Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
iya kwance masa shi saini Dana kulla Yace amman Tunda kince kinason ganinsu zansa akaiki Domin ba kulle nake miki ba duk inda kikeso zaki iya zuwa Tunda duniyarki tana hannuna Mahaifinki mijinki mahaifiyarki nasan koda Kinyi niyyar guduwa dole zaki nemeni Tofa gaskia ne janar kace kaima kwallon shgene Idan Naga comment da yawa kafin safe saimuci gaba Misalin qarfe tara na safiyar gobe in Allah ya kaimu Bawai kuma nace kusa rai bane cewa nai idan Aure. Kan. Aure Chapter22 Ya saki hannunta ya cilla mata key din mota Da card dinsa yace duk sanda kika shirya kixo ki Sameni a office wannan kuma makullin motane ki hau kije duk inda kikeso Burina shine ki wala kiji dadin rayuwarki Ba burina kiyi zaman kadaici ba ya miqe ya fice abinsa ba tare Daya sake waiwayar inda take ba Tunda safe afnan ta tashi da zumudin son ganin halinda Mahaifinta da mijinta suke ciki don haka bata tsaya sanyaba ta fada toilet Tayo wanka t fito t murxa mai da hoda Sannan ta nufi wadrof ta dauko Wasu kaya yan ubansu material Sannan ta dauki wayarta da key din motar Tayo waje Kasancewar abuja Kamar gida take a wajena hakan yasa batasha Wahalaba. Wajen gane office din janar din Tanayin parking din motar tasa waya ta kirasa kamain ta gama fitowa Daga motar har yasa sojoji suxo su mata iso zuwa office din nasa Office din ya hadu iya haduwa. Daidai da kujeran office din abin kallo ne Yana zaune kan kujeran dake gaban babban tebur din ta gilashi Fuskansa dauke da farin gilashi ya maida hankalinsa kan wani File yana sanye da kayan sojoji a jikinsa. Yai mata nuni da kujeran dake kallnsa Ba musu kuwa ta zauna. Ta qara nutsuwa matuqa dan office din kadai Da yaddah sojoji keta zirga zirga a wajen ya isa Ya tsorata dakakken namijima balle mace Kamar afnan Saidaya gama shan iskarsa sannan ya dago yana kallonta Yace lallai kin qagu da kiga wannan mai gidan naki wannan safia haka Nadaisan ko break bakiyiba ko? Shiru tai Shima bai sake mata maganarba ya latsa qararrawar dake gefensa Ba,a jimaba saiga wani sadaukin soja ya shga ya Sara masa ba tare daya Kallesaba yace maza madam taxo aje a hado mata break Yace Owk sir ya sake sarawa sannan ya fice Afnan ta jawo dakiyar duniyarnan ta yabama kanta sannan tace Ba kalaci ya kawoni office dinkaba kasan meya kawoni Kasa a kaini inga mahaifina da mijina kawai Bai tanka mataba illa ci gaban da yai da rubuce rubucensa Yar qararrawar tai qara da alamar akwai mai shgowa ya bada izni aka shigo Sojan dazunne ya dawo dauke da qaton tire Tamkar shgowarsa ta daxun yana zuwa ya Sara masa Sannan ya sauke tiren a gaban afnan yana fadin gashi ranki shi dade Bata tankaba harya fice kuma bata da niyyar motsawa Hakan yasa ya saci kallonta sannan ya sake maida hankalinsa kan abinda Yake din. Ba tare daya. Kalletaba yace duk sanda kika shirya kikaci saina Kaiki wajensu inkuwa kikaqici to saiki tattara ki koma inda kika fito Ba yaddah ta iya haka ta siyaya Ruwan zafin a cikin cup ba tare datasa madaraba lipton kawai tasa sai suga ta dinga kurba va wai don tanajin dadinsaba Saidin ba yaddah kawai zatai Cikin dan qanqanin lokaci ta kammala ba tare daya kalletaba ya qara latsa Yar qararrawar Sojan ya dawo yace maja a kwashe wadandan kayan ai gaba dasu Cikin rawar jiki ya tattara yai waje yace sannan kacema sajen ballo yai maza