Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
bakin ta cikin wasa yana fad'in "Ni sa'ar ki ne kike murgud'a min baki?." kauce wa tayi batare daya same ta ba ta ce "Wai manya manya da ku wai sai goggo ta shiga kitchen ta girka muku abinci bazakuyi aure ba, kowa sai yazo ya tsaya wai sai an girka an bashi yaci yatafi gurin ai ki, ai na rantse goggo ki dai na musu girki duk wan da bazai yi aure ba yarika fita yana zuwa restaurant yana cin abinci." Faisal daya d'auki plt d'in soyayyen dankali da kwai da goggo ta zuba masa, ya kai lomar kwai bakin sa ya ce "Zan je na kai wa Kawu ko da dubu ashirin ne na lallab'a da ke a maneji." ido ta waro tare da fad'in "Allah ya yi min tsari sabo da na zamo kaza dole a bada dubu ashirin a kaina, ko miliyon ne ma bazaka samu ba, na kai ka ina zuu ko wasan gona?." "Kaji yarin yar nan za'a taimake ki kike wa mutane zakin baki." cewar Zaraddin yana rike hab'a. hararar su tayi duka kana ta d'au plt ta mikawa goggo Larai tana fad'in "Ni duk kun cika ni da surutu har kunsa junwan da nake ji ya karu." goggo Larai ta zubo mata dankali da kwai tana fad'in "Je ki karya rabu da su sai akace muku kai muke nima da ita da za mu karb'i dubu ashirin ai me biyan sadakin ta sai ya shirya." dariya tayi cike da jin dad'i ta ce " Fad'a musu dai goggo na." Faisal ya ce "Ai ashirin d'in ma a hakan tai mako za'ayi mata." waje tayi tana fad'in Allah ya sawake mata.. Tana gama yin breakfast ta mike ta fito, har lokacin Naseeba na bacci bata farka ba, kayan da ta wanke ta duba sun bushe ta kwaso, ta dawo d'akin tasaka cikin laida, tasaka hijabi ta fito dan kaiwa masu kayan kayan su. a bakin kofar fita daga side d'in suka had'u da goggo Larai, ta ce "Ina zuwa?." SEEDRAH ta ce zanje na d'auko mana kayan mu ne a gidan Nabeela." ta ce "Yauwa to ga wani yana sallama da ku a waje." d'an shiru tayi tana tunanin to waye?, sai kuma tasa kai ta fita tana ce wa goggo sai ta dawo. a tsaye jikin mashin ta tadda Kamal a kofar gidan, kallo d'aya tayi masa ta d'auke kai zata wuce, da sauri ya sha gaban ta tare da fad'in "Barka da safiya antashi lafiya ya mai jiki?." gajeren tsaki ta ja takuma sa kai zata wuce batare da ta ce da shi komai ba. yayi saurin kuma shan gaban ta ya ce "Da ma magani na kawo mata dan nasan zata bukace sa, wannan kuma kayan ku ne daku zubar jiya garin gudu." yayi maganar yana nuna mata d'aya laidar dake d'aya hannunsa. a hatsale ta ce "Tunanin ku kenan sai dai kun mance magani bazai tab'a dawo mata da kima da martabar da kuka zubda mata shi ba, wlh bakuci banza ba kujira sammaci daga kotu." da sauri ya ce "Mun ji a yi hakuri muna jira kuma zamu karb'i hukuncin mu, amma dan Allah ki kai mata maganin nan." kamar bazata karb'a ba tuno da kawar ta tana bukatar magani dan jikin ta yayi tsami sosai sai ta fizge laidar maganin a hannunsa had'e da laidar gyale da bra d'in ta da jiya suka watsar da shi garin gudu, ta juya ta koma ciki. a d'aki ta tadda goggo Larai tanayiwa Naseeba sannu da jiki da alama farkawar ta kenan, ta karaso itama tana yi mata sannu, jin goggo tana