Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ce "Mama ta shi mutafi asibiti jikin nan naki magani kad'ai bazai wadatar ba." Mama ta ce "Bani magani tukun nasha gashi can." ta nuna mata wani laida dake gefe, da sauri ta mike tad'au laidar ta bud'e magungunar da Mama take sha ne a ciki masu yawa, da sauri taje ta d'ibo ruwa a kofi tana mamakin a ina aka samu kud'i aka siyi magunguna masu yawa haka. ta bud'e maganin ta ciro yanda take sha ta tallafo kanta tasaka mata maganin a baki had'e da ruwa tasha. kana ta gyara zamanta da kyau tayiwa Mama pillo da kafarta dan tasan yanzu bacci zai d'auke ta, ai kuwa ba a d'au wani lokaci ba bacci yad'auke ta. Shiru SEEDRAH tayi tana kallon fuskar Mama wani irin tausayin ta ne ke shigarta, ganin yanda ta rame tayi duhu mai da kwallar daya ciko mata ido tayi tare da sauke numfashi. a hankali tashiga kunce kitson dake kanta tana kitsa mata su da d'ai-d'ai harta gama. SEEDRAH na zaune harsai da Mama ta farka da kanta, tana ganin ta bud'e ido tashiga jera mata sannu ya take jin jikin nata. Mama ta mike zaune ta dubi SEEDRAH tana fad'in "Ke ai kafarki sai tayi tsami yabaki saka min pillow ba kawai." ta ce "Mama bazaiyi tsami ba tashi muje asibiti kawai adubaki." "Da wani kud'in SEEDRAH maganin dana sha ma ya wadatar." ta ce "Ga wasu 'yan kud'i a hannuna S.MAN ne ya bani su cikin kud'in aikina muje asibiti kawai Mama." da kyar ta lallab'a Mama ta yarda suje asibiti dan cewa tayi ta barta kawai ita tasha magani ta warke. asibitin da dama can Mama ke zuwa suka tafi nan da nan kuwa suka sami ganin likita, bayan ya duddubata ya ce zai sauya mata magani wan da in sha Allah sai tafi jin dad'in sa fiye da wanda take sha. bayan ya rubuta maganin SEEDRAH ta karb'i takardar suka fito sunayi wa likitan godiya. gurin sai da magani dake cikin asibitin SEEDRAH ta nufa bayan ta ce wa Mama ta zauna kan wani kujera ta jirata taje tabiya kud'in gwaje-gwajen da akayi mata takuma siyi maganin da likita ya rubuta musu. ko da ta mika takardan aka bata magungunar ta karb'a kana ta dubi matar dake bada maganin tana fad'in "Yauwa nawane duka kud'in mu ya kama?." matar taduba takardan maganin kana ta dubi SEEDRAH ta ce "Am akwai wani maganin da aka sako ta ciki wan da bamu da masaniya a kansa shi kud'in sa d'ari tara ne shike nan kud'in." SEEDRAH ta ce "To sauran fa da kud'in gwaje-gwajen duk bamu biya ba." ta ce "Iya kud'in dai kenan." da mamaki SEEDRAH ta ce "Asibitin yadawo na gwamnati ne?." murmushi matar tayi mata batare da ta ce mata komai ba. ta juya tana mai mamakin yanda akayi asibitin ya koma haka dan dai ita a sanin ta ma, kud'in data zo dashi sai dai suyi maneji bazai kai kud'in zuwa suga likita har ya siya musu magani ba. bare kuma wannan maganin da aka canza basai an fad'a ba kasan mai tsada ne. tazo in da Mama take ta zauna gefen ta tana fad'in "Mama yaushe asibitin nan ya koma na gwamnati kigafa iya d'ari tara suka karb'a, naga ko asalin asibitocin gwamnatin ma sai ka siyi magani da kud'in ka." Mama ta ce "Ikon Allah ko dai sun yi rafkanuwa ne." "A'a wlh Mama haka ta ce min iya kud'in kenan." Mama ta ce "Ikon Allah to Allah