Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
mata da Hankali Idanunta suka ciko da kwalla tace yaya adnan kainefa kake qaramin qarfin kwiwa Akan soyayyarmu kodai ka fara sanyine? Da sauri ya dago yana. Kallonta cikin tashin hankali Yace haba afnan kinfi Kowa sanin alqawarinmu Akan soyayyarmu wuya ko daddy bazai tabasa daya ya rabu da daya ba Ko kina zaton da akwai abinda zaisa mu rabune? Da akwaishi dan kaza kaza ta bankada masa wani bamagujen zagi Kole ku rabu ya zame Maka wajibi ka barta Indai har ina numfashi Ta wargaxa musu. Iv dan dake hannunta suka baje a gabansu Cikin tashin hankali afnan ta dauka tana dubawa Yayinda shi kuma adnan din bai daukaba saidai ya karanta wadanda suka Zubo jikinsa Ba komai bane illah na daurin auren afnan da janar jibi alhamis Dukkansu sun shiga rudu dan nasu daurin auren Asabar akasashi. Hajia nafi taja murmushi kamin tace Wannan kenan adnan. Ka saurari sauran sakamakon ja dani dan tabbasa Sai Naga bayanka kaida uban riqon naka Cikin tashin hankali afnan din ta tashi ta rirriqe mom din nata tana kuka tace Kiyi haquri dan Allah momcy wlh bazamu taba iya rayuwa idan Bama tareba Kuma Wanda kike qoqarin hadani dashi dinfa ba musulmi bane bafa Da bakinsa yacemin yayi riddah momcy meye hukuncin auratayyah Da a matsayin na musulma? Tas tsa ta dauketa da Marin da saidata kifa sannan ta nunata da dan yatsa Ki hankali dani na rantse miki domin yanxu na janye wata alaqa ta haihuwa tsakanin nidake. Zan iya miki duk wata azaba da zan iyama maqiyina Ban dauki duniya da wasaba dan wlh zan iya badake Akan duniyar Don haka ki guji wani yinkuri da kikasan zai iya wargazamin shiri inkuwa kinqi Ta murza yatsun ha Sukai qara ta juya tace wannan kuma da yake gabanki Ban tatasa domin nanda Wasu yan awanni an fara wantawa da tarihinsa Ta fice abinta Maganar momcy ta qarshe itace tafi dagama afnan hankali Afnan ta dafa kai tana shirin kwalla wata kururwa Yai saurin riqeta Yaja hannunta a hanzarce Yace zo muje afnan wannan lokacin ba lokacin kuka bane Ta jari jakarta suka fice a guje Saidai suna isowa inda motar adnan din take suka soma kallon kallo Dan kuwa motar sojojine sunfi kala goma Sai jiniya suke kafin suyi wani motsi har janar ya fito daga motar dake gaba Sojoji sunfi talatin suka rufa masa baya Hannu kawai ya daga musu duk suka tsaya ya qarsa gabasu afnan da adnan din Yana wani tafiya irinta isassun mazaje masuji da mulki Ya kallesu daya Bayan daya kamin yace Two starsa ina zuwa haka? Wai wani murmushi kamin yace badai Kuna yaudarar kanku bane ta hanyar Guduwa? To kuje ina? Kun manta karan battane tsakaninku da janar? To kujedin amman inason ku sani duk inda qafarku ta sauka Akan idon janar ne Ya dubi adnan yace kyakkyawan saurayi amman na tausaya Maka ta Yaddah tsautsayi zaisa ka baqunci lahira da wuri Mai yasa ka yaudari kanka samari kake qoqarin mallakar matar datafi qarfin ajinka? Kash.... ya girgiza kansa Daka sauya tunanina yaro wataqila daka hango wata wacce ta Banbanta da afnan Cikin kakkausar murya afnan din tace Dan Allah malam saurara mana ai mijin dayafi dacewa dani shine adnan Kamilallaen mutunne kawai zai iya gane hakan kai ba zaka iya ganewaba Sbd Bakasan darajar soyayyah ba To ka sani raba masoyi da masoyiyarsa tsinke soyayyar gaskia ba abune mai Sauqiba Wai wata malalaciyar murmushi kamin yace ni kuma wannan abune mai Sauqi a wajene In naso saina tsinke soyayyah a cikin