Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kuwa duk suna falon gabaa daayaansu Kai tsaye idonsaa kan kausaar yai Zuciyaarsa ta tsinke daya lura shikenan sun haramta ga juna kenan Jinda yai ana fadar ah aleeyu ne yasa yai Saurin dauke idanunsa yaa shiga yana nine momy Suka gaisa sosai shida mommyn da daddyn baayan sun Gama gaisawane Daddyn yace ai saiki kaishe can falon baaqi ku zantan ko Cikin zumudi tace taso muje tashi kawai yai ya bita ba tare da yace komaiba amman hankalinsa da Tunaninsa nakan kausar Bayan sun fitane daddyn yake cewa a wani sbn bank da za*a Bude kwanannan na samar masa aiki. Zai zama manajan bankin Momyn tai murna sosai A falon ya sameta ta saki wani irin murmushi Tace yauwa nawan kokaifa idanunka sunfi komai daukar hankali Tadanyi shiru kamin tace nasan badaa son raankaa ka kawomin wannan ziyarar ba To amman ba yaddah zakai yaddah na ganka yau haka nakeson ganinka gobe jibi Kullunma ka gane ko? Idan bakazoba to ni zanzo kuma ko gabansuwa kake to Saina baka kunya Tunda na lura kai komima kunyarsa kakeji Sannan idan daddy ya tambayeni ina zanje ko ina naje nace masa kaika kirani kace naje na sameka Kallonta kaawai yake dan Kwata Kwata baya hayyacinsa Dan haka yabarta tanata zuba kusan awa daya sai surutu take ko qala baice mataba Saima tashi da yai yace zai tafi ta riqeshi wai a dole saiya qara jira Saida yai da gaske ya samu ya zame ransa cike da baqin ciki Ba yaddah zaiyi dole yasama ransa sa,ida Allah yasa hakan shiyafi zama ailkhairi Ba yaddah ya iya haka ya dinga jera kwanaki kullun sai yaxo Ya samu aikinsa dan harya soma zuwa office Sun bashi gida qato tsaraarre tare da wata mota mai numfashi ta banki da miliyoyin kudi domin wanke talauci Momy tasa amarya tare da kausar Akan suje su gaishe da iyayen aleeyun Momy ta shirya musu tafia harda aleeyun da tsaraba Na kece raini Direban Gidan ya daukesu a mota sai garin musawa a jahar katsina unguwar saniyawa Tunda suka hau hanyar qauyen naafisa ta dinga waige waige Can dai ta kasa daurewa ta dubeshi tace Tace kai aleeyu wai yanxu mutanene ke rayuwa a Cikin wannan dajin kauyen? Tambayar tata ta bigi zuciyarsa tazo masa wuya Yai wata murmushi da za* a iya kira da yaqe yace A wannan dajin kauyen da kika gani mahaifinki yai rayuwa tun yana dan shekara sha biyar har yakai ashirin Tsit tai tankar ruwa ya cita amsar tai mataqar yima kausar dadi Dan ko banza yayi maganin iskancinta Aure kan Aure Chapter4 Tunda suka hau hanyar qauyen naafisa ta dinga waige waige Can dai ta kasa daurewa ta dubeshi tace Tace kai aleeyu wai yanxu mutanene ke rayuwa a Cikin wannan dajin kauyen? Tambayar tata ta bigi zuciyarsa tazo masa wuya Yai wata murmushi da za* a iya kira da yaqe yace A wannan dajin kauyen da kika gani mahaifinki yai rayuwa tun yana dan shekara sha biyar har yakai ashirin Tsit tai tankar ruwa ya cita amsar tai mataqar yima kausar dadi Dan ko banza yayi maganin iskancinta A qofar Gidan nasu direba yai parkin suka sauka nafisa sai bin lungun Gidan nasu da kallo take Yai gaba yana kuzo mu shiga yai gaba suka biyoshi a baya Ba laifi Gidan shafaffene da siminti da hanzarinta innan tasa ta taSo tana sannunku da zuwa maraba da Manyan baqi Ku shiga daga ciki Kowa ya cire takalminsa amman nafi taqi da nata ta shiga Dakin sai kamshi yake ga saitin kujeru Kausar ta zauna daga qasa nafi kuwa ta dare kan