ubangiji yasaka musu da alkhairi." ta amsa da amin kana suka mike suka fito daga cikin asibitin suna mai mamakin lamarin har suka komo gida. Ko da suka dawo gida bayan su Umma sun shigo sunyi wa Mama ya jiki sun fita, SEEDRAH tabaiwa Mama maganin kamar yanda tagani a rubuce. sannan ta shiga kichin ta girka mata abin da tasan zata d'anci da marmari cikin kayan abincin da 'yan uwan ta suka turo mata. SEEDRAH na zaune a gefen ta tana cin abincin suna d'an tab'a hira, Mama ta dube ta cikin kula ta ce "Ke ban ga kinci komai ba." murmushi SEEDRAH tayi ta ce "Zanci sai nayi sallah." kai Mama tajinjina. hannu SEEDRAH ta mika ta janyo laidar magani wan da d'azu zuwan ta tagani cikin d'akin ta baiwa Maman ta sha tana fad'in "Yanzu Mama ya za'ayi da wannan maganin tun da an canza miki wasu, gashi da yawa kuma maganin, Baba ne yasiyo ya mayar kawai yayi musu bayani subashi kud'in." Mama ta ce "Bana tunanin shi ya siyo dan tun da farar safiya ma ya fita, d'azu ne ina kwance yaro ya yi sallama ya kawo ya ce kuma wai inji Falalu mai kyamis, to ban sani ba ko Baban nakune yayi masa magana ya basa bashi ban dai sani ba kam watakila shi d'in ne, kokuma Halimatu dan naji kafin fitarsa yana ce mata tabashi bashin kud'i dan jiya saurayin ta yazo ya mata kyauta." kai SEEDRAH ta jinjina tare da fad'in "Tun da Falalu ne bari na kai masa nasan zai bada kud'in idan an bashi, in kuma ba a basa ba sai ya karb'i abin sa." Mama ta ce to, ta d'au mayafin ta da laidar maganin tayi waje. Ko da ta isa gurin Falalu bayan sun gaisa ya ce "Kwana biyu ina kika shiga ne SEEDRAH ko kinyi tafiya ne?." Eh kawai ta ce masa kana ta d'aura da fad'in "Maganin da ka bayar a kaiwa Mamana ne nadawo maka da shi, munje asibiti d'azu ancanza mata magani, shin Baba ya baka kud'in maganin ne?, idan ya baka to dan Allah ka karb'i maganin ka bamu kud'in idan kuma bai baka ba to gashi ka rike abinka." ya ce "Eh anbani." ya ciro kud'i ya kirgo ya mika mata. ta karb'a tare da yi masa godiya ta juyo gida ta baiwa Mama kud'in ta ce ta ajiyewa Baba in agun Halimatin ya karb'a in ya dawo ya maida mata. Har yamma lis SEEDRAH na gidansu cikin walwala tana kusa da Mamarta, ganin bata da niyyar tafiya ne yasa Mama ce mata ta tashi ta koma gurin aikin ta dare nayi. ta ce ita kwana zatayi bazata iya tafiya ta barta bata da lafiya ba. Mama ta ce ita kam ta sami sauki ta tafi abinta, da fari tuburewa taso yi sai da Maman tayi da gaske kafin tayarda zata tafi amma wai sai in Baba ya dawo sun gaisa tukun. Mama ta ce tatafi abinta kawai sa gaisa a waya dan bayanzu zai dawo ba sai dare. acikin kud'in da ta zo dashi kud'in abin hawan da zai komar da ita kawai ta cire ta bawa Mama sauran ta ce ta ajiye tarika amfani da su. tayiwa y'an gidan sallama ta tafi badun taso ba, Mama ta rakata da addu'a da sanya wa rayuwar ta albarka. Tana fita Suhailat ta biyo ta ta ce "Yauwa SEEDRAH kina da lambar Ya S.MAN ki bani?." kai ta girgiza cike da takaicin 'yar'uwar tata ta ce "Ni kuma me zai had'ani da lambarsa aiki kawai nake masa ba a dana lambarsa ba." tsaki Suhailat taja ta ce "Jeki ba cewa nayi ki gaya min magana ba samo lambarsa ai bazai bani