Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
jikin motar tanajin abindake faruwa tace zonana malam Shareta kawai nine mahaifiyarta ga katina kakai masa kace zamuyi magana Godiya ya shiga yinmata ta Shige motar Sannan Shima ya juya A mota kuwa sai fada takema afnan tana fadin in bacin sakaryaba Waya gayamiki irin wadannan manyan mutanen akema wulaqanci Babban mutum Kamar janar har yace yana son lambarki ki tsaya wauta Da sakarci. Mutuminda yadda ake tsare da shugaban qasa Shima haka ake tsare dashi Motocin da yaxo dasu ko gwamna bai hau irinsuba Kowa shakkarsa yake Yana girmamashi wofi dake Kowa na fatan rabuwa da iyayensa lfy ammanke Sai haukar banza kawai kike Itadai afnan batace mata qalaba harta gaji da bambamin fadarta tai shiru Satin adnan shiddah da tafiya Sannan ya dawo Afnan ta shiga murnan tamkar wacce akaima albishir Yana dawowa abban afnan ya damqa masa. Asibitin daya gama Gina masa Murna wajen adnan kamarme Adnan ya fara zuwa aiki komai na tafiya daidai yaddah akeso Da dare misalin qarfe tara afnan na sashin adnan Yana mata wani bincike cikin laoptop dinsa wayarsa tai qara Ya dauka ya duba yana duban number Yai saurin kallon afnan Sannan ya katse kiran Afnan ta kalleshi tana masa kallo irinna tuhuma kamin tai Magana kiran ya sake shigowa Caraf ta kwace wayar kan yai ankara harta nufi waje Cikin firgici ya bita falonta ta nufa tana shirin kullewa ya turo qofar Don haka nu nufi bed dinta da gudu yasa kafa ya hardota ta tafi taga taga ya fizgota Ta dawo jikinsa Daria take sosai tace yi haquri yaya amshi wayar taka gashinana Amsa yayi ya kama kunnenta yace kin rainani afnan waini Sa,ankine? Tasa qara tana bashi haquri Ya saketa yai gaba haryakai bakin qofa. Ta miqe tana fadar Aidai ga wayar nan tawa na baka Yai saurin dubawa yace au hakanefa da sauri ya bita kafin ya cimmata harta fada toilet ta rufe Yai tsaye cike da takaici ba yaddah ya iya dole ya tsaya yanna mata kagiya Yace fito ki bani kinji yar matata babu abinda na boye Wanda bakisan dashiba ta windo ta leqo tana masa daria Tace Allah bazan miqoba har saina karanta komai A qufule yace waike ina wasa dakene? Yi haquri kinji kinsan babu kyau binciki Bata tanka masaba ta fara duba number dake kiransa frnd kawai taga ansa Dan haka bata gane ko waceceba Tai saurin zuwa inbox dinsa txt taga na farko natane na biyuma natane Na ukune taga ansa frnd dan haka tai saurin budewa Dan karantawa(peace be upon u adnan Pls adnan save my life wlh I cnt. Do without u. Nice na dace da zama zabinka Sbd nice ajinka am beauty edycated an rechest Pls adnan I wnt to be ur wife Your sady baby Gaban afnan yai mummunan faduwa Wacce sady din badai tata ba Hannunta na rawa ta cire number taga aiko itace Ji tayi wani juwa na neman kayar da ita ta dafe kai tana kiran sunan Allah Ta rufe ido tana fadin wayyo Allah na shga tara Ya Allah ka taimakeni karna rasa adnan Jikinta ya saki ta Bude toilet din ta fita tama rasa ina zata Falon mom dinta ta nufa akwance ta sameta saman kujera tana chartin da laptop Tana ganinta hajia nafin ta tashi gamida cire gilas din fuskarta Afnan ta shge Jikinta tai lamo sai numfarfashi take Momcn nata tace Waye ya batamin ran yar autatace iye Idonta ya kawo kwalla murya a sanyaye tace Momy adnan ne Tace me yai miki dan iskan yanxu naje naci masa mutunci? Ta girgiza kai tace ba