Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tana tafia ya shga Dakin nasa ya tattaro duk Wasu kayansa da yasan yana aiki dasu ya kwashe yakai Dakin afnan Sannan ya hada dayin Mata gargadi kan wlh koda magana marar dadice ta hadata da afnan saiyasa an kulleta har dan makullin ya vace Batace masa komai ba harya fice ya nufi sashin afnan din Wacce ya lura da akwai damuwa a cikin ranta Don haka yaje yaci gaba da lallashina da bata kulawa harta samu dan sassaucin zafin da ran nata ke Mata taci gaba da harkokinta ba tare data sake shiga sabgar Maryam ba harkar gabanta kawai takeyi Har huutunta ya qare ta koma wajen aiki duk abinda tasan tanayi na game da harkar gida bata fasaba Tun kafin takwas na safe take kammala girkinta ta dibarma Maryam nata takai Mata sannan ita da mijinta suma suci kowa ya wuce wajen aikinsa Ibrahim ya sakema afnan mota yasai Mata jeef qirar. E. O. D motar ta hadu matuqa don haka yanxu babu abinda ya dameta na game da Maryam don. Tun takwas take fita office ita da ibrahim bata dawowa sai hudu shi kuwa sai shddah yake dawowa kafin ya dawo ta kammala komai na game da aikin gida ta qawata jikinta da kwalliya Tana kichin wani lokutan da kansa yake shigowa ya taimaka Mata su kammala aikin tare A haka har hajia ta dawo da yaran ibrahim din wai sbd uwarsu na gidan Don haka afnan ta rungumi yaran hannu bibbiyu tana basu kulawa yaddah ya kamata Hakan yasa ibrahim ya qara shaquwa da yayan nasa don wani lokutan idan ana hira har kashewa yake da yayan hakan kuwa ba qaramin farantama. Afnan din rai yakeba Ita ko Maryam ta saki yaran ne don su dinga dako Mata rahoto shiyasa bata damuwa da shishigema da yaran sukema afnan Kullun kuwa da baqin ciki take kwana don kuwa zaunar da yaran take taita bugun ruwan cikinsu su kuma suyita zayyane Mata komai Abin yaxo ya dinga gagaranta barci. Sbd baqin kishi Shikuwa gogan gaba daya ya daina shga harkarta Ko hanyar Dakin nata baibi idanma yana zaune a falone yaga ta fito saiya tashi ya shge ciki Kai ko gaiSuwa bai yarda tana tadasu da Maryam abin ba qaramin damunta yakeba Ita a haukarta wai zaman aure take don haka ta fara fito da feleqenta wata kwalliya tata bata tashi yi sai yana zaune a falon shiko baya nunama yasan tanayi Kai ko kallon inda take baiyi Ko kadan bata birgeshi yana mamakin yaddah akai jahilci yaima kanta katutu Bayan sallar isha,i afnan ta Gama shiryawa cikin wata ganyar green din atamfa rigar ba qaramin kyau tai mataba kuma tahau jikinta an Mata dinkin rapper Tana fitowa ya jera musu abinci Akan dinnig area Tana gamawa kuwa saiga ibrahim din sun dawo daga masallaci shida salim riqe da hannunsa Tai masu sannu da zuwa sannan tacema salim ya daki abinci mamansu yakai Mata sannan ya kira sajidah don suci abinci yace to ya dauka yaje yakaii Mata sannan ya kira sajidan Nan suka zauna da zubama kowa suka faraci Ibrahim har ibrahim ya fara santin daya saba kaman daga sama suga ganta a gabansu ibrahim ya gimtse daga darian da yake ya hade fuska yana kallonta sai wani girgije girgije take wai ita a dole ta hadu Tana tsaye da Wasu Riga da wando damammu Ana ganin ko ina na shef din jikinta Gaba daya kayan basu Mata kyau ba amman ita a ganinta ta qure adaka ne ibrahim din yace malama lfy? Maryam din ta watsa masa wata uwar harara wai ita