fad'in bari takira almajiri meyi mata shara ya siyo mata magani, SEEDRAH ta mika mata laidar maganin tana fad'in "Ga magani nan ma ankawo mata, abokin ango ne angon ne ya aiko sa da maganin shine yake sallama a wajen nan." goggo Larai ta ce "Ai ko ya kyauta dama hidimar bikin sa ne yasa ta zazzab'in, to bari taci abinci sai ta sha." goggo ta fita zuwa kitchen domin samo mata abinci. Naseeba tayi kasa da kanta jin hawaye ya ciko idon ta tuno da halin da take ciki. SEEDRAH ta maso ta tare da dafa kafad'ar ta ce "Wan da yakawo ki nan jiya shine yakawo maganin." kai Naseeba ta jinjina tayi saurin kai hannunta karkashin idanunta ta taro hawayen da suke kokarin zubo mata, batare da ta bari SEEDRAH ta gani ba, dan ta san idan tagani sai ta fita yin kukan har kuma goggo Larai ta fahimci abin da ake ciki. SEEDRAH ta ce "Da ma zan je na d'auko mana jaka da wayoyin mu ne a gidan Nabeela daga gurin na biya na kaiwa matar data bani kaya jiya na amso tawa." Naseeba ta ce "To sai kin dawo kada ki jima kiyi sauri." ta ce to. tana fita Naseeba ta sami damar fitar da hawayen da yake ta cin ta a zuciya... Gidan Nabeela SEEDRAH ta fara zuwa, a kafa ta tafi sabo da babu wani nisan kirki sakanin su da gidan goggo Larai, duk unguwa d'aya ne layi ne dai ba d'aya ba. a parlour ta tadda Nabeela da angonta K'abir sai faman rarrashi yake. suna gaisawa ya shige cikin bedroom, Nabeela da ta turo baki gaba tana wani mammatse ido, ta ce "Wato shine kuka ki dawowa ko?, sabo da mugunta ai da kuna nan da duk haka bai faruba." dariya SEEDRAH ta yi ta ce "Ayya sannu kin ga in da idanunki suka kunbura kuwa." baki ta kuma turo wa ta ce "To ba dole ba mutum bayajin dan Allah." dariya takuma yi mata a kasan ranta kuwa tana ayyana, ita tama sami rarrashi da kima a gun mijin ta, ga kawar su can abin tausayi, wani katon banza ya turmushe ta batare da biyan sadaki ba. SEEDRAH ta ce "Je ki kawo min jakan mu da wayoyin mu natafi, yan zu zamu wuce gida zazzab'i na damin Nasiba." "Ayya yanzun tafiya zakiyi madadin kuzo da Nasiba'n nan kafin ku wuce, kibari sai anjima ki tafi." Nabila ta fad'a kamar zatayi kuka. SEEDRAH ta ce "Tap gida zamu wuce yanzu, kin san bamuyi da Mama zan kwana ba nasan zatayi ta min fad'a gara na koma da wuri." Nabila ta ce "To shike nan amma yaushe zaku zo?." ta ce "Sai kin kwana biyu zamu kara zuwa." Nabila ta d'auko mata jakar su badun taso ba suka rabu tana kwalla. Gidan su Maman Zeey SEEDRAH ta bi da sallama tashiga gidan, Maman Zeey ta amsa sallamar da murmushi dan ta gane ta. bayan sun gaisa Maman Zeey take fad'in "Shine jiya kika tafi babu sallama?." murmushi SEEDRAH tayi, Zeey ta fito suka gaisa kana ta mika mata laidar data sako kayan da jiya suka bata, Zeey ta karb'a taje ta d'auko mata nata da ta barshi a nan, ta amsa tare da yi musu godiya tayi musu sallama ta fita. a bakin kofar gidan suka had'u da Kamal, ta d'auke kai tayi gaba.. kamar zaiyi mata magana sai kuma ya yi shitu, yabi bayan ta da kallo har ta b'acewa ganin sa. sakai ya yi ya shiga gidan. Zeey ya tarar ita kad'ai a tsakar gidan, ta