Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
miki Ni banciba please yunwa nakeji Ta tura masa da ai mutum daya bazai iya cinye abincin Dana zubo ba Ya tura Mata da ai abincin daya naci sauran daya Ta tura masa da ban ganeba Ya tura Mata da Kixo inda nake zaki gane Tai murmushi ta tura masa da anqi wayon Yace please my wife inajin kewarki a jikina yinwarki ta addaban Don haka ta kashema wayar tata taci gaba da kimtsa yaran bayan ta kammala tace to muje kuyima abbanku saida Safe kamar suce bazasujeba saidai ba yaddah suka iya ita kanta ta fahimci hakan Don haka sukaje yin masa saida safen a daqile ya amsa musu abin baima afnan dadiba na ko in kulan da Ibrahim ke nunama yaran nasa Sannan tajasu suka koma bed din nasu. Tai musu addu,a ta fito inda ibrahim din yake ta nufa ta nuna masa rashin Jin dadinta sosai Akan rashin ko in kulan da yake nunama yayan nasa bai bata amsa mai dadiba illa kaai ce Mata da yai kada ta damu komai lokacine idan lokaci yayi ba saita ce masa yaja yayansa a Jikinsa da nuna musu soba akwaia abinda yasane lokaci kuda ya kasa Gano kanta Saidaya sanar da ita cewa in allah ya yarda zai canja zai dinga Jan yayan nasa a Jikinsa sannan fara,arta ta dawo Daganan kuma zance ya sauya salo ya sureta sukai bangarenta. Nayi qoqarin binsu amman ina kafin na qarasa harsun datse qofar tasu hakan yasa nayo baya nace bari na garzaya wuri adnan naji ya abin take A asibitin Washe gari misalin qarfe sha biyu na rana adnan ya farfado Abban afnan na gefensa soma motsa yatsun hannunsa da yai yasa alhaj aleeyun soma karanto masa addu,oi Harya Bude idanunsa sannan aleeyun ya kira likita a waya yake sanar dashi abinda ke faruwa Da hanzari suka nufo Dakin harsu uku da kayan gwaje gwajensu Suka Gama gwaje gwajensu sannan suka kira sunansa in banda kallo babu abinda yake binsu dashi Suka sake yin masa wata allular barcin na take barcin yai awon gaba dashi saidai barcin bamai tsawo bane Baifi minti talatinba ya farka a yanxu nurse suka turo data kula dashi Yana farkawa ya miqawa aleeyu hannu yace Abba fadamin meke faruwane dani? Aleeyun shima ya riqe hannunsa yana sannu adnan sannu kaji ai daman likita yace zaka samu sauqi Bai kuma cewa komaiba ya lumtse idanunsa Nurse din dake kula dashinne ta hada mishi tea mai kauri gamida sa masa Wasu qwayoyi a ciki. Sannan ta dauko wata yar tasa da brus ta matsa masa maklin ta bashi yai brush sannan ya amsa kofin shayin ya fara kurba a hankali a hankali Can kuma saiya tsaya dashan shayin Aleeyu yace yadaia dnan wani gurinne ke Maka ciwo? Ya girgiza Kai da muryarsa irin ta marasa lfy yace ba ko ina Abba Ina afnan? Tambayar ta doki zuciyar aleeyu Wanda har saida tsa ya koma kan kujerar da yake zaune. Ya fada cikinta rakwab Tuni zufa ta fara keto masa Lol wacce amsa Abban afnan zai Bama adnan Oho Nima ban saniba Mu hadu a Aure. Kan. Aure Chapter36 Yanayin yaddah Abban nasa ya shga yasashi shima shiga Cikin Yanayin tsoro har baisan sandaya saki kofin tea din dake Hannun nasaba ya Fadi cup din ya fashe yace Abba lfy Wani abune ya samu afnan din? Don allah meya sameta? Aleeyun ya kamashi ya kwantar yana fadin cool down adnan Baka ganin halinda kake cikine? Koma ka kwanta babu yaddah ya iya hakan Ya koma ya kwanta yana fadin to fadamin abinda