Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
shawara shiyasa nake alfahari Dake. Kuma nake farin cikin kasancewarki aminiyata Itama Suryn ta rungumeta daganan zance ya sauya salo sukaci gaba da Aikata Masha,ar tasu Rayuwa taci gaba nafi tanace har saida aleeyu ya tsunduma Harkan siyasa kuma ya fada da hannun dama aka shga Fantamawa dashi. Ya samu muqamin ambasador Dan haka arziqi yaci uban nada An gama Maka ma nafi katafaran gidanta Wanda keda Part part da yawa dan wannan gidan ko gidan shgaban qasa sai haka Ta sake siyo Wasu Maka makan motoci Aleeyu harya fara tsorata da ita yai fadan yai fadan harya Gaji dan haka yasa mata ido. Tace masa su. Tashi su koma gidan Data Gina yace wannanne kuma baki isaba Nana aka shga taqaddama tace idan shi bazai komaba to ita zata koma ita daya Don ba zata iya rayuwar matsi da takuraba Ta dinga zama a wani dan qaramin gida sai kace akurki ba Wannan ai sai qawayena su rainani abin ba qaramin sosama aleeyu rai yaiba Ransa ya baci yace Indai har kikaga kin zauna a wani gida Da ba nawaba to saidai Idan in babu. IGIYAR AURENA. Akanki Tace wat kut ai IGIYAR AURE sunan wani littafi ne Aleeyu ka sani da aurenka zanbar wannan gidan ko kanaso Ko bakaso koka shirya ko baka shiryaba dan haka Kwarama ka lallashi wannan. Bagidajiyar matsiyaciyar zuciyar taka Wacce batason taga taci gaba a rayuwarta Yace watttttttttttt nafi ni kike fadama wadannan baqaqen kalaman Tace yez an fada Maka din ko kanada abinyine Lol. Nafi kenan. Naga alamun itamafa akwai baki Aleeyun zai yarda kuwa koko yaya Shin wai Shima shajinin ko zai yarda koko yaya Amsar na cikin chapter11 in Allah ya yarda Barka da shan ruwa. Aure. Kan. Aure Chapter11 Yace wattt nafi ni kike fadama wadannan baqaqen kalaman tace anfada Maka din Koda abinda zakaine. Harya Bude baki da niyyar maida mata martani Tunanin me yai kuma sai ya fasa Baici gaba da saurarontaba kawai ya fice ya barta anan Abun yai mata zafi tanason ta fantama gamida walwala duniya tasanta amman Ina abin ya gagara Kullun Tunanin da take kenan Kamar ba itace ta aje miliyoyin nairoriba Tace kodai yakice aurennan na aleeyu zatai taje tai rayuwarta yaddah takeso? Kiran wayar da ake ya katse mata dogon kiran da ake mata Ta dauki wayar sury ce tace ke qawata ina cikin tashin hankali Yanxu tsohon mijina auwal yaimin waya wai gashi ya sauka a naija Yacemin wai ina ina nadai ce masa ina kano dan na samu aiki acan Yanxu haka wai yana hanya ya hayo motar kano Nafi tace abu mai ssauqi sury ki saukeshi a gidanki na sirri aiba Koda yaushe shi chirman din yake gariba Tunda yanxu haka ai yana abuja ko? Saiki komacan idan chairman din ya dawo saiki sallami shi tsohon mijin naki ki ce Masa zaki koma aiki dan daman a cikin wani kauye kike aikin kuma kike zama har sai an karbeki Sannan kike dawowa Sury tace kina ganin zai yarda? Inajin tsoro fa nafi tace ke haba ki cire duk wata fargaba kinji Tace to shikenan ta kashe wayar Aleeyu na zaune saman kujera yana harhada Wasu takardu nafi ta Shgo ta zauna a gefensa Bai kulataba yaci gaba da aikinsa ta dafa kafadunsa tace aleeyu Dan Allah kayi haquri Ka daina fushi dani nibawai na raina arziqinka bane Kawai dai ina neman mana hutu kaida yaranka ne Amman kayi haquri idan kayi fushi Naga ko sury da kudina ta Gina gidanta kuma suke zaune ita da Mijinta a ciki Shin ni nawa mijin me zaisa bazai iya zama a