Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
daka wajen ganin gaskiya ta tabbata Hakan ya samu ana cikin wannan hatsaniyane aka likitoci suka bata shawarar a. Fitar da adnan din waje don ciwon nasa. Idan ba,ai da gaskeba zai iya rasa rayuwarsama gaba daya Ba damar na bishi kasancewar ga halin da abbana ke ciki da kuma zaman da ake a kotu Gashi mahaifiyata harda ita wajen qullama mahaifin nawa sharri Don haka na Bama qawata alhakin kula da mijin nawa Bayan an Gama shari,a ne kotu ta yankema. Janar hukuncin rataya ita kuma mahaifiyata shekaru 25 a. Gidan yari sai muka tattaro muka dawo garin kano inda Ita kuma qawar tawa sady ta wuce qasar Germany domin kula da mijin naWa Daman munyi da itace Akan idan taje sati daya kawai zataiyi ta dawo mu tafi tare Tun daga wannan tafiyar ban sake sa sady a idonaba Naje cigiyarta gun mahaifiyarta tace ina ai basanma anyiba Abbana yayi duk wani bincike ajen Gano asibitin da suke amman ba,a samu nasaraba Sbd haka muka haqura amman ya bada cigiya a media da offisoshin yansanda Akan duk Wanda ya ganshi ya sanar da hukuma Harna haifi yayana aslim da taslim babu lbrn adnan da sady bayan na yayesune da yan Wasu satittika saiga sady ta kirani a waya Wai naxo na taresu a filin jirgi na sanar da kakata Cikin zumudi na nufi filin girgi ina zuwane na gansu ita da shi adnan din da jaririya nake tambayarta inda ta samo jaririya take fadamin wai Ai sunyi aurene acan a asirce don karsu kauce hanya Hankalina ya tashi matuqa don haka na barsu na nufi gida ban sakebi ta kansuba sai sau daya shima a asibitin da abbana ya Gina masa naje na sameshi mukai musayar harshe Tundana dawo ban sake damun kaina a kansaba sai wta rana da ake children's day a makarantar yara Ananne na hadu da adnan da qawata sady Bayan am kira yara an basu kyaututtkua aka kira taslim da aslim daga baya kuma aka kira siyama aleeyu musawa Ganin yarana na amfani da sunansa hakan ya fusatashi Har saida ya mareni da sharadi da Kiran yarana shegu wadanda basu da uba. Kuma ya gargadeni akana na Akann na canjama yarana suna don kalen uba nake musu Naji takaicin abun a raina Sannan a wannan kotun mahaifina yaxo aka raba aurena da adnan da irin wannan jawabin Lauya yace na gode Sannan ta koma mazauninta Lauya ya dubi Alqali yace ya maigirma mai sharia wannan jawabi na afnan ba abin dubawa bane don kuwa ka a makaranta ana Iya samun masu suna iri daya Misali zainab aleeyu. A. Zainab aleeyu. B Idan kuwa hakane don an samu suna yaxo iri daya ba abin dubawa bane Sannan tana iya yiwuwa kamace da kuma macin din suna Don haka wannan ba abin dubawa bane Na gode mai shari,a sannan ya koma ya zauna Alqali ya qaraci yan rubuce rubucensa sannan yace ko lauyan wacce ke kare mai qara tanada abin cewa? Ta miqe tai gaisuwa sannan tace eh ya mai giema mai Shari,a. Wato inason kotu ta sani anyi shari,a a baya tsakanin adnan afnan da aleeyu musawa Akan an Mata aure kan aure Shi. Janar na qararsune Akan aurensa aka fara daurawa da afnan sannana aka daura da adnan inda sadiya muhammad mai nasara ta tsayama afnan da mahaifinta tsayin daka har saida gaskia ta bayyana Ta qarasa gaban Alqali gamida miqa masa jarida ga hoton afnan Nan da abbanta da qawarta sady an rubuta An rubuta gaskiya ta bayyana da manyan harufa Sannan