Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kawai ta girgiza ta kashe wayar batare da takuma cewa komai, bakin ciki had'e da haushin S.MAN ne kawai ke cinta a zuciya. taji ta yarda zata zauna tayi aiki a karkashinsa ko dun ta tsare mutuncin iyayen ta, daga kaidin S.MAN da baisan in da mutunci yake ba. Kwanan sa biyu da tafiya bayan tagama dukkanin ayyukan ta tana zaune a parlour, manne da waya a kunnenta suna soyewa da habibinta Kamal daya dawo jiya. cikin hirar tasu yake cewa "Baby nifa na gaji da rashin ganin ki naso a ce jiya dana dawo garin nan, dake nafara tozali ban san me yasa kike son horani da rashin ganin ki ba, kibarni nazo na ganki please." kai ta kwantar jikin kujera cike da shaukin so ta ce "Kai da ka kusa mallakata gaba d'aya saurin me kake." "No nasani kibari na ganki zanfi samin sukuni." ido ta d'an lumshe tana tunanin ta inda zata fara tasan maigadi bazai tab'a barin sa ya shigo ba ita ma kuma bazai barta ta fita ba. muryar sa tajiyo yana fad'in "Zanzo yanzu please kada ki hanani ganin ki, nasan S.MAN baya kasar dan jiya duk da gajiyar dana kwaso na hanya bai hana ni zama kallon wasan sa ba, yanzu ma haka ina gaban TV ina kallon maimaicin wasan nasa na jiya." to ta ya zatayi ta fad'a masa ya kulle ta ya hanata fita yakuma hana wani ya shigo gidan, murya a marairaice ta ce "Kabari zan zo gida gobe sai mu had'u." "Har gobe!." yafad'a cikin nuna damuwa sosai. "Yi hakuri mana da yau da goben ai duk d'ayane." duk yan da yaso yasan dalilin hanashi ganin nata taki sanar masa ammsar dai d'aya ce yabari goben zasu had'u. a haka dai sukayi sallama tana jin ba dad'i dan ita kanta ba karamin missing d'in sa tayi ba. numfashi ta sauke lokacin da take aje wayar, ta d'au rimut ta canza tashar da take kallo bawai ko dun tana fahimtar abin da akeyi a TV ba gaba d'aya lissafin ta a jagule ya ke. Nan ko idananuta ya sauka kan S.MAN da ke zuba uban gudu a katafaren filin kwallo, yana sarrafa kwallo cike da kwarewa had'e da KARSASHI cikin jajayen fata. dogon tsaki taja "Mttsss wahalalle haka zaka kare da guje-guje Allah yasa kafad'i ka karya kafa." tamike tana kokarin barin gurin. ihun da tajiyo a cikin TV'n ne yasata juyowa da sauri. ido ta gwalalo ganin yanda aka wani d'agashi sama yan uwan sa bakaken fata suna ihu cike da sananin farinciki. turawannan kuwa sai dafe kai suke da alama dai abin bai musu dad'i ba. camera kuwa sai hasko sa yake had'e da tutar Nigeria, abin gwanin ban sha'awa gwanin burgewa. sai da taji yanayin yad'an burge ta sai kuma ta kawar da kai tuno da ko wane ne shi d'in. baki ta tab'e tawuce d'aki.. Washegari kuwa tun sassafe Kamal ya d'agata a bacci dan baccin nata baiyi nisa ba, yanzu takan samu tayi baccinta son ranta kafin ta tashi tayi ayyukan ta. tama rasa wace karya zatayi masa tashiga kame-kamen abin da zata fad'a, shi ya rigata fad'in "Alhajinmu ya kira ni yanzu yatura ni Kano kinji dad'i ban saki a idanuna ba." numfashi mai sauti ta sauke cikin kasa da muryar da bacci bai ishe ta ba ta ce "Allah ya tsare min kai ka dawo na ganka nima nayi missing d'in ka sosai." "Bakiyi missing d'ina ba da kin bamu damar ganin juna." "Karka ce haka Allah ya dawo min da