Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
wannan jiki mai daraja ce da ki ma, ba irin na ballagazan mataye masu raba jikin su sadaka a titi ba." hayakin sigarin sa ya buso tare da d'aura yatsansa kan lips sa ya ce "Shiiit wu ce ki b'ace min da gani." ya yi maganar tare da lumshe idanunsa yana cigaba da zukar hayakin sa. "Mssstt." ta ja dogon tsaki kana ta juya tab'ar gurin tana maganar zuci "D'an iska d'an kwaya d'an shaye-shaye bayi da aikin yi sai shan taba, yawani samin bakin shan tabarsa cikin baki msstt." takuma jan wani tsakin. tara miyau tayi cikin bakinta tawuce bathroom taje ta zubar, ta d'au burosh ta wanke bakin ta tana yamutsa fuska. tafito ta zauna bakin gado tana d'aga kiran Kamal da ya shigo wayar ta yanzu. Bayan kwana biyu Da yammacin ranar SEEDRAH na like da waya tana waya da abar kaunarta Kamal suna karantowa junar su karatun soyayya. cikin hirar ta su ya ce. "My SEEDRAH." ya kira sunanta ta ce "Na'am My Kamal." "Kifito gani a kofar gida." ido ta d'an waro ta ce "Wani kofar gidan?." "Gidan S.MAN nagaji ina bukatar ganin ki kin san dai zuciyata tayi matukar kokaki na tsawon watanni bazata iya ci gaba da hakuri ba ki fito na ganki dan Allah." numfashi taja a zahirin gaskiya itama tana bukace da son ganin nasa. "Gani zuwa." tafad'a tare da mikewa tsaye ta kashe kiran. bata jima da yin wanka ba dan haka bata bukaci yin wankan a yanzu ba. kaya ta ciro cikin wardrobe riga da siket na les had'e da gyale ta saka kayan daya zauna d'amas a jikin ta, pauda da man lips kad'ai ta shafa amma fuskarta yayi wani irin sihirtaccen kyau. ta saka 'yankunne da sarka kalar kayan kana ta kashe d'auri mai kyau. ta zura takalmi mara tudu sosai kana ta feshe jikinta da turare ta yafa gyalen a kafad'a ta d'au wayar ta ta fito ta nufi bakin get.. Baki da hanci maigadi ya bud'e yana kallonta harta nufowa inda yake, "Masha Allah kai Allah yayi halitta anan wai ashe dama haka take ban tab'a ganin ta a haka ba, kullum da katuwar hijabi fuskarta a d'aure." yafad'a a fili yana washe baki. SEEDRAH kuwa kayataccen murmushin dake shinfid'e kan fuskarta ta dad'a fad'ad'awa ta karaso in da yake. wani murmushi takuma sakar ma sa ta ce "Barka da warhaka sannu da aiki." baki ya kuma washewa ya ce "Yauwa yauwa barkanki dai sannunki." kai ta gyad'a da murmushi ta ce "Akwai bako a waje kabud'e masa ya shigo." d'an jim ya yi kana ya ce "Yallab'oi fa bai sanar min da zuwan wani ba, yau wa gashi can ma daga sama yana hango mu." yayi maganar yana nuna S.MAN dake tsaye can saman bene ya zura hannunsa d'aya a aljuhu d'aya hannun nasa kuma na kare da waya a kunnensa yana magana. kai ta d'aga ta kalleshi, taga idanunsa a kanta. ta saki murmushi kana ta maida dubanta ga maigadi ta ce "Au ashe bai fad'a maka ba shi ya ce nazo na sa abud'e masa kofar." "Au to haka akayi to bari a bud'e masa." da saurin sa yamasa jikin kofar yakuma washe hakora yana bud'e karamar kofa.. S.MAN na tsaye yana kallon su, duk da baya jin abun da suke fad'a. amma ya fahimci dashi ta yi karya maigadi ya bud'e kofar, dan yasaka masa dokar da bazai tab'a iya ketare shi ba muddun idan ba shi yasa shi ba. Kamal ya sako kansa cikin gidan yana amsa gaisuwar da maigadi yake mika masa