Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

rasa, Amma wllh idan har da gaske Shuraim na da sa hannu a dauke yarinyar nan sai na nuna masa ni na haifesa..... Sai ya yaba ma aya xakinta" Hajiya Sadiya tace "Ni duk ba wnn ba Maryam, yanxu dai daga nan har xuwa wata biyu ko daya da rabi babu ruwanki da yarinyar nan, tsakanin ki da ita ido, ko magana ba dole kiyi mata ba, sai mun bari kowa ya sakankance sannan sai a shammace su...." Mumy na share idonta tace "Tunanin da nayi kenan nima, shi kuma Shuraim don ubansa dama masters din nan dai da baya son yyi yanxu shi xai tafi yyi, ga Sudais har ya kusa gamawa, to dolensa sai ya tafi shima yyi, ko ya ki ko ya so wllh tllh sai ya tafi...." Hajiya Sadiya tace "Shkkn wllh, kinyi maganinsa cikin sauki" Mumy ta nemi waje ta xauna tace "Ita kuma wnn karuwar yanxu nake da lkcnta a gidan nan, na amince xan banxatar da batun makauniyar har na yan watanni ita kuma yanxu xa mu fara gogawa da ita" Hajiya Sadiya tayi dariya tace "Ki goga da wa? Matar da in ta fita tun safe sai yamma, ai bata da wnn lkcn sai dai makauniyar" Kiran Abba ne ya shigo wayar Mumy ta gyara xama da sauri ta daga ta kai kunne cikin sanyin murya tace "My Barrister"





Heedayah isn't free, you read for free πŸ€·πŸ»β€β™€οΈπŸ€·πŸ»β€β™€οΈ

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....

I am just super amazed at the well wishes from different angles, I really appreciate my lovely fans, Allah ya bar min ku, nagode kwarai da birthday wishes, Allah yayi mana albarka gaba daya, Ameeen.πŸ₯°πŸ˜πŸ˜˜πŸ’–
Those that didn't wish me kuma should come and patronize meee ejoo, shi ma love neπŸ₯Ί




Ina masu son kamshi in and out, I mean kamshi irin na manyan mata fa, to ga opportunity, hope dai ba ku mance Innar su Mujaheed da Imaan ba, to ta ce a baku shawara ku siya turaren wutan nan don yana daya daga sirrin kamshin dake tashi a parlon ta kullum, tace me xa ayi da gidan da bbu kamshi, mace bbu kamshi kuma ai bata cika mace ba, daya daga tsatsonta ke hada wnn lafiyayyen turaren wutan da bbu irinsa, for more info contact 08038103096.....

Khaleesat ma dai da turarurrukan take amfani wllh, trust me it's nice and very affordable....😍



3months later....


