Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
muka Dade muna ginawa ta zama saidai tarihi kenan Yanxu soyayyah ta da adnan ta zama tsohon yayi kenan Yanxu shikenan yayana sunyi rashin uba kenan Innalillahi wainna ilaihirrajun Abinda take nanatawa kenan yan biyun aslim da taslim suka shgo falon Da gudu suka fada Jikinta suna mata yan kwarancinsu Afnan ta kamosu ta rungume ji take tamkar ta tsaga kirginta ta shgar dasu Sbd wani santsar sonsu dake fizgarta nanfa taci gaba da rera kukan nata Kamar waqa lol Lamarin nata ya soma tsorata Kowa a gidan dan kuwa bata da wani aiki sai kuka Abinci kuwa yaddaha aka kai mata na safe haka za,a kawo mata na rana a tafi Dana safen yaddah aka kawo mata na rana haka za,a kawo mata na yammah a Tafi Dana ranar gaba daya ta daina cin Abinci ta rame Yanxu batason magana ta zama wani slent Duk inda inna taso wajen kwantar mata da hankali amman ina Abun yaci tura Dangin mahaifiyarta suna zuwa akai akai Musamman Maman nafi da take kira da hajia Itama tana zuwa anty kausar ma haka Domin kuwa sun rabu ita da mijin nata babu aure a tsakaninsu kasancewar tundaya aureta bata haihuba hakan yasa ya qaro amarya Zama kuma yaqiyin dadi musamman da amaryar ta samu ciki ta dinga hada kausar din damai gidan nasu kai taji dai ba zata iyaba nan ta nemi saki Dan daqar ya iya sakin nata domin kausar irin matannanne Wadanda da wuya namiji ya iya rabuwa dasu Yaudai lamarin afnan ya soma isar inna dan haka koda takai mata abincin rana ta samu bataci na safeba saidai dan lemon datasha Inna ta zauna tana kallonta taga duk ta fige ta lalace tayi baqi Inna tace lallai afnan kinsa ranki a wani irin yanayi Indai namijine to a lbrn maza Ba abinda kika fara gani Ki zaunba ki kashe kanki a banza a wofi. Wandama kike danshi baisan kinayiba Yanacan yana shagalinsa da wata macen ya barki anan Kina wahalar da kanki Nidai shawarata gareki kisama kanki dangana inkinqi to dan Nidai bazansa a kiramin adnan na rokeshi ya maidake dakinkiba Dan mu kanmu ya manta damu da irin alherinmu gareshi dan haka kisama kanki salama Ki cire wani adnan a ranki ki samo miji kiyi aurenki kawai Da sauri ta dago ido tana kallon inna tace yanxu da aurenya ake fada mata ta samo wani namijin ta aura bacin auren dake kanta itako ai koda cewa akai adnan ya mutu batajin zata iya sake aure Ballentana yanna raye ta lumshe idanuwanta Wasu zafafan hawaye suka zubo daga idanun Inna ta miqe gamida Jan wani tsaki mtwss Indai kayane ke kya kaisu yarnan Ki zauna ciwon zuciya ya kasheki don Indai mazane a hadisin maza yanxu Kika soma karatu lol kunji inna mazama har wani hadisine dasu. Hmmm Muje zuwa Afnan kukanta kawai take batada mai lallashinta sai a yanxune ta somajin ciwon Rashin uwa Tabbas uwa maganice dan koba komai tabbas zata saurari abinda ke cikin zuciyar Yar tata Amman banda irin tata uwar Wanda ita farautar yar tata take kota wane irin hali Wayyo umma ko a wane irin hali kike yanxu ko kina mace ko kina raye oho Haka kawai taji kewar momyn tata ta kamata so kawai take ta Ganta koda a hotone Inama ace uwar tata Kamar sauran uwaye take Tabbas data samu sassaucin kuncin rayuwa ta share hawayenta ta fada toilet Ta watso ruwa mai kawai ta murza ta dauki makullin motarta Gidan kakarta ta nufa mahaifiyar nafi. Dan kausar itama yanxu acan take Tasan idan taje can koba