fuskarsa d'auke da murmushi. ya yin da gaba d'aya hankalin sa ke kan SEEDRAH da ganinta ke kokarin zautar dashi. wani murmushi mai cike da so da kauna suka rika sakarwa junan su tamkar zasu rungume juna. "Bismillah." ta fad'a tana nuna masa hanya da hannu. a hankali suke takawa suna cigaba da sakar wa junan su murmushi had'e da daddad'an kalaman kauna da soyayya irin na wad'an da sukayi kewan junan su. Daga can sama kuwa S.MAN har lokacin na nan tsaye yana kallon su, sai dai a yanzu fuskarsa babu annuri. ganin ta nufo da Kamal gurin hutawar sa da sauri yajuya yanufo kasa.. suna kokarin zama S.MAN yakaro gurin. ganin sa yasa Kamal fasa zaman cikin nuna farinciki da jin dad'in ganin masoyin sa agaban sa ya mika masa hannu yana fad'in "Barka dai gwarzon jarumin mu nayi farinciki ganin ka sosai." Kamal ya ruko hannunsa batare da ya mika masa hannun nasa ba, yarike gam yana mai farin cikin ganin d'an kwallon da ya fi kauna arayuwarsa. yaciro wayar sa yamusu selfee yana cigaba da fad'in "Yau zansha comments a media dan kuwa yanzu zan d'aura hoton nan." SEEDRAH kuwa fuska ta yamutsa ganin yanda Kamal d'in yawani zaƙe, shiko S.MAN sai wani shan kamshi yake. ta ce "My Kamal zauna bari na kawo maka ruka." ta d'an dubi S.MAN ta ce "Wannan shine Kamal mijin da zan zaura." takarashe maganar da kad'a narkakkun kwayar idanunta. kana tajuya ta nufi ciki dan d'auko wa Kamal abin sha. kichin ta shige ta d'au d'an madaidaicin tray ta d'aura drink's kala biyu a kai had'e da glass cup. ta juyo zata fita sai ganin mutum tayi a gaban ta. wani kallo ya wasa mata "Yaushe kika sami gurin zama da har zaki shigo min da wani gardi d'an kauye cikin gida, har da d'aukar drinks zaki kai masa, da kud'in Alhj Musa aciki a ka siya." harara ta wurga masa tare da murgud'a masa baki ta ce "Kagode Allah ma da har wani yashigo gidan ka yaci abinci ko sha wata kilama ta sanadiyyar haka kasami gafara da rahamar Allah, kan abubuwan da kake aikatawa na sab'on Allah, Kamal mutumin kirki ne mutumin kwarai in har iskanci da shaye-shaye shine waye wa to har abadan bazai tab'a wayewa ba zamansa a hakan kuwa yafiye masa rayuwar shaye-shay...." bata kai ga karasawa ba taji saukar mari a fuskarta. zafin marin yasata sakin tray'n yafad'i kasa ya tarwase. ya fizgota ya had'ata da jikin garu ya matse ta, sosai kake iya hango b'acin rai kan fuskarsa. cikin kakkausar murya mai nuna zallar b'acin rai ya ce "Kin tab'a kamani da kwaya ne?! kin tab'a ganina ina shaye-shaye?! kin tab'a ganin wani kayan maye cikin gidan nan!!?." yafad'a cikin karaji sosai yakuma matseta. "Idan kika sake jifana da kalmar d'an shaye-shaye sainaga wan da ya tsaya miki!, bantab'a shan wani kayan maye ba ni ba d'an shaye-shaye bane, sigari kad'ai nake sha shin ban tab'a fad'a miki bane!." waye kema da har sai na rika fad'a miki abin da yashafi rayuwata iye!." yasaka kafarsa ya take nata had'e da murkushe sai da ta saki karar azaba, kana yacigaba da fad'in. "Kefa 'yar aiki ce wakawai wacce ubanta yaci bashi ya kasa biya, wlh idan kika sake dangantani da d'an shaye-shaye sai na b'ab'b'allaki na taraki anan!!." ya hankad'a ta gefe yajuya yafita a kichin. "Wlh Allah ya isa mugu azzalumi kawai." ta tsunkuya ta rike