ya sameta Abba ni nasan dai ba lfy donda lfy lau da ina Bude idona da ita zanyi tozali Aleeyu yace yanxu dai ka kwantar da hankalina ka natsu ka samu cikakkena lfy . Afnan tana cikin qoshin lfy don da kaina zansa tazo ta dubaka Adnan din yace to amman abba.... Ya daga masa gamida cewa ya isa kayi abinda na umurceka dayi kawai Ba yaddah ya iya hakan ya koma ya kishin gida gamida amsar wani tea din da nurse din ta hada masa yana kurba Dukda ba dadi yake masa ba. Afnan taja yaran ibrahim a jikina kamar yayanta cinsu shansu da tsaftarsu don ko mahaifiyarsu sai haka Burinta a kullun bai wuce taga yaran sun samu soyayyah mai tsafta a wajen mahaifin nasu ba Da yammacin ranar wata asabar bayan tayima yaran wanka. Ta shiryasu cikin Wasu sababban kayansu Itama ta hade cikin wata Riga butic me hade da jeans dinsa bayan anyi sallar magrib taja hannun yaran zuwa babban Falo inda ibrahim din ke zaune Akan kafet dagashi sai trequater da singileti Afnan ta qarasa wajensa ta duqa gamida kama qafafun Nasa tana mammatsawa Ibrahim din ya kalleta yana murmushi yace wannan kyau haka madam duk ni daya? Afnan din ta ware idanu tai masa signa da yaransa na tsaye Yace to meye rungungumeki nayine a gabansu? Afnan ta riqe baki wani irin kunya ya saukar Mata dukda kuwa da turanci yai maganar Afnan ta miqe ta kamo hannun yaran ta dinga nuna masu yaddah zasu dinga masa tausa sannan ta tashi ta nufi kishin dan dauko musu. Abincin daren data shirya musu kafin ta dawo hirace sosai ta barke a tsakanin uba da yaran nasa Wani dadine ya kama afnan din don har abada ba zataso ganin yaran da iyayensu ke rayuwa dasu kamar yaddah ta rayu da momyn taba itadai ta rasa gatan uwa ta rasa shayarwar da iyaye kema yayansu Ta rasa gumin jikinta sannan ta rasa soyayyarta Afnan ta sauke tiren dake hannunta sannan tasa hannu ta goge yar kwallar data silalo Mata ba tare dasun an kaarasa ta koma ta dauko sauran kayayyakin gamida shimfida ledar xin abincin a tsakaiyarsu Bayan ta jejjera komai sannan ta dubi yaran daketa daddannan jikin Abban nasu tace to ya isa haka ku taso muci abinci Gaba dayansu suka nufo kan ledar sunaci suna santi daga yaran har Abban nasu afnan itakebama salim a baki ganin bason ci takeba ibrahim yace a,a dakata ni bari nabama salim din a baki don na lura bason cin kikeba Murmushi kawai tayi taci gaba dacin shima sannan shima ya maida hankalina wajen Bama yaron abindai. Kwanin ban sha,awa Bayan sun kammalane afnan ta kashe kayan abincin takai kichin sannan ta dawo ta canja chennel. Din zee aflam fil din India ake mai kyau don hak suka maida hankalins kan kallon sai misalin sha daya sannan ta kashe komai ta dauki salim ibrahim kuma ya dauki sajida suka kaisu makwancinsu sannan suma suka wuce nasu Dakin Yaune ranar da ibrahim ya mallaki afnan a. Matsayin mace don haka ranar taxo musu. Cikin farin ciki fiye da dukkan ranakun da yai a rayuwarsa don haka farin cikinsa a ranar yaqi boyuwa ji yake tamkar ya daki afnan din ya goya yaita xagaye gari da ita Don haka koda gari ya Waye bai bari tayi komaiba sajida da salim ya kira yace su shga kichin don su hada ma kansu break fast a ganinsa a zasu iya tunda duk shga kichin din da afnan din take dasu takeyi shiyasa Baiji komai a aransaba ya taimaka musu wajen kunna