yaje Gurdroom a dauko min wadannan yan sada kwaurinnan a kawominsu Yace Owk sir da sauri ya fice yayin da afnan ke nanata sunan da Aka kira mahaifina da mijinta dashi Baifi minti gomaba saika sojoji hudu sun shgo dasu a rirriqe Tamkar sun riqo maguna Afnan ta zabura ta miqe a daidai lokacin da gabanta yai mummunan faduwa Ta rirriqe mahaifin nata tare da afnan wadanda sukasha bugu har suka fita daga hayyacinsu fuskokinsu da jikinsu duk sun kukkunbura sunyi Luhu Luhu tamkar an qukqulle biredi Ko ina na jikinsu ciwukane dukda Wasu sun kame amman har yanxu basu Daina zubda jiniba Dukkanninsu daqar suke gani Sbd duk idanuwansu sunyi Luhu luhu Afnan ta rirriqesu tana wani irin kuka tana kiran sunansu Abba yaya adnan Waye yai muku wannan danyen aikin haka? Wayyo Allah na shga uku Kuka take sosai tamkar wacce aka kawoma gawarwakinsu Dukkansu babu Wanda yake iya magana Sbd tsantsar azabar da sukasha Janar ya miqe tsaye ya tattaka inda suke cikin tsantsar isa Ya zagayesu kamin ya dawo gefen afnan ya duqa yace Ki basu shawara tun tuni nace dasu su amince Akan tuhumar da nakemusu susa Hannu Akan takardar yarjejeniya su rantse kuma su dauki alqawari bazasu qara Safara hodar iblis ba tare da safarar qananun yaraba Ni kuma nai musu alqawari zan sakesu Afnan ta miqe da sauri. Tace ba zasu aminceba janar domin aiba wawayebane Da zasu amince da laifin daka daura musu kuma kake tuhumarsu dashiba Wato kana nufin ka kashesu Akan wannan hujjar kenan? To baka isaba ta. Dafa kafadar mahaifina tace kayi haquri abba Karku sake duk runtsi kusa hannu koda kuwa zai dau rankune Don zaiyi amfani da wannan ne domin ya bata muku tarihi Insha allahu abba zanyi iya qoqarina koda zan rasa rainane saina kwatoku daga hannun wanna azzalumin kuma saina kwato muku haqqinku Insha allahu Ta sakeshi ta riqo hannun mijinta Wanda suketa zubar da jini Ta girgiza kai tace Ina sonka mijina abinda ya sameka bazaisa naci amanarka ba Don da ace babu masifar data iya rikar dan adma toda soyayyah batai Ranaba Sai masifa ta farune kadai ake iya samun alfanun soyayyah na haqiqa Don haka wannan lokacinne kadai yafi kowanne lokaci dacewa Dana kasance dakai bazan cutar da aurenkaba bazan illata rayuwar Masoyanaba. Janar dake tsaye zuciyarsa na wata irin suya ya dakawa sojojin tsawa Jikinsu na rawa suka kwashesu Sukai gaba dasu ya koma ya zauna sai huci yake Tamkar Wanda yasha wani uban gudu Afnan ta share hawayen nata ta koma ta zauna Akan kujran data zauna dazun Cikin sarkewar murya tace Mai yasa vaka tura wannan case din zuwa kotu ba? Tamkar bazai amsa mataba can kuma kome ya tuno Oho Ya dubeta yace. Sbd case ne da ni ya shafa ba buqatata nace na kaisu kotuba Buqatata su amsa laifinsu anan sannan na kaisu da hannuna A yanke musu hukuncin daya dace Afnan tace to amman mai yasa kake Abun babu yan jaridah? Da sukasan da labarin balle yakai kan yan siyasa har izuwa kan shgaban qasa? Yace Sbd in hakan ta faru a yanxu da bani da kwakkwaran hujjoji Nine zan kwana a ciki Shiyasa na bari har izuwa lokacin da zan kammala harhada hujjojina da Zasu zamemin makaman yaqin nawa Ta kirgiza kai tace dakyau ta miqe ba tare data mai sallamaba tabar office din Zuciyata ta gama narkewa da lamarin don haka tana fita kai tsaye headquetres na Yan sanda ta nufa bata samu matsalaba wajen sadata da. iG kasancewar sunan Mahaifinta da