kai Amjad yayi yace "eh ranka shidaɗe ina tune da maganan ɗayan sharaɗin" to Allah maka albarka, maganan ɗayan sharaɗin zaku yisa da ita Gimbiya amma kamun nan inason sanin dalilinka na qin Karɓan dukiya da nace zan bawa wanda yaci gasan.
Cikin girmamawa Amjad ya fara magana "Ina mai neman afuwanka mai martaba akan wannan abu da na yanke ba tare da wani dalili ba. Jinjina kai mai martaba yayi yace "shikkenan Yarona Muhammadu Allah maku albarka duka, da Ameen ya amsa, Gimbiya kuwa tana sauraran su batace qala ba.
Mai martaba ne ya kalleta yace "Gimbiya maganan ɗayan sharadinki zaku yi tsakaninku, ni kuma na gama nawa maganan Aure nan da wata huɗu 4 in Allah ya yarda, sannan zai cigaba da zuwa wajan ki daganan har lokacin da al'ada ta ɗibar bazai ganki ba in anfara hidima. Kai kuma yaro na zaka iya zuwa cikin gidan nan a duk lokaci da kaga dama ba tare da sai anmaka iso ba ko jagora kaima ɗan gida ne nan gidanku ne.
Godiya Amjad yayi wa mai martaba dake qoqarin miqewa, tashuwa mai martaba yayi yace tom "zan tafi fada Gimbiya zata kawo maka abun karyawa banyarda ka fita a gidan nan ba tare da ka karya ba, gyaɗa kai Amjad yayi Tom ranka shidaɗe, ke kuma Gimbiya ki sa a kawo masa abun karyawa ki tabbatar ya karya kamun ya tafi" mai martaba na gama magana ya buɗe qofan ya fice a palourn.
Mai martaba na fita ta tashi ta koma kan kujera ta zauna ta maida abun fuskanta ta rufe.
Murmushin gefen baki Amjad yayi ganin yacce take wani cika tana batsewa, kau da kai yayi kaman baison yin magana yace "Malama Gimbiya ki cire abunda kika sa a fuskan naki sai muyi magana ko"
A gadarance tace malami baza'a cire ba in ya dameka zaka iya zuwa ka cire bazan cire ba, kamun ta rufe baki taga mutun a gefenta( hhhh!!! aiki da cikawa)
Saurin matsawa tayi ta yaye abun fuskan nata ta harari gefe tana tura baki, cewa yayi "na zaci zaki tsaya na cire ne kinsan qaramin aiki nane acikin abubuwan da zan iya"
suna cikin haka jakadiya tayi sallama ta shigo ɗauke da qaton tire da aka cika da kayan abinci kala-kala da kuma kayan marmari da abubuwan sha, ganin Amjad kusa da Gimbiya sai tayi qasa da kanta. Tashuwa Amjad yayi ya koma ɗayan kujeran ya zauna ya dake kaman ba shi ba, qarasowa tayi ta ajiye tiren abincin a gaban Amjad, ta tashi ta juya zata fita Gimbiya tace "wa zai zuba masa abincin in kin tafi? Kallon Gimbiya Amjad yayi ya kalli jakadiya dake shirin dawowa dan zuba Abincin yace "karki damu baiwar Allah zaki iya tafiya" godiya jakadiyan tayi ta juya ta fice a Palourn.
Kauda kai Gimbiya tayi tace "da ka bari ta tafi kai zaka zubawa kanka abinci ko waye? Ya kalleta yace "Ke zaki zuba mun ba wata ba, sannan ina fatan kin iya feeding. Saurin kallonshi tayi ta buɗe qaramin bakinta ta murmusa! Subhanallahi Murmushin da ya kusa ɗauke wa Amjad numfashin sa da sauran jarumtar da yake da, tace "you most be joking indai MEHWISH ce kake nufin zata yi serving naka and kana magana akan feeding, girgiza kai tayi tace funny you".
Duk maganan da yake kaman an sashi dole yayi haka yake maganan, dogon magana in ba da Ummansa ba bayayi bai saba ba magana wahala yake basa wani bin har yayi ciwon kai in ya yawaita magana.