adole fari take Ta wani maqe murya tace ban ganeba ibrahim wai meka maidanine. A cikin gidannan? Ka juyamin baya Baka shga sashina bakacin abincin Dana aje Maka Baka kwana dani Tace Haba ibrahim yanxu sbd wannan karuwar zaka juyamin baya haka? Ibrahim yace wacece karuwa matar tawa ita kike kira da karuwa? Lallaima Maryam baki da kunya. Yanxu har akwai karuwar data wuce ke dubi shigar da kikai a matsayinki na musulma bayan kinfi lowa sanin babu wata alaqa ta aure dake tsakanin dake Ko kin zata Nima jahiline irinki to wlh ki shga taitayiNki donni ba mutumin banza bane Maryam ta hatsala tace aiko indai ni jahilace to uwarkace babban jahila tunda. Ai tasan da sakin ta daukoni ta dawo dani gidan naka Nai...... Kafin ta qarasa ya dauketa da wani wawan Marin da har saida hawayen wahala suka fito daga idanun nata Ta dafe wajen tana wai ni ka mara ibrahim mari? To qarya akai ai itace babban jahil... Kafin ta qarasa ya qara Mata wani wawan Marin Harda tokari ta koma. Gefe a gala baice amman dukda haka bata daina cewa to wlh inaso ka sani ni Maryam sai naga bayanka tunda harka iyasa hannu ka mareni wlh saikayi kuka da idanunka Badai Akan wannan karuwar ba tai kwafa gamoida girgiza kai Yai yinkurin kamota ta fice a guje afnan ta rigoshi tana bashi haquri kayi haquri kayi haquri please adnan ban sanka da zafin raiba karka biye Mata Baka ganin va daidai takeba zafin kishine Dana rabuwa dake ke damunta bayin kanta bane kayi haquri don allah kaji? Yaja wani ajiyar zuciya sannan ya zauna idanunsa nakan afnan din ita kuwa aikin basa haquri kawai take Yai wani takaitaccen murmushi yana girgiza Kai Wasu zafafan hawaye Suka zubo masa Yace rayuwa kenan afnan irin abindana taba guda kenan shekarun baya da suka wuce Nasan wata rana sai,an gorantamin ni nasan hajia tanada ilmi daidai gwargwado saidai bata aiki dashi Ita kullun son ranta takebi sabanin gaskia da matakan binta Babu ruwanta da abinda allah da manxonsa suka fada duk duniya babu mai iya tankwarata sai alhaji mahaifina kenan Shine kadai ya isa ya daura doka ta kasa shallakewa Bayanshi kuwa babu Wanda ya isa Kuma na rasa Wanda zai gaya Mata gaskia a cikin wadanda suka darata a gaban idonta ko bayan idon nata Nasan ganin idon mahaifin nawane da nawa Amman yau gashi har ana fara zaginta a gaban idon kuma cikin wadanda tafi kyautatamawa Afnan hajia taso Maryam fiye da yaddah tasoni Ta nuna Mata soyayyah fiye dani data haifa Hajia babu Wanda tafiso irin marar gaskia da marasa kunya ga irinsu Nan kin fara gani yau a gabanki Tabbas hajia ba zata tava Gabe cewa inada ranaba ba zata tavajin digon sonab sai ranar da nabar duniya kuma Tabbas wannan ranar tananan zuwa Afnan tace a.a dan allah ka daina fadin haka ai komai na duniyarnan mai wucewa ne Bai tanka mataba don haka tajashi jikinta sosai ta share masa hawayen nasa. Sai lallashina take tamkar dan yaro lol Afnan ce zaune a. Office yau aiki yai Mata yawa sbd wata rikitacciyar shari,a data kunno musu don Haka sau biyu ana Kiran wayar tata tana tsinkewa ba tare data daukaba Ana ukunne tasa hannu ta dauka don taga alamun mai Kiran baida alamun haqura Ba tare data duba sunan mai Kiran ba ta Kara a kunne gamida sallama yace hello adnan ke magana Kiyi maza maza Kixo gida keda mijinki Abba na nemanku ba tare dajin abinda