kuma sai yaushe zamu ganki?
Dariya tayi ya kamar matar nan tayi kewan mijin ta ne ba ga yayana a gida ba karki damu na kusa zuwa
Umma tayi murmushi "tace yo ba dole ayi kewan miji ba kunje kun zauna abunku a jiddah shiru-shiru bakwa leqo mu kin hanani samun ladan sa maki tuwo kici.
hira suke cike da da zolaya da fara'a sai ka ranste qawaye ne ba matar yaya da qanwar miji ba
Ummeyh tace "Ummansu Insha Allah qarshen satin nan xan xo naga mataaye na ( da matan baba qarami) da kuma uwata da yayyuna uwa uba yarana"
Cike da jin daɗi Umma tace "Allah yasa kur kisa mana rai this time ma Gwaggon yara mu gama shirya tarba baquwa taqi zuwa, Allah tabbatar dai ya kuma kawo mana ke lafiya.
Nikam ya doter da jikin nata fatan jikan namu ya barta tayi lafiya?
lah kinga na manta ban faɗa maki ba mijinta ma ya buge wani bawan Allah suna asibiti yanzu haka ɗazu ma yayanki ya dubo su ya shiga Abujan.
Subhanallahi hastari dai to Allah ya sauwaqa ya kuma kiyaye na gaba
Umma tace "Ameen ya Rabbi Gwaggon su". Suka yi sallama ta kashe wayan maida duban ta wajan Little tayi Angon gilani yi shiru abinka anjuma zan kaika ko ba abokin ka ya dawo mana da car kaji, da qyar ta samu ya lallashu yai shiru ya daina borin.
Ameerah suna isa gida a gajiye ta shiga wanka tana fitowa ta faɗa gado sai baccin gajiya, ganin bacci ya ɗauke ta murmushi yayi yace "mutum sai rigima an girma ba'a san an girma ba wai abaroki asibiti bayan zaman da kika yi ashe kina jin bacci wiffey case" ya shige bathroom shima ya wasta ruwa yazo ya kwanta gefen ta bacci yai gaba dashi.
Fitowa tayi daga toilet en ɗaure da wani babypink towel, gaban dressing mirror ta wuce direct mai ta shafa kawai tayi gefen da ma'ajiyan kayakin ta suke, riga da skirt na less ta jawo ta sanya amma skirt en yaqi shigan ta, kallon kayan tayi tace "abu baka fi 1 month da saya ba har ka masteni ya Rabb wani irin hips ne dani kaya su ta mawa mutum kaɗan" guntun tsaki taja tai jefi dashi ta jawo wani gown ta sanya ta rufe fuskanta as usual ta fito jakadiya ta samu tsaye a qofan tana jiran fitowan ta "Barka da fitowa uwar ɗaki na mai dogon zamani" hannu Gimbiya ta ɗaga is okay kije ciki in kin gyara akwai wani kawa a qasa ki bawa mai so okay.
Tana gama magana tayi gaba dan zuwa sashen mahaifiyar ta.
Umman Amjad da Abban sa kewan yaronsu suke sosai ba ɗan kaɗan ba Umma har da ɗan ramewanta
Suna zaune akayi sallama, jin anfara shigowa gidan sai Abba yace a qariso.
Ahmad abokin Amjad ne ya shigo sannu da zuwa Umma ta masa ya durqusa har qasa ya gaida Abba da Umma duk suka amsa da fara'a, Umma Amjad yana nan ne?
Abba yace "Amjad dai? Baku haɗu bane kan ya tafi ko bakasan zai yi tafiya ba?
Abba ban sani ba gaskiya jeji ya shiga ne ko Doha?
Murmushi Umma tayi yarona Ahmad wani jeji qasan gaba ɗaya ya bari fa baka da labari kenan ya tafi wani qasa acan wai Nigeria aka ce mata nake ga.
Buɗe baki kawai Ahmad yayi amma dai ba muyi hiran zai yi tafiya ba har na barin qasa ko da yake ma bamu cika haɗuwa ba, yanzu dai Umma a taimaka mun da layin sa da kuke waya.
"Amadu Ni da Umman taku duka wayan jagwal ne sai a hankali kawai" Abba ya faɗa yana murmushi,. Tom Abba amma mai yaje yi?
Umma tace "wannan yaron nawa sai a hankali wani irin abota kuke haka ni mairo wai bai faɗa maka abinda ya faru bane?"