Ba tare da ya kalleta ba yace "can you come and serve me or I should come over there and make you serve me"? hararan gefen da yake zaune tayi taqi tasowa, kallon hararan yayi ta gefen ido ya ɗan yi Murmushi irin na nafiki iskancin nan, aransa kuwa cewa yake "zaki setu ne yarinya bari ki shiga hannu duk stiwan naki zan magance sa staff" a zahirin kuwa da ya murmusa baice qala ba, illa miqa hanu da yayi ya ɗau apple yana ci.
Ganin yana cin apple cewa tayi "better da ka taimaki kanka ka nemi abinci if not ba randa zan yi serving naka ni Mehwish" ta faɗa tana karkaɗa qafan da tayi Cross-leg tana danna wayan da ke hanun ta qirar iPhone 14 pro.
Kallon ta yayi, baice komi ba yaci gaba da taunan apple nasa kaman yana storon taunawa.
Jin bece komi ba takuma cewa "Yes gwanda kayi shiru dan ni ɗin ƳAR SARKI CE ko aurena kayi sai dai nasa amaka ba dai na maka ba, inkuma ka hana sai kayi da kanka faqat".
Ba tare da ya kalle ta ba yace "ke kikasan ke ƴar Sarki ce, for me I don't know this, all i know is that ke mata tace I will soon own you and make you deed whatever I want, so you should be minding your words dan karki bari nasa harda wanke bayi a ayyukan da xakiyi a gidana nan da wata huɗu.
Saurin kallonsa tayi tace "Au ashe har;na zama matarka, and kana lissafin zanyi ayyuka, murmushi kawai tayi tana kallonsa.
Lumshe ido yayi, bai ce komai ba, gaba ɗaya kallonta da irin kallon da take masa da wannan killer smile natan na haddasa masa shiga yanayin da bai son kusantan sa bare ya shiga, stiririn tsaki yaja kaman a kasalance yace "can you please stop looking at me with dis ur tiny eye's"
haɗe fuska tayi alaman taji haushin abinda yace, cewa tayi "Ko makaho ya ganni ya san idanuna ba qanana bane bare mai ido. taci gaba da cewa "am abu na gaba da yake sharaɗin qarshe wanda zai tabbatar mun zaka iya aurena ko ba zaka iyaba shine, mahaifiyata bata da lafiya kuma a sharaɗina dole wanda zan aura sai ya nema mata magani, mai martaba yace maka wannan sharaɗin bai zama dole ba amma ina so na sanar maka wannan ne babban sharaɗi na.
Yana jinta har ta gama magana bai ce ko qala ba, ko ci kanki baice ba. Tashuwa tayi tace" inka gama zaka iya biyo ni muje ka ganta" tana gama faɗan haka ba tare da ta staya ba tayi gaba abunta.
Tashuwa yayi ya bi bayanta, ba ta ainafin cikin gidan suka bi ba ta cikin sashen mai martaba suka bi hanyan da zai sada su da shashen Sarauniyar. duk inda suka wuce bayin wajan gaida su suke har qasa da shi da ita duka.
Sun iso qofan ɗakin ta buɗe qofan t masa iso, da sallama dukansu abakinsu suka shiga ɗakin, a kwance Amman nata take sai dai da alama mai martaba ya goge mata jiki ya sauya mata kaya (dama ko shi ko Gimbiya suke wannan aikin).
Tace masa "ga Ammaa na, a take kuma sai kwallah ya cika idonta, tun da ya ɗaura idon sa akan matar yaji tausayin ta da na iyalanta duka ya rasta jikin sa, sai ya raya da ace ke wannan ciwo ya zaiji, a take ya ji mugun tausayin Gimbiya ya shigesa lokaci ɗaya.
Zuwa kusa da Ammaan nata yayi ya durqusa a gefen gadon, addu'oee masu yawan gaske yayi mata na karya sihiri da kuma kariya da neman sauqi, ya kuwa minti talatin a durqushe, da ya idar da addu'an ya kama kanta ya tofa ya shafa mata. Miqewa yayi ya masta kusa da ita yace "karki sa damuwa a ranki Insha Allahu Ammaa zata samu lafiya bada jimawa ba kuma Ni Muhammad Amjad na maki alqawarin sai randa na samowa mahaifiyar ki magani tukunna za'a yi aure na dake, inafatan hakan ya maki?
Ba tare da ta kalle sa ba ta share hawayen ta ta ɗaga kai.