kujera ta daura qafa daya kan daya sai kadasu take tana taunan cingam Aleeyu bai shigoba dan yana waje suna magana da inner tasa Kausar ta yafitota murya qasaqasa tace dan Allah sauke qafafunnan naki anty ki cire shoes dinnan babu dadi wlh Taja wani gajeran tsaki tana fadar har Wasu tsofaffin kirkine da zan Guji bacin ransu A wace tashar ake nunosu ko a wace jaridar ake bugasu? Ta qarajan wani dogon tsaki tana Kada ki kuma batamin rai Bata sake magana ba Sbd tahowar innar Baqi hansha hanya ya aka baro iyayen? Duk kausar ne ke amsa Mata sannan direba ya gaisheta Saida suka Gama gaisawane sannan nafi tace ina yini? Lfy lau ta amsa tana tambayarta ya hanya Inna ta dubi Direban tana wacece sirikar tamu? Yai murmushi ya nuna Mata nafi sai taga makar kausar ya nuna Mata dan haka fara!ar tata ya qaru Dan ta yaba da natsuwar kausar din Inna ta miqe ta kawo musu burabuskon alkama Wanda tai musu da miyar kaji Abinci sai qamshi yake aleeeyu ya kawo musu lemuka da robar ruwan swan Sannan yacema Direban da ya taso suje suci nasu a can Dakin tsohon nasa Kausar ta dubita tace sauko mu dan taba abinnan kar muqici ba zasuji dadiba Da wata harara ta bita tace nice zzanci wannan abincin?wato kwalara ta kamani ko? To bazanciba in sunxo sun iske bamuciba haushi e kashe su Bata sake maganaba kausar din ta sauka ta zari flate ta zuba burabuskon dadin abin ya ratsata nanfa ta zauna ta cika cikinta Da suka Gama inna ta shigo domin tattara kayan Kausar tace barshi dan Allah mama bari zan tattara Inna tace kekam barshi dan Allah yarnan keda kukaxo baqunta Tsalam sukaji murya nafi na fadin kekam ki barshi ta kwashe mana Kinfa cika naci Kamar tsohuwa Kausar taji kalaman nafin tamkar saukan ruwan zafi tace a,a inna barshi Barshi ai nayau ne kawai Dan haka ta kyaketa Ta tattara taje ta wankesu tas Bayan ta Gama ta nufi Dakin nafi ta bita da harara tana fadin to ayawo Ina kikaje a wannan garin me kama da bola? Bata tanka musu ba Sbd inna na Dakin kausar ta qosa su Tafi Sbd yaddah nafi keta kwabasa musu kartai abinda zatasa a zagi iyayensu Tai sa,a kuwa aleeyun ya shiga yace kuxo mu gaishe da malam gashinan ya shigo saimu wuce Kar muyi dare a hanya inna tace a,a su bari ko sallah sayi ko? Basuce komaiba suka wuce kausar ta duqa har qasa tana gaida malam Nagartaccen dattijo Nafi ta qare masa kallo tace a xuciyarta ashe aleeyu shi ya biyo kyakkyawan dattijo Tamkar shi e kansa Ya maida hankalinsa kan kausar dan yayi zaton ko Itace sirikar tasu Nan yai musu addu,a sannan kausar tai sallah Bayan sun kimtsa aleeyu yasa direba ya shigo musu da tsaraba sannan Sukai sallama Suna kan hanyane kausar ta dubi aleeyu tace Kai yaya aleeyu ashema garin nake ba wani kauye bane sosai aini ina sha,awar irin wannan garin Da ace nan zaku zauna da babu abinda zai hana na dinga zuwa muku hutu Ji Sukai tace kan abinda malam ya hana ta ta kundumo Mata wata Ashar tana fadin kausar me kika maidanine? Kina nufin a kawoni wannan takurarren garin Ammman baki qaunata duk garinnan ina kika ga yai miki kama da inda za,a sakani? Allahi ya kyauta nai rayuwa cikin gidadawa yan kauye jahilai Karki sake maimaitamin wannan kalaman Inba so kike ranki ya baciba dan nida garinnan har abada Shiru kausar tayi dan abin yamafi qarfin tunaninta Shikuwa aleeyu takaicine ya Gama kumeshi ji yake tamkar ya maqureta ya huta Yace Aransa anya tasu zatozo