ta miqama Alqali hotunan afnan da adnan tun suna a skull da kuma yar qaramar. Camara mai hade da video rananr kamun daurin aurensu A take aka kunna kowa ya gani lallai ko wannan kadai sun isa shaidu Sannan inason kotu ta bada dama domin kawomin iyayenda suke iqirarin sune iyayen adnan din da suxo su fadama kotu yaddah akai suka raineshi. Makaranta da yayi dama yaddah rayuwarsa ta kasance ni Kuma ina tare da shgaban makarantar da adnan yayi tundaga primary principal dinsu na sakandire Sannan barister zainab tace da wannan shaidun nakeson Kotu data yankema wadannan maqaryatan mutanen da suke iqrari sune mahaifan nasa hukunci sannan tasa adnan ya amshi yayansa a matsayinsa na uba kuma ya amince da yayansane Na gode ya mai girma mai shari,a Sannan ta koma ta zauna saida Alqali ya Gama yan rubuce rubucensa sannan ya dago yace Inason sajen. Kaida jami,an yansanda kuke duk inda adanda suke iqrarin sune mahaifan adnan suke a tahomin dasu yanxunnan aikija duk iya bincikensu da sukai da kwatancen da akai musu. Abin ya faskar don daman masu iya magana na fadin idan asubanci kayi donka Riga ani wani shi kwana yayi. Domin rigaka sun tattara dan abinda suka samu sun ware Don haka suka dawo suka saNar da Alqali abinda ke faruwa. Ba tare da bata lokaciba Alqali ya danqama adnan yayansa sannan yaci sady tara harna naira dubu dari uku Da. Hukuncin wata bakwai a gidan yari gamida horo mai tsanani Adnan yai kuka kamar ransa zaifita yace ashe shiyasa sady keta kakkarewa da yace zaikai kotu daya nace shine tadau fushi dashi hardasu tafiya gidansu Lallai dole yaje gidan nasu tabbas yau saitaga fushinsa Akan wasa da hankalin da tai masa Kowa ya watse a kotun a Adnan yabi aleeyu yana roqonsa gafara Aleeyu yace ka daina zubar da hawayenka adnan ni dama ban riqeka a raiba don nasan ba acikin hayyacinka kake abubuwan da kakeba kuma har gobe kananan a matsayinsa na dana Yace na gode Abba Allah ya saka da alkhairi aleeyun yace amin Aleeyu ya nunama adnan malam yace wannan shine kakanka ya zube a gabansa yana neman gafara Ya shafi kansa yace karka damu adnan ai rashin sanine Bawai da gangan kayiba Karka damu kaji tashi tsaye Yana share hawaye can ya hango afnan tare da ibrahim da barister zee zee gefe daya kuma mustafane ibrahim na riqe Da hannayen taslim da aslim Adnan din ya qarema afnan din kallo ita da yaran nata a take yaga tsantsar kamar da suke Axuciyarsa yace lallai wadannan yayansane kuma jinisa so kawai yake ai masa iznin ganawa da yayansa amman sai yaga kamar duk cikinsu baba Wanda yai niyyar yin hakan Yananan tsaye har malam da aleeyu suka shge mota innda mustafa da matarsa barister zee zee suma suka shge da alamun wucewa zasuyi ibrahim kuwa na tare da afnan yan yaran na maqale dashi itama afnan din tafiya zatayi tayi tayi Akan yaran su taho su tasu amman sukaqi waisu a dole daddynsu zasubi ba yaddah suka iya a dole ta barshi ta nufi inda motarta take qiqam ta ganshi a gabanta don dama guri daya sukai fakin ita dashi Kallon sama da qasa tai masa sannan taja wani dogon Murmushi tana fari da ido Tace lallai kaci assingmenta adnan tunda harka iya Gano tsakanin nidakai wwake taqama da uban wani Waye ke kalen uba ta tabe baki sannan ta fada motarta taja Ta barshi anan tamkar mutum mutumi Yafi minti goma