kai lafiya kawai." "Amin zamuyi waya anjima dan naji da bacci a idanunki." ta ce To... Satin S.MAN biyu ya juyo badun yagama abin da yake ba sai dun son kammala wani aikin da yake da shi a Nigeria'n. da safe tana kwance tana bacci a kasa akan sallaya bayan ta idar da salla ta gabatar da azkar, sabar bacci bata iya mikewa ta hau gado ba ta b'ingire a kasa a gurin. cikin bacci taji an naushe ta. sosai taji zafin bugun duk da kuwa nauyin bacci irin nata, da kyar ta iya bud'e idanunta da suke cike tam da bacci, dishi-dishi take ganinsa. shiko kuma naushin ta ya yi da takalmin kwallon da ke kafar sa tamkar mai shot da ball. zumbur ta mike tarike gefen cikinta in da ya nausheta ta ce "Wayyo Allah na me nayi maka?, Allah ya isa mugu wlh bazan yafe ba." "Bacci ne yakawo ki gidan nan?, oya tashi kije ki had'a min breakfast, kin sami guri kin baje kefa ba kowa ba ce face 'yar aiki, kada ki sake sanyi AC da daular gidan nan yasa ki mance da abunda ya kawo ki." Fuska ta yamutsa kana ta ce "Ashe dai ni kowa ce tun da ni 'yar aiki ce, kamar yanda kake aiki ake biyan ka haka nima nake yi, sai dai bambanci na da kai inayin aiki na ne domin samin albarkar iyaye na, kai fa aikin banza aikin wahala kake, ba gara ni bama kai sai kayi ta gudu ka had'a zufa kafin a biya ka idan Allah yaso ma ka karya kafa, ashe kuwa gara aiki na da naka." ta karashe maganar da murgud'a masa baki. Kallon wanda batama san me take ba ya mata, dan yunwa ce fal cikin sa dan tun isowarsu da safiyar yau ya duro da yunwa bai sami abinda yake so yaci a cikin jirgi ba. kunsan d'an kwallo mabukacin abincine sosai. ya ce "Zaki tashi ne ko sai nayi shot da ke." "Ba sai ka d'aga jijiyar wuya ba aiki zan yi shi tun da albashi nake karb'a." ta fad'a tana mikewa tsaye tana gyara hijab d'in dake jikin ta. bai kuma magana ba ya juya tare da jan tsaki ya fice a d'akin. itama tsakin taja "Mugu azzalumi Allah ya isa min, ina bacci na mai dad'i yazo ya wani katse min." sai da ta sauya kayan jikinta kafin ta fito. sai a lokacin taga gari ya yi haske sosai. turus ta d'an yi a bakin kofa ganin mutane zaune cikin parlour'n su rai uku duk kanin su sanye suke da kayan kwallo, suna ta hira rabin hirar tasu ko na kwallo ne. taja kafarta tazo zata wuce su wata zuciyar ta ce kada ta gaishe su duk halinsu d'aya ne da S.MAN d'in, wata zuciyar kuma ta ce ta gaishe su tun da baya cikin su. "Ina kwanan ku." ta fad'a a takaice duk suka amsa cikin sakin fuska. tayi saurin wucewa kichin duk suka bita da kallo. Da yawa tayi abincin ganin mutane a gidan tana kammala had'a breakfast d'in ta kwashe su cikin babban tray ta nufo parlour'n. dai-dai lokacin da yake saukowa daga steps wannan, karon sanye yake da wando iya guiwa da riga T-shirt. kyakkyawan fararen kafafunsa babu takalmi yana d'an buga kwallo yana saukowa da shi a hankali cikin wani irin salo cike da kwarewa. yana karasa sauka ya yi shot da ball d'in sakiyar abokan nasa suka cab'e. da sauri ta nufi dinning tana kokarin aje tray'n ta sinkayo muryarsa "Ke kawo nan." ya yi maganar yana zama kan kujera." ta juyo a sannu ta kawo shi sakiyar parlour'n, tana kokarin dire tray'n d'aya daga cikin su ya yi saurin tasowa ya