daya kuwa Ansha biki amarya ta tare a katafaren gidanta Lokacinda iyayen aleeyu sukaji ba kausar bace amaryar abin bai musu dadiba saidai babu yaddah suka iya Rainin hankalin nafi sai qara gaba yake sam bata ganin mtuncin iyayensa Da danginsa ko kadan shiyasa yanxu dangin nasa baSu cika kawo masa Ziyara ba Tunda akai auren shekara biyu kenan bata taba zuwa gaishe da iyayensa ba Yayi nacin har ya gaji Yan,uwa har an fara yi dasu jowa yasan baiyi sa,ar mataaba Daya samu lbrn iri wulaqancin da takema danginsane Yaxo yai Mata tatasa shinefa yanxu idan sunxo take barinsu suna shiga Gidan ammanfa zasuga wulaqanci hardana bugawa a jarida Ya Bude idanunsa wandanda suka rine tamkar garwashin wuta Ina amfanin rayuwa da macen da batasan darajar iyayen Mijinta da danginsa ba da wadannan tunane tunanen har Barci ya kwashesa Saida aka kira Sallar asuba sannan ya samu damar miqewa yai sallah sannan ya fara shirin tafiya office a sashin saukar baqi ya samu kwaggon nasa inda yake musu bayanin yanxu Zai hadasu da direba Wanda zai kaisu kasuwa ya siyo musu duk abubuwan da suke buqata daganan ya kaisu tasha Su hau mota daganan ya ciro kudi masu yawa ya miqama kwaggon yace ga wannan kui kudin mota da tsaraba sannan ku riqe Wasu a wajenku Godia suka dinga masa kwaggo harda kwallan farinciki Sannan yai musu sallamaa ya wuce office din nasa Misalin qarfe goma na safe nafi ta farka daga barcin da take Kai tsaye toilet ta nufa ta watsa ruwa sannan tayo qasa domin yin break Bayan ta zaunane take kwalama ladidi kira da saurinta ta qaraso tana gani hajia Tace Meye da meye anan? Ta fara lissafa Mata tadan yamutsa fuska kamin tace zubamin dankalin Ad sandwich a gefe Ta amsa da to Bayan ta Gama ta fice Kamar daga sama taji ana knocking Tace hu is knocking Sorry sweety taji an fada ta miqe da sauri tana fadar Am coming my dear Ta meqe da sauri ta Bude Dakin tana budewa suka maqale juna tana fadin am Sorry sury Amman fa nayi matuqar farin cikin ganinki Tana fadin sury Wlh yanxu shawarar tafiya gidanki nnake dan Nayi mising dinki Wlh ki yarda dani Surayyah ta zame hannunta tana fadar ke ni rabu dani mayaudariya kawai Wlh afi baki sona dole na Nemo mai debemin kewa Mata da yawa sunamin tallar kanki ammman naqi nace dole saike wai don kawai kar naci amanarki Amman ke ko a jikinki Nafi tace ba haka bae hajiya surayyah kin ganene mijin nawane bai barina ina Hutawa Wata harara ta watsa Mata tace sannu mai miji Aini kaina da nawa mijin nake wannan harkar Bama miji dayaba Bari na fada miki wani sirri ba miji daya gareniba ni matar Soja ce kuma matar chirman Nafi tace ban ganneba sury fahimtar dani Saida taja wani dogon murmushi kamin tace tun daman can asalina yar qarin bauchi ce Acan iyayena da kakan Nina suke Ni kadai iyayena suka haifa kuma suka gani inngattacciyar tarbiyar Arabi data boko Bayan na Gama digirinane na hadu da wani Soja mai suna auwal Soyyah ta shiga tsakanina dashi har manya sukasan da zancen aka daura mana aure Kwatsam aka canjama auwal aiki zuwa qasar inugu Ni kuma na nace sai na bishi can Shekararmu daya acam daganan aka turamu Lagos wani qauye Anan muka zauna na saba da mutane harkar duniyata kawai nasa a gaba Ke har maza nnake kawowa Gidan nawa Garine da ba ruwan Kowa da kowa Kwatsam rannan aka tura mai gidana wani cose a qasar amurka Na shekara biyu ya shirya yai tafiyarsa Ban