe kayan fa." Ya daka mata tsawa yana faɗin haka wanda ya sanya ta fito da sauri ta ɗauki sauran kayan.
Tsaki mai ƙarfi ya ja tare da rufe mirgina motar har ya kusa haɗawa da hannunta. Sannan ya bita cikin gidan yana takun isa. Wayarsa a hannunsa kamar yadda ya saba duk lokacin da ya dawo ita ce take zama abokiyar hirarsa.
Da ya shiga cikin falon sai ya zauna a kan kujerar ya hakimce yana latsa waya, yayin da take gefensa cikin damuwa tana kallonsa.
Murmushi ya ke yi har da buga ƙafa. Murmushi da yake yi zai tabbatar maka da mata yake chatting ɗin, duk da cewar ba sabon abu bane a gareta, amma sai da ta ji wani irin ƙunci ya mamaye ta, yayin da wutar kishinsa da ƙaunarsa suka yi matu rubdugu.
"Kina gidan uban wa na yi ta kiran ki ba ki ɗaya ba?"
Tambayar da ya yi mata ya dawo da ita cikin hayyacinta.
"Wallahi babu inda na je, bayan na dawo makaranta, sai dai in wayar ta mutu ka san ɗauke wa take yi."
"It didn't concern me.'" Ya ce tare da make kafaɗa sai kuma ya ɗora dacewa,"Shegen son gasa da goga kafaɗa da 'ya'yan masu hannu da shuni. Kina 'yar gidan Malam Shehu ko uban me ya sanya kika na ce sai kin yi makaranta? Na gaya miki ɓacin Mommy wallahi da ke da makarantar nan har abada!"
Shiru ta yi ta yi tare da mayar da kanta ƙasa ba tare da ta tanka ba, don ta saba. Neman hanyar da zai gabata abinci ya ke yi.
"Ma za ki tashi ki dafa mana abinci." Ya ce ba tare da ya kalleta ba.
Kallonsa ta yi da sauri tana hawaye, amma ganin baya kallonta ya sa ta miƙa cikin galabaita tana haɗa hanya.
Binta da idanu ya yi tare da sakin wani wasan tsaki. Ƙazamiya ji shigar da kika yi da daddare kina zaune da wata banzar doguwar riga. Ni na ƙara auran mata Bahaushiya an yi an gama yare zan ɗauki don sun fi ku sanin darajar mijinta iya tattalinsa, saboda na san da ace ita ne, yanzu ta yi shigar da zai ɗauki hankalina. Ko da yake ina abin da za a nuna ƙirji kamar silifas?" Ya faɗa hankalinsa na kan wayarsa.
Idan da sabo ta riga ta saba da cin mutuncin da yake mata, ko da a gaban kowa ne, amma duk lokacin da ya gaya mata, sai ta ji kamar ta kashe kanta don baƙinciki.
Da ta shiga kicin ɗin, sai da ta yi kuka mai idan ta sannan ta kunna gawayi da ƙurar tana kallon gas ɗin ta da ya daina repelling tun da suka gama amarcinsu.
Da ƙyar ta samu gawayin ya kama kasancewar jiƙakke ne. Bayan ta hura wutan sannan ta zuba ruwa ta koma don ta gyara waken ganin akwai gyara.
Tana girki tana hawaye har ruwan ya tafasa ta sanya waken.
"Ke! ma za ki zo ki ɗauki wannan ɗan banzan yaron na ki ya tashi zai hana ni kallo." Ya ƙwala mata kira yana faɗin haka.
"Abba Hairan, kai fa uba ne a gurinsu bai kamata ace kana kiransu da munanan kalamai ba."
"Ƙarya na yi? Yabon ne kuke yi mini ke da shi a cikin gidan nan in ban da kuci ku yi kashi?"
Shiru ta yi ta kasa ce masa komai sai zuciyarta da take mata rukunin ɓaci rai.
"Wuce ki bani guri tun kafin ƙi ƙara ɓata mini rai na sanya ki kashe girkin nan." Da sauri ta shige kicin ɗin domin ta san cewa ba ƙaramin aikinsa bane.
Goya shi ta yi da yake kuka yana ƙunnai ta cigaba da girkin da shi. Ganin ta ɗora girkin ya san mya shi daina kuka yana kiran ta gama. Tausayin yaron ya cika mata zuciya har sai da ta ji kamar ta yi kuka.