a wajen bashida mafita dayafi shima ya shga motar tasa yabar wajen saidai koda ya shga motar zuciyarsa bata daina mai sake sake ba Waye mutmin daya daukar masa yara ina zai kaisu? Ina kuma son da afnan din tai iqirarin tana masa a kotu? Wadannan tambayoyinne suka tsaya masa a kwakwalwa harya isa gidansa Kamar yaddah yake zato babu kowa a ciki Kai tsaye toilet ya fada ya watso ruwa wai a ganinsa ko zai samu sassaucin abinda ke damunsa a zuciyarsa Amman ina babu abinda ya ragu na damuwa daga zuciyarsa Kamarma qara ingiza masa damuwar ake Ya daura kansa saman fridge so yake yaita rera kuka kozai samu sa,ida amman ina kukan yaqi zuwa Robar ruwa ya janyo daga fridge din ya bulbula a bakinsa Can kuma ya tsaya cak ya jefar da goran ruwan Ya durkushe anan qasan tunanine kawai ya hana zuciyar tashi sakat yace Waye shi? Taya za,ai yaga sauran yan-uwansa?taya matarsa zata dawo gareshi? Ta za,ai ya rungumi kyawawan yayansa? Ya qara kifa kansa a qasa sosai. Shin ta yaya memorynsa zai dawo masa Amsar daya kasa samu kenan anan ya kusa wuni babu mai lallashinsa yace ya zaiyi dole ya rungumi qaddararsa hannu bibbiyu Anya kuwa zan iya abinda zuciyarsa ta sanar dashi kenan To bari mugani Muje zuwa Babu Wanda bai tausayama adnan ba musamman aleeyu Da yake ganin adnan din na cikin wani irin Hali nda yake buqatar taimako Yake buqatar su jashi a jikinsa Afnan kuwa duk abinda take qarfin haline tsoronta daya karta bayyana damuwarta a kirata marar zuciya Mai nacin soyayyah Don haka duk yaddah taso ta tausaya Masa. Sai taqi ta dinga danne zuciyarta don kawai ba yaddah ta iya Innama da ana bata lbr har kwalla tai masa tace mai yasa ba,a taho dashi nanba Lol kaji mutane Wanda Ada kowa kyararsa yake Adnan ne zaune a cikin katafaren office dinsa ya kasa komai zuciyarsa sai tarayo masa abindaya faru a kotu take Kamar mai mafarki ya tashi zumbur ya lalubi key din motarsa yace Wlh tallahi mai rabani da sady yau sai Allah don ta Gama zubar min da mutunci kuma. Don tunda nake ban taba samun Wanda yai min wasa da hankali irintaba. Lallai saina nuna Mata kuskurenta ayau kuma a yanxu ya zari key din motarsa a zafafe yabar offishin nasa Aure. Kan. Aure Chapter31 Cikin zafin rai ya isa gidan nasu Wai basanan daga ita har uwar tata hajia sury wai sunje. Tailand harkan kasuwanci Baiji dadin hakanba don yayi yuyyar samun sady a. Gidan nasu Afnan na zaune a. Offici dinta amman ta gazayin komai don haka ta daura idonta kan takardun dake gabanta ba tare datasan abinda ke damuntaba Masinjane ya shigo cikin girmamawa yace ranki e Dade kinada baqo a waje ba tare da tayi tunanin ko wayeba tace ce masa ya shgo Yace to bai jima da fitaba taji an turo qofar office din nata ta daga Kai don ganin mai shigowan Adnan ne kallo daya ttai masa ta fahimci yana cikin tsanananin tashin hankali Zai zauna tace a,a waya Baka iznin zama koka mance a offishin Lauya kake bana likitaba Adnan Wanda harya dosana qugunsa ya miqe muryarsa na rawa yace tuba nake ranki ya Dade ba tare data tanjaba ta dauke kan nata Ba yaddah ya iya dole ya bayyana Mata abinda ya hanashi Barci koda bazata saurareshiba Murya a raunane ya kira sunanta afnan Don Allah don annabi ki tausaya ma zuciyar data rayu da sonki kuma take dawainiya da soyayyarki kiyima masoyinki uzuri