karb'i tray'n ya sauke shi kasa yana jefa mata murmushi. kai ta kawar gefe. "Sannu da aiki." taji an fad'a ta d'an d'ago tagane mai maganar wanda yatab'a kwatanta a hannun S.MAN ne lokacin can wato Sagir. takaitaccen murmushi ta masa kana ta bar gurin. Bashir da ya aje tray d'in ya zauna ya mike kafafunsa a gaban tray'n. ya kalli S.MAN yana bud'e kulolin wani kamshi ne ya bige sa ya had'iye miyau ya ce "Mutumin ya za ayi ne kam nifa wannan ta min." fuska S.MAN ya had'e ya ce "Sai ka d'auke ta ka sakata a aljuhu karika yawo da ita bunsuru kawai." "Ah haba wannan ai matar gaban mota ce in shi bai san yadda zaiyi da ita ba ni na sani." Anwar da ke daddana waya ya fad'a a hatsale S.MAN ya ce "Zaku iya tashi ku tafi da ma ban gayyace ku ba salon ku janyo min raini gurin yarin yar can da ma gata fisararriya." dariya Sagir ya yi ya ce "Idan aka kore ku daga nan kuyi restaurant dan ni dai kunsan ina da iyali abin da yafi abinci zanje a bani naci na more." hararar sa S.MAN ya yi. Bashir ya ce "Kabar yi da mu da S.MAN ka ke dan dai kasan dukkanin mu da kud'in auren mu a kasa har da sa rana abincin dai muma zamu cisa cikin kwanciyar hankali." tsaki S.MAN ya yi yamike yaje yasoma yin breakfast d'in sa... Suna kammalawa sukayi waje. SEEDRAH na kwance tarika jiyo hayaniya ta bayan windo'n d'akin da take ta mike ta je ta leka. ta hango su suna buga kwallo, baki ta tab'e afili ta furta "Manya da su sunata wani guje-guje kamar wasu yara." shiru tayi idanunta a kansu ganin yan da suka dage suna ta kokarin karb'ar kwallon a gurin S.MAN sun kasa shigo sai wani zuba murmushi ya ke ga dukkan alamu dai yana jin dad'in yanayin. jin karar wayar ta yasa ta sakin labulen ta isa in da wayar yake ganin mai kiran nata yasata sakin murmushi ta zube kan gado ta d'aga kiran suka shiga rerawa junan su karatun so.. Bayan kwana uku da dawowan S.MAN SEEDRAH tayi shirin zuwa gida dan tayi kewar gida sosai. tafito da shirin ta tanufi bakin get koda ta tab'a kofa tajisa a kulle ta juyo ga maigadi shima d'in ita yake kallo ta ce "Zan fita." maigadi ya ce "Ba a bani izini ba." kamar tasa ihu dan bakin ciki hata taji, bata kuma cewa komai ba ta juya ta koma ciki. direct sama ta haura ta shiga babbuga kofar bedroom d'in. yana zaune a sakiyar gado yayin da laptop ke gaban sa yana sarrafashi da hannunsa guda d'aya hannun nasa kuma narike da sigari yana d'an zuka. sa rai yaji bugun kofar amma ya d'auke kai jin ta dage da bugun kofar tana cika masa kunne ya ture laptop d'in ya mike rai b'ace ya bud'o kofar da karfi. ai kuwa ta tafi suuu ta fad'i kasa timm. "Wayyo Allah na." tafad'a tana yarfe hannu da sauri ta mike tsaye tana gara gyalenta tare da kawar da kanta gefe tayi saurin juya masa baya dan ba komai jikin sa sai zallar boxes. gyalen ya kama ta baya ya shako ta tare da fad'in "Awani dalili zakizo kina cika min kunne a nan." da sauri ta zare gyalen ajikinta tamasa gefe tana shafa wuyan ta da mai da numfashi, cikin hanzari kuma tayi waje, dan bazata iya cigaba da tsayuwa a gabansa tana ganin sa sirara ba. a bakin kofa ta tsaya batare da ta kallo cikin d'akin ba ta ce "Kasa maigadi ya bud'e min kofa na fita gidan mu zanje." "Bazakije ba in