damuba dan inada masu debemin kewa A haka na hadu da manyan mutane can gida kuwa babu masu ziyartata dan nayi nisa Saidai idan nine ke keson ganinsu naje na hada musu sha tara na arziqi A haka na hadu da wani dan siyasa mai rike da muqamin charman Na lokal government dan asalin garin kano ne Saidai shi bada watsewa ya nemeniba dan duk a zatonsa ni budurwace A haka ya nuna yanasona da aure na amince na nuna masa nida Mahaifiyatace kawai a gidanmu Yasa ranar da zaixo ya gaisheta Muka hada baki nida matar da nake haya a Gidan nata Na tsara Mata yaddah nakeson abin ya kasance ta amince Kabir umar yazo shida abokansa suka gaishe da matar a matsayinta na mahaifiyata Suka bata maqudan kudi Muka hada baki da wani dattijo Akan ya tsayamin a matsayin qanin mahaifina ya amince na biyasa aka dauramin aure da wannan charman din aka dauko Amarya surayyah aka kawo garin kano Shekara uku kenan da aurena da chirman ina zuwa akai akai ina gaida iyayena Shima Alhaji yana zuwa gaishe da wannan matar data tsayamin a matsayin uwata Shi kuwa mijina auwal. Soja mijina na farko har yau bai dawoba saidai Duk qarshen wata ya turomin da. Rabin albashinsa ni kuma naita wadaqata Yaddah nakeso Dan yanxu sai muyi wata bamuyi wayaba Yar iskaceni? Da yanxu inacan a jibge ina jiran gawar shanu Dawowa ba rana ba lokaci Nafi ta jinjina kai tace lallai surayyah kin cika gawurtaCciyar yar duniya Aure kan aurefa kenan kikai?'' Tace so wat inban morema duniyataba yanxu hajiya Nafi to sai yaushe Zan more Gani yanxu ina hawa manyan motoci Na mallaki manyan gidaje ina shga manyan store na ratsa contry din danaga dama Sannan ina tare da manyan yan gwamnati Inda bani dasu koke ba zaki yarda na rabekiba Cikin satinnan na lunco manya manyan jeef baqaqe guda uku Da wata. Shantaleleliya fara da naga akaimin odersu gada ingland Na zuba escot har sha shida ina tafe ana min jiniya duk inda na shiga girmamani Ake Nafi tace kai dan Allah hajiya surayyah meye sirrin fadamin naji? Sani hanya yar uwa Sury ta riqe baki tace waceni da daura zanin uwar miji Ai ina tabbatar miki da bazaki iyaba mumabar wannan zancen kawai Nafi tace haba hajiya Sury kinsan babu harjar bakin ciki tsakaninmu Fadamin ko meye Wlh zan iya Inhar zan samu dukiya na tara na sai manyan motocin da duk inda na gifta zan dinga jamyo hankalin jama,a Kowa ya rinqa girmamani Sury ta dafa kafadarta tana kin samu yar uwa inhar zaki iya Ni kuma zan kaiki har bakin rigiyar da zaki dinga zabaro kudi Zaki zama miloniya Cikin kwana daya Ta maqalqale surayyah tana fadar Na gode aminiyata dan Allah fadamin ta wacce hanyace Sury ta girgiza kai tace kwantar da hankalinki bazan tonama kaina Asiriba kizo ki watsa min qasa a idoba Kice ba zaki iyaba Kwara na kaiki gindin abin yaddah baki isa ki kubce ba Wata yar dariya ta sake sakawa ta qara rungume surayyar Suka fara aikata masha,ar tasu Daga qarshema miqewa Sukai suka haura sama dan faga inda suke yan aiki na iya Giftawa su kansu a kowane irin lokaci Sai Bayan sallar issha,i Sannan suka rabu da niyyar gobe zataxo ta dauketa dan kaita inda rijiyar kudin nasu take Cikin farin ciki Nafi take danji take tamkar tayi kudinma tagana Dan harta fara hangi kanta Cikin manyan motoci Kekekekekekekekekekekekekekek duniya ina zaki damu Hm lol. Nafi dai toh badai zance komai ba AURE KAN AURE Chapter 5 Aleeyu bai dawo gidansa daga gurin