na!urar girkin Yana tsaye yana kallonsu suka hada ruwan shayi da wainar kwai gamida. Soya dankali Ibrahim ya dibarma afnan nata ya ya nufi bangaren nasa harta tashi ta nufi toilet yanajin saukar ruwa don haka ya aje ya fita saShinta ya nufa ya zabo Mata kayan da zatasaka Riga da siket ya zabo Mata inglish wear masu kyau sannan ya fito Sajida da salim ne Akan dinnig table ya qarasa wajensu yana fidin yadai. In banda shayi da biredin babu abinda suka iya ci a tsakanin wainar kwan da dankalin Jikin ibrahim din yai lakwas yace yadai sajida ba zakuci bane? Salim yace babu dadi wlh daddy bai dahuba ibrahim din ya ture hannun yaron dake qoqarin Kai masa wainar kwan baki. Sannan ya maida kallonsa kan sajida yace au daman duk kaya miki girkin da taje har yau baki iyaba? Salim yace daddy ko shayinma baiyi dadin na anty ba don allah daddy kace taxo ta dafa mana Ibrahim din yaja wani gajeran tsaki ya nufi sashin nasa ya samu harta fito daga wankan tana kwalliya Bayan ta gamane ya taimaka Mata tasa kayan wohoho ba qaramin kyau tayiba Nan taje zance ya sauya salo yaci gaba da nuna Mata wani sbn salon soyayyar ba ita ta samu damar zare jikinta daga nashiba sai misalin azahar don Haka ta nufi inda kayan tea din suke shayi mai kauri ta hada cup biyu ta miqa masa daya. Ta amshi daya Kurba biyu kawai tayi. Sannan ta yagi wainar gwan takai Bakinta saidai ta gaza taunawa don kuwa qarnin kwan shine ya cika Mata baki kamar ba,a soyaba hannunsa yasa ta zazzage Wanda ke cikin bakin nata tace Waye ya soya wannan kwan kasa magana yayi sannan ta dauko dankalin domin taci. Shimadai Jia iyau don ko kadan bai soyuba da gudu ta fada toilet ta wanke bakinta taxo bakin gado sai daria take masa don duk a zatonta shine ya hada Ya miqa hannu zai kamota ta zille gamida fita tana kyalkyala masa daria tana fitane taci Karo dasu sajidah suna kallon film din India kichin ta wuce direct ta dafo musu kuskus miyar kwai gaba dayansu suka hadu a dinnig sunaci sai santi suke musamman ibrahim dake fadin Ada ba ruwana da kyau sbd duk matan dake girki dashi saina dinga Jin qarninshi a tare dasu Amman ke ko kadan duk yaddah kika sarrafashi banajin qarninsa a tare dake saima wani daddadan kamshi dake tashi shin wai nama taba fada miki kin iya girki kuwa? Afnan ta kyalkyale da daria tace vaka taba fadaminba Sajida gaskia kuyima daddyn Nan Naku waigi Dukkansu dariar suke yace kin dauki abun santi ne ko? Yace na rantse ban tava tunanin kuskus nada dadi hakaba Afnan daria harda kyalkyalawa tace Kai ibrahim wannan santi haka Sajida tace wai anty mai yasa kullin kikai mana shayi sai naji yana wani kamshin dadi amman yau nawa baiyi hakaba Afnan tace Kai ashe yan matane yau sukai mana girki Saidai ko har yanxu baki iyaba idan kuwa baki iyaba mukai miki aure mijinnki korarki zaiyi yace baki iya girkiba Yar tai daria tana satar kallon abbanta anda ya dauke kansa hankalina nakan abincin kawai Afnan din tace karki damu sajida tunda har kinason ki Iya daga yau. Koda bamu shga kichin ba zan zauna na dinga kyar dake yaddah ake girki dalla dallah Afnan ta miqe sbd bugun qofar da ake don taje taga ko Waye. Hajiya iklimace ta shigo kamar an bankadota mahaifiyar ibrahim kenan Afnan tai saurin zubewa tana kwasar gaisuwa da wani kallon banza