Daga haka ya miqe zai fice bayan sa tabi har suka fita a sashen mahaifiyar tata, ba wanda yace da ɗan uwansa qala kowa da abinda yake tunani a ransa, rakasa tayi ta juyo ɗakin ta ta wuce direct, tana cike da alhinin Maganan ciwon Ammaa nata, ga shi maganan da yayi harda alqawari ya baya mamaki dan tasan mai martaba bazai taɓa fasa maganan auren nan da wata huɗu ba.
Sai dai har a ranta ta yarda da shi tana ji a jikinta Insha Allahu za'a dace.
Maganan da basu qarasa ba kenan shima ya fito, dogari ne yazo da motor ya staya gefen sa ƴallaɓoi ka shigo mai martaba yace a kaika gida, ba musu ya buɗe murfin baya ya shiga dogarin yaja motor suka nufi gidan su Amjad..
Dogarin har qofan gida ya kawo sa, sauqa yayi ya masa sallama ya tura qofan gidan nasu ya shige. Abban sa ya tafi kasuwa Umma ce kawai a gida ya sameta.
Ummansa na kallonsa ta yi guɗa tana murmushi tace "Kaga Angon Gimbiya Jarumin Umma ɗan gidan Abba" Amjad murmushi kawai yayi wa Umman tasa amma bai ce komi ba.
Ganin yanayin sa sai jikin Umman sa yayi sanyi, amma batayi yunqurin tambayan sa me yake faruwa ba. Ruwan wanka ta kai masa yaje yayi wanka. Bayan ya fito Umma tace masa "jarumin Umma zo ka karya" Umma ta a qoshe nake na karya a can. Ko ba komi taji daɗin da har ya karya a can ɗin hakan na nufin Insha Allahu komai lafiya, sai ta ci gaba da ayyukan ta, shi kuma ya shirya ya fito ya ma Umman tasa sallama ya bi Abban sa kasuwa.
Ko da ya isa kasuwan Abban sa yayi farincikin ganin sa, ya so tambayan sa ya suka yi a gidan Sarkin amma ganin suna kasuwa sai ya bari sai sun koma gida zai tambayesa.
nan suka zauna suna kasuwan su tare sannan Amjad ya kan yiwa Abban sa tambayoyi akan wasu ciwuka Abban sa na qara masa bayani, duk da dai shi irin sana'ar nan baiwa ce kawai ta Ubangiji...
Bayan shigan ta ɗakin ta, kwanciya tayi a kan qayataccen gadon ta da yasha shumfuɗi, a kwancen ta rage kayakin jikin ta a haka har bacci yayi awon gaba da ita.
Itace bata farka ba sai daf ana qiran Sallahn azahar, jin kanta na ciwo sakamakon kukan da tayi ɗazu sai ta nemi magani tasha taje ta wasta ruwa ta ɗauro alwala ta tada Sallah.
Ta idar da sallah ta shirya cikin riga da skirt ruwan kwai, irin kayan ƴan India. Bata sa ko ɗan kwali ba ta ɗau alkyabban ta ta sanya ta fice a ɗakin, a palourn ta tarar da Laure na goge goge, goggoji da ke jera abinci a dining en dake sashen ta takalla tace "ina jakadiya? Goggoji ta juyo har ta durqusa dan bata amsa sai ga jakadiya ta shigo, tana magana a waya. Ganin Gimbiya tsaye ba tare da ta kammala wayan ba ta kashe, durqusawa tayi Allah ja kwanan uwar ɗakina mai kike buqata? Gimbiya batace qala ba ta nufi hanyan qofan baya daga nan sashen ta wanda zai sada ta da lambun dake gidan sarautan nasu.
Ganin haka jakadiya ta yi sauri tabi bayanta, kamun Gimbiya ta isa har jakadiyan ta shumfiɗa mata darduman da zata zauna ta wuce cikin part en Gimbiyan da sauri. Gimbiya zama tayi ta yaye alkyabban ta dan tasha iskan dake kaɗawa a lambun mai daɗin gaske, jakadiyan ce ta kuma dawowa ɗauke da tray dake a shaqe da kayan marmari ta zo ta ajiye a gaban Gimbiya, kanta aqasa tace "Allah baki tsawon rai uwar ɗakina, shikkenan ko da wani abun da kike buqata? Sai yanzu Gimbiya ta buɗe baki tayi magana.