Ke kanki kinsani ina cikin hayyacina ba zan iya yin miki abinda nai miki a baya ba kin soni afnan bazan iya sanin sonda kikai minba a accen rayuwar Ki taimaka ki nunamin wata sbwr soyayyar a wannan rayuwar please afnan Ya duqa saman gwiwoWinsa idanunsa sun ciko da qalla yace ki yarda dani afnan Tabbas kalamanta sun ratsa zuciyarta saidai ba zata Yarda son nashi yai galaba akantaba Shiyasa har a yanxu taqi yarda dasu hada ido Yasa hannu ya share qallar dake qoqarin zubo masa Yaci gaba da cewa Wlh afnan tunda naji irin soyayyar da mukai nidake a waccan rayuwar data goge a kwakwalwata nnaji kawai inason maimaita irinta Afnan ta miqe cike da fusata don tanada yaqinin idan ta biye masa to abinda take gudun aukuwa zai auku Ta daga masa hannu tace saurareni malam oho Bakin daya zageni yau shine yake roqona hannun daya mareni shine yau yake lallashina To inason ka sani xuciyata tayi nisa batajin kira don koda maza sun qare babu abinda zanyi dakai Adnan meye zan qaru dashi a wannan qaramar zuciyar taka marar alqawari? Yana shirin magana ta nufi hanyar fita domin tabar masa office din Ji tayi ya riqo gefen kwat dinta ta waiwayo da hanzari ranta ya Gama vaci Saidai maraicin data gani a a fuskartane ya karya lagonta amman da babu abinda zai hana bata daukeshi da wawan mari ba Cikin daure fuska tace meye haka doctore Yace afnan don Allah karki guji adnan dinki yayanki Wanda yafi kowa sonki Wlh duk duniya dani kika dace afnan Ta tabe baki tace a wancan tsohuwar rayuwar kake amsa adnan amman a yanxu doctor kake Kaje koka jira duk sanda ka tuna da wancan tsohuwar rayuwar da kake fada kuma ka tuna da irin soyayyar da mukai Saika dawo na amsheka a matsayin adnan yayana Wanda yafi kowa sona Ta fice ta barshi anan ji yai kamar zai koma ga mahaliccinsa Sbd qunar da zuciyarsa take Tana kallonsa ya fito daga office din nata sannan ta koma da sauri ta rufo qofar kamar wacce take tsoron kar wani dodo ya shgo ofishin Tana zama ta hada kanta da taburin dake tsakiyar. Ofishin ji take wani abu na yawo a cikin zuciyarta Zainab ce ta shgo ofishin amman bataji shigowar nataba saidai ji tayi an dafarta ta dago da idanuwanta da suka rine sukai jajir sbd. Tunani Zainab tace yanxu zan shigo na hadu da wannan dan iskan me yaxo yai miki afnan taji kamar ta watsa Mata ruwan zafi Sbd zafim maganar datai Mata don Haka cikin nuna rashin fahimta tace wanene kuma dan iska zainab? Baki ta tabe tace adnan mana yanxu na ganshi fitarnan da zanyi Wani murmushi takaici afnan din taja tace yanxu abban Twinss din kikecema dan iska? Zainab dan uwananefa kuma kin sani Zainab ta riqe baki sannan tace tab lallai duk Wanda ya shga tsakanin masoya to shine zaiji kunya amman Nan Wani kalar zagine baki masa ba a yana dan uwan naki Nidai gaskia a riqe mana amanar ibrahim don nasan irin halinmu na Mata Hmmm afnan din taja gajeran murmushi tace zainab kenan amman kin ban mamaki wlh Yaddah nake ganin taraiyyarki da mustaba sai nake ganin idan kece abinda ya faru dani ya faru dake kenan bazaki iyayin adalciba? Zan iya rantsuwa da saikin aikata son ranki Amman duk yaddah nake qoqari ina bakin yina har an fara samun wannda yaga gazawata Yanxuma kenan anya Nan gaba ba gani za,ai ban tabuka komaiba? Da alamun tayi nazarin irin abunda afnan din keji