zataceba ya kashe wayar Afnan tabi sunnan dake jikin wayar kamar wacce aka tsikara ta zari. Makullin motarta tai waje Ta kira ibrahim din tana fada masa Kiran da Abban yake musu yace to su hadu acan ba tare datama kowa maganaba tahau motarta ta nufi gida Tai fakin a qofar gidan jikinta sai rawa yake. Ganin mutane tsaitsaye daga cikin harabar gidan Har gudu gudu take wajen shiga gidan wata juwace ta nemi kadata a. Lokacin data hango gawa lullube da likafani Afnan ta zube qasa ba tare data ankaraba ta yaye likafanin innalillihi wainna ilaihi raju,un Kullu nafsin za,ikatul maut. Evwe soul shall test dead Mahaifiyartace allah e ma rasuwa wato hajia nafi Kuka ta saka mai tsuma zuciya aleeyu ne Akan gawar adnan da iyayen hajia nafin Harda kausar Adnan yasa hannu ya janye afnan din gefe daya don Bama masu daukar gawar dama domin sata a cikin makara Gaba daya yaji tausayinsa ya lullube zuciyarsa. Ya rasa ta yaddah zai fara lallashina sai ce Mata yai Kiyi haquri Kinji afnan addu,a zaki Mata shi mamaci ba,a masa kuka sai addu,a Daqar ya samu ta daina kukan sai hawaye kawai Daganan shima yabi yan rakiyan gawar zuwa kushewa Afnan ta qule a daki wurin sauran dangi sai sharar qallah take tace shi kenan yanzu mommynta ta tafi Yanxu shikenan ta zama marainiya ta rasa uwa Nan take rayuwarta da momyn nata ya dinga dawo mata Har qawancen mommyn nata da mommyn sady hajia sury surayyah kenan idan baku mantataba Wacce tunda aka fara case din mommynta da Abban nata ta juyama qawar tata baya ba,a qarajin duriyartaba Kenan a cikin dadi ake sonka babu Wanda zai soka idan kana cikin wahala? Gaskia ne afnan rayuwar tamu ta yanxu sai a slow allah dai isa mu dace A zuciyar afnan din babu abinda takema kuka illa makomar mahaifiyar tata don tasan da wuya tai kyau Bata sake neman ibrahim ba har dare saidayaxo ya dauketa Kullun shi yake kawota ya maidata har ranar da akai sadakar uku misalin qarfe hudu kowa ya kama gabansa Afnan na tare da yaranta tai mamakin yaddah yaran suka shaqu da adnan sosai haka Don ko wajenta basa zuwa idan suna tare dashi adnan ne ya shigo falon afnan din ba kowa a ciki daga ita sai yaranta saidaya qare mata kallo tsap suka gaisa Sannan ya miqa mata wata ambulan Yace wannan ambulan din wasiqa ce momynki ta rubutata a Lokacin data samu sauqi A Lokacin da ciwon nata kuma ya tsanantane mukaje dubata nida Abba shine masu tsaronta suke cewa ga wasiqanan inji momynki wai don allah abaki wasiqar hannu da hannu hakan yasa na riqeta da hannuna Na Kawo miki ita yanxu gatanan Hannunta na karkarwa ta amshi wasiqar gamida soma karantawa kamar haka /////// Naku har kullun My apology to. Y,ll nasan a lot ov ppl. Zasuyi Fushi course ov ban Kawo musu ci gaba lbrn Nan jiaya ba da kuma yau da wuri ba. Kuyi haquri again hakan ya farune sbd. Big bro dinmu da yake aure so serious ina busy ne. Don nasan da yawa wadanda muke chart dasu zasuga tun day before yesterday nake offline so sbd haka sai kuyi haquri Kamar yaddah bro dina yai aure allah yasa. Duk samarin wannan page namu suma su samu suyi auren. Yan mata kuma alllah ya kawo muku mazajen auren Harda zawarawan page dinnan kuma haka allah ya fito muku da mazaje. Mai mace daya allah e Buda masa ya qara mai biyuma haka mai ukuma haka mai hudu kuma sai yai haquri. Shima admin