Kaka ce tsaye kan Khadijah inda take shiga ba nan take fita ba, Khadijah sai turo baki take tana yatsina fuska, Haka Rabi'ah dake tsaye bakin kofar parlon Mumy, Kaka tace "Yar banxa kawai me bakar fuska kazama, mummuna, ni dai wllh da ba don ina asibitin aka haife ki ba ma cewa xanyi ke ba 'yar Amadu bace canje aka masa, dama hutun da suka baku a makarantar cewa suka yi ku dawo gida ku dinga yi ma babban ku rashin kunya ban sani ba?" A fusace Khadijah tace "To wai ni kaka me nayi maki ne, ni kadai ne kika gani a parlon nan...." Kaka tace "Wllh Sudess xan kira yanxun nan ya casa min ke idan kika kara xagina, kawai don yarinya Allah ya yo ta makauniya sai ki juye mata shayin da take sha ki dura ruwa a kofin saboda bakin hali ko me? Sannan wannan yarinya Farida ta maki magana xaki hau ta da dambe kamar 'yar da6a? To bari yanxun nan xa a kira min Sudess, Allah ya rufa min asiri ya dawo shekaranjiya ai da lalacewa ta sameni" Khadijah ta fashe da kuka tace "To ita faridar Ina ruwanta da ni xata tsoma min baki?" Kaka tace "Aa wllh da ruwanta, bayan ni da uwarta Rakiya akwai me son Deedayah ne a gidan nan, to sai kilan Amadu duk da bamu san xuciyarsa ba, nan nan nan uwarki ta cakali Rakiya da fitina jiya Rakiya ta ki kulata, Farida kuma duk da dai agola ce a gidan bata fiye min ku ba sau dubu, Aa wllh ta fiye min ku, Maryam dai jaraba kawai ta haifa matsayin 'ya ya, idan ma bakin ciki kike faridar ta fi ki kyau ne ai sai ki fito ki fada in sa Amadu ya samar maki ko 'yar man kanti ne ki shafa kiyi hasken" Khadijah ta mike fuuu tayi wucewarta bangaren Mumy tana cewa "Gobe ta sake saka baki a harkana wllh wllh sai na mata dukan tsiya na farfasa mata baki" Farida dake tsaye bakin kofar Mami tare da Heedayah da ta rike rigar faridan, ta tabe baki tace "Toh ba sai ki dokeni ba, wllh karya ki xan yi...." A fusace Khadijah ta nufo Farida gadan gadan, kaka ta shiga kwala ba isiya kira da karfi, dai dai shigowar Shuraim parlon, Kaka ta fashe da kuka sosai tace "Shkkn kuma ni don mijina ya mutu ya barni bani da gata sai a ajiyeni a gida daga safe har dare ina ra6on katti yara fada, shi Amadu ya fita neman na xuba ma bakin salati, ita kuma wnn kinibabbiyar xabiyar ta bi sa ita ma aikin, uwarka kuma gantalalliya suna fita ta tafi gantali ita ma, wllh tun fitan iyayen suke dambe kamar raguna har an ji ma TVn Amadu, yanxu da baka dawo daga Zaria ba ya xanyi da raina yau, da gangan malam suka basu hutu don su kashe ni...." Shuraim ya kalli Farida da ta wani turo baki, ya kalli Khadijah da ta koma kofar parlon Mumy da gudu, ya karaso cikin parlon yace "Ku dawo nan gaba dayan ku" ko rufe baki bai yi ba Farida ta ja Heedayah suka shige parlon Mami ta sa makulli, Khadijah ta marairaice sanin in har ta shiga ya bi ta to mai