Umma bai faɗamun wani abu ba gaskiya kinsan sa da rashin son magana bare dogon hira, taɓa baki Umma tayi to Allah ya shiryamun shi, Nan ta kwashe labarin duk abinda ya faru ta faɗa masa.
Kama taɓa Ahmad yayi ya gyara zama "wato dai ranan abun da ya kaisa gidan sarki kenan shine bai faɗamun ba shine har da kishi kar na rakasa" abinda ya gama faɗa a zuciyan sa kenan kamun yace "to Umma Allah sanya alkhaeryh Allah basa Sa'a ya dawo dashi lafiya, dama zan koma ne inshà Allahu zan dawo nima in lokacin bikin yayi"
Ameen ya Rabbi yarona kaima Allah kaika lafiya Allah nuna mana lokacin da rai da lafiya
Miqewa yayi yace "Abba Umma sai wani lokacin" ya faɗa yana yin hanyan fita, da addu'an Allah kiyaye hanya Umma da Abba suka bishi har ya fice.
Umma ta juyo ta kalli Abba murmushi tayi tace "wannan yaro naka Allah ya shirya sa wai dan ma abokin sa ne".
Sai bayan magrib Ameerah suka koma asibitin
Sun same sa a kan darduma, jikin sa da sauqi
likitan ne ya shigo yace "Insha Allah gobe zai sallamesu in yaso su qarisa jinyan qafan a gida ko nan da sati 1 zuwa 2 ne kamun ya warke sosai dan qafan ne kawai yanzu damuwa amma b abinda yake damun sa"
Godiya Daddyn Little yai wa abokin nasa yace "Allah kai mu goben frnd".
Da Ameen likitan ya amsa kamun ya fice a ɗakin
Gaisawa suka yi duka da mara lafiyan suka masa ya jiki ya amsa da sauqi.
Har aka yi sallan isha'i suna can, sai da lokacin ya ɗan tafi ganin dare nayi suka masa sallama
Suka kamo hanyan gida.
Sai da suka yi sallan isha'i kowa ya taɓa hutu kamun suka tafi sashen kawun nasu wanda suke qira da baba qarami suka gaidashi da matan sa suka dawo kowa ya wuce dan ya kwanta don gajiyan bai tafi ba.
Soja ne yake ta laluɓa wayan sa amma shiru babu wayan ba labarin waya, fitowa yayi yaje ya duba har cikin motor nan ma babu waya, abun da ya faru ɗazu a hanya ne ya faɗo masa a rai tabbas ba ko kokonto yarinyar nan ce ta ɗau wayan nan.
Juyawa yayi ya koma ciki ransa a ɓace yayi hanyan ɗakin da yake na su Maha, da ya Abdoul ya haɗu yana zaune a palourn Kakus yana danna waya
Ganin Soja sai ya Abdoul ya tsayar dashi yace "our able army sai ina haka? Ya Abdoul ɗakin su Mahreen zan karɓo wayana
Ya Abdoul yace okay plss a turomun Mahreen ɗin tazo ina dinning area
Tom ya Abdoul.
Sallama yayi a qofan dakin nasu, Mahreen ce ta amsa ya Habeeby ka shigo
Shiga yayi ya bata saqon qiran da ya Abdoul ke mata, himar ta jawo ta saka ta wuce dan amsa kiran da ake mata.
Bayan fitan ta in da Mahreen ke kwance tayi ɗaɗɗaya ya nufa, yana zuwa wajan ba jinkiri kawai ya jawo ta qasa ji kake timmmmm!
Kaman a mafarki ta ji an buga ta da qasa ihu ta saka 'Wayyo Mutum ko Aljan na shigesu za'a karya"
Cewa yayi "qanin ubanki ne zaki tashi ne ko sai nayi ball dake? wai ke ina wasa dake ne kam da har zaki ɗauki wayana? Kin tashi kin ban wayana ne ko sai na harbe ki idiot kawai
Jin muryan sa kuma tasan halin sa tashuwa tayi a hankali tana hawaye dan tabbas ta bugu
Ɗauko wayan tayi ta basa tana Allah ya isa kuma sai Allah ya saka mun.
Sarai yaji me tace amma sai ya basar heɗe ransa yayi yace "ke me kika ce?
Tura baki tayi ni ba abinda nace
Qwafa yayi ya duba wayan yaga chajin shi bai ko sauqa ba alaman bata yi komi dashi ba kawai neman magana ne, tsaki yaja "Ni na rasa mai yasa bansa security a wayan nan ba" da ya gama seta mata zama yai hanyan waje dan ya koma ɗakin sa.