ku tayashi da addu,ar samun beb kyakkyawa. Lol Mu tara a. Next chapter Aure. Kan. Aure Chapter39 Ta fara karanta wasiqar kamar haka Salam Zuwaga yata afnan naso ace da baki nake baki wannan wasiyar. Amman hakan bata samuba don nasan tawa taxo qarshe Afnan na tabbata a rayuwata ta duniya ban aikata komaiba Sai son zuciya. Wanda ya kaini ga halaka Tabbas allah kadaine yasan makomata . Afnan ki gafarceni don na tabbata babuni babu rahamar ubangiji Afnan a duniya cikin manyan zunubai babu Wanda ban taba aikatawava. Addu,arku kawai nake bara wata qila allah yaji qaina yaimin afuwa Afnan ki duba cikin Dakin dake bayan boysquaters din gidannan ai qoqarin budeshi akwai ajiyata a ciki Nasan duk Wanda yaga wannan ajiya zai tsinemin yai tir da Allah wadai dani Amman wannan tsanar ba zata dameniba burina duk Wanda ya hada alaqa da wannan ya yafe min wata qila kona samu wani dan sassauci daga wurin ubangiji Afnan koda kowa ya juyamin baya ke karki juyamin baya duk tsanani Akan abinda kuka gani Gudu nake kada bayan raina a zargi mahaifinki ke kasai nakedashi a duniya addu,arki. Tafi ta kowa Afnan wlh nayi nadamar abindana aikata kuma na nemi gafarar ubangiji don allah karki qini kamar yaddah kowa zai qini yata afnan please Allah ya hada fuskokinmu a qiyama amman ni harna fara hango kalar azabun dake jirana tun a kabari ///// Afnan ta chukukuye takardar dake hannun nata tana wani irin kuka mai sauti. Tana Kiran sunan mommyn nata da qarfin gaske Adnan dake kusa da ita ya rude gamida riqeta yana fadin lfy? Cikin kuka tace kiramin abbana yaya adnan kiraminshi Cikin rudewa baisan Lokacin daya kwasa a gujeba baifi minti biyarba sai gashi shida Abban nasa Jiki na rawa tace moje Dakin dake bayan boysquaters Abba mommy tace tanada ajiya a ciki Ba Wanda ya tanka mata suka nufa can bayan gidan Wanda Bama kowane ke zuwa wajenba Adanbayan gidan Dakin yake kwata kwata babu mai zuwa wajen Saidai Dakin a rufe yake da wani qaton kwado gabadayansu suka cirko cirko suna kallon qofar Mahaifin nata aleeyu yace yanxu ya kenan Waye zai iya yanke wannan kwadon? Adnan yace bari na dauko zarto muga ko zan iya yankeshi Aleeyu yai murmushi yace adnan kenan an gaya Maka yanke wannan kwadon qaramin aikine ai jeka kawai ka kirawo irin masu gyaran qofar Nan suzo su balle qofar Afnan taji kamar ta hana saidai babu wani mafita dole a kira mai gyara domin ya bambare qofar Don haka adnan yasa waya ya kira engeener mansur sale Baifi minti ashirin ya isoba don daman shi ido a kudi ne Da kayan aikinsa yaxo don adnan din ya masa bayani Yana duba kwason yace Kai wannan kwadon aradu bazai taba yankuwaba saidai kawai a cire qofar Babu musu Abban nata yace a cire gaba dayansu suna tsaye yake aikinn cire qofar Yafi minti talatin dukda kayan aikin nasa sannan ya samu damar cire qofar Kamar jira suke ya cire gaba dayansu suka nufi cikin Dakin babu komai a ciki fayau sai wani girkeken akwati dake tsakiyar dakin Aleeyune yasa hannu ya daga akwatun adaidai Lokacin daya zube qasa yana Kiran sunan allah. Innalillahi wa inna ilaihi raji un. Gava dayansu har rige rigen leqa akwatun suke ita da adnan Shima injiniya masur ya sawo Kai yana fadin lfy? Meke faruwa? Afnan na hada ido da abinda ke cikin akwatin ta Fadi qasa sumammiya Babu abinda aleeyu da adnan ke