yan mintuna Adnan yace wannanne kuma karyarka Tasha qarya mai girma janar Ada nayi Tunanin mutum irinka mai kwargiji da isa yaro kamata Ya girgiza Maka tunanina har karasa yaddah zakai kake min barazana kasheni Kai lallai na cika namijin mazaje Shin ka mancene har abada ina manne a zuciyar afnan wacce riba kake ganin Zaka samu. Ga macen da kakeson aura alhalin ita kuma bata da ajiyayyen soyayyar da zata baka? Janar yai murmushi yace yaro kenan shin ka mance. A wannan zamanin babu Abinda kudi ba zasu iya siya makaba? Koda kuwa dan Adam ne ballentana wata qaramar alhaki wai ita soyayyah Adnan yace aiko kudinka ba zasu iya siyan Maka soyayyah ba dan ko da zasu iya Dasun sai maka Kuma kudi kan iya siyan dan Adam amman ba zasu iya siyan zuciyaba Shiyasama ake samun mayaudara a cikin alumma har kake yarda da mutum yaxo ya cuceka Mai girma janar inaso kayada makamanka dan ina guje maka ranar jin kunya Randa zakasha kayi wurin dan cikinka Domin kifin fadama baya gasa Dana gulbi in bandakaima Dattijo kamarka inakai ina yarinya kamar afnan Aiko ba,a kwadaba limzami yafi qarfin bakin kaza Da alamar ran janar ya fara baci da zantuttukan adnan don haka ya nunashi dadan yatsa yana fadar lallai yaro kayi gangancin taran aradu da ganmo Tabbas duk Wanda ya shga sabgata na rantse saina kakkarya kafafunsa Nasa ya zama mabaraci a a cikin gari Tabbas saina nuna Maka aikin Jan biro maganin taqadirin dalibi Ni janar na rantse sai Naga bayanka bata dadiba. Na rantse sai kayi Mutuwa dubu kafin kayi ta gaskiya Hahahaha ran maza ya baci ya abin yakene karfa alluran Manyan mazajen ta tashi mu hadu a nxt chapter Danjin yaddah Aure. Kan. Aure Chapter19 Adnan Yaja hannunta yana ke muje kada wannan mara aikinyin ya Bata mana lokaci Ai mai tsoron a mutu shi yake mata maho Mu kuwa mun shirya mutuwa Indai Akan soyayyarmu ne Suka fada mota adnan Yaja suka barshi anan zuciyarsa cike da wani irin Gawurtaccen baqinciki Ji yake Tunda yake ba!a taba wulaqantashi irin na yau ba Don haka dole raine zai zama fansar wannan facin rain nasa Ya juya a zafafe ya shga cikin gidan tamkar gidan ubansa Hajia nafi tai saurin tarar sa tace saunnu da zuwa ranka shi dade mu shga Hannu ya daga mata. Saurara hajia nafi abubuwafa suna neman lalacewa Yanxu na hadu da yarannan suna shirin guduwa kinkuwa san abinda hakan Ke nufi? Hajia nafi taja wani gajeran murmushi tace na sani janar Afnan da adnan sun tafi qauyen musawane domin hidiman bikinsu wanda Za,a daura ranar asabar bazamu hanasuba Sbd ida shirinmu Kai ai Kaga Naka ranar alhamis za,a daura. Jibi kenan Ana daurawa da kaina zan tura a dauko Maka amaryarka idan ka shirya Sai a lokacin janar ya saki wata ajiyar zuciya kamin yace Na fasa kisan Yaron nan hajia tabbas Tunda ya shgo hanyata na rantse sai yayi mutuwa kala dubu kafin yaita gaskia Nafin tace wannan ma daidaine ranka ya dade komai kayi ai girmankane Yai wani azzalumin murmushi ya jaro Wasu takardu daga cikin yar qaramar bribcase dinsa yace Wannan takardan wannan campanyn da kikace ansa akasuwa kinason ki siyane sai kuma wannan takardar wannan sbn gidan da ake gidamin na abuja ne Duk na mallaka miki su Yace kiyi haquri hajia nafi wannan qananun kyatane duk sanda afnan Ta shgo gidana a matsayin matata sai na miki kyautar data birkita miki Lissafi Wohoho wani irin dadi daya rufeta batasan lokacin data runngumeshi tana Kwararo masa godia ba Hmmm nafi kenan anyi