Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kuka, irin kukan da babu wani mutum da ya taba Yi a gaban shi, saboda shi din Bai kasance me yawan Shiga sabgar mutane ba, Bayan gaisuwa babu wani Abu da ya ke Kara Shiga, sede idan abun aiki ne ko Kuma wani important abu. To Amma fa Bintu zaune tana kuka, kukan da yake jin shi har cikin zuciyar shi, yake Jin kamar dama she has been holding for long Kuma yau ta samu yadda zata fito da hakan. Se yaji dukka hankalin shi ya tashi, yaji ya rasa words din da zaiyi amfani da shi wajen comforting din ta, Haka Kuma Bai San me yasa yake Jin wani irin rashin hankali Yana shigar shi ba. Sosae nayi kuka, ni kaina so nake na daina kukan ganin yadda Dr Akram yake ta cemin he's sorry, kilan tunanin shi na bashi ko laifin shi ne Dan yayi magana, unknowing to him Ina kuka ne saboda komai na rayuwa ta da ya shude Yana dawo min, tamkar anyi min fami Haka nake ji. "Babu Wanda yake so na a gidan mu, a waje kowa fada min yake ni mummuna ce, suna ce min nayi kiba da yawa nayi shedding fat din jiki na. Sir ya zanyi? Ya mutane suke so nayi tunda bani da power over yadda nake son jiki na ya kasance" Yayi shiru Yana Jin abin da nake fada, se da na Gama yace " I understand abin da kike nufi Bintu. I'm so sorry that you went through all this alone. Kiyi shiru yanzun muje nayi dropping din ki a gida" Naji dadin wannan maganar Dan kuwa gani nake bazan iya cigaba da magana ba, idan na cigaba Kara kuka zanyi saboda Ina iya hango tausayi na cikin idanun shi and that happens to be my weakness! Na Mike sannan na dauki jaka ta, ya dauki keys din Shi yayi gaba, se da na Fara fita sannan ya biyo baya na. Motar shi ko a faculty daban take dukda wancan karon da daddare naga motar Amma yadda take daukar idanu dole na gane ta, kafin ya karaso ya bude min yayi min alamar na shiga, na bude na shiga baifi minti na biyar ba se gashi yazo, ya bude gefe na ya shiga, ya dube Ni hannun shi rike da ruwa da kuma Apple juice da ake siyarwa can baya, natural fruit extract ne. Ya Miko min yace " Ki Sha!" Haka na amsa ba tare da musu ba dan bazan ma iya musun ba. The drive was absolute silent har ya kaini kofar gida, yayi parking na juyo na kalle shi da kodaddun idanu na nace " Sir nagode! Nagode sosae Allah ya saka maka da alkhairi." Yayi min murmushi yace " Kada ki manta gobe muna da test, kiyi karatu sosae, I want you to emerge at the top!" Na gyada Masa Kai na Ina fadin in shaaa Allah, daga Haka na fito na wuce cikin gida. Se naji Dadi yau daya cikin zuciya ta, naji Nima akwai mutum daya da yayi honoring du na, har ya damu Dani ya Kuma ke son yaji abin da yake damu na! Dukda Nima mamakin yadda akai na sake jiki da shi nake, na Rasa me yasa Amma koma dai menene Ina Jin shi din wani me daban cikin rayuwa ta! Bayan ya zauna yaga shiga ta gida sannan ya juyar da Kan shi da nufin tafiya gida, se yaga wani dattijo ya fito.daga gidan, Kuma yanayin shi irin nawa ne, har ya Fara kokarin bude motar Dan yaje ya gaishe shi se Kuma wata zuciyar ta tuhume shi da dalilin hakan? Da ya kasa Kare Kan shi se kawai ya ja motar shi ya tafi gida. Yana zuwa kamar kullum yayi parking sede yau community din tasu kamar akwai damuwa, Bayan ya Shiga ciki ya tarar da Safiyya na kokarin fita, ya tambaye ta me yake faruwa tace Masa Alhaji Gidado ne bashi da lafiya Yana asibiti, ci abinci kazo muje idan baka gaji ba. "Muje na kaiki, Allah ya Kara sauki!" *** "Ni