kwatar ta sai Allah, Rabi'ah dake makale kofar ita ma tace "Allah ya so ni dai..." Kaka tace "Wa??? Ai kece katuwar munafukar ke ke sa Khadijah tayi komai, duk bakin ki daya" Rabi'ah ta fashe da kuka sosai tana kallon kaka, Shuraim ya hade rai yace "Baxa ku dawo nan ba nace" Khadijah ta Rabi'ah suka fito main parlon suna matsar kwalla, Cikin rawar murya Khadijah tace "To ita Farida fa Yaya" buge bakinta yyi, kaka tace "Ai ba kyaleta xa ayi ba, abinda ba tsoron ta yake ba" Da wayar rechargeable ya xane su a tafin hannunsu gaba daya, yayi wucewarsa dakinsa, Kaka da tayi tagumi tace "Dama dai neman wanda xai duka yake tun daga Zaria, Banda haka ga dai katti sa'anninsa a titi ya baro ya shigo gida ya ci xali, ku dai kuyi hakuri ku bar sa da Allah kawai" Rabi'ah da ke kuka sosai ta dinga hararan kaka, Khadijah na Shessheka tace "To mu kadai xai doka, ita faridan fa" kaka tace "Waye ubanta da baxa a doketa ba tunda aka doke ku, ai yanda yyi maku haka xai mata ba cuta" Rabi'ah tace "To Heedayah fa?" Kaka ta kalleta da sauri tace "Aa ke kuma baki son gaskiya, waye kuma Heedayah? Me tayi xa a doketa, to ko ma tayi in dai shi ba wawa bane akan me xai doketa, ko kula ku kinga tana yi a gidan nan, to ai ita ba gantalalliya bace kamar ku" Khadijah ta mike tana hararan Kaka ta wuce part din Mumy, Rabi'ah ta ja tsaki ta mike ta bi bayan Khadijah, kaka tace "Oho dai an dai sha mazga" Farida ta ja tsaki tace "Haka xa mu yi ta xama kenan baxa mu ci abinci ba, ni dai baxan sha cornflakes ba" Heedayah dake shan cornflakes dinta ta ta6e baki tace "Ni ina ruwana, wnn da kike ganinsa din nan mugu ne, wllh duka xai maki in kika fita" Farida tace "To a ina ya san ni da xai dokeni? And ni fa Ina ce shine Sudais" Heedayah tace "Aa ba Yayana bane, wannan Ya Shuraim kamar naji suna ce masa, I never liked him even for once" Farida tace "To da ina yake tun da na xo ban gansa ba" Heedayah tace "Ban san Inda yake ba, but yana dawowa every Saturday" Farida ta ta6e baki tace "To kawai bai san ni ba sai ya dokeni" Heedayah tayi dariya tace "That's because he is wicked" mikewa Farida tayi tace "To kinga mu lallaba mu je in xubo mana" Heedayah tace "Ni baxan je ba" Farida tace "Plss mana I can't go alone, da sauri fa xan xuba mana mu dawo" Heedayah ta juya manyan idanuwanta tace "To ki jira in gama shan Cornflakes dina" Farida tayi tagumi tace "Tohh" Heedayah na gama shan Cornflakes din Farida ta ja ta suka fita main parlor, bbu kowa parlon sai Tv dake kunne, Farida na rike da hannunta suka shige kitchen da sauri ta kulle kofar, Sajida da Karime ne suka yi lunch a gidan, Farida ta bude warmer da abincin ke ciki ta debi shinkafa knn xata bude na miya aka bude kofar kitchen din, Shuraim ne ya shigo da wayar rechargeable a hannunsa, tana