aikiba Wucewa yai can gidansu nafin acan Sukai sallar magrib da isha,i Anan ya samu ana Maganar auren kausar ya samu anayi nanda sati biyu Ita da wani controler na Custom ta gama digirinta kuma ta fito da kwali mai kyau Hira suke sosai Ita da aleeyun nata mommy kuwa harkarta kawai take Ta numfasa tace kasan kome zaka siyanmin yaya aleeyu? Tacce yauwa kaha inason kayannan wadanda ake tallansu na chaina Tace dan Allah ka taimaka ka siyamin irinsu yayana Wlh babu irinsu a. Naija Yace lissafo inajinki Tace akwai wata gas cooker da vegetable marchne sai warmer Nandai ta lissafo masa duk abubuwan da take buqata yace karki damu akwai wani abokina da Aikinsa kenan shigo da kaya zan bashi. Sai ya siyo miki Wani qara ta saka tana murna tace na gode yaya Wlh naji dadi shi daddy wai komai saidai a siyamin anan qasa naija Yace kema ai nasha zakiso haka yaddah kike fadin kina kishin qasarki ta hausa Da al,adun malam bahaushe shiyasama kika karanta hausan har kikai Digiri akai Tace baka gane bane yaya ni inada burin nai aure na ganni a qaton kichinne na Hada wannan na sarrafa wancan Kullun mijina ya dinga ganin abubuwan da baimasan dashiba na dinga qirqiran Abubuwa kala kala Wanda a lokaci qanqani sai kaga na siye hankalinsa da tunaninsa koba hakaba Wata irin daria ya saka shida momyn nata Dan basu taba tunanin kunya irinta karsar zata iya furta hakanba Aleeyu yace ke kausar ashe kema kin iya haka kike nunama mutane salihanci? Rufe idonta tai ta tashi da gudu. Ta nufi dakinta wai Ita ta tunaninta bata dauka wannan Maganar Rashin kunya bace Aleeyu ya dubi agogon hannunsa yaga har goma saura hakan yasa ya miqe yaima Momy sallama ya nufi gidansa Nafisa kuwa duk ta shiga damuwa. Na rashin ganin nasa Tundaya tafi office bai kirataba inta kira baya picking tai masa text yaqi reply Tace why har yanxu bai huce bane batasan aleeyu da riqo ba saidai saurin fushi Tun Bayan magrib take jiransa har qarfe tara hakan yasa ta Miqe dan gani tai kwalliyar tatama ai ya tsufa ta cire kayan ta hade Cikin wata hadaddiyar rigar barcinta Wanda ake ganin komai na jikinta Kai tsaye Dakin nasa ta nufa Ta haye kan lumtsatstsen gadonsa ta rufe jikinta da bargo gamida Rungume filo tana lallatsa waya Kamar ta sani sashin nasa kuwa ya nufa dan daman kausar ta rigada ta cika masa Ciki da abinci hakan yasa bai tsaya neman komaiba ya fado Dakin nasa yana ganinta a kan gadon nasa sai yai Kamar bai Gantaba ya nufi. Bathroom ya watso ruwa Bayan ya fito ya Saka kayan Barci ya kintsa Tayi tunanin zai waiwayeta amman ina saidai gani tai Yaja filo abinsa yana qoqarin kashe wutan Dakin a zuciyarta tace wai mai yasa aleeyu ke Mata hakane duk ajinta amman ace wai itace kebin namiji Jitai tamkar itama ta kyaleahin amman Ina sonsa da kaunar kasancewa dashi ba zasu bartaba Hakan yasa ta mirgina ta daura kanta saman kirginsa muryarta tamsar wacce zatai kuka ta kira sunansa Tace yaya aleeyu dan Allah kayi haquri karka horani ta wannan sigar na Yarda kaimin duk wani irin horo amman karka dinga horar dani a irin wannan lokacin da nake Cikin tsantsar buqatarka Bai tanka mataba dan baima da alamar magana hakan yasa ta Lumshe idanunta tana kising dinsa ta ko ina Aleeyu kenan jarumin maza amman bata wannan sigar ba Dan haka ya bada kai bari ya hau tuni aka manta da haushin da ake da ita Washe gari saida yai da gaske ya kwace daga