Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
lashe takarar kujeran gwamna ba qaramin. Cikin farin ciki sukeba a wannan rana Washe gari kuma aka daura auren aleeyu musawa da kausar muftahu. {Woooooo. Hehehe abu yayi} Daurin auren ya samu halartar manyan masu kudi yan siyasa da shuwagabanni Afnan tafi kowa farin cikin auren mahaifinta da antynta Don daman ita burinta guda abbanta yai aure. Gashi kuma yayi A ranar da aka daura auren a ranan ta tare Tana gidan aka rintsar da alhaj aleeyu a matsayin gwamna saida akai dan gyare gyare sannan suka tattara suka koma gidan gwamnati Alokacinne kuma aleeyu yasa aka maida auren afnan da adnan ba tare da dayansu ya saniba. Sbd wasan yan burum burum da suke gaba daya sunqi tsayawa su sake da juna ga yaransu sun girma don yanxu haka suna promary two ne Aleeyu baibi takansuba yasa aka Gina musu katafaren gida aljannar duniya. Babu abinda ba,a zuba na more rayuwaba Komai daga qasar waje aka kawoshi Daidai da sutura saida aka sakama kowannensu sabbi Gidan ya tsari matuqa fiye da tunanin mai tunani Anty kausar ce kawai tasan abinda ke faruwa don haka ana gobe zasu tare a gidan ta kira afnan Falonta ta zaunnar da ita tana wani murmushi Tace afnan inason ki nutsu ki dauki abinda zan fada miki ki ajeshi a qarqashin zuciyarki Ba kuma wani abu bane afnan so nake na sanar dake matakan zama da mijine Shi namiji da kike gani idan har kinason mallakarsa saikin riqe abubuwa guda goma. Na farko shine 1]haquri afnan saikin zamo mai haquri duk rintsi karki zamo mai sa,insa da mijinki duk yaddah takai daya bata miki rai danne zuciyarki. Kibar abun a zuciyarki ubangiji da kansa na cewa ina tare damai haquri Waye mai haquri Wanda yanaji yana gani za,a bata masa a cucesa a kuntata masa amman ya nuna komai ba komai bane. Ba kuma don bashi da yaddah zaiyiba 2}ki zamo maiji kiqi ji mai gani kiqi gani Meye ji kiqi ji shine kinaji da kunnenki za,a bata miki amman ki nuna bakimajiba Ko ai miki abu kina gani don daman don ki ganin akayi to saiki nuna bakima ganiba 3]saikin zamo mai ladabi da biyayyah yi nayi bari na bari Duk abinda mijinki ya nuna yanaso to kiyi qoqarin yin masa. Wanda ya nuna baiso kuwa duk yaddaj ranki. Keso toki yi haquri ki barshi Idan mai gidanki yace mikomin wannan karkice masa Kai kaima akwaika dason sa aiki kafa fini kusa dashi A,a miqe kije ki dako masa idan kin kawo masa ki risina sannan ki bashi Afnan dai zaune take tana sauraronta harta Kai I zuwa na goman na sihune mai cike da darussan. Zama da miji Sannan ta dinga fada mata magungunan da zata tanada wajen gyara jikinta kala kala Afnan tai murmushi gamida cewa aini anty wannan nasihar taki dama bari kikai Har sai Lokacin da zanyi aure. Don kuwa zataimin amfani sosai amman kuwa yanxu zan iya mantawa da Wasu abubuwan Anty kausar din tai murmushi sannan tace maganr da muke dakema yanxu. Haka na Gama tanadar duk abindaya lissafa miki don yanzuma zaki soma amfani dasu Afnan ta zaro ido zatai magana anty kausar din ta daga mata hannu alamun batason Jin komai Dole taja bakin nata tai shiru ta dinga bin anty kausar din da kallo Tun daga abubuwan sha Dana ci hardana hayaqi babu Wanda