gidanaba? Ya kalleta da idanunsa kury kafin yace Aiba lallai Mijinta da naki su zama dayaba Mijinki mai ikone da gidansa Bazan koma mace tai iko daniba Kuma duniyama zata zageni ace na turaki kinata barnatar da dukiyar gadonki Munata bushasha alhalin kullun fada nake miki Akan rashin dacewar Yin hakan. Kimin addu,a duk sanda Allah ya horemin Zan Gina miki gidan dayafi naki Shiru tayi kamin tace shin idan nace kasai gidan mu Koma ciki zaka siya? Wani murmushi mai cikie da takaici Yaja kamin yace Hajia nafi kenan aiko inada kudin siyan wannan gidan naki bazan siyaba Dan bashine a gabanaba abinda ke gabana shine zuwa hajjinsu inna da malam Tadan tabe baki kamin tace Naji yanxu ka bada miliyon hamsin na siyar Maka da gidan Wai wani murmushi kamin yace nida miliyon hamsin din waya aje wani? Tace to kawai ka bada miliyon ashirin na siyar Maka Ba yaddah ya iya ganin ta nace yace to shikenan ya rubuta mata Cheaque ya bata Ta amsa a yamutse Yau shine ranar da suka tunkari shajini da Maganar. Alfarmarsu tason Yabar mata yarta afnan amman ta masa alqawari duk cikin data samu to nashine Zata bada. Daqin aminncewa yai saida suka hada da magiya harda zubar da kwalla Sannan ya amince Gamida kafa mata Wasu shariddan Lokacin da aleeyu yaje ganin gidan ya tabbatar da gidan yafi qarfin kudinsa Dana an zubama gidan miliyoyin kudi Haka ta matsa masa suka koma a cikin satin hankalinsa ya kwanta Aifa ta samu yaddah takeso sai qarya ya qaru ga babban gida da manyan motoci Gashi Mijinta ya shiga cikin gwamnati ana damawa dashi Sai harka ta balle ita da matan manya duk qqawayenta yanxu Daga matan kwamnoni sai matan kwamishinoni da matan manyan yan siyasa Aleeyu ya saka afnan a makarantarsu adnan tana aji uku ya kammala sakandire Dinsa aleeyu ya shiga fafutukar neman fitaar dashi waje Baa,a son ransaba dan shidai yafison a barshi tare da qanwarsa Saidai ba yaddah zaiyi haka aleeyu ya samar masa Gurbin karatu a jami,ar califoniya dake qasar amurka Afnan sarkin kwallafa da wayau saida dibara Sannan aleeyu ya samu ya Rabata dashi. Adnan din ya tafi Saidai yayi nadamar yin hakan dan afnan ta hanakanta ci dasha Kullun kuka wai a kaita gun yayaanta adnan Kullun sai adnan din ya kira waya yaji muryar yar qanuwarsa Wannan shaquwa tasu kanbama Aleeeyu maamaki Yacema adnan din ya dage da karatu da zarar ya kammala ya daawo Zai aura masa ita itama hakan ya fada mata Sannan ya samu natsuwarsu Adnan ya maida hakalinsa sosai wajen karatunsa na likita Kuma komai yaxo masa cikin sauqi Sbd hankalin daya maida akai Haarya samu ya kammala karatunsa cikin nasara ya dawo Gida Aleeyu ya sake samun daukaka sosai a harkar siyasarsa dan yanxu ya Zama ministan kudi. Kudi sun zauna Nafi ta samu yaddah takeso sai bushasha kawai take duniya sabuwa Mijinta ya Taka babban matsayi Afnan tana cikin farin ciki yau yayanta adnan zai daawo dan haka tun data tashi da Asuba ta dinga kai kawo ta shirya masa wancan ta hadamasa wannan Hatta bangarensa ita da masu aiki aka taru suka gyara masa shi Qarfe sha daya daidai ta fada toilet ta watso ruwa Ta fito ta zauna gaban dressing mirro Mai ta murzama fatarta Sannan Tabi fuskarta da fowder Tabi labbanta da Jan baki pinki colour Tafi minti shabiyar tana wannan kwalliya shafa wannan lakaca wancan fesa wannan Sannan ta tashi ta nufi wadruf dinta inda ta dauko Wasu kaya yan ubansu Idan ka ganta ba qaramin kyau