kin ga kin bar gidan nan to kin gama biyan kud'in da wancan tsohon banzan yaci ne." ya wurga mata gyalen ta yarufo kofar. kugu ta rike cikin d'aga murya ta ce "Kai kuma katon banza baka isa ka hanani zuwa gidan mu ba wlh sai na je." tajuya fuuu tayi kasa. A d'aki tarika kullawa da kwancewa ta yadda zatayi ta bar gidan nan dan tagaji da aikin gidan yafad'i wani abun da za ayi masa abakin kud'in sa.. tana nan bata ankaraba har aka kira sallar azahar, bayan ta idar taje ta kulle kofar ta da key tazo ta haye gado tayi kwanciyar ta tana fad'in "Na rantse yau bazanyi girki ba sai dai kaje waje ka siya kuma zuwa gidan mu yazama dole tun da ni ba 'yar cikin ka bace." S.MAN na dawowa daga masallaci ya hango dinning wayam babu komai, rai b'ace ya nufo d'akin da take yajisa a kulle ya bubbuga kofar shiru, SEEDRAH kam tana kan sharar baccinta bata ma san yana yi ba. ya d'auko wani key d'in ya saka kofar taki bud'uwa. hakan na nufin ta kulle kofar bata zare key d'in ba kenan. kwafa ya yi tare da girgiza kai alamun zamu had'u. a ranar dai S.MAN gidan Ummi yaje yaci abinci.. SEEDRAH kuwa bacci yafi mata cin abinci baccin ta tayi ta shara sai yamma lis ta farka taje ta d'auro al'wala ta gabatar da sallar la'asar. abincin da ta ci da safe ta rage shi taci yanzu. S.MAN bai dawo gidan ba sai dare ko da ya kuma hango dinning ba komai ransa ya dad'a b'aci, yakuma tab'a kofar da take ma yajisa a kulle. ya wuce ya haura sama. wanka ya yi ya sauya kaya ya haye gado yana 'yan dube-dube a wayar sa. A b'angaren SEEDRAH kuwa duk dad'ewan baccin ranar da zatayi baya hanata baccin dare dan haka tana sallar ishe taje tayi wanka, ko kaya bata saya sakawa ba ta kwanta da zani d'aurin kirji ta shiga sharar baccinta cikin kwanciyar hankali. S.MAN yakai wajen karfe 1 na dare yana aiki a wayarsa da kuma computersa sai a lokacin ya kashe su duka kana ya mike yana shafa cikin sa ba shakka yunwa yake ji, ya kalli gefe kan bedside in da ta saba ajiye masa d'an abin tab'awa da kuma flas na tea babu ko alamar su. duruwa ya ja sai ga wasu makullai da yawa sun bayyana daga cikin su ya zaro wani ya rufe durowan yafita. d'akin da ke kusa da nata ya bud'e ya shiga ya nufi in da wardrobe d'in d'akin ya ke. yasaka hannu a sakiyar wardrobe d'in yabud'a da karfi sai gashi ya rabe gida biyu ko wanne yatafi suuu gege kofa ta bayyana a sakiyar su. makulli ya zura ya bud'e kofar saiga wardrobe dake ta cikin d'akin da take, shima karfi ya gwada masa ya bud'asa kana ya shige ciki ya mai da wardrobe d'in d'akin da yabi ya shigo ya had'e shi sannan ya rufe kofar. wardrobe d'in d'akin da take cikin ma yamayar ha had'e su baza ka tab'a cewa akwai wata hanya a sakanin su ba.. Can ya hangota kwance tana sharar baccin ta cikin kwanciyar hankali. yana zuwa bakin gadon baiyi wata-wata ba yakai mata mari a fuska. cikin bacci taji zafin marin sai dai ta kasa iya bud'e idanunta dan zaton ta mafarki take. mika tayi tare da yin juyi ta dad'a bajewa da kyau cikin magagin bacci ta kai hannunta ta sosa gefen fuskarta in da ya mare ta nan kuwa taci gaba da baccin ta. ganin bacci ma tacigaba da yi, wani irin fizgota ya yi ta zo bakin gadon hakan kuwa ya yi sanadiyyar