bataiba a gabanta Washe garima tunda safe masu gyaran jiki sukaxo suka fara aikin gyarat itadai in banda ido babu abinda take binsu dashi suka gyarata tsap masu kwalliyama sukazo suka duqufa ita kanta tayi mamakin irin kyan datayi Da yamma likis. Aleeyu yasa aka kira masa afnan ta lulluba da mayafi Adnan ta samu a zaune gefen Abban nata don haka itama ta samu waje ta zauna. Tana sauraron Abban nata Aleeyu yace. Assalamu alaikum warahmatullahi ta,ala wabarakatuhum. Ya jama,atul musulmi Da farko inason. Nuna godiyata da allah daya nunamin wannan ranar mai tarin albarka Wanda zan iya cewa banida sauran wata matsala a rayuwata burina ya Gama kammala Makasudin taraku anan lkuwa shine son sanar daku aurenku da aka mayar nakeson nayi. Ranar alhamis dinnan data gabata don haka na hadaku anan ne don nai muku nasiha Dukda nasan Bawai rashin iya zaman aure bane yaja muku rashin jituwankuba Amman dukda haka inason ku zamo masu haquri juriya da riqon amana Wannan shine jigon zaman aure Afnan kibi mijinki sauda qafa yi nayi bari na bari. Komai zaki zama a rayuwa afnan a qarqashin mijinki kike a qasa dashi kike Dole yasaki kiyi kiyi. Kuma yace ki bari ki bari Aljannarki tana qarqashin diddigensa Kuma har abada baki da kamarsa domin yafi iyayenki Iko dake Sannan kaima adnan kasan afnan yar uwarkace. Har abada Baka da kamarta. Don haka ka riqeta amana ko bayan raina adnan karkasa afnan tai kukan maraici Ka fito da soyayyar da kake mata a fili karka boye koda digo wannan shinne abinda zai kawo muku Jin dadi azaman takewar auratayyar ku domin ita rayuwar aure rayuwace. Ta soyayyah da kaunar juna Don haka yanxu ku tashi ku tafi gidan da nace kaje ka duba idan yayi Maka kace yayi To na mallaka Maka shi duniya. Da lahira ga takardun Adnan din yasa hannu biyu ya karba gamida godiya Sannan aleeyu yasa hannu ya zaro Wasu takardu biyu yace karbi wadannan na jikokinane. Aslim da taslim takardun estate ne guda biyu Sannan itama ya bata kyautar wani kamfani dayasa aka Bude masa sabone bai Dade da zuba ma,aikata a cikinsaba Sukaita rafka masa godiya sannan adnan ya tashi ya fice afnan kuwa kasa tashi tayi sbd ji tayi abin yaxo mata banbara kyaui Anty kausar ce ta miqe gamida kama hannunta suka fice qatuwar jaka ta dauko ta zuba mata magungunan data hada mata na mata sannan ta rakota har bakin mota gamida yin mata nasiha Yana zaune cikin motar qatuwar gaskece mai numfashi Securities suka Bude mata gidan baya ta shiga inda adnan Din ke ciki yana kwance abinsa sannan dreba yaja motar sukabar harabar gidan Babu Wanda ya tankama wani a cikinsu kowa da abinda yakea saqawa a cikin ran nasa Har suka isa katafaren gidan aljannar duniya Yanada manyan gate har biyu da Babban qofa a ko wanne gate da masu gadin wajen Iya haduwa gidan ya hadu don idan mukace zamu tsaya fasalta yaddah gidan yake sai book din yakai na biyar Dana shiddah A harabar gidan ga ma,aikatanan kowa nata aikinsa Suna fitowa daga motar dukkan ma,aikatan gidan suka nufosu har rige rigen isowa suke Suka zube suna kwasar gaiSuwa sannan duk suka gabatar da kansu Bayan sun Gama kowa ya kkoma kan aikinsa su kuma suka nufi cikin gidan afnan ta dingabin