taiba Dan daman kyakkyawace Da sauri ta suri key din motarta ta nufi falon momyn nata Ta isketa tareda Wasu qawayenta Ta haye saman kujeran da Momyn nata kekai Ta dubi matan dake cikin Dakin Wanda zasuyi sa,ar mom din nata Tace sannunku sukace yauwa afnan kina lfy tace lfy lau Sannan ta dubi momyn nata tace Momy fita zanyi Ba tare data tambayetaba tace saikin dawo afnan dina Harta miqe ta hango wata qaruwar roban swan ta janyo tace nasha Momy tsumine tace eh sha ta kafakai saida Tasha sosai Sannan ta tashi ta fita Hajia kubra tace ke hajia nafi yanxu tsuminne kikebama yarinya budurwa Itada ba mijiba? Tai murmushi tace to yason ranki ai duk wani irin magungunanmu na mata Da kika sani Indai ina shanshi to itama ina bata tun tana qaramarta dan Inaso tun yanxu na fara hadatane kafin tabar hannuna Ke bafa qaramin buri na dauka Akan yarnan bafa nanda dan Qanqanin lokaci zata zamemin jari Shiyasa nake tsumata tun tana qaramarta hakan shi zaisa ta banbanta da Sauran mata darajarta tafi ta ko wacce mace Dan maza su dawo anan dinmu ta nuna tafin hannunta suka kyalkyale da daria Kubra tace ammanfa bakida dama mutuniyar nasan afnan sai Manyan yan boko likitoci louyoyi da bankers Lalalala ta katseta wanne irin Wasu likitoci ko lauyoyi wlh Bazan amince ta auri qananun yan boko ba Burina yata ta auri sugaban qasa ko wani basarake ko Wanda qasa ke ji Dashi shine kawai burina Danni a rayuwa Indai Akan kudine banqi kowama ya rasaba Indai ni zan samu Hajia zeena tace koda yake ai kwamnatinma takuce hajia nafi Wanda keda ya Kamar afnan idan baija jari da itaba to meye amfaninsa Suka tafa tace kedai ganemin hanya qawata Afnan na fita harabar gidan ta hango adnan shida daddy suna fitowa daga Mota adnan din yahau Wasu baqaqen suit Kace daman danshi akayosu Afnan ta lumshe idanunta Sannan ta budesu a hankali Wani abu na ratsa zuciyata tace tabbas wannan shine yaya adnan dinta mai Sonta daman haduwarsa takai haka? Suka nufota tai saurin shgewa falon. Tana bata rai aleeyu ya kamo hannunta gami da zaunar da ita yace Kallleninan mamana jia nace miki jirgin sha,biyu zai biyo ashe na shadaya ya biyo yana dira yaimin waya naje na daukoshi Dan nasan halinki da shiririta shiyasa bance kije ki daukoshiba ba gashi na Kawo miki shi da hannuna ba Yace Bude idanunki kiga yayanki yaddah ya koma dan saurayi mijin yan mata Ta goge hawayen nata da hannunta ta saci kallonsa Akai sa,a Shima kallon nata yake. Tunda suka shigo yake mamakin yaddah Akai cikin shekarunda basu wuce shiddah ba afnan ta zama. Budurwa sosai Tsaantsar kyawu da siga mai dauke hankalin namiji Ya bayyana a jikinta Lallai tsarki ya tabbata ga ubangiji wannan halittar Wani lallausar murmushi ta sakar masa Wanda har saida kumutaunta suka lotsa Ta matsa kusa dashi tace ur welcome yaya adnan ina Maka murnan kammala Karatunka Tanx afnan ya fada yana murmushi Wanda har saida wutshiryarsa suka bayyana Sannan ta juya ta kalli abban nata tace daddy an kammala gyara masa sashinsa Sannan na hada masa wata yar qaramar walima ta murnan dawowansa da wanne Zai fara? Yace ya fara wanka ya shirya Sannan sai a gabatar masa da komai Tace tnx daddy Ta juya ta kamo hannunsa tace muje na nuna Maka sashinka Yace to yar qanwata Ta kaisa falon nasa ya tsaya yana kallon ko ina yace woo duk ni daya afnan Tai murmushi har bedroom dinsa ta rakashi Tace yanxu kaje kai wanka kafin