na rabuwa Da masoyi kuma ba irin rabuwa na cikin hayyaciba Anya zuciya zata iya jure zafin irin wannan rabuwa? To idan kuma itace ya zataji? Musamman yanxu da adnan din ya dawo yake nuna yaji ya gani Ta dafa kafadarta tace Kiyi haquri qawata na fahimci abinda kikeji kuma na tabbata idanda nice bazan iya juriyar da kikaiba Nidai abinda nakeso dake a yanxu shine kici gaba da juriyar da kike kodan fita daga zargi a idon jama,a Afnan tace Wlh zainab vazan taba cin amanar ibrahim ba bazan taba rabuwa dashiba inhar bashine ya rabu daniba Ya watsamin barkono a idoba Sannan bazan taba sauraron adnan ba koda kuwa zai mutu a gabanane don kuwa ya rigada ya tsinke igiyar soyayyar dake tsakaninmu Tace badonn kuma wai sbd ibrahim ba ko wai sbd aminda mutane zasuceba a,a saboda kankin kainane kawai Afnan ta miqe ta sabi jakarta tana kallon zainab tace ke ni kinga tafiyata Itama miqewar tayi tana Allah e huci zuciyar manya ammanfa Nibada wata manufa nai wannan zancenba Tace yo da wata manufa mana ai inhar baki da baki suna haduwa to dole watarana sai rai ua baci A tare suka jera suka fice daga ofice din Afnan tana kwance Akan gadonta tana kallo a cikin Laptop dinta yaranta duk sun kwanta ajikinta. Tayi rigingine laptop din na saman ruwan cikinta Tom an jerry suke kallo ita da yaran nata Lami mai aiki ta shigo tace ranki ya Dade inna tace wai kixo falo kinyi baqo Tace to kice ina zuwa tace an Gama ranki e Dade ta juya ta fice Aje musu laptop din tayi tace to gashinan ku kalla kuma sauran wajen rigima kuyimin barna babu Wanda ya tanka Mata a cikinsu don duk hankalinsu nakan jerry yayi Satan cinyar kaza lol Nade kanta tayi da kallabin dake hade da jallabiyar tata Ta nufi hanyar falon tana shga gabanta yai mummunan fadiwa. Gani tayi ya qara Mata kyau ga kwarjiki a take ta nemi natsuwarta ta rasa saida tai da qar sannan ta tattaro dakewar duniyarnan ta dorama kanta Ta qarasa cikin falon ko kallon inda yake bataiva tace inna Yanxu lami taxo wai kina nemana nayi baqo Inna tace a,a ba baqo kikai ba adnan ne yaxo shine nace Kixo ku gaisa Sannan ta juyo ta kalli kujeran da yake tace ok guud sannu da zuwa dacta ya gida Jikinsa yai sanyi duk wani kwarin. Kwiwa dayaxo dashi ya sulale Muryarsa kansa tayi rauni yace Lfy lau afnan ya aiki? Ta tabe baki ta juya tana shrin komawa sannan tace lfy Ji yai tamkar yasa hannu ya janyota saidai babu dama yana kallonta harta bace Ji yai gaba daya zaman ya gunduresa gashi inna sai damunsa take da hira na yan uwansa Jinta kawai yake don ba tuna komai yakeba a ransa yace dama kira masa afnan din tayi ta basu wuri qila da zaifi fahimta Tana isa falon nata taji wayarta na ruri ibrahim ne tana dauka ta Kara a kunne. Ina waje abinda taji ya fada kenan ya kashe wayar Fita tai ba tare data kula yayan nataba dake gaban laptop don batason susain yaxo suje su dinga takura masa A waje ya tsaya saman boot don motarsa Yana jiran ganin ta inda zata fito ta isa inda yake tana murmushi tace wannan wannan zuwan naka na bazata kumafa? Lfy dai ko? Yace duk nakine sweet heart afnan ta riqe haba tana murmushi tace waceni da daura zanin uwar miji na yawo tsirara ai maryam itace sweet heart ba niba Ya kanne ido daya yace ai kowacce da wurinta sannan ko wacce zata iya amsa sunan daya a cikinku Tace hakadai ka fada yace hakanema ki shirya gobe domin muje siyan kayan lefenki Afnan ta zaro ido tace wani lefe kuma ibrahim nida ba budurwa ba Kawai za,a tsayamin dawainiya Ya harareta da wasa yace laifine don ango ya siyama amaryarsa kayan domin ta dinga yin masa kwalliya?