komai Momy wai sady diyar gidan Momy surayyah ce take sonsa harda aiko masa da text Wat wata gigitacciyar tsawa ta daka mata tace kinga dakata tare da hankadata Gefe har kanta ya budu da bujera jini ya fara juba ta mike tsaye Jikinta har rawa yake tace me kike shirin fadamin? So kike kicemin sonsa kike? Ban miki kashedi da shga harkar matsiyacin yaronnan Ba?dubeki mana kina nufin nasha wahalar nakudarki abanza kenan? To wlh karya kike in sonsa kike nida kaina zan tsaya mata ta aureshi Itace daidai da ajinsa ba keba Ita yar gidan sanater ce ke kuma babanki chief minister ne Kinga kuwa akwai tazara sosai a tsakaninku Tace sakarya kawai wucemin da gani tunkan raina ya gama baci Sannan gobe qarfe goma jirgin janar Abdallah zai sauko Ma,ana zaizo wajenki inkinga dama ki wulaqantashi Wlh da sai na miki wulaqancin da keda kanki zaki dunga Tunanin shin wai nice Na haifeki ko kuwa Danni Akan kudi ba abinda bazan iyaba kinajina maza ki bacemin. Da gani gaba daya ni bani kika biyoba wannan matsiyacin uban naki kika biyo Wanda arayuwarsa kullun baison ci gaba sai ci baya Jiki a sanyaye tabar Dakin tana jinjina kalaman uwar tata Aure. Kan. Aure Chapter13 Afnan ta miqe goshi na xubar da jini tabar falon Ko kadan a haja nafi bataji tausayintava saima wani dogon tsaki dataja Ta koma ta kwanta tana fadar Nonsense Juwace ta soma kwasarta tana isowa bakin kofa Sukai ido hudu da adnan A gigice ya nufota yana fadin lfy afnan Me yaji miki ciwo subhanallah Ya zaunar da ita ya juya a guje ya kwaso kayan aikinsa A rude ya kamo hannunsa data dafe kanta dashi ta fizge hannun Ya girgiza kai yana a,a afnan kar muyi haka Ya miqe ya zauna kan kujerar da take Ya riqeta sosai Sannan yai mata dresing din ciwon Ya dubeta cikin nuna tsananin kulawarsa ya kira sunanta Afnan ki gafarceni. Na rantse miki da Allah ban taba mafarki saba miki Alqawari da mukai ba Sannan text din da kika gani a waya wlh tundata turoshi ban mata replay ba ban kuma sake daukar wayarta ba Yau sati guda kenan kullun saita kirani yafi sau ashirin Nasan idan har kika duba wayar dakyau zaki tabbatar ban taba kirantaba Kuma na daina daukar wayar tata Kimin uzuri my luve wlh bazan tava cin amanarkiba Na amince daki dauki layin wayar ki karya kisai Wanda yai miki kiban naci Gaba da amfani dashi. Kinji ya tambayeta Wani sassaukar numfashi ta sakar ta lumtshe ido alamar tanason yin Barci Sbd maganin daya bata Haka ya samu ya lallabata ya kaita dakinta ya rufeta da bargo Yaja mata qofa Koda abbanta ya dawo yana cikiyarta adnan yace ai taji ciwone hankalinsa ya tashi Yaje ya dubata saidai har lokacin bata tashi daga barcinba Sbd maganin datasha Yanada qarfi sosai Washe gari tundata farka kanta yai mata wani irin nauri daqar ta iyayin sallah Ta koma ta kwanta don haka da aleeyu yaxo dubata bai sameta ido biyu Ba shi kansa adnan din sau biyu yana xuwa bai samunta Hajia nafi ta aiko yarinyar dake mata aiki tace taxo ta kira Mata afnan ta samu ta farka saidai jikin nata bakwari Ba zata iya tashiba Yar aikin bata Dade da tafiya ba saiga hajia nafin ta shigo fuskarnan a turmuke Ta taba jikin nata taji ba zafi sosai tace tashi na taimaka miki ki shirya Dan kuwa har baqon naki ya qaraso sunacan falo sunacin abinci Afnan din batace mata qalaba ita dakanta ta tasheta ta kaita Toilet ta hada mata ruwan wanka Sannan ta fito ta zaba