Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ta kirani taimin Tatas shin ta ina zan bullo Sury tace mai yasa ba zaki kawar da duk Wanda zai kawo miki cikas ba Nafi tace ta yaya sury tace saifa kin runtse idonki kuma kin cire dan sauran raguwar imaninan dake cikin ranki dan na tabbata in janar ya auri afnan Saikin zama wata tauraruwa a idon duniya Cikin yanayin tsoro nafi tace to ta wacce hanya? Oho nima ban saniba mu hadu maybe anjima idan na samu tyme Danjin ci gaba Inama Kowa da Kowa barka da sallah Sai naxo amsar barka da sallah na Aure. Kan. Aure. Book2 Chapter 15 Nafin tace ta yaya? Sury ta qara gyara zama tace Indai kina qarqashin ikon Aleeyu. Baqin ciki bazai barshi ya barkiba don haka saiki shafama idanunki Toka tun a wannan karan ki bijirema buqatarsa Ki tadamasa hankali ki birkita masa kwakwalwa nina Gaya miki da kansa zai saduda ya dawo yana binki gwiwa biBbiyu Kuma karki sake sauraronsa kici gaba da harkokinki kawai Kin manta munada iyayen qarya ne.? Don momyn ki taqi goya miki baya Ki sanarma janar daya turo iyayensa nida kaina zan samarma afnan waliyyai tare da masu daura mata auren Qawata kibama yarki Wanda kikeso Tunda babu Wanda yai miki Naqudarta kekikasha wahalarta ke kadai Ana daura auren na tabbata da kansu zasu dawo su biki dan nasan aidai ba Zasuyi mata aure kan aureba Nafi tace lallai na yarda da shawararki qawata Amman da harna fara Tunanin yaddah zan maidama janar makudan kudin Daya turomin tare da kyautar wani katafaren kamfani Da yaimin Tace kinjifa qawata amman yarinya take neman janyo mana tsiya Sury tace h to inma kika tsaya sanya to ke kikaso Tace a,a ai banga ta zamaba yanxu Zan kirasa nace ya turo iyayensa cikin satinnan Ki gama tsara mana komai yaddah zai kasance tace to an gama Yammah likis adnan ya dawo daga aiki ya duba baiga afnan ba Don haka ya wuce Bangaren baba hauwa Anan ya sameta sunata Hira Shima ya zauna yana fadan Ya gaji da yawa baba hauwa baki rage dan burabuskon nan da kikeba? Tace babu saidai dambun masara da wata qawata ta kawomin daxun Akwai ragowansa daman afnan na rage mawa Ya miqe yana fadan lallai kam Baba hauwa wasama kike yar taki da ko sannu da zuwa idan mai gidan nata ya dawo bakiyiba Nidai ki fadamata bugu nake dan yarinyama ta sani tun yanxu Baba hauwa tace ba wannan maganarba yarinya tun rana tana kichin tana Maka Hidima shine yanxu ka dawo ko sannu da gida babu ballentana har ta kawo Maka Delisions din data hada maka? Yace aina qoshi baba hauwa bari taci nata ni naci dambun Wani takaicine ya kule afnan din tace wato abincin da ta bata lokaci tun rana Take masa dan tasan shi yafi so shine zai kwaleta a gaban baba hauwa Tace ai nasan laggonsa don haka ta miqe Da sauri ta warce kwanon dake niyyar surewan cike da batsewa Ya kalleta To kawo ko malama tai shiru Au ba zakiban ba? Allah na kwaso yunwa a office dan Allah kiban Ganin bata da niyyar bashi hakan yasa ya warce kwanon Saidai mezai gani wayam babu komai a ciki Da sauri ya dubi baba hauwa tace au na Manta ashe fa ta cinye Yadan sosa qeya yace daman baci zanba tsokanarki nake Kawomin abinda kika girka min Ta zaro ido wa? Lallaima wasa kake Ya marairaice yana fadar haba qanwata ai nasan ba zakibar yayanki ya wuni da Yunwa ba Shiyasa kike birgeni tambayima baba hauwa inba girkinkiba babu girkin dakemin Test a baki Ta karkace kai tace