komai zata samu sauqin zafin da zuciyata ke mata Danji take tamkar ta zarota ta huta amman ba dama yanxu hakanma dakiyar zuciyace kawai Aleeyu na zaune a a falonsa afnan ta shgo Bayan ta gaisheshi tace gani abba Yadan miqe daga kishin kiden da yake Akan kapet din yace yauwa aafnan amshi wannan ya miqa mata wata takarda ta amsa hannunta na rawa ta soma budewa Yace yauwa duba da kyau offer ce kin samu aiki a babban kotun dake. G. R. A anguwarsu hajia wohoho dadine ya kamata tama rasa irin godiyar da zatai masa Har saida taji hawayen farinciki tace na gode Abba Allah e saka da alkhairi ya qara budi cikin jin dadi yace amin afnan Allah e maki albarka kuma yasa miki albarka A cikin aikin naki tace amin abba Yace to tashi kije dan yaga alamun tanason masa qorafi dole ta tashi ba Tare data fadi abinda ke cikin ran nata ba Ta soma zuwa office wato wai katon office aka bata mai dauke da part biyu Na ita da mataimakiyarta. Barister zainab ayuba (zee. Zee) Matashiyace mai kimanin shekaru ashirin da bakwai Da aurenta yayanta biyu salim da salima Kyakkyawace sosai Kallo daya zakai mata kasan boko ya ratsata don wayayyace gata da iya dressing Don kace don ita aka qirqiro kwalliya duniya sun shaqu da afnan Don haka ko a office ina aiki yai musu sauqi sai,a hadu a office din daya aita dumin debe kewa Yaddah afnan ta lura mustafa mijin zainab yana matuqar ji da matar tasa don ko kadan baison abinda zai taba masa ita ballentana har ranta e bace Don sauda tari idan baida aiki a office yakan dauko yaransa biyu suxonan suyita Hira cikin so da qaunar juna Kamar karsu rabu Kamar idan ta tasji ba gida zata va Wannan soyayyah ta zainab da mijinta mustafha shuke qara tunxura afnan Tace da yanxu itamafa irin wannan soyayyar adnan zai dinga nuna mata ita da yaranta ko ta rafka taguminta da hanayenta biyu Bayan ta aje Biron dake hannunta Zuciyata na bugawa a hankali a hankali Shin yanxu haka zataita dawainiya da soyayyar namijin da baisan tanayiba Anya damuwa da take ciki bazaisa xuciyarta fashewaba Dole taje ta samu adnan koda hakan na nufin rugurgujewar zumuncinsu Dole taje ta girgiza zuciyarsa Kamar yaddah ya hana nata sukuni Da sauri ta miqe ba tare data nemi shawara zuciyataba ta zari farin gilashinta dake cikin kwabarsa ta saka ta janyo katuwar jakarta ta rataya a kafada gamida Suran key din motarta ta fice A wajen falon Wanda yake tamkar qaramin falo yana dauke da qananun kujru na siba Kuda hudu biyu barin dama biyu barin haqu daga can gefe kuwa wani kantace ta Gilashi Yau anan zainab da mustafa ke zaune shida wani abokina Wanda afnan din batason ko Waye shiba batama taba ganinsaba Kallon afnan yakai kan hannun zainan Wanda ke sagale Dana mustafan Take zuciyata ta sartsy tace kai wannan masoyan sudai basu iya boye soyayyarmu koda a gaban waye A zahiri kuwa cewa tai to romiyo da juliyet nina fita idan masinja ya shgo da wadannan files din ya baki saiki shiryaminsu Kafiin zainab din tace wani abu har mustafan ya cabe yace gaskia fa madam ki Daina wahalarmin da babyna duk wani dan aiki da kikasan yanada dan wlh kidan dunga taimaka mata dan banson tana Whl sosai Mutumin dake gefensu Wanda zazna iya sashi cikin jerin maza masu kwarjini Da cikan zati ya cafke da cewa kaidai malam ka kyaleta ta aikinta kawai duk bakai ke takura mataba ka aje aikinka a office kaxonan