Bayahn fitowan Mahreen wajan zama ya abdoul ya nuna mata ya mata umurni da ta zauna dan samun su tattauna
Bayani yake ta koro mata daki-daki na yacce yai kewansu sun jima basu zo Bauchi ba
Sai da ya tabbatar ta sake dashi suna hiran kamun ya numfasa a yanayi na muhimmin magana ya dube ta yace "qanwata ki aramun duka hankalinki anan zamu yi magana mai muhimmanci kinji"
kallon sa tayi da murmushi tace "yayana in da qarin hankalin ma duka na ara maka ina sauraranka"
Nan ya kwashe duk abinda ke xuciyan sa abinda yake ji game da ita tun da ya ganta ya faɗa mata(hausawa suka ce abari ya huce shi ke kawo rabon wani).
Qanwa ta ina sonki so kuma na gaske son Aure wanda in son samu ne ayi bikin nan cikin wata 1 kai yamun nisa ma irin dai week hakan nan
Tun da ya Abdoul ya fara jawabi tayi qasa da kanta ta ɓoye fuska a hijab da ya kai aya ya buqaci da ta ɗago ta basa amsa taqi ganin ya masta ko takan wayan ta dake hannun sa bata bi ba tayi hanyan ɗaki har da ɗan gudun ta
Dede tana shigowa ɗakin shi kuma Soja zai fice a ɗakin kenan suka kusa yin karo
Ransa a ɓace amma ganin Mahreen tsayawa yayi ya dara yace "yarinya ta kamu kenan taga handsome yayana*
Wucewa tayi tana rufe fuska bata ce komi ba.
Duk abunda ke faruwa kuwa Hajiya kakus ta fito ɗaukan abun gurza goronta data bari a palourn sai ta tarar da draman da ake yi
Ganin duka jikokin nata na son junansu abun ba qaramin daɗi ya mata ba( a tunanin ta Soja ma hira yaje) haka taje ta kwanta da farinciki.
Ya Abdoul ganin ta gudu sai abun ya burge sa ya kuma qara masa qaunan ta "tabbas inason mace mai kunya" abun da ya faɗa ya miqe yana murmushi
Soja yace "yayana Allah kaimu musha biki"
Ya Abdoul da farinciki Yace "Ameeñ our able army"
Dariya soja ya kuma yi ya wuce wajan baccinsa, shima ya Abdoul fice wa yayi ya nufi nasa wajan baccin a sashin su, wanda yake dama da soja ne amma yace a sashen kakus zai kwana.
Ya Abdoul ko da ya koma ɗakin sa haka ya kwanta yana ta juye-juye shi dai har ga Allah yake son qanwar tasa kuma bai qi a ɗaura masu aure ko yanzu ba.
(haba malam abdu daga uhmn sai ehem ko a hand kake ne?
Kunga inko a hand yake ya hwaɗan nice ourmman batoolerh mai wuqa da nama sai nasa a aura masa ita yanzu)
ko ba haka ba FAN'S ?
Mahreen na shiga ɗaki ta samu Maha na sharar kwalla sai tace "menene ya sameki ko wani abun ya habeeby ya maki?
Maha kaman zata rufe addan nata da duka tace "Idon matambayi ne ya sameni, ba habeeby ba habibu mutum sai son jin gulma"
Kallonta Mahreen tayi tai murmushi ita dai tana farinciki bata da time na surutu da Maha
"Allah shiryaki" shine abinda tace tayi kwanciyan ta tana ta murmushi ita dai tana ji kaman ta jita a jikin yayan nata.
Mutumiyar kuwa Allah ya isa take jawa soja yafi cikin girgi.
Autan Umma yana komawa ɗaki kwanciya kawai yayi ko ta kan wayan bai bi ba ransa fess ya fara maganin renin yarinyar nan.....