kayi ka gama ni kagama tafiyata Da gudu ya bita ta shge falonta ta boye a Bayan kyare yaita dube dube Amman bai gantaba Can ya hango qafarta yai saurin yaya labulen ta daka qara ya qarasa wajenta Yana fadin am sorry my love yunwa nakeji karna mutu Da sauri tace to tsaya na kawo maka Tai saurin ficewa daidai bakin koqar taci karo da mom din nata hajia nafi Gabantane yai mummunan faduwa ta babbake qofar muryarta na rawa ta Fara fadin Sannu momcy da qafafunki aida aikowa kikai naxo da kaina Tace keda baki zuwa aini nazo Muna cikin gida guda amman saina wuni ban saki a ido ba Tunda kikaga ina miki fadan ki rabu da wannan dan iskan matsiyacin yaron Sbd baida komai ne me ya mallaka da har zai iya riqeki? Banson yaron nan afnan ban qaunarki Tun yana yaronsa ba yaron kirki bane Afnan data lura adnan na jiyo maganar nasu sai taji wani iri ta Riqo hannun mommyn nata tace Muje Momy daman wajenki zani Tace naqi tafiyar baqar munafuka yanxu haka yana cikin Dakin naki Fadamin abinda yake baki da kike wannan maqalqale masan? Ta zumburo baki tana haba mommy dan Allah ki daina haka Taja hannunta suka wuce zuciyata sai rawa take Daqar ta samu ta jata sukabar wajen Bayan sun isa Bangaren momcyn natama Daqar ta samu ta kubce tanata hanzarin shga kichin domin Hado masa abincin ta dauko ta wuto falon nata bayanan ta aje ta nufi Nasa falon nanma bayanan Don haka ta nufi falon baba hauwa nanma bayanan Jikinta a sanyaye ta dawo falonta duk duniyar tai mata zafi Yanxu taya zata bulloma wannan lamarin? Ta dauko wayarta ta kirashi harya tsinke bai dauka ba Dole tasama zuciyata sa,ida saidai wunin wannan ranar haka tayishi babu walwala Bayan tayi sallar magrib da isha,i ta fito falon dake tsakanin nata da nashi ta Zauna. Burinta taga ta inda zai bullo amman tafi minti talatin bashi babu dalilinsa Ta gaji ta miqe ta nufi sashin baba hauwa Acan sukaci gaba da Hira saidai rabin hankalinsa nakan adnan Tara daidai Barci ya soma cin qarfinta don haka ta miqe ta nufi Dakinsa har lokacin a rufe yake Zuciyata a dagule ta nufi Dakinta ta jame kayan Jikinta ta fada toilet Ta watso ruwa ta rigar baccinta ta saka Ta haye saman gadonta saidai barcin yaqi zuwa gani take kamar Adnan zaizo gareta har qarfe sha daya shiru Batasan lokacinda Barci ya sureta ba Tawon wani lokaci taji tamkar tsayuwar mutun akanta Ta bude idanun nata ba mafarki takeba adnan dinne tsaye akanta Ta yunkura da sauri tana kallonsa Jikinsa a mace ya zauna a bakin gadon Lallai ba mafarki takeba adnan ne dagashi sai gajeran wando da singileti Tai saurin maida kallonta kan agogon dake Dakin taga biyu da Wasu yan mintina Tace a ranta to lfy? Ya riqo hannunta yace afnan yanxu momynki ta kirani wai bakida lfy Rai a hannun Allah naxo. Na kidime afnan bansan lokacin Dana iso nanba To amman sai na ganki kwance kina Barci afnan nidai inada yaqinin ba mafarki Naiba. Wai kona haukacene? Tambayar da basu da amsarta Kuriy kawai tai masa da idanu Adaidai lokacinda momcy ta shigo Dakin ita da abban nasu Suka maida kallonsu kansu Mumcy tace to yau ka gani da idanunka abinda nake fada Maka kana fadin ba Gaskia bane yanxu me idanunka suka gane maka? Abban nasu baice komaiba saidai wani sashin na zuciyarsa data shiga nazari Mumcy taikan adnan da duka tana ihu Wayyo alllah na bani na lalace dan iska ya batamin rayuwar yarinya Allah ya isa