duk ka cikata da zance $afnan tace rabu dashi ai mun saba Zainab tace Allah ibrahim karka shgarma wannan taki bada hayar da mai tausayin Nata zai kusantato kuma saita dinga takura mana Nida. Gudan jinina rabin raina Afnan tace ke nidai kinga fitata ba tare data amsa Allah shi kiyayen da mustafan ke mataba damin ta lura kular sa ita yakesonyi Kai tsaye asibitin da abbanta ya ginama adnan din ta nufa dukda batada yaqinin zata sameshi a asibitin Tayi mamakin yanda asibitin ya qara bunqasa ya zama na wane da wane Majority din likitoci duk yturawane lallai asibitin abin tunkahone a garin kano Idan ka shga asibitin ba zaka taba yarda da a. Naija kakeba don komai na asibitin safarin kalar na wajene Azuciyarta ta yabama abbanta dayi masa addu,a da tambaya ta samu aka sadata da office din adnan din Saidai masinja ya sanar da ita yana ganawa da marar lfy don haka ta samu saman daya daga cikin qayatattun kujerun dake wajen ta zauna Qafarta daya kan daya tana kada key din motarta dake hannunta Tsawon wani lokaci Bayan ya kammala da marar lfyr ne masinja yai mata iso Tana bude office din kamshi da sanyin. A. C suka dakar mata fuska ta lumshe idanun nata a hankali ta qarasa cikin office din Qaton office ne Wanda aka qawata da na,urori na zamani Komai na office din Abun kallone Ido cikin ido suke kallon juna yasha baqar suit sai juyi yake saman wata arniyar kujera ta gilashi Kallo daya yai mata ta cikin farin gilashinsa yaci gabada rubuce rubucensa hakan ya Qara ingiza zuciyata ta qarasa gabansa Ganin Tayo kansa gadan gadan yasa yai saurin tsayar da ita cikin daure fuska yace ga wurin zamanan. Sady matatace kawai keda right din kusantata ba irin,,,,,, Tunanin me yayi sai kuma ya kasa qarisa zancen nasa taja wani kujera ta zauna Tana murmushi gamida kada kai tace ba zama naxoyiba. Doctor Adnan aleeyu musawa Sunan da yake amfani dashi kenan tun a skull Tace naxone na tabbatar da abinda zuciyata ke zargi tadan rankwafa gamida Daura hannunta kan tebur din ta tallabe fuskarta da tafin hannuwanta sannan taci gaba Shin wai da gaske ka mance da wacece afnan kokodai kana sane rabuwace da ita kayi niyyah? Zancen yaxo masa a bazata don haka kallon kurillah yake mata yaga ko xai Iya tuna a inda ya Santa Sannan yace wacece kuma afnan jinsin mazane kona mata?meye hadin sunanta da nawa? Inama na Santa bare nai burin rabuwa da ita? Cike da takaici afnan ta miqe ta juya masa baya saida tai taku daya zuwa biyu sannan ta tsaya tace ta inda ka mance bari in tuna maka Nice afnan aleeyu musawa kajita yaddah sunanmu ya hadu Ka sanni a yan uwantaka ka sanni a soyayyah Sannan ka sanni a auratayyah Ta waiwayo da sauri tana kallonsa idanuwanta sun cika da kwalla Tace mai yasa ka juyamin baya yaya adnan mai yasa kakeson rabuwa dani A daidai lokacin da Nida yayanka muke buqatarka kasancewa dakai? Ji yai tamkar tana caka masa wwuqa. A qahon zuciyarsa ido waje yace ke mahaukaciya banza jahika A ina na sanki har mukai soyayyah dake dahar zaki dubeni kice wai akwai yaya A tsakaninmu? Kinje kin gama gantalinki kin samo yayan titi duk cikin garin Gano ki rasa Wanda zaki jonama yayan saini lallai dole nadau. Babban mataki akanki To inaso ki sani yar matsiyata ban taba zinaba Tunda nake Sbd haka yanxu abinda nakeso dake shine fitamin daga office tun kafin nasa securities suxo sumin waje