kafarta tana yarfe hannu. Allah ya isa tarika ja masa yafi cikin kwando, ba karamin zafi da rad'ad'i kafarta yake mata ba. Kiran Kamal ne yashigo wayarta bayan ta d'aga ya ce "My SEEDRAH natafifa yayan mu ya ce akwai abun da yasaki kiyi masa a ciki zan dawo idan kin gama." shiru tayi bata iya cewa komai ba. ab'angaren Kamal d'in ma kashe wayar ya yi, SEEDRAH ta mike tana bin wayar da kallo ta ja kafarta tana d'in gishi ta fito. a parlour ta ganshi zaune da waya a kunnensa yana magana. harara ta wurga masa tare da jan tsaki mssttt. harta gotashi ta ji ya ce "Zo nan fitsararriya mara kunya wa kike wa tsaki." a kufule cike da jin haushinsa ta ce "Da wan da ya tsargo." takarashe maganar da murgud'a baki cike da tsiwa tashige d'aki. tana kokarin rufo kofar ya sako kansa cikin d'akin. ido ta kura masa tar cike da tsana kana ta yamutsa fuska. shiko kan lab'b'anta ya kura wa ido kana ya matsota. tabud'e baki zatayi magana kawai ta sinci bakin sa cikin nata, wani irin tsotsa yake mata mai had'e da mugunta. ido tarika ciccirewa tana ture shi a jikinta, kana daga bisani ya sake ta, ya ture ta gefe yafice cikin d'akin. Zubewa tayi a bakin gado tare da sauke numfashi mai sauti, sai kuma da sauri takai bayan hannunta ta goge bakinta. A fili ta furta "Bazai yiwuba." sai kuma da sauri ta mike tafita bata ganshi a parlour'n ba, sama ta haura nan ma baya parlour, ta isa bakin kofar bedroom d'in sa ta bubbuga da karfi, zata kuma bugawa taji an tab'ata ta baya. da sauri ta waigo ad'an razane hayakin sigarin daya zuka ya fesa mata a fuska. da sauri ta kawar da kanta had'e da d'anyin tari. hannu yasaka yajuyo fuskarta tare da yi mata tambaya da ido alamun me ya kawo ta. da sauri ta janye fuskarta tana kokarin barin gurin dan hayakin bakaramin tada mata hankali ya yi. ya dakatar da ita ta hanyar ruko hannunta ya janyo ta jikinsa kana ya maidata ya mannata da jikin garu yasaka hannu ya kare ta ta hanyar dafe jikin garun. sigarin hannunsa ya yar kasa kana ya take da takalmin sa, d'aya hannunsa yakuma sakawa ya dafe jikin garun yazamana da yasata a tsakiyarsa. da ido yakuma yi mata tambayar me ya kawo ta. kai ta kawar gefe tare da saka hannu tashiga ture kirjinsa. rankwafo da kansa ya yi gefen wuyan ta tare da fesa mata numfashi batare da ya d'ago kansa ba ya ce "Idan rashin kunya kika zo min zaki gwammaci dama baki zo ba, oya wuce kibar nan." yafad'a yana janye hannayensa, ai kuwa da sauri taja kafafunta tayi gaba. Sai da ta dawo d'aki take jin haushin kanta dama tsayawa tayi ta ja masa layi a kan abubuwan da yake mata. A b'angaren S.MAN kuwa bathroom ya wuce yana matse MAN d'in sa daya ke ta zillo cikin wando. kayan jikin sa ya tub'e ya sakarwa kan sa ruwa yana jan tsaki. ya b'ata lokaci yana tsaye ruwa na sauka a kansa bai kuma sa Man d'in sa ya kwanta ba tamkar dad'a kara masa girma da kumburi a ke. jin ana kiran salla yasashi yin al'wala ya fito. yayi shirin zuwa masallaci ya tafi. Bayan SEEDRAH ta idar da sallar isha ta fito ta nufi kichin. kayan tea d'in sa ta had'a masa had'e da ruwan zafi a flas ta kwasa ta haura sama. bedroom d'in sa ta nufa sanin bataji motsin dawowar sa daga masallaci ba. tana kokarin dire tray'n saman bedside d'in da take aje