Fadi sai sunan allah. Injiniya ya leqa akwatin yana fadin wai meke faruwane? Ganin abinda ke cikin akwatin shima ya rikitar dashi bakinsa na rawa yace alhaji muftahu kafin ya rufe bakin nasa saiga yan dubu dubu na fita daga bakin nasa Ai kafin kowa yai magana ya kwasa a guje. Babu abinda ke fita daga bakin nasa sai kulya ai yuhar kafirun har ya fice daga cikin gidan kamar zautacce. Da alamun duk addu,ar daya ya kama ta kubce masa ne Gaba daya adnan ya rasa abinyi ga afnan a sume ga abbansu ya zama kamar mutum mutumi saidai idanuwanta kawai dake kiftawa Ga kuma akwatin akwatin gawar alhaji muftahu mahaifin hajia nafin toya kenan Don haka yaita maza ya girgiza Abban nasa yana fadin abbanh kayi haquri ka tashi don musan abinyi Kaga mai gyarannan dan jaridah ne karfa yaje ya watsa wannan zancen a idon duniya Aleeeyu ya dafe qirjinsa dake masa matsanancin ciwo kamar zai rabe biyu Muryarsa kamar ta Wanda ya shekara biyu a asibiti Yace bazan iya motsawaba adnan ka kira inna taxo ta kama afnan sannan ka kira iyayen nafi yanxu maza maza Hannun adnan din na rawa ya kirasu sannan ya taimakama Inna suka fice da afnan daga Dakin aka shafa mata ruwan sanyi ta farfado saidai bata cikin hayyacinta Ana Kiran sallar magrib iyayen nafi suka iso adnan yai musu rakiya har izuwa Dakin da akwatin yake Gaba dayansu sun shiga tashin hankali sai kuka suke mahaifiyar nafi kuwa sai tsine ma nafin take tana fadin kada allah yai mata rahma a cikin kabarinta Adnan ne yasa masu daukar gawa sukaxo suka dauki gawar alhaj muftahun aka nufi makabarta da ita inda masu gadin gidan sukai musu rakiya Aleeyu kuwa na bangarensa ciwon zuciya ta tirnikeshi ganin abin na gaba yasa ya sureshi sai asubiti Mu hadu a next chapter Sannan inason na sanar daku cewa banson. Yawan complai. Da yawa daga cikinku sai Kaga anacikin lbr sai su dinga tambayan ya akai ba,ai guri kaza ba Meya faru da wane kaza. Duk irin wadannan tambayoyin ba qaramin. Cimin tuwo a qarya yakeba. Kamata yai ku bari a Gama book din duk inda kukaga ba!a taboba ta Zaku iya complai akai ba,a ana cikin tsakiyar lbr ba don allah a gyara Sannan masu qorafi Akan ba,a musu post da wuri inason su sani Admin nada aikinyi. Akwai week din da zakuga gaba daya week din da safe nake post to wannan week din ina off kenan banida aiki ina hutu shiyasa nakeyi kullun da sassafe Akwai kuma week din da sai yammah koda dare nake post to wannan week din admin na cikin aiki ne. Don bazan aje aiki naxo ina muku post din da bakwa comment ba yess Don. hak sai kuyima admin uzuri Naku har kullun Aure. Kan. Aure Chapter40 Bayan adnan din ya tafi da Abban nasa asibiti Ita kuma afnan ibrahim yaxo ya dauketa Amman ya rasa kanta kuma taqi fada masa abinda ke faruwa Lallashi kawai yake da nasiha. Washegarima da zazzabi ta farka mai tsanani hankalin afnan ya Gama tashi Dakansa ya shiga kiscin ya hada mata abinda zataci Don yanxu ya soma qarewa kasancear shga kicin din da suke tare Ta kasa Kai komai bakinta ibrahim ya rasa inda zai saka kansa Don haka wajen qarfe sha biyu na rana ya soma shirye shiryen kaita asibity amman taqi don haka yasa nurse don taxo ta dubata Tana kwance a falo ya tasata a gaba wani Lokacin har hawaye yake sharewa zuciyarsa ta Gama karyewa Don haka yaranma nasa suka sasu a gaba sukai tsuru