Mami na gaji, ko kadan ace mijin ka baya ganin mutucin ka, kullum cikin rigima da tashin hankali ake. Kuma idan mun zauna mu kasa gane abin da yake faruwa tsakanin mu" Daga dayan bangaren wayar Mamin tace " To Samiha Nima kullum na gaji da Jin korafin gidan ki, bake kadai bace ba 'Ya ta, na aurar da yawa. Idan akwai abin da kike Masa da baya so kiyi kokari ki daina" Kafin Samiha ta bawa mahaifiyar ta amsa se jiyo muryar Bashir tayi Yana kwala Mata Kira tamkar zai cire makogaron shi, cikin kosawa tace "Mami kin jishi ko? Kinji yadda yake Kira na kamar wadda tayi Masa sata ko? Mami na gaji" Ita kanta tana mamaki tasan bayan rabuwar su da Bintu soyayya sukai sosae ita da BashPrince00, soyayya wadda kowa ya tashi kwatance se anyi dasu Amma bayan sun Yi aure ko wata biyu basui ba tamkar an dauke musu nutsuwa Haka suke, Babu kwanciyar hankali ko kadan ya Kuma Rasa gane dalilin da yasa zaman nasu ya koma Haka. Ba zai iya tantancewa ba, idan Kuma ya zauna yayi tunanin shi dai yasan har cikin zuciyar shi Yana son ta, Amma ya rasa me yasa da ya dawo gida ya ganta se yaji she's getting on his nerve. Ya Sani ba halin shi bane ba fada, itama Kuma Haka Bata da fada Amma Kuma dukkan su sun canja sun Zama mafadata kamar wasu karnuka. Karasawa yayi ciki tana tsaye ta saka hannun ta a kugunta, har wani jijjiga jiki take irin kana cemin kule zance cas! Da ya taho niyyar shi yayi Mata magana a hankali Amma da yaga wannan abun se yaji ya sake fusata har wata zuciyar na fada Masa ya faffalla Mata Mari tunda Bata da kunya. Amma se yayi saurin girgiza Kai, anything Amma Banda duka, " Ke mahaukaciya ko ke kurma ce da kina ji na Ina kiranki kinyi min banza!" Wani lokacin abubuwan rayuwa se ana hakuri, Babu yadda zaayi ace Kuna zuane Kuma tare daya ba zaiyi hakuri da.daya ba, wannan ba hanya bace me bullewa ba. "Wuta ka taka da zaka dinga yimin irin wannan Kiran, na gaji na gaji da Zama da Kai, auren ka Babu abin da ya tsinana min ban da tashin hankali da musifa..." "Ni kike cewa Haka? To shikenan tunda Haka Kika ce kije na sake ki saki daya!" Tayi dariya tace "Alhamdulillah tafi nono fari, Nima na huta" Daga Haka kowannen su ya bar corridor din ya nufi dakin shi, kunsan yaran masu kudi, kowa ya Fara hada suitcase din shi Dan tafiya gidan su. Amma se Samiha ta Fara ayyana Wai fa auren ta ya mutu, auren ta da Bashir fa ya mutu, ai se ta bare Baki ta Fara kuka kamar zata tsaga dakin, shima a nashi bangaren bayam ya Gama rubuta takardar se ya zura ma takardar idanu Yana mamakin Kan shi, da hannun shi zai saki Samiha, me yake faruwa da shi? Ina dukkan son da yake Mata ya tafi? Ikirarin forever is the deal ya wargatse kenan? Se ya lalubi wayar shi ya Fara Kiran mahaifiyar shi da yake Kira Ammiey. Bugu daya ta dauka " Ya akai naji muryar ka Haka? Ita Kuma Samiha ta Kira Ni tana kuka. Me yake faruwa daku?" Shima da zai samu kukan zaiyi, idan da zai iya tabbas kuka zaiyi Amma shi bashi da saurin kuka ko kadan. "Ammiey na saki Samiha..." "Saboda me? Me ya faru? Me tayi maka?" Helplessly yace "Na gaji Ammiey, auren ta ya fita a raina, shekaru kusan biyu da auren mu Ammiey na kasa samun nutsuwa, kullum gidan mu kamar Tasha Haka yake, saboda fadan da muke. I need to take a break. " Ammiey ta saki ajiyar zuciya cikin rashin Jin Dadi tace " Ba zaku zauna kuyi sulhu ba? Gani kuke kashe auren naku shi ne mafita ubana? Ka jira ni Zan zo gidan yanzun!" Haka ya zauna da waya a