gaishe shi ya amsa tare da tambayar ta ina Mukhtar?, dan tun jiya yake neman sa bai gansa ba, ya yi masa kiran duniyar nan a waya baya d'aga wa. ta ce "Ai ni rabo na da Ya Mukhtar tun jiya da kuka fita sallar magriba, kai d'aya ma kazo ka ci d'anwake na baka kushe ba, kuka fita da yarinyar jiyan nan, wai wace ce ita ne Ya Kamal ko me iya girkin ne ka samo?." ta karashe maganar tana dariya. shima dariyar ya yi mata yanufi d'akin Mukhtar yana fad'in "Bari na duba shi ko yana ciki ina zuwa dai." ya na zuwa bakin kofar d'akin Mukhtar ya tura kofar yajisa a rufe gam, har ya yuya zai wu ce ta jikin windon d'akin yajiyo karar wayar sa. ya maso jikin windon tare da zuge glass d'in windon ya leka. can ya hango sa kwance saman katifa rigingine fuskarsa na kallon sama. kofar ya dawo ya shiga bubbugawa yana fad'in "Mukhtar kazo ka bud'e min kofar nan." sai da ya yi ta bubbuga kofar kamar zai b'alla kafin ya taso yazo ya bud'e masa, baya ya yi ya koma ya zube kan katifar yana mai dafe kansa. Kamal ya shigo d'akin tare da mai da kofar ya rufe, ya tako gaban sa yana mai kare masa kallon tuhuma, hannunsa ya zura cikin aljuhunsa ya zaro agogon Mukhtar d'in da jiya ya gani yafad'o daga jikin Nasiba, ya mika masa yana fad'in. "Ga agogon ka da ka mance da shi jiya." kai Mukhtar ya sunkuyar yana mai taunar lips d'in sa na kasa, tabbas yana mai danasani da nadamar aikata wa yarinyar nan fyad'e, wan da shi kansa baisan ta yan da akayi zuciya ta kaisa ga ai kata hakan ba, tun bayan faruwar haka jiya yarasa ina zai tsoma rayuwar sa ya shigo gida babu wan da ya sani ya kulle kansa har yau. Kamal ya dube sa da kyau ya ce "Me ka aikata kenan kasan girman laifin abun da ka aikata kuwa Mukhtar?!, yaushe ne halin ka ya juya izuwa halin banza Mukhtar? mu da muka biyo su domin share tantamar mu ko matan banza ne, shine kai zaka nuna halin banza a kan ta, yaushe halinka ya koma haka ne Mukhtar?." da sauri Mukhtar ya d'ago tare da ruko hannun Kamal murya a raunace ya ce "Aboki na kafi kowa sanin halina, kasan wannan ba halina bane, wlh tun jiya da hakan ta faru nakasa samin sukuni a rayuwa ta, ban san yan da akayi har na kai ga aikata hakan ba, tabbas na yar da idan mace da na miji suka keb'e guri guda to shaid'an ne cikon na ukun su, shi ya angiza ni izuwa aikata hakan, wlh ban san ta yadda akayi na sinci kaina cikin aikata hakan ba." d'an shiru Kamal ya yi bashakka yasan ko waye abokin nasa, tabbas shaid'an ya sami galaba a rayuwar sa a karon farko. ya ce "To sun ce bazasu kyale ba zasu shigar da kara kotu." da sauri Mukhtar ya ce "Ina maraba da karb'ar duk wani hukuncin da za a yi min, wata kila hakan zaisa zuciyata tasami sassauci daga halin da nake jin kaina yanzu, Kamal zuciya ta kamar zata fashe dan zafi." ya janyo hannun Kamal ya d'aura shi dai-dai kahon zuciyarsa. Kamal ya jinjina kai cike da alhenin abin kana ya ce "Bakaci abinci ba tun jiya har yau taso kaje kayi wanka muje kaci abinci." kai ya girgiza cike da jin zafin da zuciyarsa ta ke ya ce "Ina jin kunyar had'a ido da Maman Zeey, bansan da wani ido