Masha Allah jama'a sahiyar alkhaery
Mu dai mun riga mun tashi👯 sai kuma inda qarfi ya qare✍️
Muje zuwa
Masoyan 𝙔𝘼𝙍 𝙎𝘼𝙍𝙆𝙄 𝘾𝙀
𝘿𝘼𝙂𝘼 𝙏𝘼𝙎𝙆𝘼𝙍 𝘼𝙇𝙌𝘼𝙇𝘼𝙈𝙄𝙉
👇
𝙃𝘼𝙍𝙄𝙍𝘼𝙏𝙐𝙒𝘼 𝙐𝙒𝘼𝙍 𝘽𝘼𝙏𝙊𝙊𝙍𝙇
💋💋 امى بتولة💋
𝘿𝙤𝙢𝙞𝙣 𝙩𝙖𝙡𝙡𝙖𝙩𝙖 𝙝𝙖𝙟𝙖𝙧𝙠𝙪, 𝙠𝙪 𝙩𝙪𝙣𝙩𝙪𝙗𝙚𝙣𝙞 𝙖 𝙬𝙖𝙣𝙣𝙖𝙣 𝙡𝙖𝙮uka:-
08146292652
𝘾𝙝𝙖𝙩 𝙤𝙣𝙡𝙮.
09161720046
𝙔𝙤𝙪 𝙘𝙖𝙣 𝙘𝙖𝙡𝙡 𝙙𝙞𝙨 𝙤𝙣𝙚, 𝙭𝙖𝙢𝙪 𝙢𝙖𝙠𝙪 𝙩𝙖𝙡𝙡𝙖𝙣𝙠𝙪 𝙖 𝙧𝙖𝙝𝙪𝙨𝙖 𝙢𝙖𝙞 𝙨𝙖𝙪𝙦𝙞, wai hausawa sukace sai an gwada akan san na qwarai. Ni Hareeyh ina maraba da ku masoya, har da alakoron talla inayi😁
# 𝘾𝙤𝙢𝙢𝙚𝙣𝙩
# 𝙇𝙞𝙠𝙚 &
# 𝙨𝙝𝙖𝙧𝙚
💦💦💦💦💦💦💦
𝙔𝘼𝙍 𝙎𝘼𝙍𝙆𝙄 𝘾𝙀𝙀
🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹🌹
𝙎𝙩𝙤𝙧𝙮 𝘼𝙣𝙙 𝙒𝙧𝙞𝙩𝙩𝙚𝙣
𝘽𝙮
𝙃𝙖𝙧𝙞𝙧𝙖 𝙨𝙖𝙡𝙞𝙝𝙪 𝙞𝙨𝙖
(𝙐𝙬𝙖𝙧 batoorl)
اللهم صلى و سلم على سيد نا رسولله saw🖤🤍
_______________________________________________________________
🅿️ 45&46
💋💋 امى بتولة💋
Kasancewan yau Sunday ba aiki da sassafe Ameerah ya haɗa kayan karyawa suka shirya suka nufi asibiti.
Isan su asibitin direct wajan abokin nasa ya nufa ita kuma Ameera tayi ɗakin da mara lafiyan nasu yake
Da sallama ta shiga ɗakin ya amsa mata
Wajan gadon taje ta zauna kamun ta gaida shi
Yaya na fatan ka tashi lafiya ya qarfin jiki?
Lafiya Alhmdlh jiki da sauqi sosai
Masha Allah haka muke so yayana Allah qara afuwa
Ya amsa da Ameen daga haka bai qara cewa komi ba Ganin haka itama bata ce uffan ba
Suna zaune shiru Daddyn Little yayi sallama ya shigo
Amsawa suka yi a tare ita da mara lafiyan
Gaisawa suka yi da Daddyn Little ya masa ya jiki? Yace "da sauqi sosai"
Ameerah ce tace "husby har ka karɓo mana Sallaman?
A'a wiffey ban same shi ba kinsan yau Sunday ba lallai yazo da wuri ba ga kuma munyi sammako
Tace "Tom shikkenan sai kazo nasa maku abun karyawa"
Sauqa tayi ta shumfiɗa masu babban darduma ta jawo kondon kayan karin ta zuba masu peppe chicken da chip's sai soyayyen kwai ta haɗa masu tea kowa da cup na sa.
Yayana ka sauqo ku karya ko
Ba musu ya sauqo a gadon suka zauna tare shi da Daddyn Little kowa ya ɗau spoon
Chips en yaci kaɗan sai kuma peppe chicken, a jiye cokali yayi ya ɗau cup na tea yana kurɓa
Daddyn Little ne yaci abinci sosai da ya gama ya ɗau tea shima
Suna gamawa ta masto ta tattara wajan sannan ta koma ta zauna
Bayan wasu lokuta Daddyn Little barin danna wayansa yayi ya maida aljihu, miqewa yayi yace "ba na koma wajan likitan nan ko ya zo" Ameera ta amsa adawo lafiya to
Office na likitan ya nufa cikin sa'a kuwa dai-dai isan sa qofan office ɗin lokacin likitan ke isowa shima, da murmushi suka kalli juna Daddyn Little yace "kai man wanne irin likita ne kai haka ka tsaya soyayya kabar mu a asibiti tun qiran asuban farko".