Shikkenan maimuna kina yin abu ne a cikin gidan?
Saurin girgiza kai jakadiya tayi a'a bana komi ranki shidaɗe uwar ɗaki na, okay kije ki gyara mun ɗaki sai kizo and bayan ke banson kowa ya shiganmun ɗaki bare har yace zai gyara mun toilet nasha faɗa maki amma inaga kina barin sauran yaran na shiga mun ɗaki. Ki gafarceni uwar ɗaki na, ban sanya kowa gyaran ɗakin ki ba sai dai jiya da dare da naje ɓangaren su Umma dan dubo jikin ta bansan ko akwai wanda ya shiga ba.
Gimbiya tace yayi kyau amma dai a kula dan banason qazanta, and ya jikin Umman? Fatan da sauqi?
Da murmushi Gimbiya tace eh uwar ɗaki na jikin da sauqi sosai ma, Insha Allahu zuwa wani sati inaji zata dawo bakin aikin ta ma. Allah kaimu ya qara sauqi ko Umma ta dawo, zata kula da sauran ɓangarorin da masu ayyukan gida amma sashe na ke zaki cigaba da kula dashi. Inshà Allahu uwar ɗakina Allah ja kwana, ta tashi ta juya dan komawa ciki ta gyarawa Gimbiya ɗakin nata.
Gimbiya wayan ta tajawo ta kunna data dan duba class da suke yi a online, tana yin master's a ɓangaren Islamic, Amma online master's. Tana dudduba class en tana shan kankana, sanda suka yi almost 1 hour suna class kamun aka gama, ganin ya qare class en yastine baki tayi ta kashe datan tayi jifa da wayan tana miqa, idon ta na sauqa akan apple da ke cikin bowl en kayan fruit en sai shi ya faɗo mata a rai, tun da ya tafi basu yi magana ba koya ya isa gida bata sani ba. Lumshe ido tayi ta sa hannu ta ɗau apple en tana ci a hankali, Sallaman jakadiya ne ya dawo da ita hayyacin ta.
Amsa Sallaman tayi, jakadiyan ta durqusa ɗan gefen ta kaɗan, nuni ta mata da kan darduman da nufin ta zauna, ba musu jakadiyan ta masto ta zauna tana "Barka da hutawa Uwar ɗakina" gyaɗa kai kawai Gimbiya tayi batace komai ba sanda ta ɗan ci kusan rabin apple en kamun ta ajiye ta juyo tana fuskantar jakadiyan, magana nakeso muyi dake shawara nakeso zaki ban, jakadiya tace "ina sauraranki uwar ɗaki na , nan dai suka tattauna......
Sai can yamma lis kusan magrib Abba da Amjad suka kamo hanyan dawowa gida, suna tafiya suna hira har suka iso gida. Da farin cikin ganin mijin nata da tilon ɗan nata ta tarbesu tana masu sannu da gajiya, ledan hannun Amjad ta amsa ta shumfiɗa masu tabarma, ruwan sha ta kawo masu suka sha ta miqo masu wani ruwan a buta, alwala suka yi suka fita dan zuwa masallaci ita kuma Umma ta shumfiɗa darduma a kan tabarman ta tada Sallah, ba ita ta tashi ba sanda tayi har da magrib.
Ko da ta idar naɗe darduman tayi ta maida, jera masu kwanukan abinci da komi tayi a babban taburman da ta shumfiɗa ta zauna tana jan carbi tana jiran dawowan su masallaci.
Umma na zaune na jan carbi can sai ta jiyo sallaman su suna shigowa gidan, amsawa tayi ta miqe ta maida carbin da hijab ɗaki ta dawo ta samu har sun zauna Amjad ya zuba masu abincin, tuwon shinkafa Umma ta masu da miyan ɗanyen kifi wanda yasha haɗi gashi Umma expert ce a iya girki.
Bismillah suka yi suka fara cin abincin, Amjad loma ɗaya biyu yayi ya cire hannu, kallon sa Abba yayi "yau kuma rashin cin abincin ya mosta kenan" Abba ya faɗa yana cigaba da cin abincin sa.