kuma karatunta Kayataccen office ne tsaruwarsa ta wuce acemai office Dan sandane ya shga da ita yai mata iso ta shga tana qarema office din kallo Zuciyata ta gama tsinkewa ganin yaddah. IG din take zaune a saman kujera ta alfarma Tun daga Jikinta har muryarta rawa suke wajen fadan sady! Fuskarta dauke da fara,a tace la,a afnan Bismillah zauna mana Ba musu taje ta zauna tana fadin wlh nayi farinciki ganinki zaune Akan wannan Muqamin matsalace tafe dani don Allah ki taimakamin sady Tace fadi abinda kikeso afnan fadi Indai har bai gagareniba insha allahu zan taimaka miki Anan ta zauna ta lbrta mata abinda ya faru tun farko har izuwa yanxu Da take maganar Kwarai sady ta samu. Zuciyata kuma ta motsa. Tunda tun a wancan lokacin tai dawainiya da sonsa don haka zata taimakawa masoyinta Da qarfinta basirarta da kuma aljihunta Ta tambayi afnan din tace kice shugaban qasa baisan da maganarba? Tace tabbas Ta dan jujjuya kan kujerar da take zaunen kanta na kallon sama kamin ta tashi Da sauri tamkar wacce aka zabura. Ta dauko biro da takarda a take ta rubuta later Zuwa office din sugaban qasa. A take ta tura zuwaga office din shgaban qasan Sannan ta dubi afnan Tace yanxu ba zaki koma gidaba afnan domin kuwa yin hakan zai iya Zama mana kuskure don haka a yanxu zan rubuta takardar shigarda qara kotu Yanxu zan daukeki zuwa gidana Rayuwa taxoma afnan da sauyi takoina jinta take tamkar marainiya Data rasa uwa da uba tare da dangi gaba daya don haka sady ta dage wajen lallashin qawar tata Ta dauke mata hankali da lbrun duniya wai kodan ta saki Jikinta Amman abin ya gagara Damuwar da afnan ke ciki ta wuce Hira ko wani a ta kawar da ita Barci kansa sai yayi da gaske yake dauketa Daga wanka ta fito daure da tawul Daya na kanta tana tsane kan nata sai kace wata qaramar yarinya ta fito sai Waqa take na turanci Tana waqar tana rawa harta iso kan kujeran dake gaban madubi taja ta zauna Natsuwa tayi ta zuba kwalliya fuskarnan tata tai luqui sai kace jaririya Bayan ta gama ta bude wadrob dinta ta dauko kayanta na yan sanda Ta hade cikinsu Kamar daman dan ita akayisu Ta hau Baqin takalmi. Gamida hular yan sanda Hmm sady kenan iyayen iya kwalliya wato kyan da tai ya isa a bude mata duk wata qofa data tunkara Bata da jiki saidai ba ramammiya bace Sady na zaune a office dinta dan yau ayyuka sun mata sauqi don haka a Sannu a hankali. Take nazarin files din dsake gabanta wadanda akeso tasa Hannu a ciki Ji tayi an fado office din nata ba tare da an nemi izniba Tai saurin dago kai dan taga ko waye Cike da mamaki taga ya tsaya suna fuskantar juna Cikin kakkausar murya yace ke qaramar karuwa Harke zakisa shugaban qasa yasa na saki mutanen da nake tuhuma To wlh inaso ki sani inhar kikace zaki shgo harkata Wlh zaiyi wuya ki iya rayuwa don wlh sai nasa a koreki a wannan dan kurkukun office din da kike taqama dashi yanxunnan Kin kuwa san koni waye? Sady tai tattaki zuwa gabansa ta zura hannayenta cikin aljihu tana kallonsa ta cikin Baqin gilashinta Tace nasan kokai Waye kai ba Kowa bane illa dan ta,adda mai. Kashe alummah Dubi yaddah ka shgomin office sai kace wani kare Cikin kunan zuci ya daga hannu zai zuba mata mari komai ya tuna kuma Sai ya dungule hannun nasa ya sauke yana huci Tai wata daria tana tafa hannayenta kamin kuma lokaci guda ta daure Sai kace ba itace ke daria yanxuba Ta nunashi