falukan da kallo Komai na gidan ya qayatar kamar ba,a naijaba Matattakalan bebe suka haye inda sukai rawun daidai Nan sukaci Karo da Wasu manyan qofofi daya ta hannun dama daya ta hannun hagu. Sai kuma daya a tsakiya Kofar da take tsakiya nanne sashin yara wacce take hannun haqu ita zata sadaka da Dakin uwar gida dayan kuma wacce take dama zata sadaka da Dakin mai gida Nan ya nuna mata bangaren nata ta nufa shima ya nufa nashi Zuciyata ta Gama tsinkewa da abubuwan da aka qawata bangaren nata dasu batasan Lokacin data duqa tana shafar wani dan qaramin table dake tsakiyar dakinba Ta Dade tana santin kayan sannan ta miqe ta nufi toilet ta watso ruwa gamida gyara Gashin kanta ta tufkeshi gamida feshe ko,ina na jikin nata da turare Wasu yan ubansun kayan barci tasa. Ta koma ta zauna saman gado tana lallatsa wayar tata amman. Bangaren xuciyarta nakan adnan ne. Ina yakene? Ina ya shiga? wannan shine tunanin daya hana zuciyata sukuni Har wajen qarfe tara babu adnan babu dalilinsa Abu ya damu afnan arai harta kasa daurewa ta suri hijab ta sauko qasan ko zata ganshi aiko yananan hankalina nakan. T. V din dake manne a jikin bango yana kallon ball Guri ta samu ta zauna amman babu Wanda ya tankama wani. Idanuwansu nakan allon. T. Vn amman zuciyoyinsu na liqe da juna Duk saima afnan din taji ta tsargu kaman kallonta yake. Don haka ta miqe ta haye saman ta barshi anan zaune Ji yayi duk kallonma ya gundureshi don haka ko minti goma batai da hawaba shima ya haye ya nufi bangaren nata Harya murza qofar nata sai kuma yaji ya kasa zuciyarsa na cike da tsoro. Gani yake afnan ta daina sonsa yana ganin kewar mijinta a cikin kwayar idanun nata Don haka ya fasa ya nufi sashin nasa Afnan kuwa tundata shga bedroom din nata ko motsi ta kasa sai juyi kawai take. Tome adnan ke nufi da shareta din da yai? Ko ya daina sontane Da wannan tunane tunanen har barci ya dauketa ba ita ta farkaba saida aka far Kiraye kirayn sallah bayan tayi sallah Akan sallayar tata ta zauna tanata aduun,oi har gari yau haske Bayan ta shiga toiket ta watsa ruwa ta hade cikin wata danyar atamfa ta sauko qasa domin karyawa Kai tsaye dinning area ta nufa har ta harhada abubuwan da zatacin taga yar gajeran takarta a gefe ta Bude gamida fara karantawa kamar haka Salam Ga makullin wadruf din dakinanan ki Bude ki cire kudin da zai isa ki Bama direba yaje yayo miki cefane ki hadamin abincin da zanci karki ajemin na wani can Nina wuce office Ayimin addu,a Tana gama karanta takardar wani haushi ya nausar mata zuciya wato bazai ma iya zuwa ya fada mata da bakinsaba kenan Ta kada Kai sannan taci gaba da braek dinta tana kammalawa itama ta samu ta karda ta rubuta masa yar wasiqa kamar haka Me za,a girka Maka mai gidana? Taja wani gajeren murmushi ta aje masa sannan ta nufi cikin gidan domin qara duddubawa Adnan ya dawo gida a yinwace don ko karin kumallo bai samu yayiba Yaja kujera ya zauna kwalin lemo ya soma budewa ya bulbulama cikin nasa yana qoqarin dudduba abunda aka girka masanne yaga yar takarda Yana karantawa wani takaici ya daki qahon zuciyarsa A fusace ya miqe ya haye saman tana lafe saman kujera a Dakin nata ya shigo Afnan kin rainani