nisa gaski muje zuwa masu karatu Bayan ta sakeshi yace karki damu wannan ba komai bace ya fice abinsa Afnana da adnan kuwa sun isa musawa cikin qoshin lfy Yayinda Kowa keda murnan ganinsu Yan uwa da abokan arziqi sai murnan ganinsu ake dan tuni ann Zagayesu da abinnci kala kala Yan,uwa sai nan da nan ake da afnan gasancewar alkhairin mahaifinta garesu Don haka ta saki Jikinta akaita harkoki da ita sai dare suka sami kansu Nanfa adnan da afnan suka samu kebewa da kakanninsu Don su tattauna matsalar kasancewar kakannin sunsan komai Aleeyu bai boye musu ba Cikin takaici malam yace kai wannan yarinya akwai matsala wajen al,amuranta Yanxu ku dauki waya ku sanar da abban naku abinda ke faruwa ni kuma insha Allahu. Gobe zan tattaro dangin babanka da zarar an gama sallar azahar a daura muku auren Inyaso duk wani shagali da za,ai saiya biyo baya Dukkanninsu zukatansu cikin fari ciki take shi kansa aleeyun da suka sanar Dashi. Zuciyarsa tai masa dadi sosai don haka yace Shima a goben kafin azahar din zai iso garin musawa da a daura auren dashi Inka kalli amarya Ada angon tamkar akansu aka fara aure Saidai inna ta gaji da rashin kunyar yaran don haka ta korasu waje tai Kwanciyarta Tamkar yaddah malam mahaifin aleeyu ya tsara haka kuwa abin ya faru An daura auren afnan da adnan Bayan sallar azahar daurin auren yasamu Halarta mutane bakin gwargwado Duk yaddah adnan Yaso Akan yaga amaryarsa amman abin ya faskara Sbd Al-adun qauye sai a hankali a dole yasama kansa sa,ida har dare yai Sai cikin darenema ya samu numberta ta shga zai soma mita tace kai yaya adnan ni kainafa ba laifina bane Duk yaddah naso mu hadu abin ya faskara to ya zanyi? Kayi haquri bari na turo da madadina ta dinga masa kissing ta wayar Yai saurin katseta wait banaso inba so kike yannxu ki ganni kan gadonnanba Don banjin kunyar Kowa Indai akanki ne Daria tai tace I miss u yayana ka kularmin da kanka sweet dreams Ta fada tare da kashe wayar ta kwanta abinta cikin kwanciyar hankali har Barci Ya sureta Washe gari alhamis aleeyu ya shirya ya nufo garin kano Inda yace zaijene domin shirya musu tafiyan nasu qasashe biyar din da yace Su zaba. Dubai. Thailand India swetzerland sannan kuma sai qasar da Adnan yai karatu wato london Don haka aleeyu ya nufi kano don samar musu biza da kuma ticket Ya kuma sanar ma kakannin afnan na wajen uwa daurin auren nasu Da akai da bazata suda shirye shirye suketayi don tahowa musawa ran juma,a Asabar a daura aure ayi walima lahadi litinin su dawo Saidai koda yaje ya sanar musu kakar afnan din Wato mahaifiyar nafi murna tayi sosai Kuma tace ba zata fasa zuwaba wato koda kamune aima amarya Domin nuna farincikinsu akansu Don haka cikin farin ciki ya nufi gidansa. Saidai me??????? Tuni murna ta koma ciki don tun daga qofar gidansa yaga motoci cike har cikin Harabar gidan nasa sojoji sun tsatstsare ko ina Zuciyarsa cike da takaici dan Tunda ake fada masa Janar na zuwa gidansa bai taba arangama dashiba sai yau Don haka dole ya dauki kwakkwaran mataki yau Don haka kai tsaye falon matar tasa ya nufa a takai taccen falonta ya sameta Saidai abin ya girgizashi Tana sanye da Wasu matsatstsun Riga da siket ne yan kanti wato @engilish wear. Sun kama Jikinta ko ina na surar Jikinta yana bayyaba Saman kujera daya suke ita da janar din yaddah har suna iya jin dumin juna Tuni kishin yan maza ya motsa ya fada falon babu ko sallama Wanda ganinsa ya hanasu