da dan yatsa Tace kai kayi kadan kasa a koreni a wannan office din sanna ni sady nayi alqawari saina kawo qarshen ta,addancinka Don dama qasa na sane ta qaleka kake yaddah kaso Ya girgixza kai yace lallai yarinya keba komai bace wajen janar Toki sani ko cinnaka bakikaiba Indai a wajen janar ne Kuma na rantse miki goshinki saiya Riga rana fadiwa Bai saurari abinda zataceba ya fice a zafafe ya barta tana wani murmushi da ita Kadai tasan fassarar sa Bayan sady ta tura case din zuwa babbar kotun dake qasa ta abuja Komai ya kammala ran monnday itace ranan da za,a zauna sauraron shari,ar Inda sady da kanta taje ta amshi adnan da abban afnan aka wuce dasu asibiti Saidai Shi adnan a sume aka daukeshi aka kaishi asibitin baisan inda kansa yakeba don haka ba,a barin Kowa na shiga wajensa in banda likitoci Yayinda suka duqufa wajen basu taimakon gaggawa Yau itace ranar Monday ranar da za,a zauna a kotu Don haka Tunda safe afnan da sady suka gama kammalawa afnan Cikin kayan lauyoyi ita kuma sady cikin kayan yan sanda Afnan sanye da kayan lauyoyi da hularta ta lauyoyi gamida wani Baqin gilashi Inda ita kuma sady ta hau wani Baqin gilshi wuluk kalar kayan nata Ladies din sun wanku iya wankuwa Kamar kullun kotun dauke take da manyan mutane inda Yansanda da kuma sojoji suka tsatstsare ko ina domin gudanar da tsaro Afnan itace ta kasance lauyar dake kare mahaifinta da kuma mijinta ita Da wani lauya mai suna nasir adamu Don haka Bayan mai gabatar da qara ya tashi ya gabatar da qaran da za,a gudanar yau Barister hafsa aliyu musawa afnan kenan ta miqe Ta gabatar da kanta a gaban kotu Shima lauyan da suka dauka ya tashi ya gabatar da kansa a matsayinsa na lauyan kasuwa Wanda ke kare tsohon minister aleeyu musawa da kuma dan uwansa adnan muswa Bayan ya zauna barister hilal. El.amin ya tashi ya gabatar da kansa a Matsayinsa na lauyan dake kare Wanda ake qara wato janar abdullahi aminu abbah Bayan Kowa ya zauna afnan ta miqe tace yamai girma mai shari,a inason Abani daman ganin janar abdullahi aminu abbah Kotu tace an baki dama ta qarasa inda janar yake a tsaye Tana isa gabansa ta tsaya sunama juna kallon kallo mai cike da ma,anoni Shin baiyi Tunanin ganinta bane koko yana mamakin ganinta cikin kayan lauyoyine Oho nima bansaniba Aure. Kan. Aure Chapter23 Barister afnan ta kalli tsakiyar idanunsa tace mai girma janar ana tuhumarka Akan kulla wani abu Wanda ba gaskia bane. Akan mai girma tsohon minister Aleeeyu musawa shin ko meye tabbacinka Akan yana safarar koken ta qananun yara? Janar cikin dakewa yace hannu dumu dumu muka kamashi A yayin da muke cheaking din jirgin daya taso daga amerika ya sauka Gida najeria mun kamashi dumu dumu da jakar koken Inda muka daddaukeshi hotuna sannan muka wuce dashi domin qara bincike Afnan ta dubeshi tace shin daman Kuna cheaking a wajen ne kokuwa a ranar kuka soma? Tunda Naga da akwai jami,an tsaron dake kula da filayen jiragen saman Yadanyi Jim kadan kafin yace inada hurumin duk sanda naso naje na tsananta bincike a duk wajen da nake zargi Tace to kenan ka fara zargin wasune shiyasa ka isa filin jirgin? Yace tabbas domin bincike ya nuna mana cewa ana safarar koken ta jiragen sama Tace wato kenan duk binciken da aka saka na,urori da jami,an tsaro dominyi ya zama hotiho kenan? Tunda har ake tafia da hodar koken daga wata qasa zuwa wata