masa a kai ya bude kofar bathroom ya fito d'aure da towel a kugunsa. hannunsa na kan MAN d'in sa yanata kokarin gyara zaman sa dake son kwance towel d'in sai tsaki yake ta ja akai-akai. da sauri ta waigo jin karar kofa ai kuwa ta ture flaks d'in yafad'i kasa ruwan ciki ya wasu mata a kafa. kara ta saka tare da tuma tsalle tana yarfe kafar bata ankara ba taji tayi karo da abu, ga kuma wani abun da yawani zungure ta kamar wani muciya. "Wayyo Allah." takuma fad'i tana cigaba da yarfe kafar. hannu ya saka ya rukota gaba d'aya yan da take wani tsalle had'e da juyi gaba d'aya ilahirin jikinta motsawa suke, hakan kuwa ya haifar masa da wani irin mashahuriyar fitinanniyar hautsunar kwakwalwa. MAN d'in sa dayake ta fama da shi tun d'azu sai wani zullo yake tamkar zai tsinke yakara kumbura tamkar zai fashe. matseta ya yi sosai ajikinsa yashiga kissing d'inta tamkar zai cinye ta. tuni ta nimi zafin nan ta rasa tashiga kokuwar kwace kanta hankali a matukar tashe. wani irin waro ido tayi jin hannunsa na yawo kan ababen kirjinta yayin da bakinsa kuwa ke sarkafe cikin nata, hannunsa guda kuwa na bayan ta yana kokarin zuge zip d'in rigarta. "Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un." abunda take furtashi cikin zuciyarta ke nan. da karfi ta daddage ta ture shi a jikin ta dai-dai lokacin da ya zuge zip d'in rigar nata da gudu tabar d'akin amatukar tsorace. tana shiga d'aki ta maida kofar tarufe tajingina da jikin kofar tare da dafe kirjin ta. "Fyad'e fyad'e zaiyi min innalillahi wa Inna ilaihirraji'un, lallai wannan ya tabbata tabbataccen mara imani mugu azzalumi." ta furta murya na rawa cike da mugun tsoro. a b'angaren S.MAN kuwa tana fita yazube bakin gado tare da jan tsaki, hannu yasaka yad'an matse kasan marar sa dake murd'a shi, tsaki yakuma ja ganin yan da MAN d'in sa take ta wani irin zillo wane zata tsinke. wani tsakin yakuma ja tare da fad'in "Mayyar yarinya kawai." A daren ranar duk bacci irin nata sai da ta raba daren kafin bacci ya d'auke ta. shima d'in cikin tsoro da fargaban kada ya yi jingina bango yakuma shigowa kamar yanda ya shigo rannan, ta kwanta da shirin goge zatabar gidan dan bazata cigaba da zama tana ji tana gani ayi mata fyad'e arage mata kima ba, yazama dole ta tseratar da kanta daga faruwar hakan. washegari guri nayin haske tafito da sauri dan tasan zuwa yanzu yagama motsa jikin sa. Da sauri ta isa bakin get bataga maigadi ba addu'a take Allah yasa kofar a bud'e take, ai ko tana tab'awa taji ta a bud'e da sauri tasa kai tafita. tana jin mai gadi yana fad'in "Hajiya dawo wa ya ce ki fita." Shafa gefen fuskar sa S.MAN ya yi dake kallon duk abin da ke faruwa daga can saman bene ya juya yana cigaba da zukar sigarin sa cikin kwanciyar hankali.. Tafiya take da sauri har lokacin zuciya da jikin ta basu dai na cirawa. sai da tayi tafiya mai d'an nisa kafin ta d'an sami nutsuwa kana ta tsari adai-daita zuwa unguwar su Nasiba. a hanya ta kira Kamal ta ce su had'u a gidan su Nasiba. tana isa ta ce wa mai adai-daitar yad'an jira bari ta karb'o masa kud'i dan bata fito da ko sisiba. ta shiga ta karb'a kud'i gurin Nasiba ta kawo masa. Kamal daya hango saukarta daga can kofar gidan su yakaraso. murmushi suka sakarwa junan