ko? Ni abokin wasankin? Afnan ta zaro ido ta tashi tsaye tana fadin me kuma nayi yaya adnan? Cikin zafin rai yace ban saniba meye amfanin rubutun da kikai kika ajemin? Taja gajeren murmushi tana girgiza Kai tace tokai yaya adnan meye amfanin nakan? Hannu ya daga zai dauketa da mari ta fasa wata uwar qara ta maqalqaleshi. Wani irin yanayine ya bijiro masa ko ina na Jikinsa yaji duk ya saki. Kafafunsa kamar ba zasu iya daukarsaba Muryarsa na rawa yace sakeni Xikin muryar shagwaba tace allah bazan sakekaba yaya adnan marinafa kace zakayi Yace sakeni babu abinda zan miki Ta qara maqalqaleshi tace allah nidai naqi wayon Wata irin nannauyan kasalace ta saukar masa da ko dan yatsunsa bai iya dagawa. Tai saurin sakinsa ganin suna shirin faduwa. Zata ruga yai saurin zanyota ya mannata da Jikinsa Ya miqar da kansa yana sinsinar kamshin jikinta har izuwa kirjinta Ananfa zance yasha banbam don ita kanta tasan sunyi mising din juna Shi kansa admin da sukaga zaqewar tasa taso tai yawa waje suka kadosa sukace idan kaji haushi kaima kayi auren Lol ba damuwa lokacine Nasan da yawa zasuso Jin yaddah rayuwar hajia sury qawar nafi ta qare da kuma yarta sady. Sai ku biyoni gobe a Last chapter. Mean qarshen. Book din a gobe idan allah ya kaimu zamu kallama wannan book din don har nasa a fara mana cigiyar Wanda zamu fara koda zuwa Monday ne idan ina freee Naku har kullun Aure. Kan. Aure Chapter42. The. End. Qarshe Basu suka samu sakin junaba sai bayan ana Kiran sallan magrib afnan na manne a jikin nasa a tare sukai wanka gamida sallah Suna gamawa ta miqe ta nufi kichin din dake cikin falonta abinci mai rai da lfy ta hada musu Yanaci yana santi shi kansa yasan yayi mising din girkin afnan din bayan ya gamane ya fita masallaci domin yin sallar isha,i itako tailet ta fada ta dauro wani sabon wankan. Bayan ta fito nanma ta bata kusan awa biyu a gaban miro bashi ya shigoba sai misalin qarfe tara na Dare. Yana shigowa bangarensa ya wuce yaje ya watsa rua gamida canja kayan Jikinsa. Jallabiyace fara sol ya sako sannan ya nufo nata sashin Tana kishin gide saman doguwar kujerarta tasa laptop a gaba gamida rapka uban tagumi da alamun abinda take kallo yayi mata dadi matuqa Hannu yasa ya dauke laptop din afnan ta zabura cikin shagwaba. Tace Kai yaya adnan don allah ka bani Ya harareta gamida rufe laptop din ya janyo hannunta yace zonan na Rama Marin Dana manta Daria tayi ta maqalqale a gefen kafadarsa ya kamo karan hancinta yace wlh sai kika tunamin Lokacin da kike fadin Saiya maqe murya yace yaya.... Tai saurin zarewa daga jikin nasa tana bubbuga qafafu cikin shagwaba take fadin nidai wlh banaso yaya adnan ka daina Daria ya shiga tintsirawa data gane kular da ita yakesonyi saita tashi ta nufi inda ta qara shirya masa abinci yace Kai afnan kasheni zakiyi ba daxunnan naci waniba yanxu kuma kin qara dafo wani Bata tanka masaba ta nemi waje ta zauna shima da saurisa ya qaraso inda take din Ta zuzzuba masa komai gamida tura masa gabansa Kamshin abincinne ya daki hancinta baisan Lokacin daya ware ciki ya nadi abincin son ransaba Ita kuwa tsatstsakura kawai tayi ta goge hannunta da tissu wai ta qoshi. Sannan