ka fito zan kawo Maka kayan da zakasa Saika fito yace tnx yar kanwata. Binta kawai yake da kallo harta wuce Sannan ya zauna a bakin gado dan yadan huta kadan Baifi minti biyar da zamanba ya miqe da sauri ya fada toilet domin yin wanka yana fitowa yaga an aje masa Wasu kaya irinta yayan sarakai komai iri daya Hatta takalmansu Wai wata yar murmushi ya shirya tsab kayan sunhau jikinsa Ya manna yar siririyar glas dinsa ba Qaramin kyau yaiba dan haka wata qasaita taxo masa Ya fito tamkar yarima dan sarki Yana fitowa yaji ana tafi raf raf ya ware ido duk qawayen afnan dinne na Skull dinsu Da kanta ta qarasa taja hannunsa har kan kujerar da aka tanada Sbd shi Afnan ta fito filin ita tai jawabi tare da baiyana matsayin adnan a wajenta Walimar ta qayatar dan anci ansha an kuma cashe Misalin la,asar Kowa ya watse Zuciyar afnan data adnan kuwa farincikine fal a ciki Baba wacce ta rainesu bata samu ganin adnan dinba sai wajen Bayan sallar magrin ta kallesa ta jinjina kai tace yanxu adnan kaine ka zama haka Cikin shekarun da basu wuce shiddah ba uhm lallai sai aure kenan Daria yasa kamin yace yar taki ta girma kenan? Tace wacce afnan ai Indai afnan ne daa sauranta kam tsulum ta sako baki tace wanne da sauran baba hauwa kina nufin nyarinyaceni har yanxu? Daria sukasa mata yaddah tai Maganar cike da shagwaba Yace kai baba ashe yar taki tanasona aure Ta xunburo baki tace niba haka nake nufiba yaya yanxu wacce take level 3 ce za,acema yarinya Nandai ya dinga zolayarta cikin wasa Har lokacin sallah yayi ya tashi ya barsu ya wuce masallaci Dawowar adnan ya qarasa shaquwa da soyayya mai qarfi tsakaninsa da afnan Washe gari da wuri afnan ta farka tun takwas na safe Sbd yau tanada lactur qarfe goma na safe Don haka ta farka tun takwas ta watsa ruwa ta tsaya wajen dressing mirro ta bata lokaci wajen kwalliya Wasu hadaddun Riga da siket ta saka. Sun mata kyau kuma sun Zauna a Jikinta kai inka ganta zakasha balarabiyace Ta maqala Baqin gilashinta gamida daukar qatuwar jakarta Mai dauke da manyan littafan makaranTa ta rataya toyo waje Sashin baba hauwa ta fara zuwa ta gaisheta Sannan ta wuce Sashin babanta Ta iskeshi yana break itama ta zauna Sukai tare Tanata zuba masa surutu daganan ta wuce wajen momcynta Tasan daman bata farka daga barciba dan haka ta fito ta wuce Bangaren adnan Saida tai knocking sau uku Sannan ya bude Yana sanye da wando treequeter sai singileti Wani irin kunyace ta kamata dan haka ta kasa shiga cikin dakin Ba tare data kallesaba tace Barka da kwana yaya adnan ka tashi lfy? Yace lfy lau afnan ya naki kwanan? Tace qalau yace sai kuma ina haka? Idanunta. A qasa tace skull dan yau inada lecture qarfe goma Yace shine kuma koki gaiyaceni tai murmushi Tace in zaka ai saimuje Kaga saima ka gaisa da qawata sady Bata samu zuwa walimaba jia basu gari ita da mom dinta Yace to shigo na shirya sai muje ko? Tadanyi wani murmushi A,a baridai na jiraka a mota To kawai yace mata ya juya ciki baiyi minti goma sha biyarba ya gama shri Yaxo ya sameta Baqin wando yasa da Jan tshirt kayan sun masa kyau matuqa Shidai komai yasa kyau yake masa ya daura siririn farin gilas dinsa Wanda ya qara Fito da fuskar tashi Ita kejan motar tana nuna masa gari da irin cigaban da aka samu Har suka isa b,u,k. Suna shga kuwa ta hango sadiya direba ya ajeta Ta fito da sauri ta yafitota Tace sady zo kiga yaya adnan din gashi