su sai kuma ta b'ata fuska. a d'an marairaice ya ce "Me kuma nayi?." ta ce "Dan ya ce katafi sai ka tafi ko da ma ba son gani na kake da gaske ba, kabi ka ishe ni da kana son ka ganni." murmushi ya yi yakama kunnuwan sa ya ce "Ayi min afuwa amma tabbas babu ko shakka ke nake muradin gani, sai dai gaba da gabanta shid'in babban wa uba ne, ayi hakuri kar a cinye ni da tsiwa." hararar wasa had'e da so da kauna ta sakar masa kana ta juya ta nufi ciki. da sauri yabi bayan ta yana fad'in "Ranki shi dad'e kimbiya ayi hakuri mana." maman Zeey dake sakar gida tana aiki ganin Kamal nabiye da ita had'e da hannu alamun roko tayi murmushi, tana jinjina girman so irin wannan. fuska ya marairaice kamar karamin yaro ya dubi Maman Zeey ya ce "Maman Zeey tayi fushi ki ce baki yardaba idan ta bari zuciyar d'anki ya fashe." murmushi mai sauti Maman Zeey tayi. Zeey dake wanke-wanke kuwa waka ta soma musu "A hayye soyayya ruwan zuma masoyiya tana wahalar da masoyi masoyiya kara wahalar da masoyi idan yana so haka zai jure." harara ya wurga mata ya ce "Yar sa ido kawai." tintsirewa da dariya tayi ta ce "Oh Ya Kamal ni kuma meye nawa." "Yi fama da wanke-wanken ki." cikin muryar dariya ta ce "Ina kai ma kuwa." Murmushi SEEDRAH tayi tawuce sashin Nasiba bayan ta kuma gaida Maman Zeey dake ta zolayar ta tawuce sashin Nasiba cike da jin kunya Kamal ya biyo bayan ta. Tana shiga Nasiba ta taho ta rungume ta cike da murnar ganin ta. ido SEEDRAH ta waro ta ce "Ke wai oyoyon naki baya kare wa ne ina shigowa ta d'azu kinyi min so kike ki murkushe mana baby." dariya Nasiba tayi ta ce "To ai duk murnar ganin ki ne rabon da nagan ki wata nawa, ga Nabila can ta kullace ki fushi sosai take da ke, har ta haihu taje wankan gida tadawo bakije jin dubata ta." kai kawai ta girgiza akan ranta ta ce "Bazaku gane bane wancan bakin mugun daya maida ni matar kulle a gida kamar wacce aka bashi ni abakin bashinsa ya siyeni haka ya maidani." taja kwafa a fili. kusa da Nasiba ta zauna inda Kamal ya zauna kusa da abokin sa Mukhtar ke zaune. SEEDRAH ta dubi cikin ta daya d'anyi girma ba cancanba irin dai girman cikin fari ta ce "Wai yaushe ne zaki haihu ne kam?." fuska Nasiba ta marairaice ta kalli Mukhtar fuska a marairace ta ce "Abban Seedrah yaushe ne zan haihu." murmushi ya yi ya ce "Kin kusa saura kad'an Ummie'n Kamal." baki da hanci SEEDRAH ta bud'e ta ce "Wai sunan baby's d'in ke nan sunan mu?." Nasiba ta ce "Eh ai Kamal ne ya saka ya ce idan aka haifi mace sunan ki za a saka mata idan kuma na miji ne sunan sa, jimin son kai fa ni da ma Mukhtar zan saka idan najimi ne." dariya duk sukayi SEEDRAHA ta ce "Kai amma naji dad'i sosai My Kamal gaskiya ka burge ni." ido ya kashe mata ya ce "Wani abun ma sai kin shigo hannuna zakiga abubuwan burgewa." hararar sa tayi ta ce "Kafara ko ni bari ma naje gidan Nabila naga baby." "Sai dai kirika zuwa kina ganin baby'n mutane ke bazakiyi zuciya aga baby'n mu ba ko." Kamal ya fad'a yana dariya kasa-kasa. harara takuma wurga masa. Mukhtar shima dariyar ya yi yana bugun kafad'ar sa kana ya ce "Yakamata kam ayi duba da lamarin nan gimbiya SEEDRAH." ita dai mikewa tayi Nasiba ma ta mike ta ruko hannunta cikin yin kasa da murya ta ce "Ya dai