wuya ba." "Da dai yafi kam ki samo da kanki ko ba komai kya kulla kawa da wulakanci." cewar SEEDRAH tayi gaba abinta. A b'angaren Maman ma ita ma kanta batason rabuwa da d'iyarta d'aya tilo duk da karancin shekarun ta takan iya jajircewa wajen kula da lamuranta, sai dai babu yanda ta iya hakan ne kad'ai zaisa su tsira da mutuncinsu. SEEDRAH na fita ba da jimawa ba Baba ya dawo Mama tayi masa bayani kan kud'in maganin da SEEDRAH ta karb'o, ya ce baima karb'i kud'in Halimatu ba hasalima bai ma je shagon Falalu ba, yadai fita niman kud'i ne yasamu yazo ya siya mata maganin sai yanzu ke nan dawowansa. amma bari ya huta zaije gurin Falalun yaji ta in da kud'in yafito. SEEDRAH nashiga gidan S.MAN ana kiran magriba, tana shiga parlour shikuma yana sauka daga sama cikin shirin zuwa masallaci. wani kallo ya watsa mata cikin gimse fuska ya ce "Bari na dawo daga masallaci zaki fad'a min dalilin daya sa kika karya dokan dana sa miki." bata kula shiba ta shige d'aki shiko yayi waje, tana shiga kuwa ta kulle kofar da key bata kuma bud'e wa ba sai washegari.. SEEDRAH ce tsaye jikin mirro d'aure da towel a kirjinta fitowar ta daga wanka kenan. bra da pant ne rike a hannunta ta saka pant d'in da sauri-sauri dan batayi sallar magriba ba ga shi kuma har an fito daga sallar isha. kana ta zame towel d'in a kirjinta tana kokarin saka bra aka turo kofa. da sauri tayi wurgi da bra'n tayi hanzarin jan towel d'in kirjinta dai-dai lokacin daya sako kansa ciki batakai ga karasa d'aura towel d'in ba. baki ta turo gaba tana wurga masa harara cikin jin haushin yanda ya fad'o d'akin kai tsaye babu sallama ta ce "A gaskiya bai kamata karika fad'o min cikin d'aki haka batare da sallama ko niman izinin shigowa ba, ko ma mene ne karika fad'a min daga wajen bakin kofa ai dai zanji." "Ni da gida na har sai na nimi izinan shiga wani guri a cikin sa, duk in da nake son shiga zan shiga batare da niman izini ba, ke baki isa ki kafamin doka a gida na ba." baki ta murgud'a cike da tsiwa tana fad'in "Gidan ka ne d'akin nan kuma gurin zamana ne' kamata yayi idan zaka shigo karika yimin sallama, ba karika fad'omin cikin d'aki kai tsaye ba." a hatsale yasoma takowa cikin d'akin yana fad'in "Doka zaki gindaya min cikin gida na ke zaki fad'a min abin da zan yi a cikin gida na ko da Alhj Musa muka had'a kud'i muka gina gidan." ganin haka yasa ta juyawa da sauri tayi kofar bayi tatura kofar da sauri tasako kafarta d'aya cikin bayin aikuwa tsamtsin tais yajata tatafi suuuuuu tafad'i timmm a kasa. wani irin gigitaccen kara tasake tare da fad'in "Wayyo Allah na wayyo bayana kafata kaina wayyo Allah na." tsaki yaja yajuya yana fad'in "Kifito yanzu idan ba hakaba sai na canza miki kamanni ki b'ata lokaci kigani." SEEDRAH ko kukan wahala ta sake tayi-tayi ta iya d'aga ko da hannunta ne ta kasa, dan ba karamin fad'uwa da buga kanta tayi ba, nan da nan guri yashiga juya mata a take ta sume a gurin.. S.MAN na zaune a parlour ganin shiru bata fito ba yamike a kufule ya nufi d'akin yana fad'in "Yarinyar nan idan ba dukan sa'a nayi mata ba bazata dai na sab'a magana ta ba." ya tura kofar da karfi yashiga, tsayuwa ya