qarasa tafawan da suke shirinyi suna daria Da alamar tai musu dadi Da wani irin kallon tsana ya dinga binsu jikinsa har rawa yake Sbd Baqin ciki Hajia nafi. Tai saurin miqewa tace yauwa ka kuwaxo Akan gaba Wannan da kake gani shine janar Wanda aka daura aurensa yau da misalin qarfe Sha daya na safe da yarka afnan Wanda daurin auren ya halarci manyan mutane Ciki harda manyan abokanka ina fatan kai farin ciki wohoho wani irin tiririn Baqin cikine da zafin raine suka hadu suka toshe masa zuciya Har yaji yana shirin faduwa Sbd Baqin ciki idanunsa tamkar garwashin wuta Yake kallonta yace lallai nafi yau nake tabbatarda kin zarce duk yaddah nake tunani akanki Allah ya sani bazan iya daukan wanna tozarcinba Don haka na yanke igiyar aurena guda aknki don haka kije inkin Samu miji kiyi aurenki Yamaida kallonsa kan janar yaci gaba Kai kuma gara zan kiraka ko baho koko salunbiyi mai qaramin tunani Koma da wanne ka dace inason ka sani yata tawace Kuma ban daga cikin mazan da matansu suke mulka Don haka ka ficemin daga gida tun kafin na kira yan jarida dasu Bata Maka suna dan ka tsallake shari,a Sannan inason ka sani yata na aurar da ita ga Wanda nakeso don haka Sai kaje ka qarata da wacce take dauraka Akan hanyar In kuma ita tai Maka to saika haqura da yar ka dau uwar Don kuwa tuni yar ta zama mallakin wani Janar yai wani lafiyayyen murmushi lokaci daya kuma ya gimtse Fuskarsa babu alamar wasa alokacin ya nuna alhaji aleeyu da Hannu yace Lallai ka shiga hanyata qaramin dan siyasa to inaso ka sani wlh sai naci namanka Danye sannan Tunda naso afnan kuma harnai nasaran aurenta to inaso ka Sani Akan idonka za,a kawomin ita. Inyi abinda nakeso da ita Sannan nasa akawominkai Akan idonta naci namanka danye Donni janar babu Wanda ya taba shga sabgata ba tare Dana kakkaryasaba nayi fatafata da namansaba Afnan dai matatace wacce aka daura aurena da ita dunbin mutane sun halarcin taron Yan jarida da manyan yan siyasa Don haka kasa ido kai kallo ni janar na rantse sai Naga bayanka Alhaji aleeyu cikin zafin juciya yace kaje ka aikata duk abinda zaka aikata Ni kuma zan kwadamaka karya kake janar Na yarda da ka saba haduwa da zakokin maza Amman baka taba haduwa da zakin da yake shawagi a cikin dajiba a yayin da yake farauta Toka sani idan zaki ya afkawa maqiyinsa faduwa yake qasa ka fita hanyata tun muna shada juna ka ficemin daga gida Cike da takaici janar ya nunashi da yatsa Lallai saimun gwada gwanji a tsakaninmu wlh saikayi danasanin cacar baki dani Zanga yaddah tsohon minister mai neman takarar gomna zaiyi Nasara Akan sugaban sojoji na qasa gabaki daya Aleeyu ya daka masa tsawa cikin tafasar zuciya yace get out nace Ka fita Zuciya na tuquqi janar ya juya yabar gidan amman zuciyarsa sai tafasa take Lallai akwai fafatawa Aleeyu yabi matarsa da kallo mai cike da tsana Tunda ya furta mata saki Jikinta ya kasa daukarta ta xube abab tana kallonsa Batajin zata iya tankawa don haka ko ina na Jikinta rawa yake Aleeyu ya juya zai fice don haka ta kwala masa kira ya waiwayo yana kallonta Cikin tsantsar tsana Cikin kuka na zafin saki tare da ture mata da kyautar da janar Yaso yai mata Tace tabbas ka zaremin mutunci da dan raguwan imanin dake tare dani Tabbas Tunda kasa na rasa wannan kyautar da janar yaimin Ka cefa zuciyata cikin kunci to wlh tallahi na rantse da Allah Nida kaina zan taimakama janar wajen ganin bayanka kaida wannan tsinannan