a mota Cikin zumudi ta jata suka tafi tana ina yake? Yai qasa da gilashin motar yanna kallonsu da wadataccen murmushi A fuskarsa Sungaisa sosai Sannan afnan tace masa yaje da motar Sannan dan Allah yaxo ya dauketa zuwa qarfe uku Yace to Harsun juya yace bakijiba don haka ta dawo ta duqa ta gilas din motar Yace I frget to tell yu I luv u. Sannan ki kularmin da kanki Taja wani dogon murmushi kamin tace insha allahu Sannan ta juya inda sady ke jiranta Sukai gaba Sadiya diyar surayyah ce qawar nafi wacce ita kadai ta haifa tun daga kanta bata sake haihuwaba Sbd agreement din da Sukai da shajini Akan duk cikin data Samu nasune to hakan take ta Bangaren nafi itama duk kanwar jace Dan aleeyu yayi qorafin Akan yawan jubar cikinta in yace mata suje asibiti sai taqi yarda tace wai daga Allah ne Saidai ita sady ta girma afnan da kusan shekaru uku dan ko a skull din tana gabanta Qawancene mai qarfi a tsakaninsu kuma halayyarsu taxo daya abu dayane Ita afnan bata damu dason Abun duniyaba duk kuwa da aleeyu yayi iya baki kokarinsa wajen bata tarbiyyah Duk kuwa da yana saqa nafi na warwarewa A makaranTa Kwata Kwata sady ta kasa sukuni adnan ya fizgi zuciyarta Tunda take bata taba haduwa da namijindaya zama ful action irinsa ba Komai nasa yai mata maganarsa murmushinsa darewarsa natsuwarsa kai ita komai nasa birgeta yake Ita kanta afnan din ta fahimci qawarta bata cikin natsuwarsa dan haka suna fitowa Daga lecca Ta kirata a waya ta sameta a inda suka saba zama Batafi minti gomaba ta qaraso itada Wasu abokananta maza suna isowa Sukai gaba suka barta Bayan sun gaisa da afnan din sady ta zauna gamida kwanciya a kafadar afnan Din tace na gaji gaskia. Gida kawai zan tafi Afnan ta dubeta tace nifa na lura dake sady bakya cikin Natsuwarki lfy? Tai murmushi tace lfy lau afnan kawaidai yanayin Garinne kira yayanki ya maidamu gida Tace ai kin hangoshima can yana tahowa Ta miqe da sauri tana tashi muje to me zamu tsaya jira Bata tanka mataba suka jera dan iskeshi a inda yake Kafin su qarasa ya fito ya budema afnan gidan gaba ta shga sady ta shiga Gidan baya Ya zagaya ya shga yaima motar key afnan ta dubeshi Kai yaya irin wannan tuqi haka sai kace kana rarrafe Ya waigo ya kalleta yace idan ba,ai tuqi hakaba ya kikeso ayi Tace cessss ka taka mota yayana irin tuqinda zai tada hankalin jama,a Yace a,a niban iya wannan tuqinba ai saida raine kuma da daukan alhakin jama,a Bata sake tanka masaba dan haka ya canja salon Maganar da Ina zamu sauke qawarki ta fada masa ya dauki hanyar Afnan ta kwantarda kujerar motar tana kallon titi ya riqo hannunta yana fadin Wai qawarki bata maganane? Ko axumin magana take? Ta waiwayo tana wai yau yadai sady baby Yayanama ya lura da relax dinki Ta lankwabe kai kamin tace banida abokin hirane shiyasa Ta girgiza kai tace hankalinki nakan yayanki adnan nikuma bansan inda zansa nawa hankalin na samu sa,idaba shiyasa na maida hankalin nawa kan titi kawai Tunda Naga alamun Iran ta yan uwan takace Daria Sukai Sannan adnan ya amsheta tace aimu Bama wariyar launin fata Asalima hirar indake xatafi armashi Ya kalleta ta gilashin mota ya daga girarsa sama wato ta yarda da abinda ya fada Tai murmushi tace yayanmu kenan lallai zaman America ta amsheka. Gabadaya yanayinka da kalamanka irin Nasune Iya kwalliya magana kai Hatta halittar taka Wai kuwa qawata ta tava fada Maka kaidin kyakkyawane? Daria