dake get out ya fada cikin daga murya Wohohohoh wato sake baki da hanci da kunne tayi tana masa wani irin kallo na tsana a yayin da taji zunidar na wani. Juya mata juwa na qoqarin kadata Kirjinta kuwa. Wani zafi daya dauka ko giftata kazoyi dukda sanyin. A. C. Din dake office din dai Kaji hucin zafin qirjin nata Ya qara maimaitawa yace ke banza karuwa nace kibarminn ofice get out kiyi gaggawar fita tun kafin nai loosing din temper din na Cikin wani irin yanayi ta juyo ta kalleshi idanuwanta sun kada sunyi jajir Kutt ganin haka yasa nayi gefe bace bari nadan rabe kafin su sauko don Naga dukansu a fusace suke Aure. Kan. Aure Chapter27 Yace get out yaddah yai maganar har Wanda ke waje zai iya jiyoshi Juciyar afnan ta qara cunkushewa. Da Baqin ciki Tace a ranta har adnan yayi girman da zai kira iyayenta matsiyata Alhalin arziqinsu yakeci yanxu haka? Cidanuwanta suka firfito waje. Cikin zfin rai ta nunashi tace kai Dakata arziqi dan masu arziqi Wanda baisan usilinsaba In kana nufin kace ka manta dani ta yaya ka iya tunawa da asibitin da mahaifina Ya Gina maka kuma ya dauraka akai? Hmm lallai dan Adam butulune Adnan ka butulcema kyautatawan da mahaifina yai maka Yaya adnan ka butulcema kyautatawan da mahaifina yai maka yanxu har shine Abin zagi a wajena Daman duk maganganun da kake fadamin a baya duk na yaudara ne? Ka tuna abinda kake fadamin ina sonki afnan bazan Iya rayuwa babu keba Kece rayuwata kece farincikina kece jin dadin rayuwata Afnan karki sabamin alqawari karki bari na rasaki don allah Ta runtse. Idanunta hawayen dake qoqarin zubowa suka samu hanyar kwarara Tace shin yanxu ka juyamin baya kenan Haba yaya adnan ban cancanci haka daga gareka ba kuma duk zyciyar daka gani bata cutar damai kyautata mata Yaya adnan rayuwa tayimin qunci na tsani duniyarma gabaki dayanta Amman a yanxu nafi tsanarka sama da komai kaine babban maqiyina dake kassaramin rayuwa Ta gama kular dashi domin haqurinsa ya gama qarewa ya nunta da dan Ysatsa har huci yake. Sbd bacin rai yace ke malama saurara haka Na gaji da sauraron wadannan kalaman naki marasa tasiri lallai da ace film ne Da ina tabbatar miki zaiyi kasuwa To idanma mafarki kike ya kamata ki farka kuma wlh ba zan barki hakaba domin Naga alamun daman can kin saba wasa da Hankalin maza Tabbas saina nuna miki cewa ni dabanne da sauran maza don nayi alqawari sainaga bayann duk maison wasa da mutuncina Tace kayi daidai ai irin wasan da nakeso mu shirya dakai kenan Adnan a wannan karon inhar ka shirya nima a shirye nake dakai A aje masa card dinta ta fice a zafafe tamkar mai shirin tashi sama Da ido ya bita zuciyarsa na masa kai kawo yace tabbas dolene na dauki mummunan mataki Akan wannan yarinyar Dake son wasa da hankalina inba hakaba kuwa zata zame masa qadangaren bakin tulu Yaja wani dogon huci. Sannan ya koma ya zauna Afnan kai tsaye office ta nufa ko sannu da zuwan da masu gadi ke mata Bata samu amsawaba kai tsaye office dinta ta shge ta dare kan kujera Gamida hada kai da tebur wani. Sabon kuka ta bude kawai mai tsuma zuciya Zuciyata tadau zafi matuqa Tanaso ta daure don ta tabbatar da yaqi yanxu aka fara Don haka dole tana buqatar dakiyar zuciya Tayi kukanta harta gaji ta soma ajiyan zuciya da sauri da sauri Zainab ce ta turo qofa ta shgo Gamida sallama Saidai ganin halin da afnan din ke ciki ya