hannun shi yayi shiru, idan ka kalla yadda suke rayuwa zaka rantse da Allah cewar wani ne yayi musu Allah ya Isa! [1/3, 20:28] Maman: 035 Dukkan su a zaune a parlor itama Kuma Ammiey shigowar ta kenan, da kanta ta shiga ta Kira surikar tata wato Samiha Santa samu tana ta kuka gwanin ban tausayi, fuskar ta tayi ja saboda kukan da take, tana ta lallashin ta har Suka fito sannan ta dauki wayar ta ta Kira Bashir, Babu jimawa ya fito, yazo gaban ta ya durkusa ya gaishe ta cikin ladabi da biyayya. Ta amsa cikin kulawa sannan ta bashi damar Zama kujerar Dake fuskantar ta Kuma take kusa da wadda Samiha ke zaune akai. " Me yake faruwa a cikin gidan ku? Da har ba zaku iya daidaita Kan ku ba se Kun kashe auren ku? Kun bani mamaki, nayi mamaki kwarai da naji Bashir ka saki Samiha, Ina kaunar da kuke yiwa junan ku? Ina yadda kuke kula da junan ku da har kowa yake shaawar ku?" Dukka sukai shiru tamkar ruwa ya cinye su, kowa a cikin su is reflecting Akan misdeed din shi, Amma kowa Kuma gani yake laifin Dan uwan shi ne! " Shi ne Ammiey!" " Ita ce Ammiey!" Suka fada kusan a tare, se Kuma dukkan su sukai shiru, hakan yasa Ammiey girgiza Kai tace " Ni bana zo fault finding bane ba, nazo naji matsalarku na Kuma baku shawarar yadda zaku maganace ta, idan har zaku cigaba da ganin laifin juna abubuwan ku bazasu tafi daidai ba. Kai na Sanka da hakuri ke na San ki da tarbiyya to duk Ina Suka tafi? Watsar dasu kukai?" Tayi musu fada sosae sannan ta bar su ba tare da ta tilasta musu su maida auren su ba, hakan da tayi musu tana son taga gudun ruwan su ne. Bayan fitar ta ya dube Samiha da tayi shiru maganganun sirikar tata na sinking cikin Kanta, itama ba Haka taso ba, ba Haka ta tsara rayuwar auren ta ya kasance ba, sede Bata da tsimi balle Kuma dubara. A hankali ta Mike Dan tafiya dakin ta, Bashir yayi saurin bin Bayan ta yace "Na janye sakin da nayi Miki! Ina fatan mu zauna lafiya!" Ta sauke wata nannauyar ajiyar zuciya ba tare da ta juyo ba ta wuce dakin ta. Wayar ta ta dauka ta Kira aminiyar ta Hafsatou Bala, Bayan sun gaisa Hafsatou tace " Me ya samu muryar ki naji duk a shake?" "Hafsatou could you believe Bashir yau ya bude bakin shi yace Wai naje gidan mu ya sake bi!" "Ke Bari Dan Allah Samiha! Wannan tatsuniya kike karanta min ba dai Bashir ba" Hafsatou mamakin wannan magana take har cikin ranta " Nima da ya fada Hafsatou ban yadda ba Amma wallahi da gaske ne!" Se ta Fara salati kafin Kuma ta nutsu tace "Kina Ina yanzun? Kada dai har kin tafi gidan Mami?" Ta girgiza Kai tana kallon suitcase din ta wadda tayi dam da kaya, tace " Ammin shi tazo, Bayan ta tafi ya dawo Dani. Amma nasan tunda aka Fara haka wata Rana zaa sake yi. So ya zanyi? Ki bani shawara" Tayi shiru tana tunani kullum tana so tayi Mata magana Amma ta rasa ta inda zata Fara , Amma yau tace to bari ta gwada saar ta "Ki saurare ni Samiha, nasan kina tunanin why is your matrimonial home always in dispute. Baki tunanin hakkin Bintu Ginsau ne?" Samiha tayi shiru tana son ta tuna wacece Bintu Ginsau ma? Se kuwan ta tuna a take komai da ya faru yayi clicking kanta tace " Sure BinGin! To Amma Hafsatou nayi Mata laifi ne?" "Kinyi mana, Zaki ga kamar ba laifi kikai ba but morally abin da kike Bai kamata ba" *** A tare suka tafi asibiti shi da Safiyya da Kuma Iman ita zeeyzeey tana makaranta. Tunda suka dauki hanya yake bawa Ummaah labarin Bintu, tunda take da shi, Bai taba ko da Wasa ya Bata labarin