jikinta dan Nema take yai latti Tai saurin fadawa toilet yai wanka ya shirya Ya aje Mata kudinda shi kansa baisan yawansu ba ya fice a tsaitsaye yayi break Yaja motarsa sai office Lokacin data saba farkawa a daidai lokacin ta farka ta fito ta fada toilet Ta hade Cikin wata hadaddiyar atamfa An Mata dinkin rapper ta saka wani dankunnenta na gold da yar siririyar sarkarsa Tayi kyau matuqa ta dauko jakarta da takalminta duk iri daya ta saka tayo qasa Itama bata wanni tsaya tayi break din kirkiba ta zari makullin motarta da daddy yasai maata Fara qal tasa akasa Mata baqin glass wato tintec Da sauri sauri ta fita dan gani take Kamar surayyah zata bata Mata Lokaci da kanta taja motar ta nufi birgede anguwar da surayyar ke zama kenan Hankalinsa ya tashi ganin yaddah aka hade gidaje wajen bakwai aka maidasu gida daya. A wawakeken gate din ta tsaya inda masu gadi sukazo suka Bude gate din saida tai tafi a ya kusa na mintuna goma Sannan ta isa inda aka tanazar domin aje motoci ta faka Jeep jeep din data gani sune sukafi komai daga Mata hankali ko waanne yafita tsawo dan har matakala garesu Tozalin da tai da farar jeef din shine yafi komai tsnka Mata zuciya Duk motocin sababbine qal ga Wasu sucurities nan a tsaytsaye harsu. Takwas Kowa duk sunsha kota da Wasu baqaqen glas nasa kai da niYyar tafiya daya daga cikinsu yasha gabana yace madam lfy? Na kureshi da kallo daan tsoroma ya soma bani bance masa komaiba na ciro wayata na kirata bugu daya biyu ta dauka Nace tawaas gani a gate securities sunqi Barina shiga kixo kimin jagora Kashe wayar tai Cikin hanzari ta manna Baqin gilashintaa Tayo waje Ta wuce faluka sunkao goma Sannan ta fito suka maqalqale Juna nace kai hajia surayyah haka gidanki ya koma wane matsayi chirman Ya kai da har kukaa samu wannan daukakar? Tace charman kodai surayyah ai rigiyar kudinane ta gyaramin wannan Gidan da kike gani Rigiyar nacan Cikin wani boyayyen falona na sirri muje idan muka dawo zan nuna Miki Tace da motarki kikaxo eh nace Mata tace to muje nace nata a,a hajia Aini qagara nai naga na daana wadannan jbga jbgan motacin? Tai daria tace sha kuruminki indai wadannanne Cikin satinnan zaki iya aje kamarsu A gidanki yanxu haka sirrin inda kudin suke nakeson na kaiki Dan ni kadai nake zuwa ko security daya ban dauka Nafisa tace to mu qarasa ko sun kusa isa inda motocin suke masu tsaronta duk suka zaburo Ta daga musu hannu tace ku dakata ba wani nisa zanba babu matsala Sukace Owk hajia a dawo lfy Nafi ta shiga mazaunin direba Itakuma surayyar ta zauna a Gidan gaba Duk tsiyarka da naci baka isa ka Gano ko suwaye a Cikin motarba shiyasa aleeyu ya tsani motar Ita kuma taqi ta cire tintec din Tafia mai nisa surayyah ta Nina Mata wata hanya suka karkata Wata anguwa suka shga waddah bata da cikowar mutane A haka har suka. Shige Cikin wani kuntsurmin daji Har Nafi ta soma tsorata tace wai hajia har yanxu bamu qaraso bane? Nafa soma tsorata Surayyah taja wani dogon murmushi ta zare gilashin idonta tace amshi saka Haska idanunki can sama zaki hango wani katafaren gida Aikuwa tana kallo ta hangi wani qatom gida mai doguwar katanga Surayyah tace to kiyi fakin a wajen ai ko Ba musu ta bakin a daidai wajen Suka fito Sukai Cikin gidan Gaban Nafi dai bai daina faduwa ba tana tsoron kar ace Ita za,a maida Kudin Don dukiyar surayyah ta soma tsoratata Wani katon falo suka