daga mata hankali Ta qarasa da sauri tana kai lfy afnan kukafa hannunta har kyarma yake wajen dafa kafadun afnan din tana jijjigata lfy afnan? Wani murmushi qarfin hali afnan din tayi Wanda zamu iya kiransa da yaqe tace Lfy lau xainab Damuwar data Dade tana damunace ta bijiromin son mijina shine zai kasheni har lahira Da ran mijina yayana sun zama maraya da aurena na zama bazawarar qarfi da yaji Tadan saurara tana sharce hawayen da suka zubo mata sanna taci gaba da cewa Baqincikina guda a rayuwa Wanda nafiso shine babban maqiyina kuma abokin fadata Saidai daga yau. Na gama dada yanxu na gama hawayena sun qafe wlh saiya gwammace bai taba sani wata ya wai ita afnan ba Zainab tace shin wai Waye kuma kukan me kike? Ta qarashe share kallan data dan maqale mata tace Nida mijinane Nasan bakisan inada aureba bakisan koni waceceba to yau zan sanar dake Zainab taja kujera gamida tagumi ta maida hankalin nata kan Afnan din Afnan din ta qara gyara zama sannan ta zayyanne mata tarihin rayuwarta tsaf Sbd yanxu babu abinda take buqa irin shawara Tana gamawa zaina cike da tausayi tace wayyo afnan na tausaya miki Kina cikin matsala Kinga jarabawa amman sai nake ganin ba kince sady ta fada miki cewa yai loosing din mewory dinsa ba? Tace eh hakane zainab din tace to kin gani ai wannan damar sady ta samu harta samu damar fadawa zuciyarsa domin ya mance da komai har kankin kansa Afnan tace kibar fadan haka idan har ya mance da komai to maiya hanashi mancewa da asibitin da mahaifina ya Gina masa Kuma yake amsa sunan da yake amsawa tun a wancan lokacin zainab tace eh kuma hakane Afnan tace. Kawai halin maza ya nunamin don. Na rantse bai rasa memoeynsaba Kai koda kansa ya rasa gabaki daya na ranshe sai yasan ya wulaqanta wata mai sunan afnan Don na rantse saina Rama abinda yai min Zainab tace a,a daba haka kikaiba Kamata yai abi ta hanya mai sauqi wajen Ganar dashi Sannan kema saiki dinga cusa kanki amman bada hayaniyab saikiga Kin samo kansa cikin sauqi Makar waccce aka fadama wani mugun abu iido waje tace Haba Zaiban ai ko sjine autan maza na gama dashi Zaina tace a,a afnan idan rai ya baci ai zuciya bata gushewa Afnan tadanja wani murmushi tace zainab kenan ai abinda zai yuwu shi ake abinda bazai yuwuba kuwa ba,a. Cikia bata lokaci akansa Zainab tace karekice haka afnan ai duk abinda kikaga bai yiwuba To saida in babu naci akai kuma da maida hankali Akan abun Tace yanxu da sadyn ta maida hankali ba gashu ta sameshiba Haba afnan yayanki zaki taimakamawa fa Nida kaina Zanzo miki da yan dubarun da zaki sameshi a tafin hhannunki Please afnan ki duba zancena Wani murmushi takaici afnan din taja Sannan ta miqe ta sabi jakarta don tasan inta zaibab din zatabi saisu wuni Anan da wannan surutan nata Tace ni kinga tafiata kinji gaba Nidashi yanxu aka fara Zzainab ta miqe da sauri ta bita tana fadin Haba afnan gaba da mijinki bata tassoba Idanma kikace sai anyi kece da fadiwa qasa warwars don kuwa kece mace Ji tayi makar zainab din ta watsa mata qarwashin wuta don haka Ko sallama batai mataba ta fada motarta taja ta barta a wajen Inda zainab din ke jinjina kai da mamakin irin kafiya na afnan da taurinkai Kodata koma gida zuciyata bata rabu da kunciba saima ji tayi komai ya kwance mata Yar juriya da dakiyar da take da ita Ada ta nemeta ta rasa Tana kallon yan yaranta saiji