wata mace ba, Wai da sunan kawa ko wani abu se yau. Hakan yasa ta bashi dukkan hankalin ta tana sauraren shi " Ummaah ta Yaya kawai Dan danka Yana da kiba, body figure din shi ko Kuma yayi Baki se ka tsane Shi Ummaah, what's beauty idan ba trial ba" Safiyya na murmushi tace " Amma banji Dadi ba, a Ina ka santa? What's her name?" Ba tare da ya fahimci yanayin yadda uwar tashi ta fassara zancen shi ba yace " Student di na ce, sunan ta Fatima Bintu!" Ta gyada Kai tace " Allah sarki!" Haka ya cigaba da bata labarin Bintu ba tare da ya ma fahimci yanayin hakan ba. A zuciyar Safiyya tamkar an haska saboda dadi, yau danta ne take zancen wata yarinya. Alhaji Gidado na kwance a gadon da aka bashi na asibiti, Dan ma ance a Dan fita a bashi waje Amma yadda yaran shi da Kuma yaran Yan uwan shi Suka cika gurin. A hankali Suka tako Yana rike da Jakar mahaifiyar ta shi, dayan hannun shi Kuma Iman ta kankame hannun. Kowa da ke asibitin yasan tabbas an kwantar da babban mutum saboda yadda wannan family din suka taru Babu kakkautawa. Aunties din shi ya gaggaisar sannan ya wuce can inda mazan suke ya zauna suka gagaggaisa, Bayan wajen awa Suka shiga suka duba shi sannan suka fito. Zasu tafi Minal wata cousin din shi ta karaso da sauri tana fadin " Hamma Akram Dan Allah nazo mu tafi ka sauke ni zanyi shopping!" Ya tsaya sannan ya dube ta yace " Bata nan zamu wuce ba!" Daga Haka ya cigaba da tafiya shi da Iman da ke tsalle tsalle, yayin da ita kuma Safiyya se lokacin zata taho ta tsaya gaisawa da wadanda suka kwana biyu Basu gaisa ba. Suna zuwa gida abinci ya Fara ci sannan yayi sallah, kamar kullum ya Yi dukkan routine din Shi kafin kwanciya sannan ya zo kwanciyar. Se Kuma Bintu ta Fado masa, ko me take Yi a yanzun?ya ayyana cikin ran shi, ya cigaba da Dan tunanin how much of pains da yake tunanin tayi enduring ita kadai cikin rayuwar ta. A bangaren na nayi karatu sosae, dukda na kasance Haka nake Amma wannan karatun se nake ji kamar I owe it to someone, naji Ina son na fidda shi kunya ta hanyar cinye test dinnan. Dan Haka babu Wasa na dukufa ni ce har dayan dare kafin na je kitchen na tafasa slimming tea di na na zubo cikin mug, Ina karatu Ina Sha har na shanye tas kafin na kuskuro Baki na sannan na kwanta, Babu jimawa Bayan na Gama duk tunanin peace din da ya Fara ziyartar rayuwa ta kwana biyu, Ina ayyana dalilin hakan se Kuma na tuna irin gudunmawar da Akram ya bawa rayuwa ta, for unknown reason se kawai na Fara murmushi Ina Jin wani nishadi me dadi Yana shiga ta. Mamaki sosae ya Kama ni na yadda lokaci daya nake Jin kamar rayuwa ta tana canjawa. A hankali dai bacci ya tafi dani. Washegari na tashi da wani irin kuzari, for the first time naji na tashi da annashuwa da Kuma walwalar. What has gotten into you Bintu? Haka na dinga tambayar Kai na lokacin da nake kitchen Ina hada meaty spaghetti da akai order. Bayan na kammalla nayi wanka naci abinci kamar kullum na Sha abubuwan da nake ganin zasu saka kiba ta ta ragu na Zama yadda nake so. Bayan na shirya na sako wani atamfa me kyau da Mamaa ta Dinka Mana, normally duk kayan zuwa makaranta ta materials ne Amma yau se naji Ina son na saka wani kayan daban. Bayan na saka na Fara kokarin daura Dan kwali se na kasa, Batuul dake shafa Mai akan gado tace " Haka saurayi kikai Naga har wani rawar Kai kike" Ban ce Mata komai ba balle na Bata amsa, a karshe na samu na daura dankwalin na dakko wani veil da ya shiga