yayi yayinda wani dadi ya ziyarci zuciyar afnan kasancewar an yabi sahibinta Adnan yace sady kenan gashi kin ari bakinta Kinci mata albasa saida Allah yasa warinta bazai damekiba Ta kada idanu tace ko daya Tunda ba. Qarya na fadaba Kai kyakkyawane kyanda mata dari zasu kalla su kyasa Idan nai Qarya ka fadamin mata nawa ka tara tsakanin America da nigeria Daria ya sakeyi yace hoo sady keko wacce irin mutunce Tace mafadar gaskia mai yaba duk Wanda yakai a yabeshi Kanada kyawun dake fizgar zuciya cikin yan sakwanni Kasan mata akwaisu dason namiji mai kama da zakin maza irinka Wannan karon dariar harda kyalkyalawa dan ya Gano zolayarsa take Afnan kuwa kasa sa musu baki tau dan ta kasa controll din zuciyata na kissa mata Lallai akwai alaman tambaya a cikin kalaman sady tome take nufi Oho Aure. Kan. Aure Chapter12 Afnan ta nuna masa wani makeken gate mai kama da qofar shiga gar Yai horn masu gadi suka bude Yai fakin sady tace a gaskia saika shgo ka gaishe da hajia ta Dan kuwa lbrnka tuni ya gama cika mata kunnuwa wajen afnan Yaso ya bijire saida afnan ta saka baki Sannan suka rankaya cikin gidan A falo na uku ta ajesu tasa mai aiki ta kawo musu lemo da ruwa Sannan tahau saman batafi minti gomaba sai gata. Tare da momyn nata Hajia surayyah Waddat hade cikin wata qasaitacciyar shiga irinta mata masu kudi Ta hakince saman kujera fuskarta dauke da murmushi Suka gaisa da adnan tai masa sannu da zuwa Sundan taba Hira kadan. Afnan tace zasu tafi Hajia sury tace wannanne baku isaba dole ku zauna a gidannan yau zakuyi Lunch Afnan tace kai Momy batasan zamuzo nanba Tace ba komai zan kirata a waya na fada mata Afnan tace a,a karki kirata mommy zataimin fada Tace bakuyi dai niyyar zamaba kawai tace a!a ba haka bane Momy ai Zamu dawo wataran Tace to Allah yasa Suka miqe Sady ta rakosu har bakin motarsu suka shga Sannan sady ta dubi adnan tana wani kashe idanu Yanxu sai yaushe kenan yaya adnan? Yadanja wani murmushi yace a,a wannan tsakaninkune keda qawarki Tadan batarai tace haba adnan yanxu dole in zamu hadu sai qanwarka ta sani? Shikenanan yanxu bani numberka Amsar wayar tata yai ya saka mata Sannan Sannan ya shga motar ta daga musu hannu Haka kawai afnan taji ranta ya baci tsayuwar sady da adnan Taji tamkar ta miqe ta shaqesu wani irin kishine Mai zafi ya tokare mata zuciya Don haka koda ya shga motar ya tada bata kulashiba har Suka fara tafiya mai nisa hakan yasa ya lura fushi take dashi Don haka ya takalota da magana Yace afnan yau na hadu da qawarki data fiki zafin dumi wai! Carkwai kenan Ta waiga ta kallesa a hasale saidai batasan abinda zatace masaba Sbd takaici Haka ya karaci surutansa har suka iso gida Yana fakindin motar tun kafin ya kashe ta fude motar da sauri ta fita Don haka Shima yai hanzarin fitowa ya riqota shidai baisan abinda yai mataba Na fushi hakaba Don haka yace. Haba yar qanwar laifin me nayi ne? Meye nai miki haka yasa kike fushi dani? Haba matar karkimin haka fushinki zaifi komai dagamin hankali A duniya zan iya jure komai amman banda fushinki Hawayene suka cika mata ido duk qoqarinta Nason maidasu amman Saida suka zubo Har lokacin zuciyata bai dena tafarfasa ba Ita kanta batasan irin kishintaba Hannu yasa cikin aljihunsa ya ciro hankachip ya bata bata musa masaba ta amsa Ta share hawayen suka nufi cikin gidan ba tare daya cigaba da matsa Mata Akan jin abindaya bata mata