mata kayan Da zatasa. Bayan ta fito ita da kanta tai mata kwalliya Adnan daya Gaza tafia aiki Sbd ciwon rabin ran nasa ya dawo a karo na Uku saidai a wannan karon yayi rashin sa,a domin hajia nafi nanan Shi kansa sai dayaji faduwar gaba Ya zube yana gaisheta baki sake ta tsaya tana kallonsa Ta girgiza kai tace eh lallai akuyar daure ta samu sake Wato inacan mutun ya maidamin diya Kamar matarsa Lallai mutun mugun iccene To bari alhajin yaxo sai inji idan shine ya baka lasisin yin haka Mugu kawai banza haifaffen kauyen kayau. Qauyen da ko wutan lantarki basu dashi Aniyarka ta bika wannan da kake gani tafi qarfinka dan ba matar talaka bace Dan iska a sannu sai nayi maganinka tashi ka ficemin da gani Ta fada da kakkausar murya Afnan ta runtse idanunta wani irin zugi na ratsa zuciyata tamkar ya fashe Ta bude idanun nata lokacin data tabbatar daya fice Ta kafe mom din nata da idanu zuciyata na harbawa Ji take tamkar ta maqare mom din nata ita kanta ta fahinci irin kallon Da diyar tata ke mata. Tace ko zaki Rama masane iye sai insan kinji zafi Batace mata komaiba ta jera suka fice Har falon da yake ta isa Saidai zuciyata ta soma sarewa da irin rashin mutuncin data tattaro Dan tun daga barkon falon Sojojine tsaytsaye ko wanne da zungureriyar bindiga sai mazurai suke TaBbas in banda tare da mommynta suke da babu abinda zaisa ta arce da gudu dan ko yanxuma dakiyar zuciyace kawai Falo na biyu yafi na farkon yawan sojoji dan Hatta bakin qofar shiga Sojojine Tsaitsaye suna shga momynta ta juya kai tsaye fuskarta ta sauka kan Genaral farine tas tas yanada cikar halitta. Irin na jaruman maza saidai Bai cika wani kyauba. Saidai akwai kwarjini a Idanunsa Shekarunsa zasukai talatin da bakwai babu alamun wasa a tattare dashi idanunnan nashi jajir dasu Yana sanye da suita baqa da jar tshirt sun zauna a jikinsa In bacin sallama data zama dole a addinance da babu abinda zaisa Tai masa sallama Ya dago da jajayen idanunsa yana kallonta Wanda sukaso Tsoratata lokaci guda ta zauna kan kujerar dake fuskantarshi Tace sannu da zuwa ciki da qasaita yake amsawa tamkar Wanda aka takura Don haka bata sake maganaba cikin Wasu yan dakiku Kamin ya gyara zamansa kan kujeran ya soma cewa Malama hafsa afnan ko to ba tare da westing din tyme ba nasan dai kinsan abinda Ya kawoni gurin momcynki ko? Nidai bawai buqatata Wasu dogayen maganganuba kin gane ko Nasan kinsan koni wanene don haka in kinji zaki iya ina mana Sha,awar kasancewa ma,auratane nanda Wasu yan qanqanin lokaci ina fatan kin gane Ta miqe ta kalleshi Bayan tayi taku daya zuwa biyu Sannan ta waigo tana masa wani qasaitaccen murmushi Tace lallai malam jenaral rashin sani yasa kai shuka a gonar da ba takaba Ta girgiza kai tace soyayyah kwara dayace tak kuma na rigada na Bama wani Don haka Kowa ye yace Maka nace ina sonka to qazafi yaimin Ko kuma ince yai Maka qarya ka gafarceni mai girma janar Banda ajiyayyen soyayyar da zan iya baka a yanxu Sannan ta koma ta zauna tace nasan dai wannan bazai damekaba ko? Yace ko daya saima ya qaraban kwarin gwiwan Zage damtse don kwatar soyayyarki da karfin damtse ko data aljihu na Ko kuna na kwaceta da qarfin mulki na Duk wannan ba abune mai Whl ba a wajen mutun mai qarfin iko irinaba Tai wani murmushi takaici kamin tace Yo ashema shirme kawai kake a cikin soyayyar Tunda bakasan meye ita sonba