zan kalle ta ba." Kamal ya ce "Maman Zeey bata san komai ba kuma nasan zata fahimce ka dan tasan wani irin tarbiyya ta baiwa d'an ta, je kayi wanka kazo muje kaci abinci." ya mike jiki a sanyaye yashige bayi... SEEDRAH tana komawa gidan Goggo Larai, ta sami Nasiba har tayi wanka. babu laifi jikin ta ya dad'a warwarewa suka saka kayan su suka ajewa goggo nata sukayi mata sallama suka tafi. sai da SEEDRAH ta raka Nasiba har gida kafin ta wuce gidan su dan ga gida ga gida ne sakanin gidan su da gidan su Nasiba. ta shiga da sallama direct d'akin Mamarta ta wuce.........! Mommyn Twins ce 🌺 *ƘARSASHI!* 🌺 *NA* *RASHEEDAT S DIRECTOR* ( _Book 1_) ~Free page~ ( _Bismillahirrahmanurrahim_) _Alhamdulillah Ina yiwa Ubangijin buwaye gagara misali godiya daya kuma a ramin lokaci na kuma dado wa a wannan karon a cikin littafi na mai suna ƘARSASHI kada ku manta kafin zuwan ƘARSASHI HAMDAH ya zo muku masoya ku baza kunnuwan ku ku kuma biyo ni cikin labarin nan mai suna ƘARSASHI ina mai yi muku albishir da faranta wa kamar yadda HAMDAH da sauran littatafai na suka saba zuwar muku🤗 ƘARSADHI salon sa da banne labari ne mai ƙwanƙwasa zuciyar masoya salon labarin na daban ne. ko dai ku biyo ni cikin labarin nan kada ku mance da sunan sa ƘARSASHI! ƘARSASHI!! ƘARSASHI!!!_ _Littafin na kud'i ne 400 Account no 3170524141 Rashida Salihu first bank kokuma katin Mtn ta wannan number 08034690723 a tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690734_ *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* 🅿️4 Mama da ke zaune cikin d'aki tana ninke kaya ta amsa. SEEDRAH ta karaso ta aje jakarta tana cire mayafin ta ta ce "Barka da gida Mama ina kwana." batare da Mama ta amsa gaisuwarta ba ta ce "Amma ai bamuyi dake zaki kwana ba kikasa babun ku yazo yana ta yimin masifa." zubewa SEEDRAH tayi kan kuje ra tana fad'in "Ayya Mama jiya baki ga ruwa ake da daddare ba shi yahana mu dawowa, a gidan goggo Larai muka kwana da Nasiba." "Shi ne bazaki kira gida ki fad'a ba? kin san halin Baban ku sarai idan ya shigo bai ganki ba yarika kira kenan." "Yi hakuri Mama, wayar tawa a gidan Nabila na barta jiya sai yau naje na d'auka." SEEDRAH ta fad'a tare da gyara zama tashiga taya Mamar tata ninke kayan su data wanke musu da safen nan. Mama ta ce "Sabo da shashanci irin naki waya ya kwana wani guri ke a wani gurin, Allah ya shirya, sai ki tashi kije ki d'aura girki da ma yanzu nake da shirin shiga kitchen d'in wankin kayan ki ya sai da ni." ta ce "To me za'a girka Mama?." Mama ta ce "A kwai shinkafa a store da Abba'n ku Sulai ya aiko da shi d'azu, ina ga akwai ragowar manja da yaji a kitchen sai ayi mai da yaji, dan Baban ku baice komai ba game da girki ga rana tana ta yi." kai SEEDRAH ta jinjina ta ce "Mama haka za'a girka zallar mai da yaji babu wake?." "To ina kika ga waken waken daya kare tun ba yau ba, je ki girka abin da ya samu kawai." a hankali SEEDRAH ta mike tana jinjina lamarin dake dad'a ta'azzara game da mahaifin nasu. abun kamar wani kariyar arziki gida kamar gidan su babu wan da zai ga gidan ya ce basufi