yi cikin d'akin yana waige-waige ganin bata ciki, can ya hangota kwance cikin bayi kasan cewar kofar bayin abud'e take. ya tako ya iso bakin kofar yana fad'in "Ke wai baki tashi ba okay nan yazamo miki gurin kwanciya ma kenan, zaki tashi ne ko sai na tattakaki anan." ido yad'an tsura mata ganin duk maganar da yake ko motsi batayi ba, sosai yad'an tsura mata idon nan ya lura da gaba d'aya bata motsi. a hankali ya sunkuyo kanta yakamo hannunta d'aya ya d'ago yaji sa a sake, sakin hannun yayi kasa, kana ya kai yatsun sa biyu dai-dai santin hancinta d'ip babu numfashi. ido yad'an waro kana a hankali ya kai hannu jikin ta yashiga bubbugata nan ma ko motsi batayi ba, tsaki ya ja yamike har ya kai kofar fita daga d'akin sai kuma ya juyo ya dawo cikin bathroom d'in da take kwance a sume, ya sunkuya ya sunkuceta cak ya d'agata yafito da ita yana zuwa bakin gado ya wurgata a kan gadon yana jan tsaki. duk da irin wurgota da yayi a kan gadon nan ko gizau batayi ba sai a lokacin ya gaskata dagaske bata hayyacin ta. kugu yarike yana binta da kallo a fili ya furta "Wai mutuwa tayi ko suma?." sai kuma ya juya da sauri yaje ya bud'e fridge yaciro gorar ruwa mai sanyi sosai, yadawo bakin gadon ya bud'e gorar yashiga tsiyaye mata ruwan a fuska da bakin gorar. wani uban numfashi ta ja a kid'ime kuma a razane sakamakon jan ruwan da tayi a hancinta, ta jujjuya kai cikin azabar jin ruwan ya wuce mata cikin kwakwalwa duk da bata cikin hayyacin ta sai da hawaye ya zubo idon ta. a sannu a sannu tashiga sauke numfashi . kana a sannu tashiga bud'e idanunta har ta bud'e su duka, a hankali ta juyar da kanta gefe sai dai da kaga yanayin yan da take yi kasan ba'a cikin hayyacin ta take ba. sai kuma tashiga maida idanun nata a hankali ta lumshe su duka asanu-asannu tashiga sauke numfashi yayin da bacci yasami nasarar d'aukarta cikin halin da ta ke ciki. Shiko na tsaye a kanta ganin alamun bacci tayi, sai yaja tsaki tare da wurgar da gorar hannunsa kasa yana mai janye idanunsa daga kallonta, dan gaba d'aya towel d'in jikin ta daga kasa ya tattare ya yi sama kusan duka cinyoyin ta a waje suke. yanayin kwanciyar ta daya jefo ta kan gadon kafarta d'aya a lankwashe yake d'ayan kuma a mike sai dai a ware yake har ana iya hango pant d'inta ta tsakiyar cinyoyinta. daga saman kirjin ta kuma kusan rabin ababen kirjinta a waje suke dan d'aurin towel d'in ya kunce. juyawa ya yi zai fita harya kai bakin kofa sai kuma ya dawo bakin gadon yana fad'in "Yarinyar nan rainin wayon ta ma da yawa yake, ke wai bacci ma kikayi dan tsabar rainin wayo wai kullum sai an fad'a miki aikin ki zaki tashi ne ko sai na canza miki kamanni." SEEDRAH kam da ma ya ya gwanace a gurin bacci bata ma san yana yi ba. wani irin fizga idanunsa ya yi lokacin da ya d'aura idanun nasa a kanta dai-dai lakacin da tayi wani irin mika tare da kuma bajewa ta gyara kwanciyar ta da kyau. da gyar ya iya tattaro yawun bakin sa ya had'iye mututt. bin santala santalar cinyoyin ta farare tass yayi da kallo, a hankali yake yin sama da idanunsa har zuwa kan ababen kirjinta da yanzu sukafi na d'azu fitowa fili, tantsan-tantsan d'in nonuwan ta farare soll suna cike tup-tup atsaye kem gwanin bansha'awa masu tsole idon mai kallonsu. Wani irin fizgo numfashi yayi tare da yarfe hannunsa had'e da tankwashe yatsunsa biyu wan da ya tab'a kokarin cusasu cikin HQ d'inta dayaji sun yi masa wani irin fizga wane kurar karfe. a hankali yashiga ja da baya har ya isa bakin kofa da sauri ya bud'e kofar ya fita har yana had'a step ya haura sama...........! Mommyn Twins ce 🌺 *ƘARSASHI!