To bari kaji na fadamaka shi so gamon jinine ba gamon gambizaba Shi so haduwar juciyane ba hasasheba Shi so kudi ko mulki ko kyau ko iko basa samar dashi Duk sone ke samar dasu Don haka Kaga kenan yanada kyau ka nemi amincin zuciyar wacce kakeso Shine abu mafi sauki Genarar Kamar yaddah ta kirashi yai murmushi Sannan ya sake kishin gida saman kujera Yace afnan kenan ni genar banayima soyayyah bauta. Kuma bana biyayyah Ga mace isace ke kwatomin soyayyah a gurin ko wacce kalar mace Don haka a cikin uku sai anyi daya Ko in kwaci zuciyarki dake kanki da qarfin damtse ko in kwaceta da qarfin aljihu Ko kuma in kwaceta da qarfin mulki Cikin ukunnan dole sai anyi daya Tace to lallai Indai da ukunnan kawai kake taqama to ba zasu taba Iya amso Maka soyayyah wajen mace ba Balle ni afnan da xuciyata ta Dade dayin nisan da mai rai bazai iya gano Adadin guduntaba Na rigada nayi nisa Akan son mutun daya dan autan maza namijin mazaje Wanda daddadan kalamansa ke narkarmin da zuciya Ta miqe tsaye tana wani murmushi sannan tace Yaya adnan kenan idan yai murmushi yai kyau idan ya daurema yai kyau In yana magana har wani daddadan iskane ke fitowa daga bakinsa mai kashe zuciya In yana tafiya yai kyau in azaune yakema kyau yake Kallonsama kawai daukemin numfashi yake. Hmmm yayana kenan Ta ida fadar tana wani kyakkyawan murmushi tamkar yana gabanta Wani haushi da takaicine suka daki zuciyar genar ji yake tamkar tana watsa Masa garwashin wuta Da gaskefa yanason wannan yarinyar dan zuciyarsa ta sanar dashi Jin yayi shiru yasa tace to yallabai ni nayi gaba Allah raka taki gona Dan kuwa zuciyar afnan ta Riga da tayi tauri ta zama tamkar dutse Dutsenma dutsen daka Wanda ko nakiya ba zata iya fasashiba Ya miqe da sauri zuciyarsa na radadi yace Yarinya Indai kudi da mulki na aiki saikin dawo saman hannuna Yasa hannu a aljihu ya zari cheaqu ya aje kan tebur ya zuya a zafafe ya wuce sojojinda ke tsare lfyrsa suka rufa masa baya ba tare data qara waiwayarsaba itama ta wuce bangarenta Adai dai sashinta suka hadu da adnan sai safa da marwa yake Duk ya hada gumi yana ganinta yai saurin qarasowa ya zaunar da ita Itadai kallonsa kawai take Jikinsa har rawa yake yace afnan yanxu yarda zakiyi a rabamu Afnan walahi ina sonki na rantse miki da Allah bazab iya rayuwa babu keba Afnan in kika barni bansan halinda zan shgaba Hannu tasa ta soma share masa hawayen da suka soma gagaro masa Ta rasa ta yaddah zata fara lalllashinsa dan ita kanta zuciyata ta karye Kuka takesonyi saidai in tace zatai kukan bata da mai lallashinta to mai lallashin nata Shima kukan yake Muryarta a sanyaye tace yaya adnan kasa rainka a inuwa babu Wanda zai rabani dakai Duk runtsi ina tare dakai Dukda nasan kana cikin tsoro danshi so Kamar tsuntsu yake yakan iya tashi Daga wannan bishiyar ya koma wancan to inaso kasa a ranka Son da nake Maka bishiya daya gareshi a cikin jeje Idanma ya tashi to saidai ya fado qasa Wanda hakan na nufin ruguwar rayuwata kenan Nidai duk runtsi ina tare dakai saidai in har kaine ka juyamin baya Yace ki daina fadin haka afnan nidake saidai mutuwa ke ko mutuwar kikai saina auri Zuciyarki Murmushi tayi ganin sonta na neman zarar dashi A tare suka wuni suna Hira mai dadi Misalin qarfe goma na dare aleeyu na zaune a sashinsa sanye da farin gilashi yana bincike a laptop Hajia nafi ta shgo tana sanye