Umma ce ta kallesa tace "wai har ka ɗanɗano girkin surkar tawa yafi nawa daɗi ko kaqi cin abinci gaba ɗaya yau, nayi favorite miyan ka kuma kaci sau biyu kace ka qoshi tabbas zan maka ɗure Jarumin Umma. Murmushi yayi ba haka bafa Umma ta, Tom Jarumin Umma in ba haka ba yaya ne? Kaqi cin abincin Ummanka meeyasa? Hannu yasa ya fara cin kifin dan dama yana daga cikin abinda yake so ɗanyen kifi barinma dahuwan Umman sa.
Sanda suka gama cin abincin duk suka wanke hannu ya taya Umman tasa tattare wajan, ya kai mata kwanukan kitchen.
Dawowa yayi suka kama fira da iyayen sa
Abba ne ya dube sa yace "yauwá jarumin Umma nasan itakam ka faɗa mata ya kuka yi da mai martaba saura ni a faɗamun. Umma ta ɗan dara wato dai anfaɗawa kishiyanka, Tom dai yana dawowa yace zashi wajan baban sa ko abun karyawa na ma baici ba, dan haka daga ni har kai muna sauran sa ya faɗa mana ya suka yi dan nikam ma Allah ya gani yaron nan ya ɗagan hankali yacce na gansa ɗazu, kuma gashi sai yaqi cin abun karyawa na.
Murmushin yayi ya sa hannun sa ya kama kunnen sa Ummata a yafemun na ɗaga maki hankali, komai lafiya Alhamdulillahi sai abinda baza'a rasa ba. Abba yace "to muna sauraran ka mene baza'a rasan ba". Nan take ya faɗa masu yacce suka yi da mai martaba da kuma baqin da ya haɗu dasu acan, da maganan kyauta da maganan aiki da suke son yayi dasu komai duk ya faɗa masu.
Abba ne ya nisa yace "yanzu yaya ake ciki jarumin Umma me mai martaban yace maka akan maganan nasu?"
Abba ba abinda yace fa sai kawai wai nazo nayi shawara da Iyaye na akan aikin. Umma tace "to jarumin Umma karatun da kayi ina fannin likitanci me? Mai ya haɗa likita da aikin soja?
Murmusawa yayi, Umma ta sun san da hakan duka, amma Dukansu huɗun shuwagabannin sojojin ƙasashen su ne, Kinga kenan hakan ba matsala bane.
Ajiyan zuciya Umma ta sauqe tayi shiru ta rasa mai ma zata ce, Abba ne yace yanzu Tom kai ya kake gani maganan kyautan kuma mai Sarki yace?
Abba maganan kyauta za'a karɓa abinda nake faɗa maku yanzu haka insha Allahu gobe anbamu komi sai hidiman kuma sai biki yazo. Tunda dai duka kuma kun rasa abun cewa shikkenan Abba karku damu kanku daganan har zuwa randa muka yanke shawara sunce suna maraba da Ni. Sai kuma abinda ba za'a rasa ba nan ya kuma kwashe yacce suka yi da Gimbiya da yanayin jikin Sarauniyan da kuma alqawarin da ya ɗauka mata. Sai hawaye kawai Umma ta fara ta kasa cewa komi dan tabbas taji tausayin matar sannan ta tausaya wa Gimbiya. Abba ma bai ce komai ba, wanda hakan ke masa nuni da iyayen nasa na goyon bayan abun da ya yanke.
Umma tace "Allah bada Sa'a jarumin, Umma, Allah sa a dace, tabbas zan so haka kuma zanyi alfahari da hakan in har sanadinka Allah ya bawa Sarauniya lafiya, wannan na tabbata zai sa Gimbiya ta soka da ga mutuncinka fiye da tunaninka a rayuwa, ina maka fatan nasara akoda yaushe Jarumin Umma.
Abba ma kusan abun da Umma ya faɗa hakan ya faɗa, dan tabbas ya jima da jin labarin rashin lafiyar Sarauniyar sai dai bai ɗauka har yanzu jikin nata ba, "Allah bada Sa'a jarumin Umma, In yayi akwai rubutun da zan yi da kuma wani maganin anan zaka kai masu su fara aiki dashi kamun ka shiga jeji ka dubo maganin tunda kaga yanayin jikin fatan mu dai Allah yasa adace"
Da Ameen suka amsa shi da Umman sa. Nan dai hiran nasu bai yi tsayi ba ya tashi yace zai je ya kwanta dan yana son ya sammaka a zuwa kai masu maganin gobe sai ya shige jeji. Rakasa ɗakin nasa suka yi kaman koda yaushe Umman sa ta masa addu'a suka ja masa qofa suka fita.