tsuru Duk abinda suke idon Maryam na kansu. Yau dai tayi kuka harta godema allah Yaddah taga mijin nata ya lalace a gindin mace tace tir da irin wadannan mazan Har wuqa ta dauka zata cakama kanta sbd tsananin kishi ta kasa ta dauko fetir domin ta qonesu kowama ya huta nanma ta kasa. Don haka ta zube a cikin daki tana sharbar kuka Kamar daga sama hajia ta Sanyo Kai falon gaba daya suka dago suna kallonta. Ibrahim yai saurin hanyewa daga jikin afnan din babu ko sallama ta fado falon Yau da alamun tashin hankalin da taxo dashi ya zarta na kullun Afnan kuwa ko kadan bataji irin fargaban da takejiba a duk sanda taga hajiyar don tashin hankalin dake tare da ita yafi gaban wannan Jaridace ta wurgama ibrahim din. Tana fadin karanta nace Ibrahim ya dauka yana duba muhimmun lbrn dake shafin farko Abinda ya gani ya rikita masa zuciya hannunsa na rawa ya Bude pagen farko ya soma karanta lbrn Wanda ya dauki hankalinsa Labarine. Akan gawar da aka gani a gidansu afnan amman babu wani cikakken rahoto bane taqamaimaiba Don ba,a Fadi mai akwatin gawar ba Ibrahim ya rufe jaridar gamida maida kallonsa kan afnan din data tashi tana gaishe da hajiyar tasa Tace. A,a riqe gaisuwarki yar mayu kada a lasheni daga gaiSuwa Nidai rokonki nake daki sakarmin kurwar da haka don kuwa shi kadai ya ragemin Afnan din batace mata qalaba ta koma ta kwanta idanunta suka ciko da qallah Ibrahim ya dubeta tausayinsa ya kamashi baisan Lokacin da yakai hannu ya kamo nataba muryarsa na rawa yace ashe wannan ne abinda kike boyemin afnan? Ashe har yanxu kina tunanin ban cancanci ace nasan sirrinkiba ko afnan? Idan har da rai wata rana zan cancanta kuma bazanyi Fushi dakeba koda kuwa da wata manufa kika aikata hakan Nidai nayi miki alqawarin kareki na kare mutuncinki da damuwarki. Kamar yaddah nai alqawari koda kuwa ace Kece maiyyar mai cinye naman mutane Nayi miki alqawarin naman jikina ki cinye zakifi Jin dadinsa Fiye da ko wane irin nama Afnan ta zame hannunta ta miqe da zummar ta share masa hawaye Kukan hajiyar tasace ya tsayar da ita kira take na shga uku ni indo Shi kenan ta Gama lashe min kurwar yaro To inaso ka sani saika saki yarinyarnan yanxu yanxunnan kaji na fada Maka Wlh koka saketa kokuma na daga Maka nono kaji na rantse don saina tsine maka Ibrahim ya sulale qasa a gabanta cikin muryar kuka yace Kiyi haquri hajia ki yafemin Bazan iya aikata abinda kike umurtata dashiba koda kuwa naman jikina zaki dinga Yanka amman don allah ki yafemin Hajiyar tace na sani wlh ni nasan bayin kanka bane Kuma mayu ba zasu shga tsakanin da Dana ba Ta miqe tana fadin nasan abinda zanyi Maryam tsulum ta fito daga dakinta tana wani irin gunjin kuka Ta nufi inda hajiyar take. Ta tsaya tana fadin Wlh sai yau na tabbatar dabake kika haifeniba kin nunamin banbanci hajia. Kuma na gode Damuwata ba wata mai yawa bace kika maida ita gaggaruma. To yayi daidai sai yau na amsa sunana marainiya mara uwa da uba na rasa gata banida madafa Don haka zanyi yaqina Ni kadai tunda ni ya shafa ta juya ta koma falon nata hajia na Kiran sunanta amman tai banza da ita don haka itama hajiyar ta fice daga gidan cikin bacin rai ZUCIYAR ibrahim gaba daya ta Gama cunkushewa yaji a duk duniya idanda abinda ya tsana bai wuce Maryam ba Shidai duk yaddah hajia ke takura masa to bai