tayi hawaye na wanke mata fuskar A ranan duk yan gidan saida suka fahimci rashin walwalarta A yanxu tunanina guda bai wuce ta hanyar da zatabi ta quntatama adnan da qawarta sady ba Shin ta wacce hanya zatabi tayi ramuwar gayyah? Oho muje zuwa Kamar daga sama taji wayarta na ruri Kamar ba zata daukaba sai kuma ta janyo number zainab ta gani Tai saurin dagawa dukda ba dadin yin maganar takeba daqar take amsa mata Zainab din tace yauwa afnan daman daxun kina fita wani case ya shigone mana Don haka ki bude email dinki Zakiga komai a bayyane Cikin qufula tace Haba zaina kinsan halinda nake ciki taya za,ai na iya daukar wani case Zzainab din tace kiyi haquri afnan case din mai girmane Don Allah ki bede don nasan ke kadaice zaki iya warware wannan al,amarin Ba tare da ranta yasoba tace to shikenan zan duna Tace yauwa afnan godia muke Maman Adnan na tafe cikin motarsa. Tsaleliya kana ganin motar kasan ba qaramin mutum ne a cikintaba kalar Ruwan tokace Sannu. A hankali yakejan motar da hannu daya yake Jan motar daya kuma ya tallabe kansa Kai daka gansa kasan yana cikin tsantsar damuwa Sannu. A hankali ya iso katafaren gidansa gari guda horn daya yayi mai gadi ya wangame gate din shi kuma ya tura hancin motar ciki Da hannu kawai ya amsa ma me gadin sannu da zuwan da yake masa Ya gagara da motar inda aka tanaza domin aje motoci Ya faka tasa gefen ta matar tasa sannan ya ratayo cot dinsa a wuya Jikinsa a mace yake tafian Harya isa wani qaton falo Wanda idan kana cikinsa saika rantse kace ba,a Naija kakeba. Komai na cikin falon na qasar waje ne Kamar Wanda aka tunkuda ya fada saman daya daga cikin kujerun dakin Ya kwanta gamida rufe idanunsa adnan ce kawai ke masa yawo a kwakwalwarsa Shi a duk duniya baida wacce ya tsana kamarta Inda so na zama samu dayasa an batar masa da ita daga doron qasa abinda yaketa saqawa kenan daga cikin ransa Sady ta fito daga cikin falonta ta hade cikin wani lallausan yadi na materiyal Ta qaraso gabansa qamshin turarenta ya daki hancinsa Ya bude fuskarsa a hankali yana kallonta ta shafi fuskarsa gamida yin masa murmushi Tace Yadai yallabai meke damunkane duk sai Yama nemi damuwar ya rasa Janyota yai jikinsa yace sarauniya a fadar adnan Kinyi kyau sosai fa Ta sakar masa wani lallausan murmushi hannunta saman qirginsa tana masa tafiyan tsutsa tace ranka shi Dade bakafa fadamin abinda ya batamin rankaba Yaja wani qaramin tsaki mtsss share kawai baby Nida wata yarinyace dakeson dagulamin lissafi amman barta kawai Zan taka mata birki Yaddah ko a sanya ta ganni sai gabanta ya fadi Sady tace kai sweety wacece wannan Yadan qarajan tsaki Da alamun Abun ya bata masa rai sosai yace ina wata yarinya da kika taba cewa Taxo ta daukomu daga filin jirgi wacce ta ganmu ta kwasa a guje ta barmu? Sady tace eh Inajinka yace to itace yau ta sameni har office taso ta cajamin brain dina Wai take fadamin na taba aurenta harda yaya biyu Waye ya mutu Waye ya dawo Yace kotu kawai zansa ta shga tsakanin da ita Cikin firgici. Sady tace a!a karkayi haka sweety ai abinda takeso kenan domin taita yadawa a gari kuma ta shga tsakaninmu dakai Kawai kaja mata kunne idan ta qara tunkararka ka nuna mata baka qaunar mai qaunarta Idan kuma tai wasa zakasa a tozartata na tabbatar idan har kai mata haka Zata fita hanyarka adnan yace oh ne sweety ina mamakin