Tana kicin ɗin ba ta gama girkin ba har sha biyu ta buga. Sannan ta ga shinkafar ta tsotse sannan ta zuba masa fulas ta kai mishi bayan ta sanya wa Musadik.
Kallon wulakanci ya yi mata tare da bude fulas ɗin fuskarsa a yatsine kamar ya ga kashi.
"Na gaya miki ki daina sanya mini spicy da yawa ko?"
"Wallahi curry powder da ganyen na'ana'a na sa." Ta ce mishi a tsorace.
Ba tare da ya kalleta ba ya ɗauki cokalin ya fara cakala yana ci wanda zuwa can ya ture abincin.
Cikin wahala take cusa abincin sakamakon ƙirjinsa da ya riƙe mata. Sam ba ta jin ɗandanonsa saboda yunwar da ta ƙwaƙwuleta.
Labarin ya zo da wani irin salo da nishadi, karku baru a ba ku labari. Ku biyo ni domin it’s just like a little introduction part, and guess what? You will really enjoy it. Believe me, my dear readers. Your happiness is my concern. Follow me on Facebook, Whatsapp, Wattpad, Arewaboo, and Bakandamiya. Ta ku, Jamila Lawal Zango (Jamsy).
FOR WHATSAPP: 07072971093
CALL: 008144072423
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/LQfVU1ABdFI14btWRhUB1K
*WASU MAZAN*
NA
*JAMILA LAWAL ZANGO*
*FIRST CLASS WRITERS*
MARUBUCIYAR
Sakacina ko halin maza
Kura da fatar akuya
Ranar wanka...
And now
Wasu mazan
08144072423
PAGE 2
BISMILLAHIR RAHMANINR RAHIM
Cikin wahala take cusa abincin, sakamakon ƙirjinsa da ya riƙe mata. Sam ba ta jin ɗanɗanonsa, saboda yunwar da ta ƙwaƙwuleta. Da ƙyar ta samu ta yi loma biyar, sannan ta mayar ta rufe, don ta san ƙila wannan abincin har gobe shine abincin da za su ci.
Ɗaukar Musadik ta yi, da ya gama cin abinci ta yi ta wanke masa hannu, sannan ta kai shi ɗaki ta kwantar. Gyara yaron ta yi, tare da ɓingirewa sai bacci. Da kyar da siɗin goshi ta samu ta tashi Hairan, kasancewar ta mai nauyin bacci.
Littafan karatunta ta ɗauka, ta shiga ɗakin cikin murna ganin jefa sun kawo wuta, za ta yi karatun test ɗin da za su yi gobe.
Yana zaune a gurin yana chatting da 'yan matansa, har agogo ya buga daya daidai, sannan ya miƙe ya kashe kayan kallon ya shiga ɗakinsa. Wanka ya yi ya fito zuwa ɗakinta .
A lokacin ta dakata da karatunta ba don ta so ba, sai dai bacci ɓarawo da ya yi nasarar sace ta.
"Ke Nasreen," Ya ce yana dukan bayanta wanda ya sanya ta farka da sauri tana zare ido.
Harararta ya yi bayan ya kwanta." Ba na gargaɗiki da ki daina sa yaron nan a gadon nan ba?" Ya ce mata cikin ɓacin rai.
"Abban Hairan, akwai sanyi ka tausaya musu."
Banza da ita ya yi tare da jan Musadik can gefe da karfi.
Shiru ta yi ba ta da bakin magana. Ta san cewa in aka kawo agola a gidansa, tsaf zai iya kashewa, tun da ɗan cikinsa ma bai tausaya masa ba.
Babu kunya ya kwanta tare da rungume ta yana sauke ajiyar numfashi a fuskanta.
Hawaye ne ke zuba a ƙuncinta wanda take gogewa ba tare da ta bari ya gane ba.
"Ni shikenan ba ni da daraja da ƙima, sai in dare ya yi nake mace a gurinsa, amma da safe baiwa?"
Jin ya yi shiru ya sa ya ta yi laƙwas, a jikinta saboda tana so shi ya kai sunan da za a kira shi namiji, amma kwata-kwata ba shi da hali, munanan halinsa da suke sanya tana jin kamar ba ta yi dace miji ba.
Ture ta da ƙarfi ya yi har ta bugu da gado. Ta rintse idanunta tana shafa gurin daidai lokacin da ta ji ya ce,"Kin wani shiga jikinta kamar mage? Nufin ki ni zan yi aikin? Ke ma kin san yau ba ni a wannan mood. Yanzu na hakan taimaka miki zan yi don kar ki je kina kwaɗayin mazan jami'a, saboda ba wani tarbiyyar ƙwarai kika samu ba?"