ta miqe ta nufi bedroom din nata ta zame kayan jikinta ta dauko wata yar figilar rigar barci ta sanya. Iya cinya sake gyara Gashin kanta tayi ta sakeshi har gadon bayanta. Sannan ta qara gyara fuskarta ta feshe jikinta da turare. Ta nufi lokar dake jikin gadonta ta. Handa bag dinta. Ta zuge gamida dauko kulli daya cikin magungunan da anty kausar ta bata ta juye a cup ta dauko peak milk shima ta juye bayan ta kadashi sosai sannan ta farasha Ta samu wuri a bakin gadonta ta zauna tana cikin shanne adnan ya shigo. Yana sanye da rigar barxcinsa mai hade da wandonsa Kallo daya afnan din tai masa ta kauda Kai Ya qaraso gabanta ya dauke kofin da take qoqarin dauka domin kaiwa bakin nata Afnan ta bishi da kallo ido waje ya daga mata gira yace yadai? Ta yamutsa baki tace kaban abuna mana Ya girgiza Kai alamar a,a cikin shagwaba tace sbd me? Yace aike wata baiwace daga allah afnan basaikin sha abinda zai kawo miki ni,ima ba Damanke can duk Wanda ya kalleki yasan ni_imatu ce Wani irin kunyace ta saukar mata tai saurin wayancewa Ta miqa hannu ta wufto kofin gamida cewa niban abuna kasan ko meye a ciki Ya miqa hannu saiya amshe ita kuma taqi yarda Ta miqe da sauri domin guduwa ya janyota Jikinsa yana fadin ina zaki tofa daganan zace ya sauya salo Washe gari misalin qarfe sha daya na safe afnan na kichin domin hadama mai gidan nata abinci. Yar alamar dake nuna akwai baqo tai qara Don haka tana daurawa ta sauko qasan don ganin ko wacece Zainab ta gani zaune Akan kujera. Afnan tai wata qara ta fada jikinyta suka maqalqale juna cikin zumudi Afnan cikintsantsar farinciki tace taso mu shiga ciki qawata akwai lbr Tana qoqarin Jan natane zainab din tace ke da baquwa nakefa Ta kalli inda zainab din tai mata nuni. Sady ce zaune da qafafuwanta afnan ta zaro ido waje ta bita da kallo Tana zaune cikin shga ta kamala hijabinta har qasa. Sai yar yarta dake gefenta Afnan ta juya tana kallon zainab tace ke kuma qawata a ina kika samo wannan? Zainab taja hannunta tace zauna kiji duk yaddah lamarin ya kasance. Bana gaggawa bane don zakiyi mamakin ta yaddah na kawo miki sady har cikin gidanki Toba wani abu bane Jia ina zaune a. Office matarnan taxo ta sameni. Ta sanar dani cewa afnan take nema Na fada mata kina hutu aikine sbd baki Dade dayin aureba Ta rokeni konasan gidanki? Da farko da nace mata, a a kasancear ban santaba Ganin haka yasa ta sanar dani ko ita wacece kuma dalilin son ganin da takeson yin miki shine donta rokeki gafaran Abindatai miki Na gasgata gaskiyarta na yarda da tayi nadama hakan yasa na kawota gareki don allah ki yafe mata Afnan ta mayar da kallonta kan sady sbd shirun da zainab din tayi. Da sauri sadyn ta sulale daga saman kujera sukai ido hudu Tace ki yafemin afnan wlh nayi nadamar abinda nai miki Nasan alhakinkine yasa duniya ta juyamin baya Ta share hawayenta dake zubar mata sannan taci gaba da cewa afnan nasan. Nasan nida mahaifiyata mun cuceku Wlh momyna ta sanar dani ita ta sanya mahaifiyarki a harkar shan jini. Sannan ta dinga izata Akan taima mahaifinki sharri Da abun ya kwabe kuma ta guje mata taqi ta taimaka mata Har izuwa mutuwarta bataxo koda gaisuwaba Amman da yake allah