mutane Wai yan mata Dasun qalla ido sun ganka da kudi shikenan dawa Allah ya hadasu inba dakaiba Yanda kikasan an watsama Kaji tsaba Sady tace ni kaina ina qara godema Allah dayaban jarumin namiji kamarka Don idan ba jarumiba babu mai iya tsallakema sharrin mata Tasa hannu taja dogon hancinta tana dariya tace duk wannan dogon hancin ke dibarsu Suka miqe tare yace muje Nidai. Na watsa ruwa Kiban abinci naci Ranar Monday Tunda sanyin safia afnan ta shirya cikin wata kyakkyawan shga kai Inka ganta. Wannan danyar budurwace jagal cikin takun qasaita Bayan ta dauki abinda zata dauka ta nufi Bangaren abbanta Yana kishingide saman kujera Ta duga ta gaisheshi cikin murmushi ya amsa yace yauwa afnan Daman inason ganinki ya kamata kije kiga mahaifiyarki Don tana buqatar ganinki ta sadudu da duniya matuqa Kiyi mata uzuri afnan tana buqatar sake gabinki Afnan din ta dago ta kalli abban nata ta jinjinama tana mamakin Haquri da tawakkali irin na abban nata Fuskarta dauke da murmushi tace Abba kaje ka gantane? Cikin murmushi yace naje afnan yanxu haka tana gidan yari Sbd ciwon daya addabeta na hawan jin Cikin firgici tace hawan jini abban ido waje Yace Naku har kullun S salankss Yauwa masu fadin cewa basusan wane hukunci kotu ta yankema janar da nafiba Da kuma yaddah afnan ta samu ciki harta haihuba inaganin da alamun Bakwa biye damune shiyasa dan duk wani bayani da kuke buqata yana cikin Aure. Kan. Aure Chapter28 Ta dafe qirji tace momyn tawa zuciyata tadan tsarsy tace amman ne Abba mai yasa banjin son momyn nawa a cikin zuciyata ne? Kamar yaddah sauran mutane ke fada sai Inji jama,a na fadin wai sunfi Son mahaifiyarsu Akan mahaifinsu Amman ni abbah har nafi jin son baba hauwa a cikin raina Akan na momcyn nawa Kodai ba itace ta haifeniba abbah? Murmushi yai ya shafa kanta cike da tausayinta yace Itace mahaifiyarki afnan itace ta haifeki da cikinta Abindayasa bakyajin son mahaifiyar taki Kamar sauran mutane Sbd ko wace uwa idan ta haifi danta takan rungumeshine a Jikinta ta ciyar dashi da Jikinta ta kuma shayar dashi da Jikinta ta raineshi da hannayenta itace kula dashi cinsa shansa lafiyarsa Da komai nasa harya girma suna shaqar numfashin juna inhar yaro ya samu wannan rainon da kulawa ki fadamin abinda zaisa. Da bazai qaunaci mahaifiyarsaba Keko taki momyn ta gujeki Sbd gayu taqi daukarki Sbd kar kiyi mata fitsari Ki bata mata jiki batasan cinkiba batasan shankiba Batasan lfyarkiba don ko asubiti zan kaiki bata yaddah taje saidai na dauki baba hauwa mu tafi tare Saida kika girma kikakai shekara goma sannan tadan saki jiki dake har kuke zama kujera daya har kidan raba Jikinta Laifi kadan zakiyi mata ta kai miki duka Saidai ni wannan ya zamanmin abin alfaharine afnan don da ace ta shayar dake da Kinsha halonta a nono Da ace tajaki a jiki dakin tashi da irin tarbiyarta kinga yanxu wannan ya zame mana Abin alfahari kenan Afnan tayi murmushi tace wai yaushe su inna zasu dawo daga qauyene? Yace tun jia nasa direba ya daukosu acanma ya kwana amman inajin yau Zasu dawo tare Aleeyun yace amman ya za,ai da batun yarannan don ibrahin ya matsa Akan yanatson turo iyayensa afnan tai shiru. Ba tare data tankaba abban nata yaci gaba dacewa Daurewa zakiyi afnan zamanki a haka bazai yiwuba aure shine darajar ya mace Tunda alqali ya raba aurenki da adnan Mai xaisa ba