* 🌺 *NA* *RASHEEDAT S DIRECTOR* ( _Book 1_) ~Free page~ _Littafin na kud'i ne 400 Account no 3170524141 Rashida Salihu first bank kokuma katin Mtn ta wannan number 08034690723 *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* page 18 Direct bedroom ya shige yazube kan kado ya kwanta ruf da ciki, kafafunsa suna rito a kasa, cike da tsananin mamaki yake jin yanayin da ke shigar sa sai kuma yakai hannu zuwa kan wandon sa, ido ya waro jin yanda bananar sa ta kumbura ta mike samb'al wane zata faso wando ta fito. dogon tsaki yaja tare da dunkule hannunsa ya naushi karifa da karfi kamar zai burmata. da sauri ya mike yanufi bathroom yana jajjan rigarsa yana bud'a ta ta kasa yana rufe abartasa data mike ta turo wando har rigar. yana shiga bayi yasakarwa kansa ruwa mai sanyi batare da ya cire kayan jikin sa ba. numfashi yashiga saukewa a hankali a hankali kana yashiga tub'e kayan jikinsa yana mai cigaba da matukar mamakin ganin yadda bananarsa tayi wani irin uban kumburar da bai tab'a sanin yana da kalar halittar ba, har wani zafi-yafi yake masa. ya d'au tsawon mintuna 20 a tsaye ruwa na sauka a kansa a hankali yaji abu mai d'umi nabin gefen cinyarsa. kasa ya yi da idonsa zuwa gurin, ruwan cikin bakin sa ya furzar had'e da iska mai huci, kana ya saka hanu yashiga wanke gurin in da ruwan madarar sa ta malala har zuwa kasan kafarsa yana yi yana jan tsaki, daga nan ya sarkake jikin sa ya fito. Ko da yasaka kaya ya haye gado daga zarar ya rufe ido sai ya rika hango surar SEEDRAH na masa yawo a gido, kokarin gusar da faruwan hakan yayi sai ya matse idanunsa da karfi dan son bacci ya d'auke sa, amma me nan ma surar tata ya kuma gani. zumbur ya mike zaune tare da bud'e idanunsa cike da takaicin yanayin ya ce "Anya yarinyar nan ba mayya bace kuwa?." sai kuma yakuma komawa ya kwanta aransa yake ayyana imma mayyar ce sai ya cire mata maitancin da duka. da kyar bacci ya d'auke sa da taimakon addu'o'in daya rika tofawa... A b'angaren SEEDRAH kuwa ba ita ta farka ba sai da aka fito daga sallar asuba. mika tayi had'e da salati ta mike zaune tana mamakin yanda akayi ta kwanta bacci da towel bata sa kaya ba a hankali ta zamo bakin gadon tamike tsaye "Wash." ta furta lokacin da ta mike tsaye jin zafi a kafarta sai kuma lokaci guda kanta ya sara mata. da sauri ta koma ta zauna bakin gado, a hankali tashiga tunano abun da yafaru da ita jiya ta san dai ta fad'i har tayi ihu daga nan kuma bata iya kuma tuna komai ba. tunani ta soma to ma taya akayi har ta tashi tazo kangado ta kwanta, ganin bata da amsar tambayarta sai ta yunkura a hankali ta mike tana d'ingisa kafa ta shige bayi. sai da tayi wanka kana ta d'auro al'wala ta fito. bayan ta idar da sallah a hankali