ba azzalumin bawansa bane Saidai shi bawan nasa ya zalumci kansa Dodon dasu momy kebama jini wato sha jini yace a dole waishi jinin dady na yakeson yasha tare da danyen namansa Momy tai juyin duniyarnan dodo yace saita kawoshi tace to shikenan zata kawo Daman Abban nawa yayi tafiya qasar london Sai yace yau zai dawo Sai taima dodon alqawari sai kuma akai rashin sa,a yaqi dawowa a wannan ranar A haka har saidaya qara wata biyu a cikin tafiyar tasa Dodon yai mata alqawarin idan har bata kawo Abban nawaba to jininta zai shanye Don haka a ranar momyna ta matsawa Abban nawa lamba Akan ya dawo Yace mata jirgin qarfe biyu zai biyo A ranar batai barciba sbd jiran da take masa Tacemai ya tsaya ita zataje ta daukoshi amman ita da niyyar idan taje daganan kawai ta wuce dashi gurin sha jini tayi Don haka ta suri mota ta nufi airport amman babu jirgin daya sauko don haka ta dauki waya ta kirashi daria ya kamayin mata Yace haba hajiya da kin dauka Nima haka nake To inaso ki koma ki fadama dodon naki sha jini jinina yayi masa daci wlh. Kurwata ba zata ciwu a bakinsaba Donn haka in yaso yasha naki jinin duk abinda kika sani nawa na tattara. Ya dawo hannuna. Ke Harda nakima na tattara na koma wata qasar a can zanje naci gaba da sharholiyata da sauran Wasu matan Sadiya kuwa daman yarkice ba tawava don nasan duk wani ahararancin da kikeyi a gari Idan kinso kina iya daukarta kikaima dodon naki saiya... Kamin ya qarasa hajia sury ta zube anan Daganan aka wuce da ita asibiti. Sannan aka sanar dani naje ita ta sanar dani duk iya shegen data aikata Naji na tsaneta banason ganinta Na juya nai tafiyata da baqincin waini ashe shegiyace banda uba Nai kuka harna godema allah Ganin yaddah duniya tasamin ido har a jarida yasa na koma wurin momyn nawa a asibiti A Lokacin Dana sameta a jinkirta halittarta. Qafafuwanta da hannayenta duk sun shanye. Bakinta da idanunta sun jirkice. Bakin sai zubar da yawu mai wari yake. Hancin na zubar da magina Asibitin suka dinga cajarmu kudi duk dan wani abu dake hannuna Dana mahaifiyar tawa saidaya qare Daga bayama sai sukace basu Gano ainihin ciwon dake damuntaba don kuwa idan har suka gwadata komai lfy Suke gani Ganin ciwo baya baya sai ci gaba yake yasa na dinga saida qaddarar mu. Motata kawai na bari nai mana visa muka fita qasar waje domin duba lfyr tata Acan allah e ma momyn tawa rasuwa na biya kudin qasa aka binneta sannan na tattaro na dawo gida Nigeria bayan na dawone na samu dan qaramin gida mai dakuna biyu da kichin da bayi na siya nake zaune a ciki Bayan rasuwar momyn tawa duk Wasu abokan arxiqi suka juyamin baya. Babu mai kulawa dani duk Wanda na raba guduna yake. Nasan alhakinkine adnan A. Lokacin Dana ganki kinxo office dina Badon allah na taimakekiba Donna cimma burinane kawai Idanda ace babu adnan a cikin case dinnan da bazan saurarekiba. Nina fitar da adnan waje nai sa,an yayi loosing din memory dinsa Sai naxo masa a matsayin da kike garesa. Nace masa nice yar uwarsa da nakeda aurensa babana shine wandaya riqesshi da mahaifiyata Don haka na samar masa iyayen qarya na biyasu inason adnan fiye da tunaninki Afnan sbd shi na aje aikina Sbd ina ganin babu