cikin qasai tacciyar shiga Saida ya kammala abinda yake sannan ya juyo yana kallonta Murmushi ta sakar masa dan haka ya miqe ya qarasa inda take Yana fadar Yadai hajia Naga bakinki tamkar da magana a ciki Tasake sakin wani murmushi kamin tace maganganu kai Yace to gani fesamin Tace nida yarkace afnan daxun an kawo Maka suriki bakanan General Abdallah kuma mun aje magana dashi Akan zaizo ya ganga domin turo Magabatansa Aleeyu ya haderai yace ban fahimcekiba nafi kina nufin har wani qato kike kawomin cikin gida ba tare da izninaba Amman lallai kin cika marar hankali yasin Ya nunata da dan yatsa yace bari kiji Yadai tawace to narigada nai mata miji Babu kuma Wanda ya isa ya sauyamin magana kin gane ai ko? Zaram ta miqe tsaye ta bigi cinya tace qarya kake aleeyu wannan karon Kaci qarya ka kwana da yinwa wlh Indai ina numfashi yata ba zata auri matsiyaciba Don haka tun wuri ka gyara bazarka inko kaqi ta tsinke Yaddah takeba babatun nata abin saima ya daure masa kai Yace lallai bakida kunya nafi harni zaki kalla tsabar idona kice nai qarya To kece ke qarya mu xuba nidake shge ka fasa Tayi wani malalacin murmushi tana girgiza kai Tace lallai aleeyu bakasan wacece nafi ba Ganina kawai kake na rantse da Allah hatsabibancinan ya wuce yaddah keke Tunani Zan iyayin komai Akan wannan lamarin shiyasama nake shawartarka Akan abinda nace dan kawai a zauna lfy Ta girgiza kai tace wlh aleeyu bakasan yaro bane kai saika tsince kanka a Hannun manya. Zaka tabbatar Lol Shirmen natama ya daina bashi mamaki. Takaici ya koma bashi Don haka cikin tsawa yace get out Ya fada a harzuqe yana tilasta mata ficewa Yayinda zuciyata harta fara tausayama bala,in data shiryama aleeyun mijin nata Dadddah shi Wanda yake qoqarin Bama diyar tata Da ita kanta afnan din don yanxu batajin digon tausayi balle imani a xuciyarta Washe gari misalin qarfe sha daya na rana Adnan ya dauki afnan domin kaita makaranTa don tanada lecture qarfe daya na rana Bayan ya ajeta Yaja motar tasa sannu a hankali yake tafiyan yana sauraron karatun alqaur,ani Bai ankaraba saiji yai an bude motar an shigo ya juya da sauri dan ganin abinda ke faruwa gabansa yai mummunan faduwa Mutanene sanye da baqaqen safa a fuskarsu baka ganin komai na jikinsu Daga idanunsu sai hannu Ko wannensu rirriqe da bindiga Tuni zufa ta soma karyo masa Cikin murya marar dadi daya daga cikinsu yace Zaka iya fansar ranka idan har kabi abinda muka umurceka dayi Don haka duk inda mukace kabi nan zakabi Kana kuskurewa kuwa dauke kanka zanyi yasin da wannan bindigar dan umarnin da akaban kenan Jikinsa yai sanyi dan ya rigada ya fiddah rai da rayuwa Don haka duk inda suka nuna masa nan yakebi Har suka shiga can cikin wani daji HmMmmm lol. Jama,a we hve done wif book1 Shin wa kuke ganin zaisa a sace adnan @nafi ko @general shin ko sury ce uwar sady. Sbd yaqi sauraron yarta Kai anya ba shajini za,a kaima shiba Guest Kan. aure Chapter14. Wif. Salankz Tafia mai nisa Sukai kamin su isa wani tangamemen gate Daya daga cikinsu yam saurin fitowa ya zanyoshi suka nufi ciki Gidane qaton gaske Ta cikin wani falo suka ratsa mai cike da daular duniya sannan suka isa wani daki Dakin na dauke da kujeru tareda babban tebur a tsakiyarsa daya daga cikinsu yace zaka zauna anan har sanda hajiya zata qaraso. Don kuyi magana Sukace karka damu babu mai cutar dakai