naganki haka tun d'azu nake ta karantar yanayin ki kamar ba a dai-dai kike ba." "Uhm ba komai kawai bana d'an jin dad'i ne." shiru Nasiba tayi bawai ko dun ta yarda da abin da kawar tata tafad'a ba sai dai dun bata son yawaita yi mata tambaya gaban su Kamal ne amma tabbas ta fahimci tana cikin damuwa. itako SEEDRAH bata jin zata iya sanar mata da abun da ke faruwa dan tana ganin abun kunya ne a gare ta duk da kuwa Nasiba aminiya ce a gare ta. tayiwa Nasiba sallama suka fito da Kamal, Mukhtar zai bisu Kamal ya ce ya zauna basa bukatar rakiya bare yaji abun da zasu fad'a. suna fita kofar gidan SEEDRAH ta dubi Kamal da kyau ta ce "Kamal kana so na kuwa?." da sauri ya waro idanunsa ya ce "Anya kinsan me kike fad'a kuwa amma sam banji dad'in fitar kalmar nan daga bakin ki ba, ko makaho ne ya dafa zuciya ta na tabbata zai fahimci irin girman so da kaunar da nake miki." ido ta rumtse da karfi kana ta bud'e su a kansa ta ce "To gobe kaje ka kai kud'in aure na gidan mu." wani irin tsalle ya tuma tare da fad'i "Yes yess yesss." sai kuma ya d'an dai-dai ta nutsuwar sa yana son karantar yanayin ta kana ya ce "Are you okay." kai ta girgiza ta ce "Yess I'm okay kayi yadda nace." "Insha Allah." ya fad'a kana suka nufi gidan Nabila a kafa suna d'an tab'a hirar su. ko da suka isa da fari Nabila ta nuna fushin ta kan rashin zuwan SEEDRAH da ta haihu, SEEDRAH tayi ta bata hakuri har ta huce ta d'auki babyn data ci suna Ishmat tayi ta mata wasa kana daga bisani tayi mata sallama suka baro gidan, Kamal ya d'auko mashin d'in sa ya kaita gida. Tayi missing d'in Mama bata tsaya hira da shi a waje ba ta ce anjima ya dawo, ta shige gida da sauri a sakar gida ta tadda su Mama da gudu tafad'a jikin Mama tana fad'in "Oyoyo Mama." murmushi Mama tayi dan tayi kewar d'iyar tata ba kad'an ba. SEEDRAHA ta mike jikin Mama ta zauna gefen ta kana ta gai da Umma sannan ta gaida Maman. duk suka amsa cikin sakin fuska suna tambayar ta ya aikin nata. Suhailat da Halimatu kuwa har rige-rigen tambayar ta ya S.MAN ya ke. mikewa tayi tana fad'in "Me zai hana kuje gidan ku gano sa." "Mara kunya halin naki na nan dai." Halimatu ta fad'a tana hararar ta, bata kuma bi ta kansu ba ta shige d'akin Mama tana shiga ta haye gado tayi kwanciyar ta, ai ko ba jimawa bacci yasami nasarar sace ta, nan tashiga rama baccin da bata samu tayi shi yadda ya kamata ba jiya. sai wajen karfe biyar da rabi ta farka, tashiga bayi ta yi al'wala ta fito tagabatar da sallar la'asar. tana zaune kan sallaya Mama ta shigo ta dube ta cikin kula ta ce "Kin ta shi?." kai ta gyad'a ta ce "Eh." kana ta langwab'ar da kai gefe ta ce "Mama yunwa ban karya ba." zama Mama tayi a bakin gado tana fad'in "Ga ragowar kunu can da jiya na dama sauran gari daddare nasha na rage, da safe nasha naso sha da rana naji kirjina na suya sai na hakura ganin zai tada min olsa." murya ta mararirace ta ce "Kunu kuma Mama abinci dai." "Uhum SEEDRAH ke nan muna dai kan jiran Baban ku har yanzu bamuga aike ba." jikin ta ne ya mutu ya yin da taci wasu zafafan kwalla sun ciko mata ido, wato dai Mama bataci abinci ba kenan tun safiya bayan kunun da ta sha wan da jiya ma haka shi d'in ta sha. "Innalillahi wa Inna ilaihirraji un ya Allah ka