fada Wanda babu komai a cikinsa a qawatashi da. Manyan Tiyils Tundaga qasa har bangonsa amman babu komai a cikinsa Surayyah ta dubi Nafi tai murmushi tace To yanxu saimu cire kayanmu dan sai mun cire kayanmu zamu iya shiga Dan ba,a shiga da kaya Nafi ta zazzaro ido tace wat kut kina nufin tsirara ake shiga? Bata sauraretaba ta fara cire kayan jikin nata saidata cire komai Sannan ta juyo ta Kaloi nafin tana murmushi tace toya kin shirya ko kuwa Nafi ta duqar da kai tai shiru tana tunani... Dan allah kuyi hakuri kwana biyu bana posting wlh wani babban uzirine yasa dafatan kowa yana cikin koshin lpy nagode... Daga naku akoda yaushe... Aure. Kan. Aure Chapter6 Bata amsa mataba ta shga cire kayan jikin nata saida tai tsirara sannan Ta juyo tana murmushu tace yadai kin shirya tai Shru tana tunani bata angaraba sai ji tai suraiyar ta janyota jikinta Ta bita da kis a haka har tai nasaran cire komai na jikin nata Ta jata suka shga wani bangare wanda Babu komai a wajenn sai nnamun daji tuni fitsari ya soma bin qafata Tuni cikinta ya murda lokacinda surayyah ta juyo ta kalleta a lokacin Zawon datake riqewa ya kece mata Dan gaba daya haliTtarta ya sauya jikinta yai wani haske Kamar wutan lantarki idanunta ya zazzaro sunyi jajir A take ta fasa wata uban ihu ta zube a wajen cak ta dauketa tai Ciki da ita Mutanene a wajen dukkansu halittarsu ta koma irinta Sury sun kasu gida biyu. Gabas da kudu Sunsa wani mutm mutumi a tsakiya Gabansa wata qatuwar tukunyace daketa hayaqi Sai Wasu surutai suke Surayyah ta iso ya miko Mata hannu ta mika masa nafin Sannan ta koma gefe inda sauran jama,ar suke ta tsaya Mutumin ya dinga zagayawa da nafin a bakin tukunyar har sau uku Sannan ya ajeta a tsakiyar filin Ya koma inda tukunyar take yana Wasu yan surutai Bayan ya gamane ya fara Kwara Mata kira da karfinsa wata iska na fita daga bakinsa Naafisa Nafisa nafisa ta meqe a gigice tana waige waige kafin ta runtse idanunta da qarfi Ya barke da wata mahaukaciyar dariya kafin yace maraba da zuwa nafi Maraba da zuwa wannan gungiya tamu Da farko muna miki barka da isowa Na biyu kuma sharadinmune na uku kuma albishir Sharadi kuwa shine duk Wanda yazo wannan gungiya tofa baya fita har sai in baya numfashi Inkuwa yace zai bijire mana to abu mai sauqi shine zamu yankashi aljani yasha jininsa mu kuma mu cinye namansa Kuma duk abinda muke buqata saian kawo mana ba,a yin mana gaddama Inkuwa kai to haukataka zamuyi Na uku shine albishir kin nemi duniya kin samu Ba abinda zaki Nema indai kudi na siyansa a duniya ki rasa dan Haka muna miki maraba da shigowa kungiyar @secret society Hankalin Nafi ya soma kwanciya taja ajiyar zuciya qarqarfa da taji ashe ba Ita za,a Maida kudinba Indai har Itace zata samu to aiko ko meye zaata iya Dan haka ta tashi tsam Tana fadan na amince kungiya ta shaida nima na zama yar gungiya abin yai Musu dadi matuqa sukasa daria Mutumin yace Nafi aljani na buqatar jininki Ji tai hanjin cikinta na kadawa ta dinga matsawa baya baya tana neman hanyar guduwa Surayyah ta fito da wata yar qaramar wuqa ido waje Nafi ke kallonta kafin tai wata Wata harta capki tannunta ta yanki fatarta ta tara wata yar qaramar kwarya Bayan ta gama tsiyayan jinin ta saki hannun nata taje ta miqama mutumin Tace gashi sha jini sunan data kira mutumin dashi kenan Ya amsa gamida sa dogon harshensa ya shanye jinin ya