karfin komai na rayuwa ba. sai gashi abun da zasuci ma yana kokarin fin karfin su, wai har ya kaiga d'an uwan mahaifin su ke aiko musu da abinci, wanda a da mahaifin su yana daga cikin masu kud'in unguwar su, rayuwa kenan. takuma jinjina kai tana fita daga cikin d'akin Mama. A sakar gida ta tadda su Suhailat da Halimatu yayun ta wan da suke uba d'aya da Umma wato mahaifiyar su kishiyar Mama. Suhailat rike da waya a kunnen ta tana daga d'an can gefe, Halimatu tana yiwa Umma tsifa. "Ina kwana Umma." SEEDRAH ta fa d'a tana karaso in da suke. Umma ta ce "Lafiya lau kawayen amarya andawo ne?." ta ce "Eh." Halimatu ta dube ta ta ce "Baba sai tambayar ki yake ko d'azu ma sai da yayi magana." "Ai yanzu Mama take fad'a min jiya ruwa ne yahana ni dawowa nakwana a gidan goggo Larai." SEEDRAH tayi maganar tana wuce wa kitchen, tashiga kiciniyar d'aura abinci. tana gamawa ta zuba a kula mai d'an girma ta kai d'akin Umma kana ta d'au na d'akin su takai, sannan ta dawo ta d'auki na Baba ta nufi d'akin sa. da sallama ta shiga d'akin nasa, Baba da ya ciro hular kansa yana kokarin ajiwa da alama yanzu yashigo gidan, ya amsa sallamar. takaraso ta aje tray'n data dauro kular abincin da plt da cokali, ta d'ago tana fad'in "Sannu da dawowa Baba." ya ce "Yauwa SEEDRAH yanzu Maman ki take ce min wai gidan goggon ku kika kwana." ta ce "Eh Baba ruwa ne ya tsare mu shine na biya gidan ta." ya ce "To a rika kiyaye wa dai, je ki kirawo min Maman naki." ta ce "To Baba." ko da taje ta sanar wa Mama Baba na kiran ta hijabin ta ta d'auka ta ce wa Mama zata shiga gidan su Nasiba ta duba ta jiya sun kwana tana zazzab'i. Koda ta shiga gidan su Nasiba a tsakar gida ta tadda Mama Kubura kishiyar Maman Nasiba wacce a hannunta take tun bayan rasuwar Maman Nasiba, ta gaishe ta tana tambayar Nasiba'n ta na ciki ne?. ta ce mata Eh. ta shige d'akin a kwance ta iske ta tayi shiru kamar me yin bacci, tana ganin SEEDRAH tayi mata murmushi, SEEDRAH ta dube ta da kyau daga jiya zuwa yau kawai tayi wata y'ar rama, girgiza kai tayi cike da tausayawa tana zama kusa da ita. a hankali Nasiba ta mike zaune, tana mai cigaba da k'wak'ulo murmushin yake da bai kai ciki ba dan b'oye damuwar ta. SEEDRAH ta ce "Yajikin dai Nasiba Allah yasa dai bata gane komai ba." ta ce "Ta so ta gane dan tun fitar ki d'azu dana fita zan shiga bayi tarika bina da kallo, har tana tambayata wai ko ciwo naji a kafata taga kamar ina d'ingishi, na ce mata a'a babu abin da yasame ni a kafar, SEEDRAH ina tunanin ranar da zata gane bazata tab'a yar da kan anyi min fyad'e bane, za ta ce maza nake bi da ma can tasaba fad'a shike nan zata sami hujjar da zata kafa har Baba ya yarda." kukan da ke son kwace mata ne yasa ta yin shiru tana mai zubda kwalla. da sauri SEEDRAH ta rike hannunta yayin da tuni itama hawaye yafara zuba a idon ta ta ce "In sha Allah bazata tab'a ganewa ba kidage da sarki da ruwan zafi har gurin ya gama warkewa gaba d'aya, yanzu tun da ta fara kawo zargi kan tafiyarki to zata saka miki ido ne sosai dan gano abun da take zargi,to kada kibata kofa kiyi