ranba Tundadai ya samu ta dawo walwalarta kamr da Sadiya na tsaye gaban mahaifiyarta ita kuwa uwar tata na zaune tana sauraron Abinda zai fito bakin tilon diyar tata Saida tai taku daya zuwa biyu Sannan ta isa gaban uwar tata sanna ta duqa tana Kallonta tace mommy kinga adnan babban likitan kwakwalwa ne Na taBbata kin hango abinda na hango Mommy adnan ya cancanci ya zamo sirikinki Ta ko wacce fuska Dan ya hada abubuwan da ko wacce uwa zayima yarta sha,awar aurensa Mommy adnan nada kyau hankali ga tunani gamida hangen nesa Sannan uwa uba ga wadata danna taBbata koda baida komai nan gaba to Zai tara dan kuwa afnan ta fadamin daddynta nacan yana qera masa wani hadadden asibiti Wanda za,a zuba masa qararran likitoci na nan qasa naija Dana qasashe waje Mommy adnan ya shga zuciyata ki taimakamin na sameshi a matsayin mijina Kuma uban yayana Ki taimakamin momy Hajiya sury tayi wani dogon murmushi kamin tace Tace lallai barewa ba zatai gudu danta yai rarrafeba sady zamannan da kikaga Nayi nima Tunanin da nake kenan Saidai wani hanzari ba guduba adnan dinnan da kike ganinsa ba iyayen Afnan ne suka haifesaba babantane ya daukoshi daga kauye lokacinda uwarsa ta rasu Anya suma ba shirin hadashi da afnan din sukeba dan gida bai qoshiba Ai baza,akai wajeba Sady tai shiru tanadan nazari danta karanci abubuwa da dama a tsakanin Adnan da afnan din tadanyi wani takaitaccen murmushi tace Tabbas na lura da wata halaqa a tsakaninsu saidai ai Momy kwace goruba a Hannun kuturu ai ba abune me wahala ba Dan afnan aiba abokiyar takarata bace Sannan kuma adnan aiba ajinta bane Hajiya sury ta kyalkyale da daria tace wannan abune mai sauqi Tunda Hajia nafin ai,a hannuna take Don haka ki kwantar da hankalinki Kamar kina jirgin sama mai ya qare Sady ta kyalkyale da daria ta rungume momyn nata tana fadin ina sonki Momy na Adnan ya soma shirye shiryen tafiyansa zuwa kauye Yaje yaga sauran yan uwansa dan haka aBban afnan aleeyu. Ya shirya masa tafiyan da gaggarumar tsaraba Afnan ta kafe tanason ta bishi Tunda rabonda daddy ya kaita anfi shekara Haka ta dinga roqon yayan nata dan tasan abbanta mai sauqi ne Saidai shi adnan yaqi yarda dan yasan halin hajia nafi sarai Dan bai manta kiyayyarsata da zaluncinta akansa Don haka yaqi dan karta janyi masa allura ta janyo garma Tunda tsakanin sashinsa da nata akwai tazara mai yawa zan saika tsallake Faluka yakai goma Shiyasama basa haduwa tundaya soma gaisheta ta dakatar dashi tace karta sake ganin qafarsa a bangarensa daganan ya daina koda bi ta hanyar falon Ranar asabar misalin qarfe goma na rana adnan ya gama shiryawa tsaf Yahau wata dakakkiyar shaddah Afnan na gedensa tana kallonsa Yana zuba kaya cikin jakarsa harya kammala Ya dago yana kallonta itama shidin take kallo Ya aje jakar ya nufo inda take Yace yaya dai afnan Naga Kamar kina cikin damuwa Ta girgiza masa kai jiki a sanyaye Yace bakiso na tafi ko afnan? Kinason na zauna kusa dake koda yaushe ko?ta daga masa kai alamar eh Yace inhar kin shrya aurena yanxu in naje kauye saina sanarma malam ya samu Abba ai maganar Inhar Kinason kasancewa dani Wani gajeran murmushi taja kamin tace Inhar hakan ta faru zanfi Kowa farinciki muyi aure mu tare a sbn gidan Da Abba zai Gina mana Kullun mu kasance a tare ina kusa dakai ina Maka Hira mai dadi Ban yarda da yawoba balle hirar dare ka gane Daria yai Yaja dogon hancinta yace