ta bita ba tare data amsaba ta shige ciki Afnan ta miqe cikin sanyin jiki ta nufi cikin falon Hajia iklima ta tsaya Akan ibrahim din tana girgiza Tace sannu shanyayye eh anyi amarya sabon jini dole kake mannewa jikinta ka tsote man kaiga sabon shga Wanda bai taba aureba ko Toka saurareni duk abinda kake kaje Kai belin din Maryam idan kuka kaqi wallahi saina tsine Maka banza sakarai kawai Ta kamo hannun yaran tace ku taso muje fon neman gindin zama shine aka kwasoku aka kawoku nan Sajida tace mudai hajia bazamuje gidankiba ki barmu a wajen anty kawai Hajia ta tafa hannu tana fadin innalillahi wa innailaihirrajiun yanxu matsiyaciyar yarinyarnan kuma ta shanyeku ta shanye ubanku ni kadaice na gagareta nafi qarfinta kenan? To saikun tashi mun tafi kuma baqaqen munafuki har kunfi son kishiya Akan uwarku Salim ya maqale kafada yana shirin kuka ta fizgoshi tace taso muje kona kakkaryaka yanxunnan Afnan dake tsaye gefe tausayin yaran ya kamata batasan sanda tai magana ba tace don allah hajia Kiyi haquri ki barsu anan Kamar wacce aka sirfama zagi ta saki yaran ta nufo wajen afnan din kamo hannunta afnan din ta daura kan kunnenta tace . Tace kama kunnena kiban umarni zanfiji Kinji uwata Afnan tai saurin janye hannun nata jiki na rawa tace Kiyi Haquri don allah hajia wallahi niba haka ba....... Rufamin baki munafukar banza Bude idanunki ki kalleni Ni nafi karfin iskancinki Da kike ganina Nan Nima tsohuwar banzace naga jiya naga yau kuma har gobe ma dani ake damawa Kai kuma saika zaba belin Maryam ko tsinuwa don na tabbata inhar kaqi belin dinta. Saina tsine Maka Sannan ta juyo tanama afnan kallon uku kwabo sannan tace ke kuma Ta murza yatsun hannunta sukai qara sannan ta juya ta figi jokokin nata sukai waje. Babu inda bai rawa a jikin afnan hatta miyon bakinta don ta fara tsorata da lamarin hajiyar ibrahim Chapter37 Jikin afnan yayi sanyi likis ta juya a sanyaye ta nufi falon nata Ibrahim ya bita da sauri yana afnan tai saurin mayar da kwallan da suka taru a idon nata ta qaqo murMushin qarfin Hali ta juya tana kallonsa Ya qaraso wajenta gamida mannata a jikina yace Kiyi haquri don allaha afnan wlh bansan...... Tasa hannu ta rufe masa baki tace meye kuma na bani haquri ibrahim me akaimin na bacin rai da har kakeban haquri? Don mahaifiyarka tamin fada aiba wani abu bane bata isa taimin fadan bane koko don ba ita ta haifeniba? Don haka karka kuma cewa komai Akan wannan dan qannan abun daya faru ta sake qaqalo murmushi qarfin Hali sannan ta nufi Dakin nata Misalin qarfe hudu na maraice afnan na kwance a falonta ibrahim ya fita ita kadaice a gidan zainab ta iso Cikin tsananin farin ciki afnan din ta tareta suka zube Akan Daya daga cikin tuma tuman kujerun dake falon Zainab ta dingabin afnan da kallo tana fadin Kai mutumiyar aurennan fa ya amsheki kinga yaddah kikai Wani masifar kyau? Afnan tace dallah can gafara munafuka dubi tabbuna a jikina ko Kixo kimin jaje Tace aiya qawata wlh naso naxo aikine yaimin yawa a office amman ai munje asibiti nida mustafa da ibrahim mun duba adnan Qirjin afnan yai mummunan faduwa cikin natsuwa tace ashe kunje kin dubashi? Tace eh mana bai fada mikiba tace a,a bai fadaminba Kuma Nima ko sau daya bai taba cemin na shirya muje na duba mara lfy ba daman nasa