tsakanina dakai Kuma wlh sai munyi shari,a dakai Tsabar mamaki da firgici ya hana adnan koda lwallwaran motsi Ballentana ya kare kansa daga dukan da take masa da kuma Sharrin datai masa Afnan tai saurin saukowa daga kan gadon ta rirriqe mom din nnata tace Ki bari dan Allah mommy karki tara mana jama,a Yatsu biyar ta cire cikin fushi ta dauketa da mari Afnan ta riqe kuncin nata lokacinda Wasu hawaye masu zafi zuka ziyarci kuncin Nata ta koma kan adnan din da duka tako ina Abban saif ya tako gabanta ya riqeta ta juyo tana kallonsa Idanunta na zubar da kwalla cikin kuka tace Ka sakeni Abban afnan wallahi sai Naga Bayan yaronnan Harmu zai batama sunan gidannan ya keta mana haddin yarinya Har cikin gida? Saita qara fashewa da kuka kunji munafuka lol Aleeyu yace ya isa haka nafi shirin film din ya isa haka ai Kinyi koqari Ya kamo adnan dake duqe ya jashi suka barta nan tsaye Binsu ta dingayi da wani irin kalllo mai cike da tsana. Lokaci guda kuma ta dawo da kallonta kan afnan din tace Lallai yayi kyau afnan zaki debo ruwan dafa kanki Dan na rantse da Allah saidai Naga bayanku badai ku kuga bayana ba Duk rintsi koda kuwa zanyi yawo tsirarane saina wargaza wannan shrin naku Da In wayi gari inga aurenki da yaronnan wallahi gwara ace kena rasa gaba daya Samun duniya ya fimin komai a aruwa Daga yau zan cire tausayina akanki Zan aiwatar miki da irin rayuwar da kika zabama kanki Koda hakan na nufin rasaki keda ubankine Na rantse da Allah zanyi abinda na Dade ina zullumin yi a baya inhar kika bijiremin Hmmm meye wannan Abun sai mun hadu a nxt chapter Aure. Kan. Aure Chapter16 Ta juya a fusace ta fice cikin kunar zuciya Hankalin afnan yai mummunan tashi ta shga tsoro da fargaba mai rikitarwa Sai a yanxu take fahimtar shin wacece mahaifiyarta data haifeta. Lallai macace. Mai zuciyar rashin imani wacce so ko tausayi baisa ta Rasa duniyarta toya kenan? Ko alama Barci ya qauracema idanunta. Fargaba da zullumi sune Suka jagoranci zuciyar tata Aleeyu na zaune cikin katafaren falonsa a cikin daya daga cikin kujerun alfarman dake dakin Ruwan tea yake kurba ba tare da yasa madaraba duk kuwa da kayan Soye soyen da aka zagayshi dashi abinda ya faru daren jiya shine kawai ya tsaya masa a rai har ya hanashi sukuni Shin wai shi da wacce irin makirar mace yake rayuwa ne? Mai kwadayi marar tawakkali? Tamkar an hankadota ta banko falon ta shgo Kofar ta koma da kanta ta rufe tare da wata gaggarumar qara Hakan ya dauki Hankalin haj aleeyu ya bita da zara zaran idanunsa harta iso gabansa Lafiya Tambayar da yai mata kenan cikin Ruwan sanyi Cike da batsewa tace lfyr ce ta kawoni Tace aleeyu Tunda Naga alamun baka da niyyar kwatarma yata Yancinta Akan zaluncin da dan uwan yai mata toni Zan dauki irin nawa matakin Kai har kaine jia zakafadamin shirin film din ya isa haka To ka sani wasanma yanxu aka fara Yaja wani salihin murmushi yana kallonta yace Da fatan dai kin taNaji manyan yan wasa ko dan kinfi Kowa sanin da Babban jarumi zaki kara Taja tsaki tace Aikai zan fadama haka da fatan kana cikin shirin yin yaqi da shaidan Na rantse matuqar ina raye sai afnan ta auri janar Saidai in bana numfashi ta juya a fusace tabar falon Wani taqaitaccen murmushi Yaja yaci gaba da kurbar Ruwan tea dinsa hankalinsa a kwance Tunda afnan tai sallah daqar ta samu wani gajeran Barci ya dauketa Wanda batafi minti