kokarin ganin komai yayi normal ta inda zaki jirkita mata tunanin ta takasa gane komai, kuma bazata ganen ba in sha Allah." kai Nasiba ta gyad'a kana tashiga share hawayen ta, itama SEEDRAH hawayen nata ta share nan suka shiga d'an tab'a hira sai wajen karfe 3 kafin ta koma gida... Da yamma SEEDRAH na share d'akin Mama wani yaro yashigo ya ce "Wai SEEDRAH ta zo inji wani a waje." Mama dake zaune sakar gida ita da su Umma ta ce "Inji wa kenan kuma izinin wa ya nema daya zo gurin ta? je ka ce masa an bashi izinin zuwa wajen ta ne." Umma ce ta dakatar da yaron da fad'in "Je ka ce ta na zuwa." kana taci gaba da fad'in "Idan ma ba'a bashi izini ba yanzu idan ta fita in tasan shi takuma aminta da shi sai ta bashi izinin zuwa wajen mahaifinta ya nemi izini sai ya cigaba da zuwa." Mama ta ce "To ai sai ki zo ki je kiga ko waye ne, ai yanzu haka ma ita tasa shi ya zo zaiyi zuwan gashin kansa ne." mayafi SEEDRAH taja ta fito tana turo baki gaba "Ni wlh ban san da zuwan kowa ba koma wane ne zan je nasa me shi ni." tayi waje tana cigaba da turo baki da kunkuni, dan ita ba'a tab'a zuwa gurin ta haka kai tsaye ba hasali ma bata hira ko a waya ne dan ko saurayi bata da shi bawai kuma babun bane saurarar su ne bata yi. da mamaki take kallon wan da ke tsaye a kofar gidan nasu yana jin gine a jikin mashin d'in sa. b'ata fuska ta kumayi taja tatsaya jikin get, tana mai mamakin yan da a kayi yasan gidan su har ya zo. Kamal kuwa na ganin ta yasaki murmushi kana yata ko in da take. "Madam barka da warhaka, suna na Kamal." ya fad'a yana mai cigaba da sakar mata murmushin sa mai sanyi. fuska takuma had'e wa ta ce "Me kazo yi gidan mu ko kazo ne har nan d'in ma kakirawo d'an uwan naka ku kuma aiwatar da mugun nufin ku a kan mu?." kai ya jinjina kana ya ce "Kizamo mai yafiya mana, wlh bai aikata abun da ya aikata da gangan ba sharrin shaid'an ne." wani irin murmushi ta sake wan da ya dad'a bayyano da ainahin k'yan fuskarta kana ta gimtse ta ce "Wai ku mutane bakwa da kunyar yiwa shaid'an kazafi ne? ranan gobe kaje ka tsaya gaban ubangiji ka ce shaid'an ne ya sashi, shikuwa shaid'an zaifito yakare kansa dan baka da hujjar dazaka kuma dogara da shi kan shed'an ne yasaku aikata ba dai-dai ba, dan baka tab'a ganin sa da ido ba, ya tabbata kuwa kune shaid'anun kanku." ido ya zuba mata yana ji da kallon yanda take zuba zance y'ar karama da ita da iya tsara zance kamar wata babbar mace. murmushi ya yi ya ce "To Allah dai yana son me yafiya, da ma nazo ne naga ya jikin nata, dan Allah ko zaki kirawo min ita nagaishe ta da jikin?." baki ta tab'e ta ce "Bazata zo ba bata bukatar gaisuwar taka kaje ka da abin ka mun yafe." ta juya tana kokarin shiga gida ya yi saurin datakar da ita ta hanyar shan gaban ta ya had'e hannayen sa biyu alamun roko ya ce "Dan Allah kuyi hakuri kuyafe wa aboki na wlh abokina mutumin kirki ne sharrin shaid'an ne kawai da kuma kaddara, idan kuka bashi da ma zai zo har nan ya nemi gafarar ta shi kansa yanzu haka yana cikin mawuyacin hali da matukar damuwa da tashin hankali had'e da nadamar abun