masa idone naga gudun ruwansa amman har yanxu baicemin komaiba Tace to kema saiki shareshi kawai wata qila kishine ya hanashi Kinsan mustafa ya fadamin abindaya faru wlh hankalina Ba qaramin tashi yaiba kinsan silar alkhairi akeson. A samu game da mutum bana sharri ba Afnan ta qure zainab da kallo tana mamakinta a zuciya tace shin mai yasa mutane suka fiye son zuciyarsune? Zainab tace name tace na baki lbrn adnan dan uwanane harda zuria a tsakaninmu amman haryau qoqarin raba tsakanin dashi kike Tace Bawai rabaki dashi nakesonyiba afnan gani nai mijinki baison mu,amalarki dashi Tace mijina ba zai hanani zumunciba don kuwa fadar uban gijine duk mai yanke zumunci baxai shga aljanna ba Zainab din tace toki tambayesa mana idan bai sairarekiba sai kimai wannan bayanin nasan zai saurareki don ibrahim nada sauqin Kai Afnan din tace bazan tambayshiba don bazan sashin yin abinda baisoba kasancewarsa mai haquri banason janyo abinda zai batama mijin nawa rai Zainab tai murmushi tace lallai afnan cikin Mata irinku basu da yawa ke ina zaton sun qarema Afnan din tai murmushi tace kyaji dashi da wannan zugar Taki ke bari na Kawo miki dan kayan motsa baki Sai bayan magrib zainab din ta wuce don ita taima afnan din ma girki. Don haka tana tafia toilet ta fada ta watso ruwa ta zabo Wasu Riga da wando masu kama jiki ta saka ba qaramin kyau tayiba Bata Dade da fitowa falonba ya shigo ta tashi da fara!arta ta tarbeshi suka xube kan kujera tace na fara Kawo Maka abincine ko sai ka farayin wanka? Yace a,a tashi kije ki dauko hijab dinki asibiti zamuje an kwanta da malam baida lfy daganan saiki duba jikin adnan Wani dadine ya ziyarci zuciyata zataje taga adnan dinta saidai bata nuna a fuskaba don haka ta tashi ta nufi nata sashin ta dauko dogon hijab dinta ta fito A mota ta sameshi bayan ta rufe gidan Kai tsaye asibitin suka nufa. Saidai likitoci sun hana kowa zuwa inda malam din yake sbd Yanayin jikin nasa. Da alamun yanadan Jin jiki Don haka Dakin dake gefe suka nufa anan ne suka samu Abban afnan din da inna Afnan ta qarasa gabansu cikin tsananin girmamawa ta duqa ta gaishesu gamida yin musu ya mai jiki Anan inna ke sanar da ita yaddah jikin nashi ya tsananta don baima sanin Wanda ke kansa Afnan tace wayyo allah malam allah e sawaqe sannan ibrahim shima ya qarasa yai musu ya mai jiki Daganan kowa yaja bakinsa yai shiru ita kanta afnan Din jikinta yai sanyi sosai donta lura jikin malam din yayi tsanani Can dai ta kasa daure zuciyata ta duqar dakai tace abbah ina aka kwantar da adnan? Yace yana can Dakin dake kusa da wannan ai shima ya warware gobe za,a sallameshi Ta miqe tana bari naje na dubashi babu Wanda yace Mata uffan harta fice Amman zuciyata sai barazanar fashewa take sbd tsananin bugun da qirjinta yake Tura qofar tayi tare da sallama yana kishin kide kan doguwar kujera mai kamar gado da alamar dai gajia yai Da kwanciyar yasa ya kishin gidar anan Yana ganin afnan din ya yinkura ya miqe ido waje yace mai ya kawoki Nan afnan iye? Ko kinxo ki qarasanine? Ya girgiza Kai sannan yaci gaba da cewa kin cuceni afnan kin cucar da igiyar aurena dake kanki Asje kalaman da kikemin daman duk na yaudara ne? Daman ashe zaki iya auren wani Wanda ba niba? Kin tarwatsa zuciyata afnan kin yaudari zuciyar da