ganinsa ta fasa ihu ta saki murfin warmer din hannunta, Heedayah ta ja gefe a tsorace, cafkota yyi, ta rikesa tana basa hakuri a tsorace, Bai ko saurareta ba ya rike hannunta ya dinga lafta mata wayar hannunsa, Kaka ta shigo kitchen din a guje tana cewa "Wayyoo wllh uwarta lauya ce daure ka xata sa ayi shureen, idan ka doke wasu ka kwana lafiya to ita wllh a seff xaka kwana bbu me ceton ka, yau fa kwananta hudu da xuwa gidan, ta dawo daga tsadadden makarantar kwanan nan, duk da dai fitinanniya ce ai tayi min wanki yau kuma ta wanke min bandaki, ko da yake jika jika tayi amma ai tafi munanan kanninka..." Sai da Shuraim ya lafta mata son ransa sannan ya saketa, ta durkusa a wajen ta dinga ihu tana kiran Mami, ya kalli Heedayah da ta rakube gefe daya a tsorace hawaye cike idonta, ya nufeta fuska daure kaka ta dakata da surutan da take ta shige gabansa tace "Aa nan kuma ne xan sa 'yan anguwa su lallasa min kai, uban me xaka mata?? Ai wllh idan ka doki gantalallun nan ka kwana lafiya to kana ta6a Deedayah maka ka xanyi a kotu, me makauniyar tayi maka, duk da dai ita ma ba kyalle bace" kallon kaka kawai yake fuska daure, ta kama hannun Heedayah ta fice daga kitchen din tana cewa "Ni dai ba ruwana" Farida ta wani hararesa ta mike xata bi bayansu, xai cafkota ta fice a guje ta shige dakin kaka... Uku saura Mumy ta dawo gidan, su Rabi'ah suka tsara mata abinda ya faru da safe, tayi shiru tana sauraron su, can tace "Tafi maxa ki kira min Shuraim din" Khadijah ta kwanta saman gado tace "Tabbbb" Rabi'ah tace "Ni dai kar ma kiyi masa magana Mumy, wllh dukan mu kawai xai kara yi" Karime ce ta shigo parlon, Mumy tana kallon su Khadijah tace "Ku fita" duk suka mike suka fita, Karime ta xauna kasa tana ta6a baki tace "Hajiya ji nayi daxu a waya tana gaya ma wani wai an kusa fita da Heedayan waje ayi mata aikin idon..." Mumy ta gwalo ido tace "Haba??" Karime tace "Wllh kuwa haka na ji...." Mumy ta gyara xama tace "Wa kika ji tace xai fita da ita?" Karime tace "Wannan ne ban sani ba Hajiya" Mumy tace "Har dai yanxu baki san Inda kaka ke boye maganin nata ba ko?" Karime tace "Ai yanxu kaka ta ma daina sa ni gyaran dakinta, Sajida ce ke yi" Mumy tace "Toh watan barin gidan Sajida ya tsaya" Karime tace "Wllh daxu da safe kafin Hajiyar ma ta fita aiki ga dai ni a xaune amma Sajida ta sa taje dakinta ta dauko mata makullin mota, ni ta ma daina bari in shiga dakinta ynxu...." Mumy tace "Akwai wani aikin da xan baki yanxu, kuma in sha Allahu idan kika yi kokari kika cika aikin, dubu biyar xan baki kyauta..." Karime ta washe hakora tace "Hajiya ai ko baxa ki ban komai ba...." Bude kofar parlon da aka yi yasa duk suka yi tsit, Shuraim ne ya shigo da sallama, fuska daure Mumy tace "Wannan ai walakanci ne, ayi shinkafa