$ Tace ba laifi bane yace to ki shirya su taslim da aslim dasu za,aje Ta amsa masa Sannan sukaci gaba da hirarsu Sai misalin magrib sannan yai Mata sallama ya tafi Sannan itama ta shga gida a daidai hanyar falo taci Karo da Adnan din shima yana niyyar fita Kallon kallo suk tsaya sunayi tsakanin shida ita Baice Mata komaiba ya giftata ya wuce inda tabi bayansa da kallo harya fice sannan itama ta shga ciki Da safe misalin qarfe sha daya ibrahim yaxo ya dauki afnan da yaranta suka shga kasuwa siyayyah yai musu ta gani ta fada inda har saida afnan din tau masa magana Akan ya barshi haka sai yamma likis suka dawo gida agajiye don dama ba wani hira sukaiba Akwati hudu ya cikoma afnan din harfa dan kit duk kayan lefene a ciki sannan taslim da aslim suma aka cicciko mutu akwatina day daya manya aka zubo masa a cikin mota Bayan sun isa gidan yasa masu aikin gidan suka shga da kayan ba wata hira sukai mai tsawoba sbd gajiyar da duk sukayi yai Mata sallama ya tafi itama taja yaranta suka nufi ciki Ranar lahadi da misalin qarfe biyu aka daura auren Afnan aleeyu musawa da ibrahim hafis mai ruwan kudi sunan da ake Kiran mahaifinsa din dashi kenan Daurin auren ya hakarci manyan mutane Awannan lokacin adnan kasa jurewa yai haka kawai yaji ya Jarabtu da son afnan din So bana wasaba sonda sai data zama matar wani yaji bazai iya rayuwa idan bata ba Kuka yake sosai shi kadai kamar qaramin yaro sai safa da marwa yake a falon nasa Baida mafita illa yasama ransa salama amman ina abun ya gagara Shi kadai a gida haka kawai ya zama kwabron qarfi da yaji Tunanin me yayi oho yallabai ba wanka ba wanke ido ya zari makullin motarsa ya fice Kai tsaye gidansu afnan din ya nufa ya dinga kutsawa ta cikin mutane bai damu da hayayyaqo masan da mutane sukayo masaba Don cikin jama,ar idan za,a daura masa wuqa bazai iya saninn koda sunan mutum daya daga cikinsuba Zaune suke ita da qawayenta inda nafisa ke fada Mata mugun Hali irinna kishiyar tata wato matar ibrahim Zainab sai rurrufewa take afnan din tace barta ta fada don nasan da irin zaman da zanje Mata munafuka ai daman na sani shiyasa tuntuni kiketa bobboyemin Zainab din tace,a,a afnan kinsan bazan turaki inda zakisha whl ba Wlh idanda ban hango zaman lfy tsakaninki da ibrahimba da bazan tabayin ruwa da tsaki Akan lamarinba Batun matarsa kuwa bana tunanin akwai abinda zai dameki sa ita gidanki daban nata daban Afnan tace kinganni Nan tsoron kishiyace dani don tundana taso bamuda matar uba Harna taso Gashi ance fitinanniyar macece kinga kuwa zama da ita sai anyi damara ZuwAira tace damarama kuwa don kisa a ranki zakije fada da shaidance yasin lol. Don wannan matar tamafi shaidan iya shaidanci Wlh Afnan. Ta zazzaro ido gamida dafe kirgi Saidai kafin takaida qarayin. Wata magana sai ganin adnan tayi tsaye a cikin falon idanunsa sunyi jajir kamar Wanda yaci babu Gabanta yai mummunan faduwa Bata iya maganaba ta miqe ta nufi inda yake baicema kowa uppan ba ya juya tabi bayansa har farfajiyan gidan ya