ta mike taje ta saka kaya tanufo waje dan lokacin gari ya yi haske. a daddafe ta gama ayyukan ta na kasa dan jikinta ciwo yake mata musamman ma kafarta da kuma kanta dake ta yi mata ciwo. ta d'au tray d'in data shirya masa kayan breakfast ciki, ta nufi step's a hankali take d'aga kafarta harta haura. a sakiyar parlour ta dire tray d'in saman table kana tashiga gyaran parlour'n koda ta gama gyaran parlour'n kofar bedroom d'in sa ta kalla sai kuma ta juya da niyyar sauka kasa sai idan ya gama abunda zaiyi yafito kafin tazo ta gyara, dan bazata shiga ta je ta ganewa idanunta abin da bai da ce ba. Tana juyawa tajiyo karar bud'e kofa a hankali ta waigo, ya mai da kofar ya rufe sanye yake da singlet da 3qrt yana rike da sigari a hannunsa yana d'an zuka ya yin da d'aya hannunsa kuma yake cikin aljuhun wandonsa. a sannu yake d'aga kafarsa har ya karaso cikin parlour'n ya zauna kan kujera yana mai cigaba da shan sigarin. fuska ta yamutsa tana kawar da kanta gefe tare da kore iskar dake had'uwa da hayakin sigarin da hannunta. cikin kuma yamusa fuska ta d'an kalli gefen da yake ta ce "Zan shiga nayi aikina ko zaka iya ce mata ta fito tajira awaje nagama." Bayansa yajingina da jikin kujera kana a hankali yad'an zuba mata narkakkun idanunsa da basu sami bacci jiya ba. "Tambaya ne yakawo ki gidannan ko ai ki?." ya yi maganar yana kokarin janye idanunsa a kanta sakamakon jin yan da idanunsa ke fizga sai yanayin yan da yaganta jiya ke dada zuwar masa sabo. Sarai ya fahimci abinda take nufi tana tunanin Teema tana cikin d'akinne baki yabe tareda maida idanunsa ya lumshe. Fuska ta yamusa akasan ranta tana ayyana bazata shiga d'akin taganewa idonta ba dai-dai ba. shiko da sauri ya ware idanunsa sakamakon ganin surar jikinta b'arob'aro tamkar alokacin ne hakan yafaru. "Ke mayya ce ko!?." Yajefo mata tambyar idanunsa a kanta. Ido tad'an waro ganin yanda ya tsareta da ido yana wani muzurai. manyan kwayar idanunta ta kad'a sannan ta ce "Eh mutane 99 na cinye inata kan niman cikiton na d'arin kenan." A hatsale ya ce "To ni nafi karfin ki sai dai kici kanki wuce ki bace min da gani mayya kawai." yanayin yanda yake maganar yaso yabata dariya sai kuma ta gimtse ta juya tasoma tafiya tana fad'in "Katab'a ganin in da maye yaci kansa da kansa dole dai ya samo abokin tafiya." tayi gaba tana murgud'a masa baki ta juya tabar gurin. Dogon tsaki yaja yamike tsaye ya yi wurgi da sigarin hannunsa. ya dunkule hannu ya naushi iska tare da furzar da huci mai zafi sai kuma ya juya da sauri yanufi steps. ko da ya sauko kasa gurin motsa jikin sa ya nufa yahaye kan machine d'in motsa jiki yakure masa gudu. gudu yake babu ko kakkautawa baya jin kuma yagaji. yashare tsawon awa guda yana gudu kafin yakashe na'urar ya sauka yana maida numfashi. Makullin motar sa ya zara yabar gidan, dan ji yake idan yacigaba da zama a gidan zata iya cinyesa da maitar ne da gaske dan shi yan da yake ji da ganin suffarta a idon zucinsa da gaske maitar take. Wunin ranar baiyi a gidan ba. dan gani yake zaman su tare a gidan ne yake sashi ganin ta cikin kwakwalwa da zuciya da idanunasa, cikin suffar da ya ke hargisa masa