da atamfar na yafa se naji dukka I'm uncomfortable. Nan ma Batuul ta Fara dariya tana fadin " Wallahi gwara ki saka hijabin ki kinfi kyau, Kinga yadda tumbin ki ya fito kuwa?" Na juya a fusace Ina kallon ta, ta karasa yafa karamin veil din ta ta fice ta barni tsaye Ina harar ta, se Kuma naji I'm demoralized bani da confidence din fita da shi, kilan idan na fita da shi mutane suyi tayi min dariya nayi wani irin, cikin sauri na maida shi wardrobe sannan na dauki hijab na saka na dauki jaka ta na fita, dakin Mamaa naje nayi Mata sallama sannan naje dakin Adda wadda ta Gama shiryawa alamar fita zatai, tace " Muje na sauke ki. Kin dai ki Suleiman ko? Naga Wanda Zaki aura ai. Har ni zance Miki kiyi Abu ki kiyi" Wani irin yanayi naji marar Dadi nace " Adda ya zanyi? Kema kin San Suleiman baya so na, so kike na dinga cusa Kai na wajen shi?" Ta fusata zata Kai min hannu nayi saurin matsawa Wai na Yi Mata rashin kunya, har Ina mayar Mata magana. Na Bata hakuri sannan nabi Bayan ta zuciya ta kamar zata fito. Batuul na gaba ni Kuma Ina baya muna tafe suna Hira wadda kusan dukka labarin saurayin ta take bawa Addar ita Kuma tana ta saurare tare da murmushi. A school suka sauke ni, na Mata godiya sannan na tafi class, gaba daya mood di na ya baci, yadda na tashi da safe cikin farin ciki ne da zumudin zuaa makaranta amma a yanzun se naji duk Raina ya baci. Bayan zuhr aka zo yin test din, yau Bai zo inda nake ba Wanda yasa naji rashin Dadi, bai Kuma tambaye nu ko naci abinci ba kamar yadda ya saba, duk se naji kamar an kukkunce min knots din Kai na. Fuskar shi Babu annuri ko kadan ni Kuma saboda zakewa Wai se nake Jin Babu dadi, guys imagine my audacity! Haka ya rarraba question papers din ko kallo na baiyi ba da yazo wajen bani, duk se naji idanuna sun cicciko da kwalla, ko dai shima ya gaji Dani he find me boring and unattractive again? Me yasa bani da sa'a ne cikin rayuwa ta? BashPrince00 ma da ya Fara so na he chose Samiha over me! Kuma a take se na tuna samihan, I'm sure tana can tana farin ciki a rayuwar ta, wannan tunanin sun da nayi se kawai na Fara kuka a hankali Wanda ko mutum na kusa dani ba lallai ya fahimci hakan ba. Duk abinda nake Ashe Yana kallona, ban gaya muku how observant gayen nan yake ba ko? To shi mutum ne me kula da Kuma lura. Har aka kammalla test dinnan banyi cikin dadin Rai ba Bai Kuma kula ni ba, sannan na kasa fahimtar ma abin da yake tunani daga fuskar shi, Dan kuwa expression din shi was very blank! Ayi hakuri a Kuma Kara hakuri... we're almost there. Thank you for hanging around 😊❤️😘 Ta_kwalam ce [1/3, 20:28] Maman: 036 Ko da Muka kammalla test din nayi tunanin kamar yadda aka Saba zai bimu ne one on one ya karba, Amma se yace Mana duk wanda ya Gama kawai ya kife sheet din ya fita, the class is over. Haka kuwan nayi na goge fuska ta sannan na sake dage hijab di na ya rufe kusan rabin fuskata kafin na fita, duk tunani na zaice na tsaya Amma shiru kake ji baice min ba, hakan ya sake tunzura ni naji kamar irin I'm worthless dinnan, na Fara tunanin ko dai shima he finds me boring kamar yadda kowa yake gani. Ina fita napep na.sauke wata Dan Haka na tare Dan tafiya gida, sede kafin na Kai ga Shiga sajida ta fara Kira na. Se da na shiga sannan na dauki Kiran, Muka gaisa ta tambayi ko na gama lecture nace Mata na gama se tace tana son nazo gidan ta na zauna da yaran ita Kuma zata je biki da Batuul! Wato Ni na Zama Nanny