dan riqon Naka Hmmmm jama,a shin zafin saki ne yasa nafi furta wannan kalamai Koko zafin rasa kyautar da janar yai niyyar yin mata? Aure. Kan. Aure Chapter20 Aure kuma an daura ya dauru kuma ya samu halartan dumbin jama,a Sannan duk sun shaida. Don haka aurenta babu fashi don na rantse da Allah saita tare a gidan janar Indai har ina numfashi koda kuwa zatai. Aure. Kan. Aure ne Ta miqe a fusace tabar falon ba tare daya tanka mataba Shima yai gaba Abinsa MUSAWA Adnan da afnan kuwa an shirya musu lafiyayyen kamu Wanda kausar qanuwar nafi ta shirya musu Kowa ya halarta tun dagakan dangin uwa harnna uba Kowa ya hallara a wajen Afnan Tasha gyara wajen anti kausar Tunda safe ake abu guda Sune har mai duguri wajen gyaran jiki Acan akai mata kwalliyar amarya sannan suka dawo Adnan sarkin naci a dole Yaja afnan wani Bangare na gidan Wanda babu jama,a A wajen Tana shga yau saurin janyota da qarfinsa tamkar yana tsoron kar wani ya kwace masa ita Har dakin barcinsa yajata ya kulle qofar Jikinsa na rawa sannan Yaja wata ajiyar zuciya Idanuwan afnan waje tace lfynka kuwa yaya adnan? Bai tanka mataba ya duqa kusa da ita duk idanunsa sun canja launi Tamkar Wanda aka shage ya kira sunanta Afnan ki taimakamin dan Allah wlh babu abinda nake buqata a yanxu saike Inaji tamkar zan mutu afnan plz Ya fada daidai lokacin daya hade bakinsa da nata Batada zabi danta lura mai gidan nata na cikin tsananin buqata Bazata iya hanashiba don kawai asu qananun hujjoji marasa tasiri Hadin kanta daya samu shiya taimaka masa ya lallaba sannu a hankali Harya samu cinma burinsa farinciki suke ciki marar misultuwa Samunta da yai cikakkiyar budurwa ya qara mata qima da daraja gamida soyayyah a zuciyarsa Ya qanqameta jikinsa yana sa mata albarka Ji yake tamkar ya maida ita ciki Sbd so Lallai ya gama sa,a da in,imatu baiwa daga rabbil izzati Yanaji a jikinsa ko mutuwa bazai iya bari ta rabasa da matarsa ba Saida aka soma neman amarya sannan suka saki juna Hartakai bakin qofa zata futa Bayan ta gama kimtsawa ya kira sunanta ta Waiga idanuwanta dauke da qauna take kallonsa ya qaraso Inda take ya riqo hannayenta ji yake tamkar ya hadiyeta yai kising dinta Yace afnan ji nake tamkar zan rabu da wani sashi na jikina Yace don Allah karki yarda a dinga min nesa dake ni mijinkine maison kasancewa dake akoda yaushe Burina kullun in jini samana kafadunki in kwanta a kirjinki ina shaqar kwamshin kyakkyawan fatarki lol kunji marar kunya Wani lallausar murmushi ta saki gamida kising din goshinsa tace I love u too my adnan Ta jame hannayenta ta fice sunama juna murmushi Cike da farinciki ya koma ya kwanta saidai kewar matarsa ne ta dinga damunsa Burinsa kawai gobe tayu subar qasar suje inda zai nuna mata soyayyar da bata taba ganin irinta ba Gaba daya gidan ya gama hadewa da jama,a babu ko masaka tsinke Yan kauyuka daban daban duk sun halarta Inna ta shirya yinin biki Inda acan Bangaren aketa shirye shiryen tafia dinner Anty kausar ne ke shirya afnan inda taketa mita Akan bin adnan Din Tace na lura so kike kije ki miqa masa kanki ba tare da mun gama hadakiba Sakarya maza ba,ai masu haka da zarar kin basa kanki kafin ki tare Zai iya zuwa daga baya yace ya fasa Don ya rigada ya samu abinda yakeso nan taita mata fada Ki nutsu ki kyara kanki ki kwatarma kanki yanci A wajen mijinki itadai afnan jinta kawai take amman aikin gama ai ya Rigada ya gama Doguwar rigace irinta India