Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
duk fadinsa nafi nawa ne Ta jata zuwa wajen gidan tace dubi ma,aikatan gidannan. Securities duk danni suke zube anan Ta jata wajen jeep jeep dinta ta buBbude matasu a xuciyarta tace wannan ko fadar shugaban qasa ai sai haka Tace kinga motocinnan duk nawane a cikinsu nake yawo tare da escot dina Ta jata cikin gidan har zuwa bedroom dinta Tajata har zuwa wajen lokarta ta janyo Wasu manya manyan album Tace matar gwamnace wannan qawatace dubi waccan matar shugaban qasace inyanxu nace inason ganinta ba bata lokaci zata baiyana Wadannan kuma duk matan ministoci ne Da manyan yan siyasa Nifa a yanxu bansan me ake kira da talauciba Yaddah naso haka nake rayuwata dan inada shi Ta miqe tasa mukulli ta Bude wata wawakekiyar wadroof dinta babu abinda ke ciki Sai tsaunin yan dubu dubu abin har yaso firgita nafi Tace kinga duk wannan dukiyar tawace sai yaddah naso zanyi dasu Ta maida makullin ta ka$o hannunta juwa jikin wani bango Babu Wanda zai dauka akwai qofa a wajen Sbd Wasu tsadaddun labulaye da akasa a wajen Suna shiga fitsari ya kusa kubce ma nafi tace duba kiga wannan mahaifinane Wanda ya haifeni da cikinsa Alhaji qasimu..... Take ya dinga aman sabbbin yan dubu dubu Tai wani murmushi ta duqa tana tsincewa Tace kin ganshi Nina kaishe makkah da kudina Nafi ta dinga bin dattijon da kallo Wanda ya koma tamkar kwarangwal Suri ta miqama nafi kudin tace ki riqesu dubu hamsin ne Ta janyota suka fice ta sake kukke Dakin suka zauna saman lumtsatstsun kujeru Ta dafa kafadarta tana fadin qawata a duniya bakada Masoyan da suka wuce kudi Su kansu iyayen sai kana dasu suke sonka Kudi suke sama mutun farinjini su sama kyakkyawa Baqin jini Inhar bai dasu Nafi kiyi kudi duniya tasoki a fantama dake a duniya A wannan duniyar in kinyi kudi kece mutunfa inkuwa baki dasu to dake da shara Duk daya kuke Dan har yayan da kika haufama qinki zasuyi Kiyi kudi mijinki ya dawo kan tafin hannunki Nafi tai shiru tana tunani kalaman sury tabbas abinda ta fada Gaskia ne To amman ta waCce hanya zatabi ta kawo daddyn nata itama? Tundata dawo gida tunanin abinda take kenan zuciyarta ta kasa natsuwa Ita kanta ta katsa zaune ta kasa tsaye Tabbas zataso ace itama ta zama wani abu a duniya Amman ta rabu da daddynta anya. Hakan zai yiwu kuwa? Ahaka aleeyu ya dawo ya sameta Yai juyi« duniyarnan Akan ta fada masa abinda ke damunta amman taqiya Dan haka ya qyaleta ana sallar magribyabar gidan Can gidansu ya nufa anan yaci abincin dare Momy ke fada masa Gobene amsar lefen kausar in yaje gida sai e fadama nafin Yace to ya dawo gidan nasa har ya gama shirin barcinsa amman babu nafi Don haka ya fita da kansa ya nufi Dakin nata Tana kwance lamo tamkar mai Barci ya hayo kan gadon Ya janyota jikinsa yana fadin sunanta da sassanyar muryarsa Taqi Bude idonta dan a wannan lokacin bata buqatar Kowa ya dameta Muryarsa tai rauni yace nasan kina jina nafi Ki taimaki zuciyata ki fadamin abinda ke damunki Wlh in kikaqi fadamin bazan samu kwanciyar hankaliba Ta Bude idanunta Wanda suka kada Sukai jajir muryarta gunin ban tausayi tace Kayi haquri aleeeyu kainane kemin matsanancin ciwo Yace amman shine baki fadaminba na kaiki Asibiti? Laifin me nai miki da kika zabi horar dani haka? Tace ba haka bane nasha magani nasan zai sauka Ya qara rungumeta yace Allah yasa yai mata addu,a akai Sannan ya qara kwantar da Ita a kirginsa dandai kawai ta samu barci Shima barcinne ya daukesa Can cikin dare nafi tai mafarki wannan mutumin Wanda suke kira da sha jini Ya biyota a cikin daji sai gudu take harta gaji ta fadi yasa dogayen hannunsa ya capkota a wuya Yana fadar zaki kawo baban naki koko na hallakaki yanxu