kifa kansa kan jikin motarsa shi kansa ya rasa gane kansa da abinda ke damunsa Tausayinsa ya kama afnan din taji kamar ta kwantar da kanta Akan gadon bayan nasa itama ta zubar da nata hawayen Saidai babu dama hakan yasa ta kira sunansa Yaya adnan meke damunkane? Daqar ya iya waiwayowa yana kallonta idanuwanta sunyi jajir yace ni kaina bansan abinda ke damunaba afnan na samu zuciyata da matsanancin ciwo damuwa da radadin soyayyar dake neman illatani Afnan na tsorata ta yaddah zuciyata ta bijire take nunamin cewa ba zata iya rayuwaba idan babu ke Afnan nayi kukan fili harma Dana boye babu mai lallashina Daga bayansa yaji ana cewa lallai indai irin wannan kukanne kuma Akan afnan to wlh har duniya ta nade ba zaka taba samun mai lallashin nakaba A fusace adnan din ya waiwayo don ganin mai qara tunzurashi da Wadannan. Baqaqen kalaman Lol shin Waye wannan oho Nima ban saniba Mu hadu a nxt Aure. Kan. Aure Chapter32 Ba kowa bane illa ibrahim bai damu dashiba yaci da cewa Afnan sonki zai zamo ajalina bakiji yaddah zuciyata ke bugawaba kamar ta huje bana iyacin komai Ki tausayamin afnan ki taimakeni idan na rasaki mutuwa zanyi. Na rantse miki don inaji a jikina Tabbas tausayinsa ya ratsata har cikin jininta Saidai lokaci ya rigada ya qure don koda bai qureba ba Zata iya amincema soyayyar docta ba Don gani take kamar da akwai banbanci tsakanin wannan adnan din da wancan yayanta adnan din data sani kafin yayi losing din memory dinsa Ta daure zuciyata ta voye abind ke damunta tace kayi haquri don yanxu ni matar wani ce Ya marairaice Mata yace afnan Kiyi haquri don Allah Ki ceci rayuwata wlh afnan bazan iya barinkiba Don Allah afnan ki kasance tare dani Zuciyata zata iya karyewa matuqa Tabbas idan taci gaba da sauraronsa Don haka muryarta na rawa tace kaga tafiyata malam tunda Kai bakasan dokar aureba Ya miqa hannu kamar ya riqota saidai hakan ya gagara gaba daya yaji duniyar na juya masa Daqar ya miqe ya shga motar tasa ya kifa Kai saman sitiyari Saidau ya Gaza Jan motar In banda sunan Allah ba abinda bakinsa ke furtawa Harya samu natsuwa sannan ya kunna motar yahau hanya Tunda afnan ta koma ta rasa natsuwarta su kansu qawayen nata sun rasa gane kanta Zainab cema ta dameta da tambayar abinda ke damunta tace don akkah Zainab barni kainane ke ciwo bari nadan samu barci karkibar koma ya shgo Nan Babu yaddah suka iya dole suka barta saidai zance barci ita kanta tasan yaudarar kanta take Don duk iya Satan barci a wannan yanayin da take bai isa ya saceta ba Misalin qarfe biyar a yammah motocin daukar amarya sukazo inna taima afnan din fada da nasiha sosai Malam ma yai Mata nasiha mai ratsa jinin jiki Aleeyu ma yai masa tasa nasihar sannan Iyaye suka tasa qeyarta zuwa anguwar sharada Duk Wanda suka kawota sun watse anty kausar kuwa bata samu zuwaba sbd batada lfy Saidai Wasu daga cikin danginsu wadanda suke mutunci sosai da afnan din Gida ya rage daga afnan sai Zainab a ciki Bayan sunyi sallar magrib Zainab ta share Mata ko ina na cikin gidan ta goge. Ta saki labulaye tabi ko,ina da turarukan wuta. Gaba daya gidan yadau kamshi lol Ta matsama afnan din ta watsa ruwa da kanta ta zabo Mata Wasu hadaddun kaya da zatasa Riga da siket Kayan sun bala,in hawa jikinta sbd dinkin yabi surar na jikin nata ta fito