Dariya ya saka wato dai freind sammako kuka yi gaskiya sannu da qoqari Nikam inacan manne da matata sai yanzu aka barni na fito
"Ɗan iska Zaka ji dashi ai Nikam buɗe mana qofa mu shige" Daddyn Little ya faɗa yana dariya
Tare suka shiga office ɗin da sallama, likita ya zauna a wajan zaman sa shi kuma ya nema wajan zama ya zauna
Gaisawa suka yi suka ɗan taɓa hira kamun Daddyn Little yace "kaga frnd sallame ni nasan zaka je duba Patience's naka so kar na ɓata maka lokaci a sallamemu mukam.
sallama ya rubuta masu sannan da sauran magungunan da ake buqata na game da qafan nasa
bayani ya masa yacce za'a sha da na shafawa duka sannan ya kamata ya kai sati a gida kamun ace ya fara fita sai dai yana da kyau ya dinga mosta qafan yana ɗan takawa dan zai fi saurin warke wa ko bai cika sati cif ba
Daddyn little yace "bakomi doctor Insha Allah za'a kiyaye fitansa yanzun fatan mu dai Allah sa ya warke da wurin
Musabaha suka yi ya kuma yiwa abokin nasa godiya yai masa sallama ya fice a office ɗin
Wucewa pharmacy dake cikin asibitin yayi dan ya sayo maganin da aka rubuta a hanya ya haɗu da Abba ya shigo qara duba marar lafiya kamun ya wuce don jiya bai samu komawa ba.
Tare suka je pharmacyn aka basu maganin duka da suka je wajan cashier Abbane ya biyan kuɗin duka yace Daddyn Little ya bari
Suna gama biya suka koma ciki wajan su Ameerah
Gaishe da Abba yayi suna tafiyan sannan ya masa godiya Allah qara arziqi Abba l
Ameera ganin Abba sai taji daɗi sunkuyawa tayi ta gaida Abban nata ya amsa da fara'a yace "sannunku da qoqari mamana"
Gaisawa suka yi da mara lafiyan
Ya masa ya jiki? amsawa yayi da sauqi Alhaji
Umma ya qira bayan sun gaisa sai ya bawa Ameerah wayan
Karɓa tayi ta gaisa da Umman, tambayanta mai jiki tayi tace "da sauqi sosai har an sallamemu"
Umma tace ta basa wayan su gaisa
miqa masa tayi "yaya na ga Umma ku gaisa"
Amsan wayan yayi ya kara a kunnen sa, lumshe ido yayi bayan Jin sallaman Umman Ameera
Bai san meyasa ba jin muryan wannan baiwar Allahn na rage masa kewan Umman sa.
Gaisawa suka yi tace masa "yanzu ya jikin naka yaro na?
ya amsa da sauqi Alhamdulillahi
Addu'oee tai masa sosai wanda yasa shi Jin daɗi fin tunani gaba ɗaya sai yake jin kamar Ummansa ce.
"Ameen ya Hayyu ya Qayyum Nagode sosai Umma Allah saka da alheri"
Suka yi sallama ya miqawa Ameerah wayan
Sallama itama suka yi tace" ga shinan Umma ba na miqa masa"
Daddyn Little ta miqawa wayan tayi amsa yayi suka gaisa da surkar tasa
yace "Umma bakomi Allah qara girma mungode sosai"
Ya miqawa Abba wayan bayan sunyi sallama
Abba kara wayan yayi a kunne ya fita a ɗakin.
Ameera tattara komi da suka zo dashi asibitin tayi Daddyn Little na taya ta yana kwashewa ya kai masu motor
Bayan sun kai komai motor Taimaka wa mara lafiyan yayi yana ɗingisawa har suka isa in da motorn nasu yake Parke, suna isa yabuɗe masa murfin back seat ya shiga ya zauna.
Sallama suka yi da Abba, escorts nasa suka tada motor sae filin jirgin dake garin Abuja
Gaba Ameerah ta shiga Daddyn Little ya shige mazaunin driver ya jasu sai gida
Hira suke sama-sama a motorn suna sako sa shi kuwa yayi nisa a tunaninsa baya amsawa hiran nasu ma (dama shiba ma'abocin surutu bane).