Tunda har kabi shariddanmu Suka juya suka fice gamida kulle qofar ta baya Adnan ya durqusa a wajen cikin tsananin tsoro Lallai yana cikin tashin hankali marar misultuwa shin meye dalilin kawoshi nan Meye manufar yin haka? Sannan suwa sukasa a kawoshi nan? Tambayoyin da baida mai amsa masasu Adnan har qarfe hudu na yamma tana kiran adnan babushi babu dalilinsa Tsawon mintina talatin kenan tana zaman jiransa Amman da alamar bazaizoba To wa zatace ya rage mata hanya? Daman sady ce Kuma ta kammala karatunta Daman kuma sundanja baya da zumuncin nasu Don haka ta ciro wayarta ta kira direbanta Wanda ta hutar dashi Sbd dawowar adnan Tace masa yai maza kome yake ya aje yaxo ya dauketa a skull yace Angama ranki shi Dade. Baifi minti talatinba ya Iso ya dauketa saidai zuciyata na cike da alhinin abinda ya hana adnan Zuwa daukar nata Gashi tanata kiran wayarsa saidai ta ringin harta dauke Ba,a dagawa to ko lfy abinda take Tambayar kanta kenan Zuciyata bata qara tsinkewaba saida taga har anyi sallar isha,i bai dawoba Har a lokacin kuma inta kira wayarsa ba!a dagawa Don haka ta kira abbanta ta sanar dashi don haka yace gashinan isowa Shima yaxu Adnan kuwa. Tundaya durkusa a wajen yafi awa guda Sannan ya tashi Sbd lokacin sallah yayi dukda tsoron dake fuskarsa hakan bai hanashi Nufa toilet dinba domin dauro alwala Nan ya fito Bayan yai alwalar yai sallar Sannan ya duqufa karanto Addu,oin neman tsari Har akai sallar magrib da isha!i yananan Hankalinsa ya gama tashi a wannan lokaci dan haka hanyar tsira kawai yake nema Gashi wayarsa na cikin mota daman a chargi yasata Yana cikin wannan tunane tunanenne yaji an turo kyauren kofa Yai saurin miqewa dan yaga mai shigowa Hajiya surayyah ce tana cikin kyakkyawan shga Kallon kallo suke a tsakaninsu cikin tsananin mamaki yake Kallonta. Ta nemi daya daga cikin kujerun Dakin ta zauna ta daura Qafa daya kan daya tana kadawa tana murmushi Sannan tai masa nuni da hannu alamun ya zauna Tace zauna mana adnan kaja ka tsaya tamkar mai shirin kokawa Bismillah zauna Ba musu yaje ya zauna gami da fadin meye dalilinki na kawoninan iye hajiya? Murmushi ta sakeyi kamin tace kana mamaki ko adnan To wannan kadan daga aiki nane dan na wuce hakama Mai yasa nasa waya na kiraka kaqi zuwa daga bayama saika kashe wayar? Yace Sbd banda wata alaqar da zata kawoni gidanki Sannan baki da wani kyakkyawan dalili na nemana Tace ko daya karkace haka adnan niko keda kyakkyawan dalili na Nemanka Domin kuwa yata sady tana cikin wani matsanancin Hali duk Sbd kai Ka taimakamin adnan banso na rasata Don ita kadai na mallaka. Inhar kaimin haka to ka gamamin komie a rayuwa Kuma na maka alqawari azurtaka da dukiya mai tarin yawa In saka a harkar siyasa kaima a dama dakai In tsaya maka har sai Naga ka zama wani abu a rayuwa Buqatata kawai ka amince da auren yata kawai Takaicine da mamaki suka rufeshi lokaci dayaa Yace to aini ban iya auren rashin yanciba hajia nasan kaina da abinda Nakeso don haka ni ban tabajin inason yarki sady ba Saidai koki tallata gaba don nasan akwai masu so fiye da yaddah zuciya Keso Hajiya sury ta miqe tsaye cike da takaici ta nunashi da yatsa tace Ka taka a hankali adnan dan yanxu rayuwarka a hannuna take Zan iya juyata yaddah nakeso Wannan kawai ya isheka ishara yaddah nasa aka kawominkai haka zan iyasa a batarmin dakai Zan iyaayin komai