yarinya Indai nine har saikin gaji dani kince Na fice na baki waje Ta zaro ido tace injiwa? Tace Allah a,a aini bana gajia da ganinka kusa dani Duk wuya mu kasance tare na maka alqawari duk wuya duk rintsi bazan Juya maka bayaba Yace insha allahu nima bazan gujekiba afnan duk runtsi Zaki sameni mai riqon alqawari Kedai kiyita mana addu,a kawai Tace insha allahu ya miqe yace kinga zaki shagaltar dani Har inda motar da direba ke jiransa ta rakashi Harya shga direba yatada mota suka tafi tana daga musu hannu Har suka fice Afnan ta juyi ta dawo dukta damu ji take Kamar babu sauran Wanda ya rage Mata a gidan Don haka motarta ta hau ta nufi gidansu sady acan ta wuni Saida magrib ta dawo Bayan ta canja kayan Jikinta ta nufi falon mom dinta Ta sameta tare da Wasu qawayenta Wanda sukazo daga turai acan ta samosu bayann sun gaisa ta wuce falon baba Hauuwa ana suka kusa raba dare suna hira Kwata Kwata babu shaquwa a tsakanin hajia nafi da yarta dan inka gansu wuri guda to gaisheta tajeyi inka gansu saika rantse ya da qanwane Dan ba zakace uwace da yaba Don babu wannan shaquwar ta ya da uwa Da safe kafin abban nata ya fita taje ta sameshi tana shaida masa yanxu suna level din qarshe Watanni suka rage ta qarasa Abban yace shikenan sai aure kenan ko tai wata daria Tace kai Abba kaima harda kai? Yace to afnan idan ban miki aureba zama zamuci gaba dayi? Ta girgiza kai alamar a!a. Tace to amman abba Da yaya adnan zakai mana auren ko? Yace au ashema nidake zullumin abinda ke raina ban saniba harkun gama Kitsa komai tsakaninku Yace lallai kan afnan ni kaina banga ta zamaba cikin satinnan zanje Musawa na sami su malam a tsaida maganar auren Naku kawai Banga abinda zan tsaya jiraba Tamkar ta daka tsalle har abin ya soma Bama abban nata kunya Yace kai afnan wai bakijin kunyata? Sai a lokacin wata kunya taxo mata ta miqe da gudu tabar falon Ya girgiza kai yana daria kamin yaci gaba da latse latsen laptop dinsa Satin adnan hudu da tafiya kullun suna maqale da juna a waya Kullun tanbayarta don Allah yaya adnan yaushe zaka dawo Yace mata tayi haquri a gama maganar aurensu sai aci gaba da shirye shiryen bikin nasu Ranar asabar itace ranar data kasance aka daura auren yar gwamna Ita da wani dan sarki Don haka bikine akai irn na yayan manya Su hajia nafi ba zama don sune qirjin biki Qarfe takwas daidai ta turo aka dauki afnan dan halarta wajen bikin denner din da aka shirya a wani abban hotel Afnan na sanye cikin dinkin ankon da akai don diner Tarone akai na manya. Tare da dangin amarya Dana ango Anasha raye raye ciye ciye da tande tande Inda makada da mawaka suka baje kolinsu afnan ansha r awa Hatta momynta ta cashe yaddah ya kamata Tun a wajen afnan ta tsargu da kallon da wani mutun ke mata tamkar ita kadaice a Wajen Har aka tashi motar mom dinta tabi Tana shirin shga taji ana kira bakijiba baiwar allah Tai tsaye tana kallonsa ya qaraso kamin yace Baiwar allah sunana jibri ibra ina daya daga cikin sojojin dake takema General abdullahi aminu Abba baya A yanxuma shine ya turoni zuwa wajenki Yace na amsar masa lambar wayarki Wani gajeran tsaki tajaa tace wannan shirmenne yasa ka tsayar dani? Toka koma kace masa duk randaya shirya amsa numbert. Ya tako da qafarsa yaxo ya Amsa. Jikinsa na rawa yace ki taimaka hajia wlh zakisa na iya rasa aikina Afnan tabishi da harara ta Shige motar Momcynta dake

Chapter 4 of 16