talatin cikinsaba ta farka Haryanxu Jikinta a mace yake ta watso ruwa ta sanya wata shaddah milk colour Sashin babanta ta nufa yana kishin gide fuskarsa sanye da farin gilashi Yana karanta jarida Aje jaridar yayi ya tashi zaune yace lfy lau afnan kin tashi lfy? Ta daga masa kai alamar eh Ya dafa kanta yace kiyi haquri kinji yata Ki zamo diya ta gari mai daukar qaddarar da Allah ya daura masa Nasan ban miki adalciba na rashin zaba miki uwa ta gariba Kamar yaddah manzon Allah yace ku zabama yayanku uwa ta gari Na rantse miki ban biyema zuciyataba wajen zaben macen data cancanta ta zame miki uwa ba Qaddara ce daga Allah nasan mahaifiyarki na biybiyarki da sharri Domin janar Kowa ya sanshi yasan wayeshi Babu iyayen kwarai da zasu yarda su bashi aurar yarsu Dukkan wani laifi da kika sani janar nayinsa sannan wannan janar din da kika Gani yayi riddah Yabar addinin musulunci gabadaya dan yanxu Dukkan dabi_unsa basa kama Dana. Musulunci Taya zan Bama wannan mutu yata Yace ki kwantar da hankalinki afnan babu mai miki auren dole Kuma Dukkan mai sharrin mai sharri zai koma kansa Don Allah na tare damu Ki kwantar da hankalinki kinji afnan? Cikin sanyin jiki tace to abba Kwance take kan makeken gadonta tana dudduba littafanta Na makaranTa kasancewar jarabawa ya qarato Wayartace tai ruri tana dubawa taga momcynta ce Saida hantar cikinta ta kada ta dauka a tsorace tace Hello mommy Kixo ki sameni a sashina abinda ta fada kenan ta kashe wayar Ta tashi da sauri ta dauki dan kwalin les din dake Jikinta ta fita Hajia nafi na ganinta taja dogon murmushi. Tace gani mommy Tace ba wani matsala bane kije bafon da nake saukar baqi Baqonki nanan yana jiranki zaku tattauna Tace ki nutsu kije ku fahimci juna inkin samanma kanki Sauqi kenan in kuma kikaga dama kije kiyi masa wulaqanci Ki nuna masa bakisonsa Aure dai keda shi Kamar anyi an gama ne Don wlh ko mutuwa kikai sai nakai gawarki gidan janar Don banga mahalukin daya isa ya hana hauranki da janar ba Don harya turo da kudin aurensa da zaran kin gama service dinki za,a Daura auren Ji tai tamkar ta watsa mata wuta a fuska ba yaddah ta iya Hajia nafi taja hannunta suka nufi sashin da take saukar baqin Tamkar wancan zuwan. Sojojine a gidan ta ko ina suna tsatsetsare tako ina Tun daga bakin gate har zuwa falukan nasu baqiqqirin dasu sai jajayen idanu Tana kaita bakin qofar ta juya abinta afnan tai tsaye aranta tace shin najene kona juya Tambayar dataima kanta kenan da batada wannan amsar Tamkar wacce aka hankada ta fada falon zuciyata cike da takaici Ya hakince kan daya daga cikin kujerun alfarman dake falon kai kace Wani basarakene ko jinin sarauta Kallon tsana take masa yanxu tafijin tsanarsa maganganun abbanta na dawo mata Tamkar yanxu yake furta mata su Janar Kowa ya sansa yasan wayeshi babu iyayen kwarai da zasu yarda su aura masa yarsu Da hannu ya nuna mata kujerar dake fuskantarsa alamun ta zauna kafada ta fada masa. Tace ko daya bawai zamane ya kawoni gareka ba Illa na gargadeka a karo na karshe daka fita harkata Na fada Maka bana sonka da akwai Wanda nakeso shin wai ana so dole ne? Yaja wani katsaitaccen murmushi kafin yace yaro yarone Afnan zanso ki zauna ki natsu ki bude zuciyarki. Ki karbi sakon da nazo miki Dashi. Wanda zai zamo miki alkhairi keda iyayenki Ta zaro ido waje tace wane irin alkhairi ne har kai kake dashi