rai rawa rawa rigar nada adon fulawowi Baqaqe amman riqar pink ne dinkin yahau jikinta Gashinnan yasha gyara sai kyalli yake yana daukar ido Wuyarta da hannayenta duk gwalagwalai ne Duk Wanda ya kalleta zaiso ya sake kallonta ta hadu sai kace wata Sarauniya fatarnan tata ta qara fitowa sosai Anty kausar ta kamo hannunta Zuwa inda aka shirya kamun A Bayan gidane saidai daga Bayan gidan an kafa runfuna guda bakwai Uku barin dama uku na hagu amman suna facing din juna sai daya na Amarya da ango Inka kalli amarya da angon sun bada ma,ana sosai Dangin amarya da ango an cashe sosai Domin an gayyato mawaqa da makida kalakal Anci ansha domin anty kausa gafiya restaurant tabama kwangilar Shirya abinda za,a rabama mutane da abinda za,aci kuma asha Don haka komai na burgewa akai Daga qarshe wani maqwani ya rufe taron da waqarsa ta amarya da ango Inda aka tasar da amarya da ango suka rausaya sosai tsawon Wasu mintuna sannan aka buqaci dasu koma su zauna Afnan cikin daria take kallon adnan ta sigar zolaya tace Kai ashe yayana ya iya rawa haka Daria yayi Shima ya lalubo hannunta ya riqe sannan ya rada mata Yace saima randa muka tare kullun saina miki Rawa da waqa da zaran nai miki laifi na lallasheki da waqa Maganar da zai qarayi ta datse shi SanadiYyar shigowar sojoji wurin Qirjin adnan yai wata mummunan rugurguza Afnan da bata lura da abinda yake kalloba ta matse hannunta cikin nasa Cikin shagwaba tace maganafa nake Baimasan tanayiba don haka ta maida hankalinsa inda yake kallo Batasan lokacin data zaburaba ta tashi tsaye Jikinta sai rawa yake Kirjinta sai baraxanar fashewa yake ganin janar a gaba sauran sojoji sunkai Ashirin suna take masa baya afnan ta juyo da sauri domin ganin haliin da adnan Din yake ko motsii bai iyayi In banda numfashi babu abinda ke motsi a jikinsa Tamaida kallonta inda janar ke tahowa tabbas kansu yayo Yana qarasowa ya hada kafafuwan adnan din duka biyun ya datsa musu ankwa Ba tare daya cema Kowa komaiba ya cakumi rigarsa ya miqe tsaye suna Kallon Kallo a haka hajia nafi ta shgo cikin wata irin shiga sai kace ba musulma ba Ta Riga da siket damammu Daga ita sai wani yalolon gyale gashinnan ta bazoshi ta baya ta datse fuskarta Da Baqin gilashi dukka kallo ya koma kansu gaba daya jama,a Kowa Yasha jinin jikinsa ganin bindiga tsirara Kausar ce tai qarfin halin qarsawa wajen yar uwar tata Muryarta na rawa take fadar Yadai haka anty nafi Hannu ta daga mata tace stop yanxu ba lokacin wasa bane ko dogon zanceba Sannan taci gaba da fadin........ Mu hadu a next chapter yau banyi post da yawaba kumin uzuri Kunsan yau juma,at ne ranar ziyara amman idan allaj ya kaimu gobe xamu daura daga inda muka tsaya Aure. Kan. Aure Chapter21 Tace sojoji sun kama mijina aleeyu da hannu. Dumu Dumu Yana fataucin hodar iblis tare da kawalcin maza da qananun yara Bincike ya nuna shida adnan suke wannan qazamar harkar Hakanma yasa ya aiwatar da aure kan aure Janar ya kama aleeyu da laifi Dumu dumu shine aleeyu Ya bashi daurin auren yarsa Akan ya zama daurin baki Janar ya amsa aka daura auren ba tare daya daina binciken aleeyu ba Hakan yasama aleeyu Bama yaronsa auren afnan ba tare da wancan auren Ya warwareba aure. Kan. Aure kenan yanxu haka Aleeeyu yana hannun Hukuma Sunxone domin tafia da adnan inda ni kuma zan tafi da yata Jikin Kowa yai sanyi da zancen hajia nafi Har Kowa nama adnan kallon azzalumin mutum Amman banda yan tsurarun