Gabanta ne ya yi mummunar faɗi jin abin da ya ce. Hankalinta ya tashi sanin cewar sam babu kyau miji ya rinƙa zargin matarsa.
"Zargina kake Abba Hairan? Duk tsawon shekarun da mun ayi ban yi zina ba sai yanxu?"
"Ko wa na iya canzawa lokaci guda. Yadda rayuwa ta canza, babu wa da zan iya yadda da shi a wannan duniyar, kuma yadda kike cuɗanya da waɗannan mazan jami'an masu kama da buntsura, ai ba zan yi shedar ki ba. Na yi karatun na san yadda mazan jami'a suke." Ya ce cikin zafi.
"Na shiga uku kaicona! Sai na yi tur da rayuwa matuƙar mijina bai yarda da ni yi ba." Ta ƙarashe maganar tare da sakin razanannen kuka sai kuma ta ɗora da cewa," Sau nawa kake chatting da 'yan mata, a kan gadona kuma magana ta batsa? Wane namiji ka ga na taɓa yin waya da shi ko na kawo shi gidanka?"
"Ke kina ke jina? In ga za ki yi aiki kiyi in kuma ba ki so, sai na ce huta rororo." Ya faɗa tare da jan filo ya rungume.
Kuka sosai ya kubce mata har da sheshsheka.
"Ke wallahi in kika tayar da maƙota sai na yi mugun saɓa miki, domin duk wanda ya tsare ni yana tambayata jikin ki zai gaya miki."Ya faɗa tare da zama a kan gadon wanda ya sa ta yi tsit sai na zuci da take yi.
Kwanciya ta yi nesa da shi tana hawaye. Ganin haka ya ja bargo yana faɗin,"Aikin banza, tura agwagwa a ruwa. Ki riƙe jikinki uban me zan ji."
Banza da shi ta yi ta kwanta tana jan majina.
Kasa haƙura ya yi don ya san ba za ta kawo kanta ba. A hankali ya ja jikinsa ya shiga jikinta tare da rungumota.
Da sauri ta mike zaune, tana kallonsa duk da babu wadataccen haske a cikin ɗakin.
"Na sha gaya maka ka daina irin wannan domin ba ɗabi'a nace na musulmi. Annabi ya horar da mu kafin aikata sunna mijinta gabatar da abin taɓi. Ko ba ka gabatar ba ya kamata ka tashe ni. Faruk, kuma ni ma mutum ce ina buƙatar mu gabatar da soyayya ba wai ka yi gaba gaɗi ba."
"Saboda ba ki da abin da zan shafa a jikinki ne. Ki zauna kina nan za ki ga na auro mace yar duma-duma wacce zan more sadakina."
"Ni ma ba haka ka auro ni ba. Ta zo wane dare ne jemage bai gani ba. Matuƙar za ka yi mata irin rayuwar da kake mini wallahi yadda za ta koma sai ya fi nawa. Kai fa ma'aikacin gwamnati ne, amma sai an yo cefane a gidanka. Hatta man shafewa watarana sai na roƙo. Duk sana'ar da na fara sai ta karye saboda ci da gida. Ba ka da mu da karatun yaranka ba. Ni nake ɗawainiya da su. Wallahi Abban Raihan, ina tausayawa rayuwarka, saboda haƙkin iyalinka da kake ɗauka."
"Fitowa fili za ki yi kice ni ɗan wuta ne, domin na lura abin da kike son ki faɗi kenan. Banza shashasha, kin san yadda na yi karatu? An gaya miki ni wawa ne, da zan saki kuɗina da na samu a wahalar ki wulaƙantar? To wallahi ki cire wannan bazan tunanin na ki, saboda na san darajar kuɗi. A lokacin da na yi rayuwar wahala babu uban da ya taimaka mini, sai yanzu za ki rinƙa tsara mini yadda zan yi rayuwa. In kin raina abin da na ke miki ki nemo in kin ɗauka neman kuɗin a banza ne."
"Wannan dalilin ya sanya nake son na kammala digirina, na samu aiki ko da koyarwa ce a private."
"A tunani ki kuma sai na bar ki ko?"
"Haba Abban Raihan sam ba ka yi wa rayuwata adalci ba, matukar ba ka
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 1 Chapter of 17