janar iye? Koko zakai mana tayin kafurcin ne? Yasa hannu ya shafi gemunsa Wanda yake a aske ya kada kafadunsa kamin yace A maganata dake babu batun tayin addini kuma koda na aureki bance dole saikinbar addininki kin dawo nawa ba Kowa da ra,ayinsa amman ta yaya Kikasan wannan boyayyen sirrin da babu Wanda ya sanshi illa makusantana? Ta girgiza kai tace karkai mamakin makusancin Naka shine ya fadamin Amman me yasa kake tsoron kar duniya ta fahimci addinin da kake? Da alamun kaima kanka baka yaddah da addinin nakaba kenan ko? Yace ko daya illa inason inyi amfani da sunan musuluncinne na In bata musuluncin kuma in hallaka musulmai a duk inda suke Ina fatan ai kin gane. Tace tirr da wannan mummunan Tunanin Naka Shine a haukarka har kake Tunanin ni zan iya auranka? Lallai kayi wauta a duniya dan bani da abin tsana kamarka ka fita Harkata pasto Don kuwa babu ni babu kai in kuwa kaqi zan fassalawa duniya Kowa yasan Aqidarka Wata dariya ya shigayi harda kyalkyalawa kamin ya nunata da hannu Yace ashe Kinyi hauka kenan yarinya ai in zaki rantse da abinda yafi komai daukaka babu Wanda zai saurareki balle ya yarda dake Duk juma,a sai naje masallaci. Idi kuwa na qaramar sallah da babbah basa wuceni duk kuwa da bayi nakeba Gashi tun daga kan kakan kakana har izuwa iyayena duk musulmai ne Kuma babu Wanda ya taba auro wata qabilama balle wacce ba musulma ba Ashe kenan baki da tudun dafawa yar budurwa Tace bandashi amman zan hadaka da Wanda baya barci Ballantana kyankyadi Kuma ni hafsa afnan saidai idan gawata za,a kai gidanka Ya miqe tsaye yana fuskantarta yace kece ke za,a kawo gidana afnan Alokacinne zaki banbance kida da karatu Nai miki rantsuwa sai na mayar dake abin tausayi Wannan hukuncin na duk Wanda ya bijireminne Sannan kada ki manta uwarki hajia nafi a hannuna take Bata da buri illa duniya ni kuma zan mallaka mata duniya a hannunta A yayin data faracin duniyar zan kwace komai daga hannunta na rantse miki Ni janar. A aminu saina mayar da mahaifiyarki mabaraciya a cikin gari Sannan yai mata murmushi mugunta ya juya ya fice abinsa Ya barta da fargaba tareda faduwar gaba Taja qafafunta har sashin momcynta Tana ganinta ta shigo tai saurin tarbanta Tace yauwa yata kokefa harya tafi? Afnan ta kalleta da jajayen idanunta muryarta na rawa tace Ya tafi Momy amman wlh bada alkhairi yake binmu ba Burinsa yai mana lalata yai mana gadar zare Muna hawa ta rufa damu Mommy wlh irn maganganun..... Da wata gigitacciyar mari ta tsayar da ita har sai dataga wuta Dagata tace da ita munafuka kawai yanason yaga bayanmu ko kinason kiga bayana Waike ni zakiyima wayau to tun kafin a haifeki nasan wannan Afnan wlh da nasan zan rainaki ki girma daga baya ki dinga bijirema umarnina da wlh tuni na badake cikin firgici afnan din tace dakin badani gawa? Aure. Kan. Aure Chapter17 Ita kanta momyn nata tasan taso ta kira ruwa Cikin tsawa tace ficemin da gani tun kafin raina ya gama baci Kasa cewa komai tai saima juyawa da tai tabar falon Ga wani ciwon kai daya adddabeta Kamar kan nata zai rabe Adnan bai dawo gida yauba sai Bayan sallar magrib kasancewar patient sun masa Yawa yana dawowa sashinsa ya wuce ya watso ruwa gamida Canja kayan jikinsa Sannan ya soma tattara yan tarkacensa Tamkar yaddah abban nasa ya umarcesa Afnan na ganin shigowarsa tai saurin qarsa abinda take ta nufi Bangaren nasa