Sbd rayuwar yata ba baka nanda sati biyu kaje kai Shawara Tana rufe bakinta tai waje Sannan qartin suka shigo sukace Kana iya tafiya Abinda sukace dashi kenan cikin hanzari ya xura takalminsa Ya fice daga gidan jikinsa na rawa ya fada mota ya fice daga gidana a Guje tamkar Wanda yake tsoron a sake kamashi Acan gidansu afnan kuwa aleeyu na dawowa kai tsaye sashin nafi ya nufa Hajiya nafi ya nufa yana zaune kan 2seater. Da cup a hannunta da ala$un Tea takesha. Wani film take kallo a tashar mbc action ko sallama babu Ya fada Dakin idanu waje take kallonsa bakinta na rawa tace Lfy dai ka shigomin ko sallama babu? Ya nunata da dan yatsa muryarsa a kausashe yace Ke saurareni Nafisa kina nufin wannan hanyar da kika bullo da ita zata Bulle dakene? Toki saurareni dakyau kiji na rantse da tsarkin mulkin Allah saina Aurar da afnan ga adnan Inhar ina numfashi a duniya don haka duk inda kikasa akakiai adnan kiyi Gaggawar fitowa dashi cikin yan mintunannan inkuma ba hakaba kuma,,,, Ya murza yan yatsun hannunsa Sukai qara ya juya ya fice ta bishi da Kallo kamin taja wani dogon tsaki mtwsss Yana fitowa ya nufi sashin afnan ya ganta a tsaye Zamama ya gagareta qarfe tara da wani abu Na dare amman babu labarin adnan Hawayene kawai ke zarya a fuskar nata tana Tunanin shin ko a wani Hali yake yanxu oho Aleeyu ya shgo falon ya zaunar da ita yana lallashinta Yace kiyi haquri yata insha allahu duk inda ya shga za,a ganoshi na kira d,p,o Yanxu nai masa bayani Hawayen dake zuba daga fuskar nata bai daina kwararaba tace Yanxu daddy shikenan shigowar adnan din yasa bata qarasa abinda zataceba Ta miqe da sauri taje ta riqoshi zatai magana kuma saita sakeshi Tana kallonsa Baice mata qalaba ya wuce wajen aleeyu ya gaisheshi Bai amsaba saidai ya jefo masa tambaya Ina ka shga aleeyu afnan tace tun kafin sallar azahar ka ajeta a makaranta Tun daganan bata qarajin duriyarkaba Sannan inta kira wayarka ba!a pickin lfy? Ina kaje? Yace Abba wayatace ta bata a lokacin da naje gidan abokina saddiq Don na dubashi baida lfy Nan na zauna ina kula dashi har saida qaninsa ya iso daga katsina Sbd ba Kowa a gidan Aleeyu yace amman dai baka kyautaba aida saika ari koda wayar abokin Nakane ka kira kai mana bayani dan kasan dole dai za,a nemeka Tubi yaddah duk ka tada mana da hankali Yace ayi haquri Abba ba za!a qaraba Yace to shikenan gobe zan tafi musawa dan tsaida. Ranar aurenku Idan kanada sako saika bada yace ba komai Allah ya kaika lfy Kuma ba wani lokaci bikin zaijaba don haka ka sameni a falo don baka takardun gidan Dana kammala muku na nasarawa Sai kaje ka duba don ganin yan gyare gyaren da za,ai masa Akwai Wasu motoci da za,a turomin daga America I zuwa sbn kamfanina Sai kuje ku duba ku zabi daya daya kaida afnan Godiya suka zube suna masa harya fice Da sauri adnan ya tashi ya dawo gefen afnan ya zauna tai saurin juya masa baya alamun fushi take dashi Ya dafe kai yace ohh my afnan kar muyi haka dake ki fahinceni plz In kika juyamin baya ina kike Tunanin zanje na samu sanyi Yace haba afnan wuni guda nai a waje aikin tai mako nayifa Ba yaddah na iya amman wlh nayi mising dinki Idanuwana sun qagu da suga kyakkyawar fuskarki Plz matar juyo ki kalleni dan gajiyar ta tafi Bata juyaba hakan yasa yai saurin komawa gaban nata Ya riqo hannunwanta yace aimin haquri my luv Yaddah yai maganar kaman