zakibama wani damaba Idanunta Sukai jajir ta dago tana kallon abban nata muryarta na rawa Yace yanxu aurena ya mutu Abba? Wlh ni ji nake a jikina Kamar bai mutu ba Tunda Wanda igiyar auren nawa ke hannunsa be warwareba baimasan an Raba ba Aleeyu yai murmushi yace afnan kenan na lura har yanxu adnan nanan a Maqale cikin zuciyarki me zaisa ba zaki cireshiba Mai zaisa ba zaki manta dashiba Kamar yaddah ya manta dake damu da kuma usulinsa? Ba yaddah ta iya dole ta daurama kanta dakiyar duniyarnan tace dole na damu Abba Ka duba fa ka gani harsu taslim sunn fara ganowa kaiba mahaifinsu bane yara yan shekara hudu yanxu idan suka girma sukacemin Waye mahaifinsu nace musu me? Nace musu mahaifinsu ya manta dasu -ye abba? Shi kansa abban nata ya soma tausaya mata don haka ba yaddah ya iya Dole ya soma lallashinta ta miqe gamida cewa Su taslim basu fada maka a makarantarsu an shirya musu fati na musamman ba kuma ko wane yaro anason ganinsa da iyayensaba? Yace aiko ban saniba basu fadaminba Tace aiko da mamaki yaddah suketa ruruta maganar fatin na dauka sun sannar dakai Yace to shikenan idan har ban makaraba zan qaraso tace to shikenan Abba ta miqe ta fice Babbar motarta ta dauka qirar jeef ta nufi hanyar makaranTa don dama direba ne ya dau yaran yai gaba dasu tun da wuri Makarantar yaran makarantace mai tsadar gaske ta masu hannu da shuni Don haka walimar tasu ta musamman ce kai dakaga yanayin gurin kasan an kashe naira Manyan mutane sun halarci wajen a cikinsu harda mai girma mataimakin gomna da muqarrabansa don duk da yaransu a makarantar Doctor adnan musawa yana daga cikin wadanda suka halarci taron shida matarsa Sady baby Zainab ma taxo itada mai gidana mustapha da abokina Don haka afnan ta saki Jikinta Kamar babu abinda ke damunta Yara sun cashe sosai manyan mutane sun miqa kyaututtuka Sannan aka fara kiran daliban daya Bayan daya domin miqa musu kyaututtukansu Ibrahim abokin mustapha na gefen afnan sai soki burutsinsa yake Wai don kawai ya samu shiga a zuciyar afnan din amman Abun ya gagara Zainab da mustapha suma qoqarin da suke kenan wai ko Allah zaisa a dace Saidai ita hankalinsa yanakan adnan da sady taga yadda suka qara kyau fatarsu ta qara haske Kamar basuba Wani irn bakin kishine ya tokare afnan din a wuya ta kuma qi dauke kanta daga kallon nasu Don haka duk wani motsi nasu Akan idonta yake Taslim adnan musawa abinda kunnuwan afnan din sukaji an ambata kenan Yayin dataga adnan yayi saurin miqewa tsaye a cikin bainin jama,a Yana karema yarinyar kallo kyautace ta musamman aka bata inda sauran mutane keta daukarta hotuna da wayoyinsu Duk kyautarta ta dara ta sauran yaran sannan aka kira. Aslim adnan musawa Kamarsu daya da ta macen Yaran sai kace yayan turawa don kyau abinda Yaja musu farinjini kenan a. Wajen jama,a Inka kalli bakin afnan yaqi rufuwa tana alfahari yaddah jama,a kenan yayan nata Shiyasa duk fitar da abbanta zaiyi saiya Tofa musu addu,oi Daga qarshene aka kira siyama adnan musawa Aka kira iyayen yara Sukai jawabi sannan akai addu,a taro ya watse Afnan ta tasa yaranta gaba vakinta yaqi rufuwa Sbd farinciki Aslim yace Momy wai mai yasa kowa abbansa na zuwa amman ke kullun ke kadai kike zuwa? Kafin tai magana taslim$ ta amshe tace ai ance mu bamu da abban abbanki shine abbanmu ko momy? Kamar ta rafka kuka murnan

Chapter 10 of 16