Driving yake a hankali
Juyowa yayi ya tambayesa bro akwai abunda kake buqata mu tsaya mu saya kamun mu wuce gida?
Girgiza kai kawai yayi bai ce komi ba
Ameerah ce tace "husby ka tsaya musai koda fruits ne to"
Tsayawa suka yi suka saya da yawa kaman masu sari, aka sa masu a boot en motorn suka biya suka qarisa gida
Suna isa mai gadi ya buɗe masu qofan yana ranka ya daɗe sannunku da dawowa amsa masa yayi
Parking space ya isa yai parking motorn
Ɗakin da suka shirya already don shi a balconyn gidan Daddyn little ya temaka masa ya kaisa har ɗakin
Ɗakine madedeci mai ɗauke da duk wani abunda mutum zai buqata a ɗaki
Gado,walldrop,resting chair,mirrow, bathroom dis and that ETC.
Komai na ɗakin blue color ne
A bakin gadon dake ɗakin suka zauna duka yace masa "sannu bro, sannan ya ɗaura da basa haquri akan abunda ya faru tsautsayi ne ya yafe sa".
Murmushi kawai yayi bai ce komi ba dama Daddyn Little yayi tsammanin haka
Mutumin bai fiye magana ba sai dai wani lokacin gwanda in Ameerah ce yakan amsa mata jefi-jefi
Bayan taga wucewan su itama cikin gidan tayi
mai gadi ne ya jido kayakin dake motorn duka ya biyota dashi sallama yayi ya jiye masu komi a palourn.
Tana shiga ɗaki ta wuce direct dan ta watsa ruwa ganin yanayin garin ana zafi
Bayan Daddyn Little ya masa sallama wucewa yayi cikin palourn nasu ganin bata nan ya wuce ɗaki dai dai ya samu Ameera ta gama shirin shiga wanka tana tsaye ɗaure da towel sai kawai taji an rungumeta ta baya
Ajiyan zuciya ya sauqe ya lumshe ido yace "wiffeyh wankan zaki shiga ki qyaleni bayan kinsan na gaji ba iyayi da kaina zanyi ba" ya faɗa da alaman shagwaɓa.
murmushi tayi kai mutumin nan kai fa yanzu ka wuce wanka da yaron ka kuma ga wani ajiyan a ciki kaga ai sai dai awa yaran ka badai a maka ba
Sa hanu yayi zai kunce towel en au wato nine ma mutumi bama za kice husbyn ba ko
Bige hanunsa tayi kai fa ka tsufa yanzu Baban Little
kutt nine na tsufa a guje tayi banɗakin tana addu'an shiga toilet
murmushi yayi! Allah ya barmun ke Ameerah ta Allah sa na rigaki mutuwa dan bana jin zan iya zama da kowacce mace bayan ke Allah maki albarka
Shima banɗakin ya shiga, wankan suka yi tare suka fito fuskansu da murmushi daga gani kasan qaunan junansu suke sosai basa fatan abunda zai rabasu in ba mutuwa ba.
Shirya junansu suka yi, suka faɗa gado tare Ameera tace "washhh baban su little na gaji" bakinta ya kaiwa cafka in baki daina ceman babansu ba sai na cire maki baki yarinya
Kissing junansu suka fara
Janye bakinta tayi tana murmushi kwantar da kanta tayi a qirjinsa tace
"Husby yanzu ya za'a yi da bawan Allahn nan? sa hanunsa yayi yana shafa kanta nima kaina abunda nake tunani kenan wiffey ban san ko zai yarda ya zauna damu har ya samu lafiya sosai ba, gashi bai son magana bare muji ko zai faɗa mana ko kaɗan ne dangane dashi.
Amma kasan me husby ni wallahi sai fuskansa kemun ɗan yanayi da na Abba
Dariya Daddyn Little yasa amma dai wiffey bakisan kama ba to kina ga mutum kaman balarabe kice yana kama da Abba shikkenan kinga anyi 1-1 kema kin zama tsohuwan idonki bai gani har gwanda na amaryata akan ke
Hararan sa tayi a wasa ni dai ka dai na haɗani da wancan stohuwan da ta gama zamanin ta
Hiransu suka cigaba dayi a haka har bacci mai daɗi ya ɗauke su .
A
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 25