Yana tsugunne yana rufe jib din jakar nasa ganinta da yai Kamar daga sama yasa Ya miqe ya karasa gabanta. Yace afnan wlh nayi mising dinki Yau gaba daya ban gankiba yahan yasa wlh nakejina tamkar wani maraya Yini dayafa kenan afnan inaga kuma an hanani ke gaba daya? Wlh da bazan san halinda zan shigaba ya qara matsawa kusa da ita Muryarsa na rawa yace afnan babban burina a rayuwa bai wuce ace yau mun wayi gari amatsayin ango da amarya ba Inhar wannan burin nawa ya cika to banida wani sauran buri a rayuwa Dan Allah afnan duk runtsi karki juyamin baya duk da nasan mommy batason abin Amman inhar taga kinasona da gaske tazata amince ta rungumeni a Matsayin sirikinta Ni kuma sai nabama marada kunya sai anyi alfahari da auren mu Na rantse miki zaki sameni miji na gari mai tattalin iyalansa Wanda zai iya bada rayuwarsa dukiyarsa jikinsa karfinsa akansu Har abada bazanci amanarkiba duk runtsi karki kujeni ni kuma duk tsanani ina Tare dake Afnan tace karka damu yaya adnan insha allahu zaka sameni mai sadaukarwa akanka Dan nidin da kake gani daman anyinine dominka Mai gidana raina fansane a gareka jikina da jinina duk nakane Motsina da tunanina duk Nason ganin biyan buqatunka ne Yaya adnan I luve u Farin cikin da yake alokacin bazai misultu ba Ya rataya jakar tasa gamida cewa daddy tace Na koma sbn gidan daya gida nama da zama kafin bikinmu dan an rage bikin nanda wata daya da zarar kin kammala service dinki Don haka kinga ai yanada kyau naje naci gaba da gyare gyaren gidan da amaryata zata tare ko? Ta daga masa kai alamar eh Saida ta liqe masa har sabon gidan nasu ta rakashi Gidan ba wani babba bane saidai ginin gidan da tsarinsa ya tafi da hankalinta Ji take tamkar a barta a ciki ta zauna ta gyara masa ko ina na gidan sannan ya daulota ya dawo da ita gida Bayan ya kaitan sashin baba hauwa suka wuce sukasha Hira sosai Sannan ya koma sabon gidan cike da kewarta Afnan jarabawa tadau zafi. Jarabawar kammala Makarantar nata don Haka ta cire tunani da zullumin komai ta maida hankalin nata kan jarabawar Cikin ikon Allah ta kammala jarabawar tata duk Tabi ta rame Sbd janar ya matsa mata lamba Duk da Shima idan tai masan ba kanwar lasa bane Gashi adnan Allah ya daura masa zafin kishin tsiya duk Tabi ta damu don haka Ta sami abbanta ta sanar dashi yai mamakin yaddah nafi ke kawo masa Qato cikin gida ba tare da izninsa ba Zuciyarsa ta baci yace taje kawai zai dau mataki Baiyi niyyar tanka ma nafinba yayi niyyar barinta da halinta saidai hakan bai samuba don Washe gari misalin qarfe hudu na yammah littafin babba a hannunsa yana dubawa Hajia nafi ta fito sanye da wata Riga da siket damammu sun kama Jikinta har sashin pnt dinta ana gani ta daura wani yalolon gyale Ta daura wata qatuwar jakarta saman kafadarta Hannunta guda kuma nna riqe da Baqin gilashinta da. Key din mota Wanni irin kallo mai cike da zargi aleeyu ya bita dashi Ganin tana niyyar ficewa yasa ya tsaidata ta kiran sunanta da kakkausar murya Nafi!! Ta waigo a slow tana kallonsa kamin tace yadai? Tambayar rainin hankali amman saiya dake ya jefa mata tambaya Da izininwa zaki fita? Taja wani murmushi rainin hankali tace kamarya? Har wani izinin wani zan Nema idan zan fita? Ina Tunanin Kamar ka manta da yar boko ka aura ba yar tallar furaba ko? Yace ai gara jahilima dake dan kuwa shi ansan rashin sanine ke kuwa