bata taba tunanin yaudarar kiba Ya riqe kansa kamar rikitacce sannan ya dago da kan nasa idanuwanta sunyi jajir yace Haba afnan Haba afnan Ashe ashe daman kalamanki da kikaimin a baya na alqawarin rayuwa dani wuya ko kunci duk qarya ne? Duk yaudarace da dadin baki? Cikin muryar kuka tace babu yaudara ko karya a cikin kalamaina kaine kaxo da yaudara don Baka buqatata Ka shirya wani tsari ka auri wacce zuciyarka ke muradi To don me zanci gaba da dakon soyayyar da bata da tasiri Ai na Maka alkawarin zan kasance dakaine idan har kaima ka kasance dani to ka kujeni ka juyamin baya ka Nunama duniya cewa bakayi dani To yaya adnan meye amfanin kasancewata da abinda baya buqatar kasancewa dakai? Dole na Barka ko naqi konaso Cikin zafin rai yace qarya kike afnan na taba fadamiki cewa zuciyar dake dauke daso to duk runtsi bata taba juyama wannan abinda takeson baya Koda kuwa shine ua juya mata Na tabbata abindaya faru dani idanda dake ya baru bazan taba butulce miki ba duk runtsi ina tare dake koda kuwa zaki dinga yankar naman jikinane sbd tsabar kiyayyah Don kuwa nasan ba,a cikin tunaninki kikeba don kuwa duk randa kika dawo soyayyata ba zata rasa madafa ba Tace a yanxu kenan kake wannan tunanin Lokacin da aka dauke alqalima takardu suka bushe na rigada nna zama matar wani Sa sauri sauri yake kallonta idanuwanta sunyi jajir Ya matsa da baya labbansa har rawa suke yace naji ficemin daga daki Ta Bude baki zatai magana ya daka matsa tsawar da harta birkita Mata yayan hanji ta fice da sauri har tanacin Karo da qofa ta firgita don ko ina na jikinta rawa yake Don haka ta zube a daya daga cikin jerin kujerun dake wani daki tana mayarda numfashi da sauri da sauri Bata jima a wajenba ibrahim ya fito ya ganta a zaune yana qarasowa wajen nata yace lfy dai afnan kika zauna anan? Ta qaqalo murmushin rashin gaskia tace na Dade da fitowa ina fitowanne na hadu da wata qawata muka zauna Muna hira yanxu ta shga wannan Dakin Yanxu dai muje muyimasu Abba sallama idan likitoci sun bada damar shga dunashin ma dawo A tare suka jera sukaimasu Abban nata sallama aleeyu ya sake yin musu nasiha sannan suka wuce abinsu Suna isa gida afnan ta cire hijab din jikin nata Ta nufi toilet ta dadama ibrahim din ruwan wanka Sannan ta iso falon ta sameshi a kishin kide ta kamo Hannunsa gamida cewa muje my hony ka watsa ruwa Saida ta rakashi har bakin toilet din sannan ta fito ta Gama shirya masa komai Bayan ya kammala cin abincin nasa hirace ta barke a tsakaninsu mai cike da nishadi dukda afnan din ta maza Kai take amman ta ciki na ciki Saidai yau nishadin nasu tafi a kullun don kuwa wani irin nishadin da kauna kawai yake nuna Mata mai wuyar fasaltuwa Kullu nafsin za-katul maut. Allah sarki evry soul shall test dead. Duk mai numfashi saiya dandana mutuwa A yaune aka sanarma da afnan rasuwar malam don haka da wurwuri ta kammala ayyukanta Ibrahim ne da kansa ya dauketa ya kaita gidan misalin qarfe takwas na safe. Tun daga qofar gidan kake ganin manyan motoci da dumbin mutane Afnan tayi kuka sosai gamida tausayama Abban nata shikenan ya zama maraya mutum mai haquri da tawakkali Duk halinsa mahaifin nata aleeyu ya dauko Misalin qarfe goma duk yan kauye Dana birni sun hallara abokan aleeyu yan siyasa da masu fada aji yan