yaddah wani ya rainataba Yaddah afnan taga ibrahim nata dawainiya da ita yasa ta rage damun dake ranta Don haka harta samu daman shga kichinn domin hada masa abinci donta lura har kalacin safe bai samu yayiba Indomie dakwai take dafa masa tana cikin bare kwan Muryar ibrahim taji yana kwala mata kira da wata irin Muryar da batasan yanada itaba Da sauri ta waiga saidai kamin ta Gama waigawar taji an hankadata can gefe. Faduwar tayi daidai da kwala qarar da ibrahim din yayi Anan afnan ta Bude idanunta domin tantance abinda ke faruwa Maryam ce tsaye riqe da sharbebiyar wuqa sai digar jini take Tuni qirjin afnan yahau bugawa Ta rarrafa inda ibrahim din ke zaune jini sai malala yake Kamar an yanka dabba daga gefen cikinsa Tuni har idanuwanta sun juye wani irin numfashi yake fitarwa Wanda ke girgiza gangar jikin nasa Afnan ta daura hannu aka gamida Kurma wata uban kururuwa mai rikitarwa. Mustafa dake shirin faka motarsa ya fito a guje ba tare daya Gama gyara fakin din motar ko kashewa ba Maryam na ganinsa ta saki wuqar tana fadin wlh bashi nai niyyar kashewa ba shigowa yayi ban ankara ba Mustafan bai tsaya Jin komaiba ya kimkimi ibrahim din Wanda har yanxu bai daina zubda jini dake jikin nasa ba Yai waje dashi ibrahim tabi bayansa a hanzarce hannunta aka sai kururwa take Mustafa ya rude Yama rasa asibitin dazai kaishi. Ga wai irin numfashi fitar rai ra ibrahim din keyi Don haka Mustafan ya kira iyayen ibrahim din ya sanar dasu bai zame ko inaba sai asibitin aminu kano Sbd yanada aboki likita a asibitin Yana tsayawa motar mahaifin ibrahim din na tsayawa Don haka basu jira aka basu keken tura marasa lfy ba suka sureshi sukai cikin asibitin dashi Doctor faruk ne da ducto lawal sukai musu Iso zuwa Dakin da za,a kwantar dashi Basu bata mintina gomaba suka shirya wajen fara aiki Akansa Tabbas su kansu likitoci. Sun sadakar da rayuwar ibrahim din Don haka likita guda ya fito daga Dakin ya sanar dasu cewa suje su laqanta ma dansu kalmar shahada abinda. Ya fada kenan ya wuce Har rige rigen shiga Dakin suke Daqar alhaj ya iya kallon halin da dan nasa ke ciki Gefen inda Maryam din ta farka da wuqa yayan hanjinsa sun zubo da alamun kuma Wasu yayan hanjin nasa sun daddatse Afnan ta kifa kanta da nasa tana wani irn kuka mai tsama zuciya. Ta laluba hannunsa ta matse da nasa tana Kiran sunansa Alhaji kuma ya qarasa kansa yana Tofa masa addu,o,i hajiyarsa kuwa ihu take kawai tana buga kanta da bango Don haka ma,aikata sukai waje da ita Ibrahim baisan inda kansa yakeba Can Jikinsa ya saki idanuwanta suka tsau kyam! Mahaifin nasa yasa hannu ya shafi idanuwan nasa suka Rufe Mustafa dake tsaye a bakin qofar Dakin yana wani irin kuka kamar qaramin yaro. Yana ganin mahaifin ibrahim din ya shafi idanun nasa ya fita daga Dakin a hanzarce Afnan bata ankaraba saidai gani tai mahaifin nasa yaja bargon dake gadon ya lullubeshi Idanuwanta suka tsaya kyam Akan mahaifin ibrahim din tasa hannu tana rufe bakinta Wasu irin hawaye masu zafi sunabin idanuwanta Babu inda ke motsi a jikinta sai labbanta dake rawa gaba daya ta gaza furta abinda takeson fada Mahaifin nasa cikin dakiyar zuciya yace ya rasu afnan Kullu nafsin za,ikatul maut duk mai numfashi saiya dandan Innalillahi wa-inna ilaihirrajiun kawai ta iya Furtawa ta Fadi Nan a sume