kawo mana mafita cikin lamuranmu." a hankali ta rarrafo ta kwantar da kan ta kan kafar Mama ta ce "Mama bakiyi waya da su kawu Yusufa bane." kanta Mama ta shafa ta ce "Banyi musu waya ba SEEDRAH nauyin tambayar su nake ji duk da nasan bazasu tab'a son gani na cikin wani haliba, amma abaka yau a baka gobe yawuci wasa, wan da ya haliccemu shine kad'ai baya gajiya da bamu kuma munakan rokon sa zai warware mana lamuran mu, ki tashi ki koma bakin aikin ki ga magriba ta kusa kada dare ya yi miki a hanya." hawayen da suka zubo mata ta share kana ta d'ago ta gyara zaman ta kan sallaya sannan ta ce..............! Mommyn Twins ce 🌺 *ƘARSASHI!* 🌺 *NA* *RASHEEDAT S DIRECTOR* ( _Book 1_) ~Free page~ ( _Bismillahirrahmanurrahim_) _Alhamdulillah Ina yiwa Ubangijin buwaye gagara misali godiya daya kuma a ramin lokaci na kuma dado wa a wannan karon a cikin littafi na mai suna ƘARSASHI kada ku manta kafin zuwan ƘARSASHI HAMDAH ya zo muku masoya ku baza kunnuwan ku ku kuma biyo ni cikin labarin nan mai suna ƘARSASHI ina mai yi muku albishir da faranta wa kamar yadda HAMDAH da sauran littatafai na suka saba zuwar muku🤗 ƘARSASHI salon sa da banne labari ne mai ƙwanƙwasa zuciya salon labarin na daban ne. ku dai ku biyo ni cikin labarin nan kada ku mance da sunan sa ƘARSASHI! ƘARSASHI!! ƘARSASHI!!!_ _Littafin na kud'i ne 400 Account no 3170524141 Rashida Salihu first bank kokuma katin Mtn ta wannan number 08034690723 a tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723_ *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* page 20 "Mama nifa bazan koma ba na dawo gida ke nan, yafad'i wani abun da za ayi masa ya fanshi kud'in sa, ni nagama yi masa aiki, ga su Aunty Suhailat da Halimatu su je suci gaba da yi masa, tun da duk suna son zuwa gidan sa da ma." "SEEDRAH kasa zaki wasa min a ido, ina kawazucin iyayen nan da nake gani tare da ke?, idan baki taimake ni ba wazai taimaka min SEEDRAH, ke yake da bukatar yi masa ai ki basu Suhailat ba." suka jiyo muryar Baba daya fad'o cikin d'akin yana sauke waya a kunnen sa, ko ba a fad'a ba tasan S.MAN ne yakira sa yaku yi masa barazanar daya saba. Baba yacigaba da fad'in "SEEDRAH ko mai na dad'a tab'arb'arewa ko dubu talatin bana da shi nawa na kaina bare miliyan 30, a ina zan samu na biya sa, zaman ki cikin gidn shi kina yi masa aiki shine rufin asirina, idan kika ce zaki bar aikin nan to tabbas muma zamu bar gidan nan, ko kud'in d'akin haya d'aya bani da shi sai dai mukoma titi rayuwar mu ta kare a can." ido ta rumtse da karfi ya ilahi ya lillahi me yake shirin faruwa da ita ne kam. Baba ya fita ya na fad'in "Kiyi tunani dai SEEDRAH." Mama ta ce "Hakuri zakiyi ki koma hakan shine kad'ai rufin asirin mu." sai a sannan ta bud'e idanunta wanda kake iya hango damuwa had'e da tsoro da fargabar faruwar wani abu cikin su. ta ce "Mama shin bakwa tunanin me duniya zasu ce a kanmu, ina gidan wani da bashi da mata ina yi masa ai ki kada kusa duniya tafara zargin mu mana, Mama ina jin tsoro ina jin tsoro Mama, kuyi hakuri ku barni na zauna a nan kusa Halimatu ko Suhailat suje suciga da yi masa aikin dan Allah Mama." ta karashe maganar da rike hannun Mama gam. shiru Mama tayi tana nazartar ta, sai

Chapter 16 of 19