dafaduka jiya, yau kuma ayi shinkafa da miya, tunda Sajidar tace maki baxata yi ba ke ba sai kiyi ba..." Juyawa Shuraim yyi xai fita Mumy tace "Ina kuma xa ka?" Yace "Naga kuna magana ne ai" Mumy tace "Kawai masu aikin jaraba suyi ta sa mutum magana, suna ba mutum wahala" Bai ce komai ba shi dai ya fita, Karime ta kalli Mumy, Mumy tayi kasa da murya tace "Yaushe ya xo?" Karime tace "Tun safe" Mumy tace "Tashi ki tafi xan neme ki anjima" Mikewa tayi ta fita... Kaka nata aikin linke linke a dakinta, Farida na dakin tana taya ta, Kaka tace "Toh dama idan ba ke ba waye xai taya ni, ita wancan makauniyar ba wai amfani gareta ba" Heedayah dake kwance tayi rub da ciki tana jin kaka bata dai juyo ba, Farida tace "Kaka wai shi ma a nan gidan yake xama?" Kaka tace "Wa?" Farida tace "Wannan da ya doke mu mana" juyawa Heedayah tayi daga kwancen da take tana kallon direction din da take jin muryarsu, kaka tace "A'a yana can Zaria yana karo karatu, ko massers naji suna kiran karatun, kinsan bbu yanda ba ayi da shi ya fita waje kamar yanda Sudess yaje can yake yi ba amma ya ki, uwarsa kuwa kamar tayi hauka don ta kwallafa ran fitansa, kin santa da fafa, so tayi ta bi duk kawayenta tace d'an ta na kasar waje yana karatu, to da yake shi ma Amadun kila ba wani son kashe kudi yake ba ya goya masa baya kar ya fita, duk sati kya gansa salalo salalo wai ya xo gida hutu, duk ya bi ya takure jama'ah...." Bude kofar dakin aka yi sai ga Shuraim, Farida ta juya da sauri ta ci gaba da linkin da take, kaka tace "D'an Halak, yanxun nan take tambayata uban me ke dawo da kai gida, shine nake bata labari" da sauri Farida tace "Ni fa ba shi nake tambayar ki ba...." Tana fadin haka ta nufi kofa ta fita ya bi ta da kallon gefen ido, ya kalli Heedayah dake kwance, kaka tace "Ka ji wai ita kuma yau bata son tayi karatun, kuma duk inda malamin yake nasan yanxu yana hanya, dubu ashirin da biyar haka Amadu ke biyansa duk wata, to banda Allah wa xai biya mu, bbu fa abinda muka hada da ita....." Heedayah ta mike xaune tana sauraron kaka kamar xata yi kuka, kaka tace "Kasan idan ba mutum ke biya ma kansa ba sai yyi ta iskanci iri iri, sai ka ga uban tsaraban da Sudess ya yo mata daga kasar turawa, ni tsoro ma kamani yyi wllh, ni dama ko tsinke shegen bai kawo min ba, shi kuma Junaidu daxu ya kirani wai nan da sati xai dawo har yace in bata suka dade kuwa suna waya, ko kanwarsa bai ce in ba ma ba, ita kuma Khadijah daxu...." Shuraim ya dakatar da ita yace "Ina tsaraban??" Kaka tace "Ae baxa su dauku ba Shureen" yace "Suna ina?" Mikewa Heedayah tayi a hankali tana laluba hanya xata fita kaka tace "Ji algunguma, Ina kuma xaki, kinji nace xan dau kayanki ne da xaki wani mike xaki fita??" Shuraim dai sae kallon dakin yake yana neman kayan.....