abinda na rasa a rayuwa Ni naje nasa aka daura mana auren sirri. Da adnan ba tare daya saniba. Mukaci gaba da rayuwarmu a can qasar harnna haifi siyama sannan nace masa mu tattaro mu dawo gida naija Na kirakine don Kixo ki ganema idonki yanxu adnan baiyi dake don kiyi zuciya kibarmin shi Nai sa,a kuwa don a Lokacin daya ganki yake cemin babu macer daya tasana a duniya sama dake Najidadin hakan don haka nasa a raina adnan ya zama nawa ni daya Gidan da momy tasa aka Gina mana muka sauka mun dawo Nigeria asibiti da komai ya dawo hannunsa Tunda duk abinda mahaifinki ya bashi takardun sunanan a wajena. Kuma bai taba kulawa takansuba har abubuwan da suka faru suka faru Lokacin daya nace sai yaje kotu ne na soma tattara inawa inawa don kuwa nasan zamana dashine yaxo qarshe Don haka a rannar daya tafi kotu Nima a ranar na gudu Amman saime tundana tafi adnan bai taba nemanaba Bai sakebi takanmuba ko a hanya bamu sake haduwa ba Saidai ya wuceni a mota koni na wuceshi Har izuwa yanxu danashiga mawuyacin Hali afnan don allah ki yafemin sannan ki roqarmin adnan shima ya yafemin wlh na tuba inata neman gafarar ubangiji Afnan ta miqe ta nufi inda take suka rungume juna sai kuka suke tace na yafe miki sady. Duk abindaya samemu iyayenmu matane suka ja mana Ta saketa sannan ta balle tissu ta miqa mata domin share hawayen nata Adnan ne ya shigo falon da sallamarsa saidai yana ganin sady yai kichin kichin darai Zainab ma batai gigin zolayarsaba ganin yaddah ya amsa gaisuwar tata a takaice Afnan ta nufi kichin taima masu aiki magana dasu kawoma baqinta kayan motsa baki Har tayi hanyar saman zainab tace ki lallasheshi don allah afnan ya yafema baiwar allahn Nan kaddah haqqi ya tambayeta. Afnan tace insha allahu ta nufi saman A sashinsa ta sameshi yana zaune sai lallatsa laptop yake ta janye laptop din tana masa tausa Suka fara lbrnsu mai dadi sannan afnan ta sako zancen sady wani irin kallo ya bita dashi mai tsantsar. Jin haushinta Yace idan naga sady sai me? Afnan ta girgixa Kai tace ba komai yaya adnan Amman sady tana cikin iftila,in da ko wane musulmi ya kamata ya tausaya mata Adnan ya aje cup din lemon dake hannunsa yace naga alamun rainane kawai kikeson batawa afnan Itama ta miqe da sauri tana fadin haba yaya adnan ta yaya zan nemi bata maka rai alhalin ni farincikinka nake nema a duk inda yake. Tace Pls yaya adnan ka dubi maraicin da asy ke ciki da kuma yarka dake hannunta koma dai menen sai an kirata da yarka Yaya adnan ka yafema sady don allah abinda take buqata kenan daga wajenka Adnan din yaja wata kakkausar ajiyar zuciya sannan yace taci alnarkacinki Na yafe mata muje na amshi yata dake hannunta na kaima Abba ya hada da yan biyun dake hannunsa son du tashi tare Afnan tai daria gamida fadawa Jikinsa tace na gode my dear my love I luv u so much. Ina tare dakai har qarshen rayuwata Adnan ya dago da kanta yana kallon tsakiyar idanunta domin gasgata abindata fada Ya saki wani lallausan murmushi gamida sumbatan goshinta ALHAMDULILLAH Saimucema wadannan ma,aurata allah e basu zaman lfy da kuma qarin qaunar juna. Da kuma. Soyayya An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 16 of 16