fa? Kokuwa kin manta da kedin ajeki akai ba zaman kanki kike ba? Tace ai duk daya wai ancema makaho ga fitila Saidai inason sanar dakai da na gaji da zaman rashin yanci da takurane shiyasa Da fatan ka fahimta? Don haka nakeso na rayu a yaddah nakeso kuma nayi yaddah nakeso A cikin gidana Yace ahh wannan ne baki isaba Indai har kina qarqashin ikon Aleeyu ne Toki sani Kinci qarya kin kwanta da yunwa wannan kalar iskancin ba!a gidan aleeyu ba Taja wani tsaki tace to saika sauwaqema kanka inhar kana nunanin kanada wani ikone Ta juya ta fice ta barshi sake da baki Yinin yau yaima afnan dadi musamman yaddah suketa shirye shiryen bikinsu ita da adnan Don sauran sati guda daurin auren Adnan ya gama buga iv Wanda zata rarrabama qawayenta don haka tun safe Ya dauketa ya dinga zagayawa da ita wajan qawayenta tana rarraba musu Sai yamma likis suka nufo hanyar gida bawai don sun gamaba sai don gajiyar da sukai Gidansa suka nufa sukai sallah ya tayata suka gyara gidan sanna suka shga kichin Tare babu Wasu kayan abinci a kichin din daga indomi sai kwai da conplex Tare da kayan tea Ta kalleshi tace kai yaya adnan wannan sune kayan abincin? Ya lankwabe kai yace toya na iya afnan daga dafa indomi sai soya dankali da hada tea na iya bandasu ban iya kirka komai ba Yaddah yake maganar har saidaya bata tausayi Yace amman in munyi aure zaki koyamin ko? Yaddah in mun samu baby's *n dinga shga kichin ina dafo muku ko? Lumtse idanunta kawai tayi ba tare datace komaiba da sauri yasha gabanta yace Dubeninan afnan idan munyi aure yaya nawa zaki haifamin? Kinga nidai inason yaya dan Allah zaki fara da bibbiyune ko uku uku Wani irin kunyane suka rufeta nanta hadamasa abinci mai raida lfy Bayan sunci sun koshi ya dauketa ya maidata gida ya dawo nasa gidan Cikin dare adnan yana kwance Bai Dade da gama waya da afnan ba Barci ya sureshi mai nauyi Kamar cikin mafarki adnan yaji ana tashinsa daga nannauyan barcin daya Sureshi Kamar inuwar mutanene suka zagayshi yai saurin bude idanunsa ashe kuwa ba Mafarki yakeba Ya tashi zaune cikin inda inda yace. La...la...fiya malamai? Meya kawoku nan? Kaya daga cikinsu yace kwantar da hankalinta dan samari Babu abinda mukaxo yin Maka saidai baka umarni Cikin dakiya irinta jaruman maza adnan din yace to amman mai Yasa bakuxo da ranaaba sai da dare? Yace sha kuruminka dan samari. Zamu hada makane da gargadi Nasan kasan afnan yar gidan Alhaji aleeyu ko? Adnan din yace eh nasanta yace yauwa dan gari Kumaa kasan Waye ke sonta uban gidanmu genar abdullahi aminu aabbah ko? Yace tabbas na sanshi Mutumin ya girgiza kai yace amman yaro kayi ganganci wajen wasa da rayuwarka Ai saida raine kai takara da Wanda zai iya ajalinka ba tare da wani ya sake tuna sunankaba Adnan din yake kai kuma ka manta da ba,a kaina aka fara sadaukar da rai Akan soyayyah ba? Dan maatashin mutumin yai murmushi sannan ya kalli sauran Wanda suke tare dashi din sai kace masu tsaron mai layar zana Yace lallai yaronekai adnan kake ko? To inaso da in gargadeka daka fita Harkar oga inba hakaba to wlh lahira zatai baqo Umarnine wannan ba shawara ba inkuwa kaqiji... Ya zaro wata sharbebiyar wuqa daga kugunsa Ya daura a wuyar adnan din yace Kaga wuqarnan da umarnin mahaifiyar afnan Zamubianbi da tuni na raba kanka da gangan jikinka So da yake daqiqiyace batada tunani shiyasa oganmu yace Mu fara Maka