qasa Yadanyi Jim kafin yace kinsan mutum zai Dade yana yana abunsa aboye inda wani zai dinga bashi sa,a amman daga sanda dubunsa suka cika sai kiga Allah ya toni asirinsa Afnan tai wani murmushi ta juya ta kalli alqali. Tace Ya mai girma mai shari,a wannan ba hujjar da zatasa a yarda da janar. A. Aminu bace Domin kuwa tsananin kula da tuhumar da filin giragen saman da America take yafi nanan Sannan wani zargine yake da harya kaishi filing jirgin sama bincike wannda bai taba zuwaba Indai harba shugaban qasane zxai tafiya ba? Sannan girman janar ya wuce da kansa yaje bincike filin jirgin saidai yasa Wasu suje suyi Kenan hakan na nuna akwai wata maqarqashiya kenan da akema mai girma tsohon minister don kawai a muzantashi a matsayinsa na dan siyasa Sannan janar ya boye tsohon minister a wajena ba tare da hukumar yan sanda ta kotu kota. Yan jarida sun samu lbr ba tsawon kwana goma sha hudu Saida hukumar yansanda suka Gano da kansu suka turama shugaban qasa Leta Akan abinda ke faruwa sannan yasa aka sakesu A yanxu haka suna asibiti ana basu taimakon gaggawa dayama ba tare da yansan inda jansa yakeba a yanxu haka Da wannan hujjoji nakeaon ita kotu data dubi halayyar shi tsohon minister tun farkon tasowarsa bincike ya nuna mutum ne mai gaskia riqon Amana da kuma dattako Tunda yake Akan muqaminsa ba!a taba samunsa da wani laifi Wanda ya sabama dokaba Tayi shiru. Sannan ta rankwafa tace na gode mai shari,a ta koma ta zauna Alqali ya ida yan rubuce rubucensa sannan ya dago yana fadar Ko. Lauyan Wanda ake qara yanada abinda zaice? Ya miqe ya gaishe da kotu sannan ya fara da Hujjojin da barister afnan ta bayar ba abin kamawa bane domin kuwa Kamar wata tatsuniyace ta shirya ina roqon kotu da tasa akawomin mutane biyun da ake zargi domin nai musu Wasu yan tambayoyi Alqali yace. IG. Sadiya muhammed mai nasara muna buqatar Akawo mana marasa lfyn da ake tuhuma koda kuwa a cikin keken marasa lfy ne Daganan zuwa ranar takwas ga wannan watan Daganan kotu ta watse Zaman kotun zamane daya halarci manyan yan jaridu don haka koda aka Tashi. Yan jarida sukayo kansu dan suji ta bakin janar da kuma barister afnan Tareda. IG don su samu abinda zasu rubuta domin dauke Hankalin jama,a Dashi saida Sukai da gaske sannan suka kubuta daga tambayoyi yan jaridar suka Fada mota direba yajasu. Sauran motocin yan sanda suka rufo musu baya Suna jiniya tamkar zasu tashi sama Sady ta dubi afnan tace zaki zauna a motane yanxu naje gida na dauko masa Pasport dinmu dan dama na rigada na saman mana visa zamu wuce Libya ne yanxu Don a yanxu rayuwarmu tana cikin hatsarine Sannan Daganan zan dauki mota na dauki marasa lfyn na wuce dasu wani boyeyyen asibiti Wanda ba Kowa yasan dashiba domin suma za,a iya zuwa ai Musu illah Banason Kowa ya sani koda cikin jami,ainane shiyasa zan tafi da kaina Minti talatin yayi yawa zan dawo Ta bude motar da sauri ta fice zuciyar afnan ta gama tsinkewa da wannan al,amari Satinsu guda a qasar Libya sady ta samar musu wani namijin lauya daga can ana ce masa barister shaldo Lauyan kasuwa ne Ana gobe za*a koma kotu suka dira a naija Shima basu dira a gidan sady ba wani A wani tsadadden hotel suka sauka Sady ta tafi a sace ta dubo marasa lfyn abban afnan ya samu sauqi ba laifi inda duk an daddaurashi a inda ya samu karaya Dukda bai iyayin komai amman ya samu sauqi sosai Tunda