Am so exhausted yau, let it not just be as if I didn't typeπŸ₯Ί


Heedayah isn't free, you read for free πŸ€·πŸ»β€β™€οΈπŸ€·πŸ»β€β™€οΈ

it's 300 via... Fcmb 3276052019 Hauwa Bello Jiddah

Then you show ur evidence via WhatsApp 07087865788....



Ta gefen ido Shuraim ya dinga kallon Heedayah dake kokarin fita ya ga ko xata ta6a sa, she was so careful ko kusa da shi bata bi ba har ta fita dakin, kaka tace "Ni sae nake ga kamar karyar makanta take yi, ynxu a hka fa sai ta fita har tsakar gida" Shuraim yace "Ina kayan?" Kaka tace "Naga jaraba, Ina ruwanka da kaya Shureen? Tun daxu ka isheni ina kaya to kai aka kawo ma kayan? Kayan me xaka dameni haka, Komai fa na da sirri, ba ruwana ni ba 'yar cin amana bace, Bai ce in nuna ma kowa ba har Amadun balle kai karan kada miya...." Wani kallo yyi mata ya juya ya fice daga dakin.... Turuss Khadijah tayi rike da bucket din ruwan kumfa a hannunta, ya kalli direction din da take kokarin xuwa da sauri, Heedayah ce har sannan bata isa bangaren Mami ba tana tafiya a hankali kuma very careful, ya kalli Khadijah da tayi wuri wuri da ido, da sauri ta juya xata koma Inda ta fito, ya bi bayanta tana ganin haka ta sake bucket din hannunta a rikice, ya ja baya da sauri ganin ruwan kumfan ya malale kasan tiles bai ankara ba sai gani yyi tayi sama sannan aka nanota kasa da karfi, wani ihu tayi can kasa makoshi, ya ma rasa ko dariya xai yi ko d'aga ta xai je yyi, ta kwalo ma Mumy kira tana cewa Wayyo bayanta, yana jin hka ya kalli Heedayah da har ta kai kofar parlon Mami ta tsaya, Farida ma ta fito da sauri don ganin me ya faru, Shuraim na jin Mumy ta bude kofarta xata fito tun bata karaso ba tana tambayar lafiya me ya faru, yyi saurin shigewa dakin kaka ya rufe kofar. Farida ta ja Heedayah suka shige ciki ta kulle kofa. Bayan isha Farida na parlon Mami da Heedayah, Mami kuma ta je kai ma Abba abinci aka bude kofa Sudais ya shigo da sallama, daga kai Heedayah tayi tana kallon ta Inda ta ji muryar sa, da farko Farida ta xata Shuraim ne sai kuma ta ga wannan ya fi Shuraim haske, Ta gaishesa ya amsa yana murmushi yace "Ya kike?" Tace "Lafiya lau" ya xauna yana facing din su idonsa a kan Heedayah yace "Ba gaisuwa Deedayan kaka" Heedayah ta jinginar da kanta da kujera tace "Ni ba Deedayah bace" yace "To ya sunan?" Ta langwabar da kai tace "Ina yini" yace "Lafiya lau Cutie, ya karatun kuna ta yi koh? And kina ganewa?" Ta gyada masa kai, ya kalli Farida yace "Ya sunan ki 'yan mata?" tace "Farida" yace "Ban ta6a ganin ki nan ba Farida, though Naga kuna kama da Junaid" Farida tayi murmushi tace "Ehh na xo hutu ne kawai" yace "Wani makarantar kike?" Tace "Nigerian Turkish...." Yace "Boarding?" Ta gyada masa kai, yace "Maa sha Allah" Heedayah tace "Yayana baxa ka sake komawa UK ba koh?" Yace "Idan ma xan koma tare xa mu koma ae" Ta wara ido tace "Da gaske?" Yace "Ehh mana sai in gaya ma su Abba da Kaka su bani ke, kowa ya shaida sannan mu wuce" Murmushi tayi tace "To kayi masu magana plss" yace "Da gaske dai xa ki bi ni? Xamu dade fa bamu dawo ba" tace "Allah xan bi ka" yana murmushi yace "Toh shkkn" Bude kofa aka yi Rabi'ah ta leko fuska daure tace "Ya Sudais kaka na kiran ka" ya kalleta kafin yace komai tayi banging kofar ta wuce, Farida tayi kwafa can kasa kasa, mikewa yayi yace "I'm coming back...." A hankali Heedayah tace "No chocolates?" Ya kalleta yyi murmushi yace "Sai na dawo" daga haka ya fita, Farida tace "Ke da kike cewa xa ki bisa ke matarsa ce?" Heedayah tace "To ba Yayana bane" Sudais na tsaye yana sauraron abinda kaka ke cewa, can yace "Toh yanxu me kike nufi?" Tace "Ina nufin in har baka bani nawa tsaraban ba wllh baxan bata ba, gwara in kwashi tarkacen da ka kawo in kai kasuwar 'yan koli in siyar, haka kawai daga ganin sarkin pawa sai miya tayi xaki, uwar me ma ka hada da ita bani da labari, duk