zamewar zanin jikinta dan dama tayi ta birgima zanin ya kunce, pant da bra ne kad'ai a jikin ta. rumtse idanunsa ya yi da karfi jin tamkar an jonashi da wutar lantarki. ya kai second 10 idanunsa a rufe kafin ya bud'e su da kyar, wan da har a lokacin ilahirin jikinsa yana bashi wani irin shock. ga mamakin sa har lokacin bacci take, ya yi matukar mamakin ganin nauyin bacci irin nata. da sauri ya janye idanunsa da suke wani irin fizga a kanta ya mika hannunsa na b'ari ya janyo zanin ta yana kokarin rufa mata jiki. dai-dai lakacin tayi wani irin juyin dayasa shi d'auke wuta gaba d'aya. ababen kirjinta da suke cikin bra suka dad'a bayyana dan dama sun fi karfin bra'n bai rufe su gaba d'aya ba. santala santalan fararen cinyoyin ta sai sheki suke. Wani irin zillo joystick d'in sa ya yi tamkar zai faso wan do ya fito, a take kuma yaji jikin sa ya d'auki b'ari. kwakwalwarsa ya tsaya cak ya dai na aiki. "No no no!!." ya furta da karfi yana dafe kansa a zuciyarsa kuwa yake fad'in "Mayya ce mayya ce ita, meyasa bakajin haka game da Teema da matan turawan da suke kawo maka hari da ma sauran 'yammata, Teema da komai na jikin ta tub'e shi take a gaban ka tayi ta wasanni da jikin ka, sai wannan fisararriyar yarinyar da ka tsana." "Ita wannan mayya ce." wani b'ari na zuciyar sa ya kuma fad'a masa. ido ya rumtse da karfi yana son d'aga kafarsa ya bar gurin amma ya kasa. ga wani irin tagwayen abubuwa da suke zuwar masa a kwakwalwa da zuciya da suke barazanar tarwasa masa zuciya da kwakwalwa.. da karfi ya fizgo numfashi kokarin sai ta nutsuwarsa ya ke da son hana zuciyarsa aikata abin da take ta bijiro masa gaba ki d'aya zuciyar sa ta makanta bata ji ba ta gani. kamar an fisgosa jikinta haka ya kwanto kanta. kunnuwansa sun toshe baya ji idanunsa ya rufe baya gani yama mance ko wace ce ita. kankameta ya yi da karfi ya had'e jikin sa da nata sosai, yana wani irin sauke numfashi. hannunsa na b'ari yad'ago ya sauke shi kan ababen kirjinta ya shafo shi ta sama in da ya kumburo ta saman bra. da sauri ya d'aga hannun tare da dunkule shi yanata fama da zuciyar sa wajen son hana kansa aikata abin da yake shirin aikatawan. ya cusa hannun ta bayan ta ya zagaye ta. fuskarsa yashiga gogawa a nata kamar mai niman wani abu sai kuma da sauri ya dire bakin sa kan lips d'in ta yatura harshensa cikin bakin ta yashiga tsotsar sa da zafi-zafi.............! Mommyn Twins ce 🌺 *ƘARSASHI!* 🌺 *NA* *RASHEEDAT S DIRECTOR* ( _Book 1_) ~Free page~ _Littafin na kud'i ne 400 Account no 3170524141 Rashida Salihu first bank kokuma katin Mtn ta wannan number 08034690723 a tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723_ *____________________________________* *🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼* *🇦SSOCIATION🤝🏻* ```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}``` https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation *_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻 https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association *____________________________________* page 19 . Yanda yake tsotsar bakin ta da kuma kankame ta, shiya farkar da ita daga nannauyar baccin da take. idanunta suna