jama,a wadanda sukasan halin Hajia nafi farin sani Cikin sheshsheqar kuka afnan tace na rantse babu wani azzalumin daya Isa ya tafimin da miji inhar ina raye Tace momcy Nandai gidan dangin ubanane ko Toki barni anan nai rayuwata a cikinsu bazan iya rayuwa da waddah duniya kawai tasa a gaba ba Ni nasan abbana mai gaskia da Amana ne wannan kawai nasan sharri ne daga wajenku Kuma ku zai koma mawa don inhar ina raye saina kayar da gaskia damai Goyon bayanta. Kuma ko Waye na rantse Maganganun afnan sunyi tasiri a Wasu zuciyoyin a yayin da Wasu suke ganin Kamar tanayine kawai domin kare mahaifinta da kuma mijinta Sai alokacin Wasu hawaye suka ziraro a kuncin adnan bana komai bane Sai na ganin hawaye a fuskar matar tasa Wanda alokacin baida hannun dazai share mata balle lallashi Tai saurin riqe hannayensa Wanda aka datsama ankwa Cikin kuka tace kayi haquri yaya adnan bazan taba barinka ba Ina tare dakai kuma duk runtsi insha allahu sai munyi nasara Akan maqiya Badai maqiya suyi nasara akanmu ba Yana shirin magana suka tasa keyarsa a gaba suna Harbin iska Hajia nafi taja afnan da taimakon wata soja suka sata a mota direba yajasu Afnan tai kuka har saida idanunta ya qafe Rayuwar tai mata kunci fiye da komai ji take in akwai abinda ta tsana fiye da Mutuwarta to momcynta ce Don dama babu wata shaquwa ta uwa da da a tsakaninsu Tun tana jaririya bata shayar da itaba bata rainetaba bata tava Goyata da bayantaba bata taba mata kyakkywan runguma a jikintaba da hartai Barci ta farka ba Balle aje ga kula da lfyrta. Sunanta dai uwa kawai Shima ce mata akai itace ta haifeta amman yanxu bata yardaba Dan dole ta binciko ta Gano shin Waye mahaifiyarta Kuka kawai take Wanda babu hawaye a cikinsa Idanuwanta duk sun canja launin kala har suka isa garin abuja Tafia mai nisa Sukai kafin su isa wani rukunin tsadaddun gidaje Inda zamu iya kiran. Anguwar da GRA Sbd tsaruwarsa Wani qaton gidane gari guda Wanda sojoji suke gadi Suka shga gidan ya tsaru yana dauke da bene hawa hudu Gidan ya gama tsaruwa dan gaba daya ma,aikatan gidan sojojine Hakan zai tabbatar mana da lallai ba qaramin ma,aikacin soja bane keda gidan Wani sashi direba ya kaisu Yadan rangwafa yace toga sashin amarya nan Ranki shi Dade hajia nafi tace to yayu kyau zaka iya tafia yace na gode hajia Haja hannun afnan din suka shga Bangaren Wanda yake dauke da faluka Da yawa komai ya tsaru a bangaren Hajia nafi ta dubi afnan tana murmushi mugunta tace wannan Gidan shine ya dace dake. Wannan rayuwar ita na zabar miki afnan Ki zauna kiyi rayuwa cikin galihu yaddah duk inda kikasa qafa akwai Masu tsaron lfyrki Kina tafia a mota a dinga miki jiniya tamkar wani sarki ko Shugaban qasa duniya tasan da zamanki Rayuwar data dace dake kenan domin ni kaina irinta naso amman Allah bai Nufaba naje na auri mahaifinki koda yake mun rabu yanxu na fara Rayuwar galihu. Na samu yancin kaina Duniya sabuwa domin gashi Naga bayansu daman na furta a baya saidai ni Naga bayansu badai su suga bayana ba Kai Alhamdulilah ta ida maganar tana wani murmushi mai tafe da daria Ran afnan ya qara dagukewa ji take tamkar ta shaqare mahaifiyar tata Sbd Baqin ciki Ta zube saman kujera tamkar mai shirin suma burinta a yanxu bai wuce taga halin Da maihaifinta da mijinta suke ciki ba Tanaji hajia nafin uwar tata ta qaraci surutun nata harta fice Zuciyata Kamar zata fashe tace lallai jahilcin mahaifiyarta. Ya wuce tunanin