fasa kwaryar gamida fasa wani uban qara yace kinxo hannunmu Nafi duk inda zaaki shiga a tafin hannunmu kike Baki isa ki layance manaba dan muna ganin abinda ke cikin Zuciyarki Don haka wa kikafi so a wannan duniyar nafi? Muryarta na rawa Sbd radadin yankar da surayyah tai mata Tace daddy na Ya babbake da wata iriyar dariya kamin yace Yace to muna buqatar jininsa kungiya na buqatar namansa Ta miqe tsaye a gigice tana fadar waye dadin nawa? Wanda yafi Kowa sona a duniya. Wanda yafi riritani a cikin yayansa Yafi sona da Kowa? Wanda ya haifeni yaci dani ya shayar dani Na tsawon wani shekaru ba tare da gajiyawa ba Wanda yaban ilmin da kansa Bazan iyaba inndai hakane na fita.........na fita.......,afi.....'' Dariyar da yake kyalkyata mata Ita ta hanata qarasawa Da hannu ya nuna mutum na farko yace Ba bada matata Ba biyu yace na yayata na bada Na uku yace nahaifina na bada Na hudu yace. Dana na cikina na bada Na biyar yace nima mahaifiyata na bada Akaxo kan surayyah tace mahaifina na fada da kuma Dana nasir Wanda shi kadai na haifa a duniya Akaxo kanna takwas yace ni matata na bada na tara Tace ni mijina na bada Akaxo kan na goma tace Nakai shekara ashirin nida mijina ban taba haihuwa ba Allah yaban ciki na haifi mace kyakkyawa ran suna dodo yace yana buqata ba yaddah Na iya haka na miqata Bayan sungamane akaxio kan uban gayyar sha jini ya daka mata tsawa yace kin ganni nan Uwata ubana matana dukkansu hudu yayyina biyu qannena biyar yayana takwas Uku maza biyar maza duk anan akai kwanjensu dodo yasha jininsu gungiya taci namansu to dan haka ko kinaso ko bakyaso ko kin shirya Ko baki shiryaba. Tunda har kungiya ta buqaci jinin mahaifinki tofa saikin kawoshi Saidai zamu iya baki zabi ki zaba shin naki ran kona mahaifinki? Dan haka mun baki nanda kwana uku koki kawoshi ko kuma dodo yasha jininki Mu kuma muci namanki Dan haka saiki zaba rayuwarki kota mahaifinki Ya fashe da wata irin daria kafin bata ya bace Kowa ya kama gabansa jikinta sai rawa yake sury tai gaba har ta bita ta daga mata Hannu ta nuna mata wata qofa tace na zatabi Cikin tsananin tsoro tace Wlh bazan iya biba sury Suryn ta dafata tace daurewa zakiyi ki runtse idonki kibi inkuwa kikasa tsoro to hanyar wani aljanin zakibi Ya tsotse miji jini Zakiga abubuwan ban tsoro da yawa ki nutsu in kika tsorata to haukacewa zakiyi Ta saketa ta nuna mata hanyar Ita kuma abi tata hanyar Kuka nafin ta saka tace shin wane irin bala,i ne ke tunkarota Lol ni kaina na fara tausaya miki Aure. Kan. Aure Chapter7 Haka ta rintse idanunta Tabi tata hanyar harta fito a gaban motar tata ta hangi surayyah na jiranta cikin Shga ta alfarma da suka taho da ita Da sauri ta dubi. Jikinta ta tuna. Ashefa a tsirara suka shiga wajn Abinda ya gigitata shine kayan dataxo dasu ta gani a jikin nata Hakan yasa ta qara firgita ainun Sury ta Bude mata motar ta shiga ita taja motar da kanta idon nafi a rufe har suka isa saidai ji tai ance. Fito Ta fito sury taja hannunta Sukai cikin gidan Muryarta qasaqasa tace sury kin cuxeni mai yasa kafin muje wajen baki fadamin inda zamuje da sharadinsu ba? Yanxu ya zanyi Surayyah tace haquri zakiyi kibi abinda shajini ya fadi dan ba!a masa gaddama Nasan zakiyi farin ciki nan gaba Nima haka nai ba gashi ina fantamawa ba Ta kamo hannunta ta dinga zagayawa da ita ciki da bai din Gidan tace Dubi gidannan

Chapter 2 of 16