(wolleh iyayen sannan na mugun qaunar sa da sonsa).
_____________
Mahreen da Maha suna gidan Umma hankalin su kwance, sai kuma shirye shiryen zuwa Bauchi da suke yi, ranan saturday soja zai kaisu suje su gano Kakus. Adamawa Kuma sai Ummeyhn su tazo zasu je, dukda Maha ba qaunan maganan zuwa Adamawa take ba.
Zaune suke da Umma a palourn, suna kallo a TV, Maha ce tace "Umma nikam gaskiya in Ummeyh tazo kice bazan bisu Adamawa ba" ta faɗa tana shagwaɓe fuska. Umma ta kalle ta tace ko meeyasa bakyason zuwa doter? Allah Umma kekam nasan kina sona zaki fahim ce ni, Kinga Arɗo wlh zalina yake ci, duk in naje sai ya zaneni ko ya kwaɗa man sandan sa, kuma ranan inaji kamun Abeeyh yayi tafiya da yace masa zamu je Adamawan yace wai kar mu yarda mu je ba tare da miji ba in ba haka ba zai bada kyautan mu a can qauyen.
Haba doter karki damu kinji kekam kina da mijinki ba mai yin kyauta da ke, kuma Arɗo bazai taɓa ki ba yanzu ai kin girma. Kallon Umma tayi tace "Umma Nifa banda saurayi bare miji kuma bakisan halin Arɗo bane shiyasa Umma" ta faɗa kaman zata yi kuka.
Murmushin manya Umma tayi! Doter ai Arɗon in ya takura maki Tom kice shine mijin naki ya baki sadaki kuyi Aure, shikkenan ba?
Dariyar Maha ta sanya yauwa Ummata kin iya kawo dabara. Little dake kwance a cinyan Maha yace "ancii cice unkui ne mijin ci ba aiyo ba(Arɗo ba).
Mahreen da ke danna waya ne ta sa dariya tace "indai mu bazamu faɗa maki gaskiya ki yarda ba Tom ɗan ki ya faɗa maki ki auri uncle nasa shikkenan dama kune iyayen sa" qarasa magann tayi tana dariyan. Maha tura baki tayi ta harari Mahreen tace "Umma kinji yaya Mahreen ko" Umma ta murmusa tace "qyaleta doter zan saɓa mata kinji" ɗaga kai tayi ta koma kan Little tace "my son kana so mu ɓata? Gyaɗa kai little yayi alamun a'a tace "okay karka qara faɗan wannan maganan ko" sai ya ɗaga ka tace "that's my good boy. Dariya litttle ya san ya yaji an yabeshi!
Qira ne ya shigo wayan Mahreen, ganin Abeeyhn su ya sa ta ɗau da wuri tana murmushi!
"Assalamualaikum Abeey masahul khair" shiru tayi na ɗan wani lokaci kamun ta kuma cewa "duk muna lafiya Abeey ga Mahan nan. Miqawa Maha wayan tayi, amsa Maha tayi suka gaisa da Abeeyhn nasu, da suka gama tace "ga Umman nan a kusa Abee ba na bata" miqawa Umma wayan tayi.
Sanda suka gaisa sosai da Umma cikin girmamawa da fara'a ya tambayi Abba da su Ameera da soja, Umma tace "yayan ku yana lafiya, baban yara Ameera kuma jiya suka koma da mijin ta duk suna lafiya, soja ma yana lafiya ya fita, Inshà Allahu duk zasuji gaisuwa baban yara" faɗin Umma. Miqawa Mahreen wayan tayi nan suka fara larabci da mahaifin nata....
--------
Washe gari da sassafe bayan idar da Sallahn asuba sama-sama ya karya ya kama hanyan shiga jeji.
Shine bai isa inda zashi ba san da gari yagama haske, har fa inda baya isa duk yau ya isa a jejin yasha yawo yasha yawo, amma kwata-kwata bai ga halaman wannan bishiya da yake nema a jejin ba, tun safe har
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 25