har yana iya magana Kuma idan an bashi abinci yanaci Ba laifi kamanninsa sun fara dawowa Saida adnan ne haryanxu bai farfado daga Suman da yaiba Tamkar wancan lokacin Kowa ya hallara a kotun barister ashir shehu ya miqe Bayan ya nemi izni daga wurin alqali ya nufi inda aleeyu yake kwance cikin keken asibiti Yace ranka shi Dade atsohon minister aleeyu musawa ko zaka iya fadama kotu Shekarunka da kuma aikin da kake yanxu? Aleeyu yace ni sunana aleeyu musawa inada shekaru hamsin da biyu nayi karatuna na primary da sacondry a kano Sannan na tafi jami,ar bayero. Dake kano wato B. U,K Anan na kammala digirina Maihaifin matata Alhaji muftahu babban dan kasuwane shine ya taimakamin wajen ka$$ala karatun nawa Ina tare dashi a matsayin yaronsa har ya samamin aiki a wani banki a matsayin manager ya kuma bani auren yarsa Daga bayane na aje aikin da kaina ba wanine yasaniba na shiga harkar siyasa Barister shehu yace amman meye ya baka sha,awar shiga harkar safarar koken....? Barister shaldo ya miqe da sauri yace ya mai girma mai shari,a ya kamata barister shehu ya iya bakinsa domin kuwa shi mai tuhumane Bawai mai yanke hukunci ba Alqali yace akiyaye baristr Ya waigo yana na gode yamai shari,a sannan canja tambayar da fadar Lokacin da aka kamaka an daddauki hotunanka da akwatun hodar koken Kokuwa zaka iya cewa bakai bane? Ya girgixa kai cike da takaici sannan yace Wannan ba gaskia bane asalima naxo abuja domin ganawa da shugaban qasane misalin qarfe sha biyu na dare jirgin hudu nabi zuwa garin kano Kwatsam sai Naga ana bincike ban damuba Sbd nasan bana tare da wani mugun abu kona rashin gaskia amman me zai faru Kawai sai suka dosheni da wata. Qaramar jaka wai tawace gashi tana dauke da hodar koken da bindigu har guda biyu a ciki Wlh bansan da watta jakaba asalima ni tawa qaramace batakai Wacce suka kawomin wai acewarsu tawaceba Amman za,a iya zuwa a binciki ma,aikatan filin jirgin da wadanda Suka bincikeni kamin na shga jirgin Duk Wasu shaidu da ake buqata a wajensu za,a samu amman niba mai ha,intar qasa bane Bana cutar qasata hasalima Bana tare da macuta Lauyan yace gashi kuma kamanninka Kamar wani na Allah Amman lokaci guda an kamaka da farautar qananun yara gashi ka Aikata aure kan aure Ka daurama yarka aure da amininka ka kuma koma Kabama abokin hulderka Yace ko kadan wannan makircin matatace amman da bakina ban furtama Janar cewa na bashi yataba Asalima bansan yana zuwa wajentaba sai daga baya take fadamin na takama abin burki Amman da yake zuciyar matar tawa a qeqashe take hakan yasa taqi saurarata Barister yace kenan kana nufin bada yawunka aka daura auren nataba kenan? Shiyasa ka koma ka sake daurama Wanda kakeso? Yace ko kadan nidai nasan na tura yarana can dangina inda suna zuwa mahaifina yace me za,a jira Washe gari aka daura auren nasu ranar laraba akai walima alhamis inda daganan na wuto. Kano daga kano na wuce abuja Wanda daganan Kuma wannan al,amarin ya rutsa dani Lauyan yace to na gode ya koma ya zauna daganan barister shaldo Ya taso cikin qasaita irinta manyan lauyoyi Yace ya mai girma mai shari,a inason a kawomin Hajia nafi. Matar tsohon minister domin inason yin mata Wasu yan tambayoyi Alqali yace idan hajia nafi tana tare damu kotu tana buqatarta yanxu yanxunnan Nafi ta dafe girji tace yau na shga uku meye kuma nawa a cikin wannan shari,ar Jin