da gargadi inkaqiji to saimu aikata Maka Dan wlh saina raba kanka da gangar jikinka Don haka shawara ya rage gareka dan samari ya cire wuqar daga wuyar tashi yai Gaba suka rufa masa baya Hmmm adnan dai ya shga tsaka mai wuya Janar da nfi sun fara tsoratashi ya abin yake Muje zuwa Danjin shin ya abin zai kasance Aure. Kan aure Chapter 18 Adnan ya shga tsananin tsoro da rudani Daidai da dan tsarsa ya kasa motsawa har aka kira sallar asalatu Saida ya jiyo ana kabbara a Wasu gurare sannan ya miqe daqar yayo sallar Bayan ya gama ya dinga rogon Allah daya cire masa tsoro yasa masa Dakiya Akan duk wata barazana da za,ai masa Ya Dade yana Koro addu,o,i sannan ya shafa yaci gaba da lazimi Gari na gamayin haske ya miqe ya suri makullin motarsa yabar gidan Alhaji aleeyu na tsaye inda motocinsa suke Anata faman gogewa masu tsaron lfyrsa wato escote dinsa suna Tsaytsaye da alamar wata tafiyace ta taso masa Adnan ya faka motarsa ya fito Da sauri ya nufi inda abban nasa yake yai saurin duqawa yana gaidashi Yace ina kwana daddy yace lfy lau adnan wannan sammako haka ko duk na zumudin ganin iyali ne? Adnan yai murmushi yana Susan keya yace Wlh abbah jiya ban runtsaba Wasu mutanene suka shgomin Saidai sun sanar dani wai aikene daga janar Sun tsoratani sosai Abban nasa yadanyi shuru nadan wani lokaci kamin yace kai yanxu ya kake ganin Zamu bulloma lamarin? Adnan din yace Abba janar nada mummunan hatsari a garemu shiyasama na Baro gidan Nidai nan zan zauna Abban nasa sai murmushi yace Adnan ka zamo jarumi mana dakakken namiji wannan ne zaisa janar Ya kasa galaba akanka Yace amman Tunda harka tsorata to zan tura securitie uku gidan Tunda daman babu mai gadi a gidan Sannan ka shirya yanxu kaida afnan Direba ya daukeku ya kaiku can kauye dan acan za,ai sha,anin bikin naku Da zarar an daura auren zakuwuce hajj Bayan aikin hajj daku sai ku wuce qasashe biyar duk Wanda kuka zaba kumin magana dan na gama shirya komai Ciki wata bakwai kawai zaku gama honny moon din naku ku zdawo Sbd tafiyar afnan Din bautar qasarta Kaga kenan lokacin da zaku dawo komai ya wuce farin ciki fal a fuskar adnan Yace mun gode abbah Allah ya saka da alkhairi kuma ya qara girma yai murmushi yace Ka shiga ku gama shiryawa ku wuce nima abuja zan wuce. Daganan Insha allahu zan wuce can musawan nanda jibi Adnan ya shga godia sai dayaga shgar abban nasu mota sannan ya juya ya shga cikin gidan Cikin zumudi a falonta ya sameta ttanata harhada kayanta Ya lallaba ya rufe mata ido daria tayi lokacin data shaqi kamshin turarensa Afnan din tace naso ace nine na fara Maka wannan albishir din shiyasama na Hana Abba ya fada Maka tun jia Zagayowa yai gabanta ya zauna irinn zaman cin tuwo Ya tallabe kumatunsa da hannunsa yana Kallonta itama kallon nasa take Saidai ba zata jure kallon tsakiyar idanunsaba dan kwarjinin nasa yai mata yawa Ta saukar da kanta qasa tana wasa da yan yatsunta Cikin sanyayyar murya yake kiran sunanta Afnan Ta kasa koda kwakkwaran motsi ballet ta dago ta kallesa Bai tsayaba yaci gabada Afnan I always want to be with u Kallon fuskarki kawai kan sani cikin nishadi inason akoda yaushe Na dinga kallon fuskarki Wlh afnan idan na rasaki zan iya mutu... Tasa hannu ta rufe masa bakin nasa tace yaya afnan Babu abinda zaisa ka rasani Ya girgiza kai alamun baison furta mata abinda zai tada

Chapter 6 of 16