rufe dan har alokacin bata gaskata farkawan nata ba, dan tafi yar da duk acikin bacci take. kokarin juyi take dan son gusar da wannan mafarkin da take amma ta kasa, duk yanda taso tayi juyin ta kasa sai taji kamar duk an daddanneta. a hankali tashiga bud'e idanunta, dishi-dishi take gani duk da kuwa hasken wutan daya haske cikin d'akin, dan da zata kwanta bata sami damar kashe wutan bama tayi kwanciyar ta. kuma ware idanunta tayi sosai tana kikkifta su. ta dage ala dole dai so take ta farka a baccin dan abun da take ji da gani yanzu taki gaskata idanunta biyu ne. sosai ta ware idanunta a kan fuskarsa, idanunsa a lumshe sai tsotsar bakin ta yake kamar ya sami sweet. wani irin razana da firgici ne suka dirar mata, da gaske ba mafarki take ba. da karfi ta daddage ta janye bakinta wani uban ihu ta kurma da karfin tsiya, da ya sashi dawowa cikin hayyacin sa. "Wayyo Allah nashiga uku na wayyo Mama wayyooo!!." takuma fasa kara mai karfi. da sauri ya sake ta ya zare jikin sa ya mike a kanta yana dafe kai. cikin matukar tashin hankali tamike ta janyo zaninta tana kare jikin ta. tsoro ne mai tsanani ya rufe ta murya na rawa tashiga nuna shi da yatsa tana fad'in "Me kamin? kamin wani abu ko? wlh idan har kamin wani abu kotu ce zata rabamu da kai mugu azzalumi." duk maganar da take a matukar tsorace take daganin yanayin sa. imagine tashiga yi gashi nan yana sex da ita,kara ta saka tashiga yamutsa gashin kanta nata fad'in "A'a wlh a'a idan kamin wani abu wlh bazan yafe maka ba sai na d'au mataki a kanka." "Shiiit rufamin banzar bakin nan naki ko na fasashi bacci ne yakawo ki gidan nan ko aiki." maganar ya ke cikin wata iriyar murya da ta gama narkewa cikin wutar sha'awa, ya kuma murtuke fuska tamau alamar ba wasa. da kyar ya iya tattaro jarumtarsa ya sauka akan gadon da kyar ya mike tsaye yana gyara zaman MAN d'in sa dake kokarin fasa wando ya fito batare da nuna wata damuwa ko shakko ba. rumtse idanunta tayi da karfi kirjinta na dukan uku-uku. dai-dai ta tsayuwar sa ya yi, ya na tangad'i kamar wanda yasha wani kayan maye ya nufi kofa ya bud'e ya fita. tana jin fitarsa ta bud'e idanunta da sauri ta fad'a jikin pilo ta saki kuka. sosai take kukan cike da bakin ciki da takaici, cikin muryar kuka sosai ta ke fad'in "Wayyo na shiga uku na Allah wadaran nauyin bacci irin nawa, dama Mama da su Aunty Suhailat sun sha fad'a min watarana sai an sace ni ina bacci, to gashi yau mugun nauyin bacci na ya janyo anyi min fyad'e ba tare da na sani ba, shi ke nan rayuwa ta ta zamo ragaggiya." kuma saka kuka tayi, tana tausayin kanta tabbas ta zamo abin tausayi. i dan ba dun kariyar arzikin daya sami Baba ba me zai kawo ta gidan sa har ya nimi keta mata haddi. lallai talauci masifa ce, badun kariyar arziki ba da bai karb'i bashin sa ba ko da ya karb'a kuma da ya mai da masa da bata zo gidan nan amatsayin 'yar aiki ba, da duk haka bai faru da ita ba. ganin kuka bazai mata magani ba ta mike tashiga bathroom. dudduba jikin ta tayi sosai bata dai ga alamar fyad'e tattare da ita ba hasali ma kuma pant d'in ta yana jikin ta kuma babu wani d'igon damshin wani abu. ko da ta fito a bakin gado ta zauna tana tunanin ta ina ma ya shigo