shiru alqali ya qara magana yace shin hajia nafi batananne Ita tana cikinnan ta fito idan kuma kikaqi fitowa to lallai fushin kotu zatau kanki Babu inda bai rawa a Jikinta kai Hatta miyon bakinta rawa yake Lol shin me take nufine tsoro takejine koko yaya Ko tana Tunanin ko asirinta zai tonune Oho nima ban saniba mu hadu a nxt Chapter Danjin yaddah zata kaya Aure. Kan. Aure Chapter24 Jikin nafi yai sanyi daqar ta iya qarasowa wajen da ake tsayawan Barister yace meye sunanki da kuma matsayinki a wajen Alhaji Aleeyu musawa? Nafi tace ni sunana hajia Nafisa muftahu. Aleeyu kuma yaronane Wanda yake Yaron mahaifina ta Fannin kasuwanci Barister yace to ko zaki iya gaya mana zaman da kukai nadan Wasu shekaru da suka wuce? Tace tun aurena da aleeyu na rigada na fahimci bamai gaskia bane Ko kusa babu tsoron Allah a idanunsa Sauda yawa nakan kamashi da laifuka marasa kyau Amman saina rufe a matsayinsa na mijina Ni kaina na lura da safaran mutanan da yake dan da yawa yasha shigomin da Qananun yara gida sai yacemin wai gidan marayu zai kaisu Daganan bana sake jin lbrnsu Lamarin mai gidana yayi qamari harya bada auren yata ga genar. A aminu Akan ya rufamasa asiri a kamun da yai masa Shi kuma ya yarda domin yar tasa burin mallakar duk wani da namijine Don haka saiya boye yaci gaba da nasa binciken a boye ba tare daya bari shi Mijin nawa yasan zagon qasan dashi janar din yake masaba Yasa ya tura yaransa qauye aka daura musu aure kan aure kenan Bayan hakanne ya tafi abuja yana sauka aka kamashi da hodar iblis koken kenan Barister yace amman ta ina duk kikasan wadannan bayanan Domin Naga kina fadane Kamar a gabanki akai Tace tabbas Wasu Akan idona akai Wasu kuma ba,a kan idonaba Yace yanxu zaki iya fadamin suwaye sukeda ikon bada aure tsakanin dangin uwa Dana uba? Tace na uba inhar suna a raye yace to yanxu zaki iya fadamin wadanda suka zama waliyan yarki? Tace abokon Mijin nawa sune suka zama waliyan yar nawa Domin kuwa mijina aleeyu bai dauki iyayensa a bakin komai ba Sbd su talakawane Lauyan yace to na gode hajia tace nikeda godia sannan ta koma mazauninta Sannan lauyan ya juya yana kallon alqali yace ya mai girma mai shari,a ina Neman kotu data qara mana lokaci zajen gudanar da bincikenmu na gode ya mai girma mai shari!a Alqali ya gama yan rubuce rubucensa da zaiyi sannan ya dago yana fadar Kotu ta daga wannan zama zuwa ranan sha tara ga wannan watan Sannan Kowa ya miqe Yan jarida Kamar daman jira suke a tashi suka yayyabe afnan Suna fadar yanxu ranki shi Dade shin meye makomar wannan aure naki? Tace wacce makoma Bayan an dauramin aurena? Ina tare da mijin da aka dauramin aure dashi Wani dan jarida ya kasheta yace Shin ranki shi Dade kina sonsa koko Kinyi la,akari da Wanda aka fara daura muku Auren dashine yasa kike zaune dashin? Tace duka biyun kuma nayi la,akari da shi aka fara dauramin auren dashi ne shiyasa Can wani Shima ya jefo mata Tambayar da taso tasa mata ciwon kai Yace hajia da alama dai zuciyarnan taki tayi zurfi Akan son dan-uwannan nakine da har kike Tunanin dashi aka fara daura muku aure ko? Alhalin janar shine mutumin da aka fara daura miki auren dashi koko Kina nufin kice ba gaskia bane? Ta hatsala dan haka cike da vacin rai afnan din tace Kayi tambaya kuma kabama kanka amsa don haka kayi tunani Akan Tambayar taka Ta wucesu cikin bacin rai Daya