da ya aikata, amma ki sani babu bawan da ya wuce kaddara na tabbata shi yafita shiga damuwa da tashin hankali acikin halin da yake yanzu, yakuma shiryawa karb'ar duk wani hukuncin da za'a yanke masa." wani kallo ta wurga masa ta ce "Yafita shiga damuwa da tashin hankali?, bayan ita ya yi wa mugun illa a rayuwar ta, shi me yaragu a jikinsa?." tayi masa tambayar tana k'afe sa da manyan idanunta. d'an lumshe ido ya yi tare da kuma bud'e su a kanta jin yadda idanunta ke yawo cikin jikin sa. ya ce "Sanin ita ya raunata shiyasa ya shiga damuwar dan Allah kizamo mai dai-dai ta lamura dan suffarki yafi kama da mutanen kwarai, nafuskanci har yanzu baki huce ba zamu dawo nan da kwana uku da shi kan nan nasan kin dad'a hucewa kibamu damar ganin ta." k'wafa tayi tare da shige wa cikin gida batare da ta kuma ce da shi komai ba, shima ya haye mashin d'in sa ya yi gaba. ko da ta koma gida Mama ke tambayar ta wane ne?, ta ce daga cikin abokan ango ne. ta fad'a mata hakanne dan bata so ta tsananta bincike a kansa. Washegari da safe bayan SEEDRAH tayi sallah a d'akin su d'akin Mama ta dawo ta kwanta sabo da damin ta da Suhailat take da waya, duk da nauyin bacci irin nata har idan ana surutu a guri sai tayi da gaske kafin baccin ya d'auke ta. cikin jin dad'in baccin da take taji ana bubbuga ta da karfi, mika tayi cikin magagin bacci takuma juye tagyara kwanciyar ta. da karfi Halimatu ta d'aka mata duka a cinyar ta da zanin ta ya yaye tagefen santalelen cinyar ta d'aya, ta na fad'in "Banza mai shegen d'an banzan nauyin bacci har wani abun guduwa ya faru a gudu a barki kina wannan shegiyar baccin naki." a d'an razane ta mike tana susa gurin da Halimatu ta zuba mata duka tana fad'in "Wayyo ni me nayi miki?." Halimatu ta ce "Banza tashi dalla kowa ya fito ke kina d'aki kina baccin asara, gawasu can sun kuma janyewa Baba kud'i a account d'in shi." da sauri ta duro a gadon tana fad'in "Yau ma kuma?." waje tayi da sauri Halimatu tabi bayan ta. a can parlour'n Baba ta tadda duk y'an gidan tsaye curko-curko Baba ya na zaune yadafe kansa da duk hannayen sa biyu. hankali tashe tazube gaban sa tana fad'in "Baba wai sun kuma kwashe maka kud'i!?." hannunsa ya janye a kansa yad'an zuba mata ido kana ya gyad'a mata kai ya ce "Wannan karon ko sisi basu barmin ba duka suka kwashe." hawaye ne ya ciko idon ta kan kace me sun fara tsiyaya ta ce "Baba katashi kaje banki mana su binciko maka masu ai kata maka haka ai dai dole zasu san ko su waye ne." kai ya girgiza ya ce "Ba na tunanin zasu yimin komai a kai dan wancan karon ma dasuka ce zasu bincika har yau babu wata kwakkwaran amsa, nayi sintirin banki harna gaji, amma dai zanje dan yau kam gaba d'aya suka kwashe ni, dan jiya da daddare aka turo min da kud'in dana siyar da filaye da sauran kaddarorina kan zan gina wani masana'an ta, yau da safen nan kuma suka kwashe duka da ragowar kud'in da ke cikin accaunt d'in." ya mike ya na fad'in "Bari dai naje ko bankin basu fito ba zan jirasu har su fito." yazari makullin motar sa ya yi waje.. Gaba d'aya y'an gidan

Chapter 3 of 19