uwansa nako ina abokian adnan ibrahim shima da abokansa su mustafa duk sun hallara ba tare da bata lokaciba akayi Gaggawar kaishi makwancinsa Harda dangin hajia nafi tare da sauran abokan arziqi duk an hallara gidan ba masaka tsinke Afnan taja yayanta a jiki Kullun ibrahim ke kawota da safe shi kuma ya zauna gurin Amsar gaiSuwa. Sai dare sannan ya dauketa su koma gida a haka har akai sadakar uku Ranar sai goma saura ibrahim yaxo daukarta Aslim da taslim suka liqema afnan din Akan sai sun bita Tana. Tsaye a jikin motar ibrahim din Wanda ke tsaye yana musu daria Daman kullun saiya matsa Mata Akan ta kwaso yaran su dawo kusa da ita itace rake qi don haka yau yasa musu ido Tace Kai ku dakata daddynku baisan zan daukekuba don haka kuyi haquri idan na dawo saina tambayeshi inya yarda saina tafi daku Taslim tace momy baga daddyn nanba ai nasan zai yarda Suka riqe hannun ibrahim dun suna daria anan ne adnan ya qaraso gamida cewa tadai fada muku gaskia ko Waye daddyn ku Amman wannan ba daddyn ku bane nine daddynku Gaba dayansu yaran kallon rashin sani suke masa Suka koma bayan afnan suka labe alamun basu yarda da shine daddyn nasu ba Macen tace aidai mommy ba wannan ne daddynmuba ga daddynmu Nan ko? Jikin afnan yai sanyi ta kamo hannun yaran Ku juya wajensa ku dubeshi shine dadddynku Ku gaisheshi Gaba daya yara suka tirje suna shirin kuka. Da sukaga ya miqo hannu yana shirin kamasu. Suka ruga jikin ibrahim Wanda ke tsaye a jikin mota ya harde hannuwa Afnan ta dubi adnan din ido cikin ido duk jikinsu ya mutu Ta tuna maganar daya furta Mata shekarun da suka wuce Afnan ki amincemin mu Gina rayuwarmu cikin soyayyah da qauna ku kasance a cikin inuwar aure. Mu rayu cikin soyayyah. Mu raini yaranmu cikin tattali da kulawa mu shaqu da abinmu don bamu da kamarsu don haka dole mu basu dukkanin lokacinmu donsu samu kulawar data dace Afnan ce tai wannan tunanin lokaci guda sannan ta kamo aslim da taslim din. Ta hado kansu su duka tai musu rada suka kyalkyale da daria sannan suka nufi wajen adnan din Afnan da ibrahim kuwa mota suka shge suka wuce dan kuwa dare ya soma tsalawa Ranar juma,a itace ranar da akai addu,ar bakwai na malam dom kowa a ranar ya watse itama afnan sai misalin qarfe hudu na yammah ibrahim ya daukota Suna dawowa ta fada kichin don hada musu abincin dare Shi kuma yana falo yana kallon ball bugun qofar da ake yasa ta saki abinda take somin zuwa taga ko waye Tace waye? Shiru ba,a amsa ba. Don haka ta Bude qofar ba tare data sake maganaba don taga wane ishashshen ne Hajia ce ta shigo mahaifiyar ibrahim da Maryam a bayanta Qirjin afnan yahau wata rugurguza rugugugugu batasan Lokacin data furta A-uzubillahi ba Cikin tsanananin tsorata da abinda ta furtan kuma saita rufe bakinta da hannu Hajian tace eh lallai Fadi kwarai ki kori shaidanu sun shgo miki gida dole ki. Nemi tsari dasu Maryam ma ta rankwasheta gamida cewa baqar munafuka wlh saikin gane kuranki Bata tanka musu ba sukai ciki itama ta koma kichin din Dukda zuciyata babu dadi haka ta daure ta hada musu abinci ta shirya mus kan babban tire da lemukan sha Takai musu bakinta na fadin sanunku da zuwa hajia amman babu wacce ta tanka Mata Saima ibrahim ne dake Mata kallon tausayi sannan ta miqe ta fice har shima ya miqen yaji hajiyar