daga cikinsu yace bai kamata ki hatsalaba hajia Akan wadannan yan tambayiyin inhar da kamshin gaskia a ciki Bata saurareshiba tai gaba abinta hakan yasa suka tare mahaifinta Wanda aka turo a cikin keken asubiti Sai kokawar zuwa yin masa tambaya suke Yauwa yallabai me zakace game da zargin da ake Maka na safarar yayan al-ummah da hodar iblis @koken? Alhaji aleeyu yai murmushi yana girgiza kai yace wannan duk sharrine kawai na Maqiya Wani dan jarida yace to amman yallabai ta yaya mai girma janar ya zama Maqiynka? Cikin zafin rai afnan ta qaraso tana fadar Ta inda marasa tausayi suka tsare mara lfy suna masa tambaya Haba sai kace baku da tausayi Ku dubi halin da bawan allahnnan ke ciki Bai cancanci ace kun tsareshi da tambayoyi a irin wannan halin da yake cikiba Ta dubi malaman asibitin dake turashi tace kukuma kuka biye musu dan Allah ku Turashi mu tafi Wani a cikin yan jaridar yace duk dai kauce kaucen akuya ai akuyace uwarta lol Maganar ta daki zuciyata amman sai bata nunaba domin ta qagara da subar wajen Kuma zamuga iyaka badai nanda kwanaki goma sha bane kawai basu qara kulasuba Sukai gabaabinsu Da yammah afnan na cikin asibitin don sai a yanxu take sanar da inna da malam Halin da ake ciki Hankalinsu ya tashi sosai don daman Tunda aka tafi da adnan suke cikin tashin hankali su dakai keta hidiman neman dan nasu hukumomin yan sanda kuwa har Head quaters saida sukaje Amman babu lbr Ko a yanxu da afnan din ta fada musu inda aleeyun yake saida ba Lfy hakan yasa suka qara shga cikin tashin hankali marar misultuwa Sannan suka fada mata cewa gobe sunanan isowa asubitin Afnan dunia tai mata kunnci ita kadai ta zauna tai tagumi babu abinda take tunani Sai rayuwarta ta baya Rayuwar da tayita cikin farinciki da walwala yanxu itace duniya ta juyama baya haka? Yanxu haka so take taga halin da mijinta yake ciki gashi sady tace wai an fitar dashi waje ko a wani irin hali yake yanxu oho Sady ta shgo asibitin tana cikin kayanta na yansanda inda Wasu cikin yan sandan ke take mata baya Hannunta riqe da wata yar qaramar bindiga afnan ta miqe cike dajin Dadin ganinta sannan suka koma suka zauna Afnan tace wlh Kamar kinsan cikin tunaninki yanxu haka nake sady Tunanin mai gidana yashamin kai burina kawai naje na ganshi Naga halin da yake ciki Sady tai daria gamida dafa kafadarta tace am sorry qawata nasan yaddah kikeji yanxu dole kadaici zai dameki Amman insha allahu komai ya kusa zuwa qarshe dan kuwa likitan dake dubashi Ya sanar dani cewa ya farfado Saidai matsala daya yayi loosing din memory dinsa gaba daya ya rasa contact Din dake kwakwalwarsa tace saidai ba komai komi zai daidaita Wani Baqin gilashine a fuskarta ta sako Wasu matsatstsun kaya ta wani yar yalolon gyale tana tafe tana taunan cingam ta iso asibitin escote dinta na take mata baya sai mazurai suke Gaban afnan ya fadi dan batasan yau ko dame taxoba ta qaraso har gaban nata tana qare mata kallo inka gansu ka rantse kace ba uwa da ya bace cewa zakai Qawayene ko kuma ya da qanwa Don nafi Jikinta girkakken jikine ba zaka taba iya cewa ta aje yaro dan shekara biyarba Taja wani dogon murmushi mugunta tana qarema afnan kallo tace lallai yarinya kin guji arxiqi kin fadama tsiya na sakaki a cikin daula kin fito kika fadama tsiya Tabbas Kinyi kuskure da har kika gujemin kikabi ubanki Wanda a yanxu yake

Chapter 8 of 16