dan yaro abin ya bata daria ta qalqale Don haka zuciyarsa tai sanyi Tunda ya shawo kan rabin ran nasa Yace bari naje kiran daddy na dawo ki hadamin abinci da tea kinji Kai kawai ta kada masa ya fice Washe gari Tunda safe misalin. Tara da rabi ya nufi gidansu nafi A falo ya samu hajia asiya zaune sanye da farin gilashi tana karanta jarida Ya samu kujera ya zauna. Ta dubeshi fuskarta dauke da murmushi tace Aleeyu mazan fama kwana biyu kai mana yaji Yai wani guntun murmushi ya zube ya gaisheta Ta amsa yar Hira suka Sannan ya shgar da maganar nafi Tunda Sukai aure yau shekara goma sha tara kenan bai taba kawo Qararta ba sai yaau da ya zama dole Yace hajia daman maganar nafi ne acan gida sun yanke shawarar hada Afnan da adnan amman ina tunkararta da maganar ya zama abin tashin hankali Wai ita yarta ba zata auri talakaba wai Tunda janar Abdallah yace yana Sonta. Tace wai shi zata bamawa Kuma janar ba mutumin arziqi bane dan ko mutanen dake qarqashinsama Kuka suke dashi Sannan yarinyar tace batasonsa shiyasa nace bari Naxo na sanar dake kiyi mata makagana dan nasan tanajin maganarki Wlh nafi nada matsala dandai kawai zaman aure sirrine shiyasa Tace nasan da haka aleeyu nasan haquri kawai kake da nafi dan bata da Kirki In banda Iban albarka ace a matsayinka na mijinta har kasa Doka ta tirge ai bai kamata ace ta Maka musuba koda kuwa ranta bai mata ba Ita da yar taka ai duk a qarqashin ikonka suke ikonkane aleeyu kanada right din da zaka yanke duk hukuncin dakaga yayi maka Don haka ni inkama janye auren afnan da adnan koda Bayan raina ban yafemaka ba Namijinekai kaje ka gindaya sharadin gidanka inta qetare ka yanke duk hukuncin Da Kaga yafi dacewa akanta Babu Wanda zai zargeka kuma zan kirata yanxu ba sai anjima ba Kaje ka qara haquri yace ba komai na gode hajia Haka ya miqe Ya fice tana sa masa albarka Yana fita hajia asiya ta kira nafi a waya tana dauka tai mata tatas Sannan taja mata kunne sosai abin yaima nafi ciwo matuqa Kuma tanaji in sama da qasa zasu hadu to saita aurar da afnan ga janer Don haka qawarta ta kira hajia sury tai kuwa sa,a tana zaman jiran natane don haka ko mintina ashirin bataiba ta isa gidan nata Cike ga qaguwa nafin ta tari qawar tata dan ko ruwa batashaba ta fara zayyane mata Abinda ke faruwa gameda hadin da aleeyu keson yaima afnan da adnan Tace na rasa mafita wlh dan iskan yaronnan so nake Naga bayansa Abin yaci tura nabama shajini shi yafi sau goma yaqi karbarsa na rasa meye dalili So nake Naga Bayan yaronnan hajiya sury duk rintsi Koda zan rabu da aleeyu saina aurar da afnan ga janar Sury tace haka nakeso qawata amman bawai ace ki liqema wani jarababben aureba Yanata whlr dake sai kace shine autan maza Dubi yaddah ya maidake a cikinmu sai kace duk kin girme mana Kodayaushe kina kudundune cikin tafka tafkan kyalulluwa Sai kace wata matar malam fitama wannan sai kiyi sati biyu baki leqa wajeba Haka escote dinki kecin kudinki a banza duk qarshen wata shi kuwa yana waje Yana holewarsa Ya zubeki a gida ke baki da wani yancin kanki sai abinda ya tsara miki Sai kace shine yai miki dakon cikin wata tara kuma yai miki nakudarsa Wlh ina baki shawara a wannan karan karki bari aleeyu yai galaba akanki Karki bari yaga bayanki saidai ke kiga bayansa Nafi tace ta wace hanya sury? Banida Wanda zai goyamin baya Hatta mommy nan

Chapter 5 of 16