tasa na fadin da binta zakayi. Qaramin mara kunya to jeka munanan Muna jira idan ka Gama ka fito sai muyi abindaya kawomu Yai saurin komawa yana fadin a,a ba haka bane hajia ayi haquri. Maryam taja wani dogon tsaki tana fadin munafuka banza kawai Da sauri ya kalleta cikin zafin rai saidai. Ba zai iya Mata komai ba a Lokacin kasancewar hajiyarsa na wajen Don haka ya mayar da kansa qasa ya duqar Afnan ce a cikin falonta ta hada Kai da kujera kuka kawai Take marar sauti rayuwar ta Mata kunci. Ga damuwar da take dannewa a zuciyarsa ga kuma wannan ta danno Tanajin yaddah rigima ta kacame a tsakanin ibrahim din da mahaifiyar tasa Inda hajiyar ke fadin Kai saurarene ibrahim nidai nice na haifeka. Ba kaine ka haifeniba. Don haka dole nasa Maka doka ka bita ko kannannso ko bakaso dole Maryam ta zauna a gidannan ko kanaso ko bakaso. Ibrahim din yace Kiyi haquri hajia don ni na rigada na saki Maryam saki uku kinga ba damar kome kenan Salati ta saka tana fadin kayi daidai da kake fadamin da bakinka cewa ka saketa. To inaso ka sani na raNnnntse ndnnann nannnnlnlanh koda aure koba aure sai Maryam ta zauna a. Gidannan Ballentanama da aurenta tunda Baka bata shaidar sakiba takarda. Da baki kawai ka furta. Donka furta Mata ka saketa ba tare da takardaba ai wanna shirmene Idan har Baka rubutaba to matarka bata sakuba Yace amman hajia,....... Ta daga masa hannu sauraramin banson Jin komai Maryam dai nace bata saku ba ita waccen uwar feleqen Nakeson karubutama takardar sakinta yanxu kuma saki daidai har uku Cass Da sauri ya dago Kai yana kallonta wani zufa ya soma karyo masa muryarsa na rawa yace. A. A hajia kar muyi haka dake allah ma ya sani duk wata biyayyah ina miki binki sauda qafa duk abinda kika gindayamin ina qoqarin kiyayewa Kin sani makudan kudi na kashe wajen fito da yarinyar Nan Daga gidan horo na Mata Kince saidai ta zauna a gidannan na amince don koda babu wata alaqa a tsakanina da Maryam ni me riqetane don yar uwatace Amman bazan iya sakin afnan ba haka Bawai ba tare da wata matsalaba. Don na tabbata yaddah take miki biyayyah ko Maryam bata miki Kiyi haquri kawai hajia Amman idan kika matsa Abba kawai zan sanar mawa Hajiyar tace ka Dade Baka fada masaba dan ubanka To inaso ka sani ni hajia iklima nayi alqawar wlh tallahi saika saki yarinyar Nan Don haka na Baka sati biyu na ratse da allah inhar Baka saki wannan yarinyarba to wlh tallahi babu Wanda zai hanani. Tsine Maka. Tsine Maka tsine Maka Kalaman da suka dinga sauka a kwakwalwarsa kenan jinsu yake kaman saukar aradu Hmmm ya lamarin zai kasance Anya ibrahim zai iya sakin afnan din kuwa? Amman ya kuke ganin lamarin zai kasance sai naji daga gareku Aure. Kan. Aure Chapter38 Taja tebur din gabanta tana fadin baqar daga bari muga abinda aka kinkimo aka Kawo mana sai kace abin kirki Raping din datauma abincinne yaja hankalita har tai sha!awar budewa Tana. Budewa wani kamshi ya daki hancinta batace qalaba ta dau cokali taci gaba daci tanaci kuma tana mita Anya yarinyar Nan ba!a gidan abinci ka ganta ka auro ba don naga tayi kama da ma,aikatan gidana abinci Shidai baice Mata qalaba har taci iya cinta tabar sauran Ita da kanta taje ta zabar ma Maryam din Dakin da zata zauna wato Dakin ibrahim din kenan Don haka

Chapter 14 of 16