lissafi. bai dawo gidan ba kuwa sai dare yau ko niman tea d'in daren ma baiyi ba... Washegari yatashi da shirin barin kasar zuwa Kanada buga wani wasan da za a gudanar. da sauri ya sauko cikin shigar kana nan kaya da suka amshi jikin sa ba kad'an ba tamkar dan shi akayi su, yana tafe cike da Karsashi yake taka kasa tamkar namijin zaki. a parlour ya taddata tana gyara, tana ganin shi ta d'auke kai tacigaba da abin da take tana yi tana bin sansanyar wakar soyayya da ke tashi a wayan ta, a hankali tana jin wani irin shauki da son Kamal dake dad'a ruruwa cikin zuciyarta. d'aga kiran daya shigo wayarsa ya yi bayan ya gama magana ya sauke wayar da d'an sauri ya dube ta ya ce "Ke saurare ni zan yi tafiya, saura kuma kiga bana nan ki ajiye ayyukan gidan nan nadawo na sami datti da kura, naga wani abu ba dai-dai ba zaki had'u da b'acin raina." yana maganar yana tafiya da alama dai sauri yake. baki bud'e tabi bayansa da kallo haryakai kofa "Wai zama zanyi a gidan nacigaba da bautatawa gidan da ba kowa ciki, na rantse bazan zaunaba ka nimo wata ma'aikaciyar ba ni ba kam." ta shige d'aki da sauri ta d'au mayafinta kana tashiga washe kaya tana sawa cikin jaka ta janyo akwatinta tayi waje. Koda ta fito farfajiyar gidan bataga d'aya daga cikin motocinsa ba har ya tafi kenan. tawuce bakin get tana kokarin bud'e karamar kofa taji sa a kulle. kallon in da maigadi ke zaune can gindin wata fulawa yana ta uban goge baki da asuwaki tayi ta ce "Malam zo ka bud'e min kofa na fita." da sauri ya furzar da abin bakin sa ya ce "Rufamin asiri zo ki koma ciki oga ya ce ba shiga ba fita, ki koma kawai abinki kije ki more daula kafin ya dawo kasar, anjima ki kunna mana TV zan shigo mu kalli wasan da zai buga amma dan Allah karkice masa nashigo." wani uban harara ta wasa masa cikin masifa ta ce "Dalla malam kazo ka bud'e min kofa kana fad'a min wasu abubuwan da basu shafeni ba na rantse idan baka bud'e ba sai na kirawo masu b'alla kofar nan." ya zari buta yayi hanyar bayi yana fad'in "Hajiya kirawo su su b'alla amma ni kam bazan bud'e da hannuna ba." Duk uban masifar da take yana jin ta yaki fitowa daga cikin bayin,ta janyo jakarta ta koma ciki ta d'aga waya takira Mama. ko sallama batayiba sabar yanda take jin kanta "Mama wai kiji mutumin nan wai ya yi tafiya wata kasar yasa a ka kulle ni a gidan, wa aljanu zan cigaba da yiwa aikin, Mama ku kirasa yasa a bud'e min kofa, idan ba haka ba Allah sai na sa an b'alla kofar nan da get d'in gaba d'aya yadawo ya same sa a ajiye, wai wani in zauna in cigaba da yin aiki meye nufinsa, ina dama aikin washi akeyi ba wa fanko ba, tun da baya nan meye amfanin aikin." "A'a SEEDRAH ki saurare ni kada kiyi yinkurin yin wani abu kibi sa a sannu arabu rafiya da Usman, kada ki kuma jawo mana wata matsalar kiyi hakuri ki zauna d'in kici gaba da yi har ya dawo." "Mama mutumin nan fa ba mutunci yake da shi ba sai ya iya cewa aikin da nayi bayanan yazama ziro baza a cire kud'in acin kud'in da yake bin Baba ba, wahalar banza kenan fa nayi." Mama ta ce "Watakila ba jimawa zaiyi ba kicigaba dayin aikin naroke ki SEEDRAH arabu lafiya da Usman." kai

Chapter 14 of 19