d'akin ita da ta kulle kofar kuma taga da zai fita ma sai da ya bud'e da key d'in da ta bari jikin kofar, "To ko ta sama ya shigo." ta d'aga kai ta kalli saman d'akin babu ta in da mutum zai iya shigowa a yanayin tsarin ginin gidan. "To ko tsafi ya ke ya shigo ta hanyar tsafin sa." haka tayi ta tambayar kanta bata sami amsa ba. daga karshe dai rakub'ewa tayi a gefen gado tana jiran gari ya waye dan bazata kuma komawa wannan baccin nata mai kama da mutuwa ba.. Washegari bayan ta idar da sallar asuba tana zaune kan sallaya tana azkhar, aka turo kofa da sauri ta d'ago tana duban kofar. daga bakin kofar ya tsaya ya hard'e hannu a kirji cikin tamke fuska ya ce "Oya tashi ki fita yanzu ki fara aiki ki b'ata lokaci ki gani." yana kaiwa nan ya juya ya fita. bayan sa tabi da harara tare da jan tsaki a fili ta furta "D'an rainin hankali ko ya d'auka kowa irin wancan karuwar da ta ke kawo masa kanta har gida ne, d'an iska kawai missttt." takarashe maganar da jan dogon tsaki. sai da ta kammala addu'o'i'n ta kafin ta mike tafito batare da ta cire hijabin jikin ta ba. can ta hango sa gurin motsa jiki da sauri ta wuce ta haura sama ta gyara kana ta sauko ta shiga kichin. ko da ta gama had'a breakfast tafito baya gurin ta haura masa da breakfast d'in. yana zaune a parlour ya d'au sigari yana kokarin kunnawa, ta iso ta dire masa tray'n a saman table d'in gabansa tana yamusa fuska. ta mike da zumbar barin gurin ya ce "Wad'an can kayan da kika ciresu cikin wanki su ba kayan wanki bane?." "Bazan iya wanke su ba." ta fad'a a takaice ta na kokarin barin gurin "What." yafurta tare da aje sigarin hannun sa ya nuna mata kofar bedroom d'in sa ya ce "Wuce ki je ki wanke su." fuska ta yamutsa wai tunanin sa zata wanke masa gajeren wando da boxes da kuma singilet ne, duk da bada hannunta zata wanke ba washing machine ne zai wanke su, bazata iya d'aukarsu da hannunta ta zubasu cikin injin ba. ta ce "Ni fa bazan iya ba su d'in ma bazaka iya wanke su ba sai an maka." ganin yana kokarin mikewa ta d'aga kafa da sauri zata bar gurin ya fizgota ta garu da jikin sa. kiciniyar kwatan kanta take tana fad'in "Ka sake ni na rantse bazan wanke ba sai dai ka wanke abin ka." d'an zubawa lips d'in ta ido ya yi yanda take motsasu. lumshe idanunsa ya yi tare da kuma bud'e su lokaci guda. ya sakalo hannunsa guda kan kugun ta ya janyo ta zuwa jikin sa. ido ta waro jin abun da ya matan zaton ta wani salon muguntan ne yake shirin yi mata. sai kawai taji ya tallafo kanta da d'aya hannunsa ba zato taji bakinsa cikin nata. wani irin waro ido tayi ya yin da zuciya da jikin ta duk suka d'auki rawa. duk yan da taso ta kwace kan ta ta kasa yakai tsawon mintuna biyar yana tsotsar bakin ta. kana ya sake ta ya zube kan kujera tare da d'aukar sigarin sa ya kunna yashiga zukarsa da sauri-sauri. wani irin mutuwar tsaye tayi mamaki had'e da tsoro suka lullub'e ta. sosai jikin ta ke rawa amma ta daure ta dube sa cicin dakiyar zuciya ta ce "Wlh Allah ya isa tab'a jiki na da kayi, wai ma me ka d'auke ni ne kam?, kana tunanin kowa irin wancan 'yar iskan da ta ke kawo kan ta gare ka ne, to wlh kada ka kuskura kasake yunkutin tab'a min jiki dan

Chapter 15 of 19