Mai tunani wai nan zaman aure ta daukota ta kawotayi amatsayinta na matar wani koko ya To meye sunan wannan AUREN? Baida wani sunan daya wuce AURE KAN AURE Tabbas yaqine ya tunkarota badan qaramiba Dole ta karema mijinta haqqin aurenta koda kuwa zata rasa ranta ne Kuma a yanxune karatunta zai mata rana abinda ta fada kenan Ta miqe ta nufi wata qofar gilas ta latsa ta bude ta shga Kamar yaddah ta hango ta gilashin bedroom ne ya qawatu iya qawatuwa Da gado da shimfidu na alfarma. A gefe daya dakin wankane Wanda za,a Iya hango mutun ta ciki Afnan ta zauna a bakin gadon ta rafka tagumi tana tunanin ta yaddah za,a Bulloma al,amarin bataga ta hanyar guduwaba tundata shgo gidan ganin Yaddah yake tsare da sojoji Shin idan tace ta guduma taje ina? Lallai yanxu batun gudu bai tasoba Zama ya cancanta ta samu domin warqare matsalolinta cikin sauqi Don haka tun daga inda take ta soma shirya komai a cikin memory dinta Kwananta guda a gidan in banda zaman kadaici babu abinda take Fama dashi Inbanda Ruwan sallah Jikinta har yau din baiga ruwaba Abu Kamar wasa saidata share sati babu Wanda ya leqota In bansa ma,aikatan gidan abinci kuwa har turewa take domin daman bacin takeba Daidai da wanka ya gagareta hakan yasa duk tai duhu Ta koma tamkar ba itace afnan ba mai tsantsar kyau da kwalliya A yanxu kuwa ko ma,aikatan gidan sunfita fasali duk Tabi tai wuri wuri Batasa aiki sai kuka kullun cikin kuka take Babu kuma mai lallashinta Tunanin mahaifinta da dan uwanta kuma mijinta Shike haifar mata da matsanancin tashin hankali marar misultuwa Da daddare tana kudundune saman gadinta Sbd sanyin da ake Idanunta a rufe dan ji tayi dakin ya canja mata daga sanyin zuwa zafi Ta bude idanuwan nata da sauri Tsaye yake ya zura hannuwansa cikin aljihu. Har yanxu kwarjininnan nasa Nanan Cikin faduwar gaba tai saurin tashi daga kwancen ganin yana nufota Ta daga masa hannu cikin tsawa tace karka sake ka kusantoni Tamkar badashi takeba Ya qarasa ya zauna a bakin gadon yana qare mata kallo Fuskarsa dauke da wani shu,umin murmushi Jikinta sai rawa yake burinta Allah yasa ta tsira daga sharrin wannan Mahalukin Yasa hannu ya riqo hannunta yana Wasu dashi Tsoro da fargava suka hanata iya kwace hannun Shiko a wautarsa sai yake Tunanin wai ko lagonta ya Gano Cikre da qasaita yake maganar Afnan yan mata a sannu daman na fadamiki sai wannan ranar ta kasance Yanxu gaki a gidana kuma a dakina kuma a matsayin matata Yace lallai ne babba ne ta yaddah na iya tsinke igiyar soyayyar data shga Tsakaninmu A wannan karon kuma a wannan gabar zanyi abinda nakeso dake Duk da ayanxu ban shryaba Sbd kase din dake gabana So nake Naga bayan maqiyana ubanki da wannan marar kunyan Mijin naki Sannan nazo na shimfida rayuwata dake har sai lokacin Dana gundura Tace amman ai kasan da auran wanni akaina ko? Ya tabe baki yace tome ya dameni nidai burina kawai shine na kasance dake Na kwanta a wanna kirjin shine kawai buqatata ba aure ko rashinsa ba Afnan ta dake zuciyata ta kalleshi sosai kamin tace To inason ganin mahaifina da kuma mijina inason ganin Halin da suke ciki Ya kaure da wata irin daria harda babbakawa yana tafa hannu harda hawaye sannan yace lallai duk Wanda ya shga sabgata saina karya qafafunsa Ai maadam ina tabbatarmiki da idan kikaga mahaifinki a Yanxu ba zaki ganeshiba Don na maidashi mabaraci kuma kullin danai masa duk duniya wlh babu Wanda ya isa ya

Chapter 7 of 16