kenan? Kowa idan ya dakko wahalar yaran shi se ya Kira Ni nayi babysitting ko? For the first time nace " Na karba order cake yanzun zanje nayi suna jira na" Na fada Ina sake tamke fuska ta, tace " To kizo ki tafi dasu gida idan yaso idan na dawo se na biyo na dauke su!" Nan ma nace " Ai na kusa zuwa gida, sede ki biyo ki kawo su" Nasan yau zatai mamaki saboda ko kadan ban taba Yi musu musu ba, duk wani abu da zasu saka ni Ina Yi dukda ba godiya ake yi min ba. Haka na kashe wayar Ina jiyo ta tana cewa Batuul ai nace na wuce ita Bata San yadda zatai da yaran ba. Ina zuwa gida na wuce daki kamar yadda na saba, kwamciya nayi zuciya ta ko kadan Babu dadi. Kawai hango dull fuskar shi nake da yadda ko kula ni baiyi ba, zuciya ta se ta Fara tuhuma ta da Wai me yasa na damu tun da kuwa nasan ni da shi Babu wani Abu da ya hada mu, he's just my lecturer, whereas I'm his only female student. To se menene Dan Bai kula ni ba, Naga Yan gidan mu karewa da muke related by blood ba kula ni suke ba shi ne Zan damu Kai na. Maimakon wannan tunanin yasa naji Dan Dadi ko na watsar da tunanin shi, a'a se ma wani bangare na zuciya ta ya Fara kokarin Kare muradin ta da nuna min, shi fa Akram mutum ne me muhimmanci cikin rayuwa ta shi din therapist di na ne, ta Yaya zaai naji Dadi idan therapist di na ya daina kula ni? Shi fa ya Dan Fara boosting confidence di na ya nuna min Nima mutum ce like all other person. Ina nan kwance se sallah kawai ke tashi na har na Fara jiyo muryar hajja, kamar an tsikare ni Haka na mike, ita hajja mahaifiyar Mamaa ce, da gudu na fita na fada jikin ta Ina dariya, ta rungume ni tana fadin " Ja'ira! Karya ni kike so kiyi?" Nayi dariya Ina Zama kusa da ita nace " Hajja Baki ce min Zaki zo ba Kuma? Sannu da zuwa! Me Zaki ci?" I find comfort and love a wajen wannan tsohuwar, Mamaa da Adda se murmushi suke ganin yadda muke da ita, ita dinma sosae take sakin jiki da Ni ko jikokim ta albarka. Na tashi naje kitchen cikin zobon da nayi na kawo Mata, na dauki Jakar kayanta zuwa dakin mu. Cikin hour daya nayi Mata grilling kifi na kawo Mata hade da abincin da akai a gida. Se da Naga taci sosae kafin na bar ta ta tafi wajen Mamaa sannan na dawo daki Ina Jin dadin zuwan ta, ko ba komai zuwan nata ya saka hankali na ya dauke daga tunanin Akram. Bayan maghrib hajja ta dawo daki na Muna ta hira har na kasa karatu, Babu jimawa Kuma se ga Iyan KT, ban sani ba ko Kun tuna ta? Idan ba ku tuna ta ba to mahaifiyar Adda kenan. Ai murnar da nake se da ta bawa kowa mamaki, ita ko dakin su Adda da Mamaa Bata je ba, yadda na karbo kayan ta dakin mu na wuce da su, na hada Mata ruwa tayi wanka sannan na hada musu abinci ita da hajja suna ta yabon girkina, Wai ko iayye na albarka. Abin da nayi zai tabbatar maka how lonely my soul is, I'm yearning for love and attention. Su Adda har Kawu anan Suka zo suka gaishe su. Wajen Tara na Gama musu shimfida anan nake Jin ai kudin Batuul zaa kawo shi ne dalilin zuwan nasu. Adda Dake zaune Bata tafi ba, hajja tace " Asiya Ina Batula Kuma?" Se Kuma Adda ta dube Ni tace " Bintu Ina 'yar uwar ki? Me ya faru Bata dawo ba?" Na dubi Adda da mamakin tambaya ta Inda shalelen ta take nace " Tana gidan sajida!" Se kuwa Iyan KT ta Fara fada " Yanzun Asiya har Baki San inda budurwar Yar ki ta tafi ba, karfe nawa yanzun? Har yanzun Baki daina sakar ma yarannan suyi abin da suke ba. Ki wasu irin iyaye ne? Ke kawata.." Ta fada

Chapter 14 of 18