zuciyar mahaifin ibrahim din ya kuma dugun Zuma cikin tashin hankali yake Kiran DOCTOR. DOCTOR. DOCTOR Hmmm jama,a wai Kuna daukar darussa a cikin wannan book din kuwa? Karku damu baifi mu qara post biyu ko ukuba zamu kammalashi Naku har kullun Aure. Kan. Aure Chapter41 Da sauri nurses suka shigo aka taimakama afnan din ta farfado shi kuma ibrahim din. Motar abulanc ce taxo ta daukeshi I zuwa gidan mahaifin nasa inda anan za,ai masa sallah. Babu inda ke motsawa a jikin afnan din sai labbanta Kuma ta gaza furta abinda takeson fada Kowa ya kalleta yasan bata cikin hankalina cikin kuka tace yanxu ibrahim ya fanshi raina da nasa kenan Maganganun daya fada mata jiya sune ke mata yawo a kwakwalwa Afnan raina fansane a gareki abin kaunata. Jinina da jikina duk mallakinkine. Afnan motsina da tunanina duk Nason ganin biyan buqatunkine Ta lumshe idanunta inda Wasu zafafan hawaye kebin kuncin nata duk Wanda ke wajen ya tausaya mata don haka kowa sai lallashina kawai yake Ta runtse idonta maganarsa ta jiya ta dawo masa inda yake cewa. Ashe daman wannan ne abinda kike boyemin afnan? Ashe daman damuwarki ba zata zama tawava? Ashe har yanxu kina ganin ban cancanci da nasan sirrinkiba? Idan har darai wata rana xan cancanta kuma bazanyi Fushi dakeba. Koda kuwa da wata mafita kika aikata hakan Nidai na miki alqawarin kareki na kare mutuncinki. Da damuwarki. Kamar yaddah nai alqawari koda kuwa Kece mayyar. Afnan nayi miki alqawarin naman jikina ki cinyeshi afnan zakifi Jin dadinsa fiye da ko wanne nama Ba tare da bata lokaciba mustafa ya kira yan sanda ya sanar dasu abinda ke faruwa ba tare da bata lokaciba suka dira a gidan inda sukai sa,an kamata a daidai Lokacin da take shirin guduwa Bayan sati guda da rasuwan ibrahim kotu ta yankema Maryam hukunci gisa. Ta hanyar rataya Ita kuma hajia iklima mahaifiyar ibrahim din kasa Gano kanta sukai a asibitin. Wani Lokacin ta zura a guje sai an kamota Wasu lokutan kuma taita sumbatu Kai da abu yaqici yaqi cinyewa gidan mahaukata kawai aka kaita kasancear abun nata qara gaba yake Mahaifin afnan da kansa yaxo ya dauketa inda ya maidata gida a Nan zatayi iddar ta. Abun kamar wasa wai itace ta dawo gida take takaba Daga ita sai inna sai ma,aikatan gidan da yan yaranta. Sbd adnan ya wuce qasar Egypt donyin wani kwas harna wata biyar Akan abindaya shafi kwakwalwa Aleeyu kuwa siyasa ta karato don haka kamfen kawai ake a Karo na uku kenan yana neman kujerar na gwamna baya samu yanadai kyautata zaton wata qila a wannan karon a dace ne. Saidai abindaya faru yafi komai dagula masa kwakwalwarsa don kuwa abokan hamayyarsa amfani suke da wannan damar suna. Masa terere Don haka shi kuma ya daura damaran gyara lamuran nasa ya kira yan jarida. Dake zaryar Jin gaskiyar lamarin ya dauko musu. Tarihin komai tun daga kan janar. Har zaman kotun da sukai zuwa ganin gawar da akai a gidansa Don haka yan jarida suka watsa lamarin mai makon yai baqin jini saima sake samun daukaka yai a wajen al,umma Lallai ya zamo cikin mutane masu gaskiya da taimakon Al-ummah. Don haka ko ina ya gota sonsa ake Wandama basu sanshi daba yanxu sun sanshi Afnan ta kammala takabarta don haka ta koma bakin aikinta Saidai har I Lokacin zuciyata vata natsuba Anyi zabe an kammal don haka aleeyu musawa ya

Chapter 15 of 16