shar da ita. Kamar yar sha takwas Misalin qarfe takwas na dare ango ya shigo gidansa tare da abokinsa mustafha Afnan da Zainab din na falon har suka shgo babu Wanda ya tanka musu har sukaima kansu masauki Mustafa ne ya soma magana yace Ummm amarsu ta ango dubi yaddah aka wani hakince sai kace sarauniya Zainab ta miqe daga inda take tana fadin toya son ranka Yace yafa sweety kinga yaddah Dakin ke kamshin amarci Kai gaskia Nima dole na zama ango kwanannan Zainab ta bishi da wani irin kallo mai kama da harara Yayi yar murmushi yace au ashefa kishiya fa ba dadi amman wata tayi ruwa tai tsaki Akan aima wata Ibrahim yace Kai malamai kufa nake jira please kwa Gama captar taku a mota Gaba dayannsu suka kwashe da daria zainab tace eh lallai yayi kyau tunda Mun Gama gyara masa wasan ai dole ya koremu Mustafa yace ai malam idan Kai haquri yanxu zamu tafi mubar Maka amaryarka Zainab tace ammman ai Mun tsaya mu sayi baki ko?ibrahim yace wah ai wlh ba wani siyan baki tashi zakuyi yanxu ku kama gabanku Mustafa ya kalleshi yana daria yace yayi ustax ka hadu da yawa Ya dubi zainab yace tashi muje kinji wannan angon gab yake daya shige da amaryarsa yabarmu anan Zainab ta miqe ta sabi jakarta da gylenta tace umm Bari mu gudu tun abin bai Kai nanba Afnan dai da ido kawai take binsu saidai murmushi da baiki kawai Zainab ta rankwafa tai Mata rada sukasa daria su muStafan suka miqe ibrahim din ya tashi domin yin musu rakiya Ta gagara motsawa daga inda take tunani kawai take shin yanxu ko,a wani irn Hali adnan yake. Ciki? Qilama matarsa ta mantar dashi komai a take taji wani kishi ya yinkuro Mata A haka ibrahim ya dawo ya sameta a takure waje daya Ya zauna gefenta yana fadin yadai madam? Batace komaiba don haka yace taso muje ki tAimakaminn na canja kayannan don muyi sallah Ba musu ta bishi falonsa suka nufa Wanda ke dauke da makekekn gado a tsakiya da duma duman kujeru biyu Afnan ta zauna kan gefen gadon tana kallonsa ya zame kayan Jikinsa dagashi sai gajeran wando Kirjinta yai mummunan bugawa tace innalillihi wa innna ilaihir rajium Bai kulataba dukda ya lura da tsoratar datayi ya shga falonsa kamar jira taje yana shga ta fice da sauri Falonta ta nufa falone fankacece mai dauke da bedroom niyi an qawatashi da kayan alfarma Ta dingabin kayan Dakin da kallo. A ranta tace lallai abbah. Ya kashe kudi Akan kayan dakinnan nata ko Kayan jikinta bata cireba ta haye saman gadonta taja filo Bawai don tanajin barciba. Illa kawai don ta rasa abinyi Batafi minti talatin da kwanciyarba ya turo qofa ya shgo Har gaban gadon nata ya qaraso dagashi sai jallabiya ta qara runtse idonta alamun tana barci Darewa yayi kan gadon yasa hannu ya janyota Jikinsa qara runtse idon nata tayi wai adole ita kunyarsa takeji Lol. Laluban kunnenta yayi yadan ciza da sauri ta miqe ta riqe kunnen nata. Yana Mata ani siririn murmushi Sannan ya rada Mata tashi muje muyi sallah ko babyna Bata musa masaba ta yinkura da alamar. Ta miqe ya qara janyota jikin nasa. Idanuwanta sukai narai narai tace sallah fa kace zamuyi Ya lumshi idanuwanta sannan ya Bude yace banso kibar jikinane afnan zanso ace Mun kwana a haka Tace mubar saLlar kenan Sakinta yayi yace no afnan muje domin mu godema Allah daya nuna mana wannan ranar Bata jima a

Chapter 12 of 16