wahalan da nayi da kai kana karami ka dawo daga kasashen turai ko abun sakace hakuri baka kawo min ba sai yar tsintuwa" dai dai nan Shuraim ya shigo dakin da ledan fruits da Abba ya sa ya siyo mata, Sudais ya kallesa sannan ya ci gaba da sauraron kaka, Shuraim na ajiye ledan tace "Shureen tunda muke da kai ka ta6a fita kasar waje ka dawo baka min tsaraba ba, ko nan nan da Zaria idan kaje ai kana siyo min 'yar lemon nan" Shuraim na kallonta ya ciro wayarsa dake vibrate a aljihu, kaka tace "Toh don me Sudess xai fita ya dawo min haka sai wata can wai Deedayah xai kwaso ma kaya iri iri kamar kanwar ubansa" Sudais yace "Saboda ta fiye min ke" shiru kaka tayi tana kallonsa a bit shock, yace "Kuma ki fito da kayan in kai mata yanxu" Kaka tace "Al-qur'an kasuwan 'yan koli xan kai su gobe da sassafe, idan na baka in tafi a karkace, Deedayar kanwar ubanka ce ko ta uwarka?? Waye kuma Deedayah? Me na hada da ita banda dai d'a na ya tsinto mana ita" Sai kuma ta xauna ta fashe da kuka tace "Ehh lallai karshen duniya ta kankama" Juyawa Sudais yyi ya fita daga dakin, Kaka ta kalli Shuraim tana matsar kwalla tace "Ka dai ga ko Shureen?? Hakan da Sudess ya min ya kyauta" Yace "Ni baxan ce komai ba sai na ga kayan" Babu wata wata Kaka ta dauko makulli da sauri ta bude gun ajiye kayanta ta fiddo akwatunan har biyu da karamin jaka, kallonsu kawai Shuraim yake, ta xuge jakar ta shiga fiddo abubuwan ciki, cikin lkci kadan ta fiddo komai ta bajesa a gaban Shuraim tana kallonsa, Kallon kayan kawai Shuraim yake, beautiful English wears, teddie bears, biscuits, dolls, chocolates, sweets, shoes, har da jewelries, Shuraim ya dauke idonsa daga kan kayan, kaka na matsar kwalla tace "Ka dai gani ko, ni fa na haifi ubansa Umaru" Mikewa Shuraim yyi bai ce mata komai ba ya fice daga dakin... Ta bi sa da kallo baki bude sai kuma tace "Toh Allah ya isa" Sudais na komawa parlon Mami, Mami dake xaune parlor tace "Mutan UK, sai yau muka hadu" Ya gaisheta yana murmushi yace "Jiya da na xo kina gun aiki" Mami tace "Ehh ina can, ya karatun kun gama kuwa?" Yace "A'a saura kadan" Mami tace "Maa sha Allah, Allah ya sa a gama a sa'a, ya su Hajiyar ku?" Yace "Suna lafiya gaba daya" Tace "To maa sha Allah, a xubo abinci?" Yace "A'a na ci" ta mike tace "To yayi kyau" bedroom dinta ta shiga ya kalli Heedayah ya koma kusa da ita yace "Ina kawar ki Farida?" Tace "Ta tafi wanke wanke a kitchen" Sudais yace "Masu aiki fa?" Heedayah tace "Mami ce tace taje ta yi" Yace "Ohkk" ta matso kusa da shi a hankali ta laluba hannunsa tace "Yaya kasan me?" Ya kalli kofar dakin Mami sannan ya hade forehead dinsa da nata yace "No..." Tace "Yau ina son in sha ice cream" yace "Ice cream?" Ta gyada masa kai, yace "Ohk bari Farida ta gama wanke wanke sai mu je gaba daya" Tayi murmushi tace "Nagode" Farida na shigowa yace "Farida tell Mami xa mu je siyo abu yanxu, with you and Heedayah" tace "Ohkk" daga haka ta shiga bedroom din Mami, ba a dau lkci ba ta fito da Hijab dinta da na Heedayah tace "Mami tace alright" sosai Heedayah ta ji dadi, ya amshi Hijab din ya sa mata sannan ya daga ta holding her hands suka fita parlon tare da Farida, Shuraim na xaune parlor shi kadai, tun da ya kallesu sau daya ya dauke kai har suka fita parlon.... Wani wajen shan ice cream Sudais ya kai su, yyi parking ya sauka motar, ya bude ma Heedayah back seat yana rike da hannunta ta sauka, Farida ma ta fito daga front seat da ta xauna, Sudais na rike da hannun Heedayah da ta makalesa suka shiga ice cream parlor din, Ya duka dai dai kunnenta yace "Wani irin ice cream kike so?" Tace "Vanilla" ya kalli Farida dake kallonsu yace "Ke fa Aunty Farida?" Tayi 'yar dariya tace "Irinsa nima" Wani mutumi ne xaune wajen da roban ice cream a gabansa, su uku ne xaune a round

Please Login or Register in order to submit comment