kawai mu huta? Ihu tasa dan ji tai numfashinta na fita daqar tace zan kawo Wlh zan kawo ba Nanda kwana uku kukaceba? Ta dinga qaqari tana koqarin amsar kanta Aleeyu ya farka a firgice yana fadin lafiyarki kuwa Nafi Ta farka a waharce tana riqe da wuyarta Yai saurin riqo hannun nata yana duba wuyan yaga yakuwa karce harda dan jini Hankalinsa ya tashi saidai nata hankalin yafi na Kowa tashi Ya dinga tofa mata addu,o-i harya samu Barci e dauketa Hankalinsa ya tashi dan yanajin tsoron ace aljanu sun fara Taba masa mata Barcinda bai iya komawaba kenan kai hatta office bai iya zuwa ba Ita kuwa sai sharar barcinta take hatta fitar numfashinsa Akan idonsa take Qarfe tara ta farka ya taimaka mata tai wanka Sukai break Ya bata magani tasha Ta samu natsuwa sosai a jikinta Tunda ta kullla mai fissheta Ganin hakan ne yasashi fada mata kawo laifen kausar cikin zumudi ta shirya ya Dauketa a motarsa ya kaita shikuma yashiga zaga abokansa Lefene na nunawa a idon duniya akwatina guda tara Kayayyakine masu numfashi a cikin akwatinan harda makullin mota sbw dall Abinda ya qara tunzura nafi kenan Tace lallai bazan zaunaba qanwata ta barni a baya ba Ba Ita ta baro gidanba sai qarfe tara na dare aleeyu yaje ya daukota Ranar data cika kwana uku ranar nafi da sury suka gama shirya yaddah Komai zai kasance Tunda safe kuwa inna ta kira aleeyu take fada masa diyar yayarta ta rasu Maria dan haka hankalinsa ya tashi a take ya hada tafiya Yaje yaima daddy da Momy sallama ya tafi Saidai ransa a bace yake yaddah yai juyin duniyarnan Akan nafi taxo suje amman taqi Har tana ikrarin ko iyayensane suka rasu ba zata ba Dan haka ransa a bace ya tafi shi daya Tun misalin qarfe takwas na safiya ya nufi musawa qarfe goma daidai ya isa Surayyah ta iso nafi tasa waya ta kira daddyn nnata Tai sa,a kuwa shi kadaine a lokacin yaana shirin tada mota Ya amsa wayar yana fadin nafi yaya mai gidanki yace bakyajin Dadi shiyasa bai tafiyan dakeba ko jikinne ya motsa? Cikin muryar rashin lfy taace dan Allah daddy kaxo gidana yanxu kaikadai amman karka fadama kowa Hankalinsa a tashe yace meke faruwane nafi meke damunki? Baibima kashe wayarba hankalinsa a tashe ya nufi hanyar sharada A rude ya shigo gidan a cikin falonya yana sallama ya ganta Yace ya haka nafi kin tasarmin da hankali daman lfyarki qalau? Tadanyi murmushi tace zauna daddy sai muyi zancen Ba musu ya zauna yana kallonta yana sauraron abinda zatace Surayyah dake labe a bayansu ta miqe ta hura masa hoda a bayansa yana shaqa Ya shiba Barci yakeba yanajin abinda ke faruwa Saidai bai iya motsa koda dan yatsarsa Su biyun suka kamashi suka fifta sukasa a boot din motar tata Sannan suka jira mai gadin gidan ya dawo daga Aiken da Sukai masa na katin waya Sury taja motar Sukai gaba Basu tsaya a ko inaba sai cikin gidan na tsafin nasu daya daga cikin gardawa Dake aiki a gidan ya sunkuce Alhaji muftahun yai ciki suma suka shige Kamar farkon zuwansu yauma haka tsarin yake Dan tana daga cikin wadanda sukabi layi Shajini ya dinga kwala wataa irin daria mara dadi Sannan ya dinga kiran Suransa har sau uku firgitgit ya farka Yana waige waige Ya gama firgita da ganin halittunnan Shajini yace Yace sannunka da isowa Alhaji muftahu barka da isowa wannan Kungiya inamaka albishir na yarka Nafisa taban jininka Jikinsa na rawa yace qarya kuke maqiya Allah yata ba batacciya bace Na tabbata ba zata iya aikata wannan qazantaccen abinba Kudai kuce kun daukonine Sbd wata manufarku Shajini ya qara babbakewa da daria Kamin ya nuna nafi ta fito jiki a sanyaye Daddy ya kalleta cikin firgici ya fara tuno abinda ya faru a baya Wata gigitacciyar qara yasa Yace ashe damann ana haka? Ahe daman akwai danda zai iya aikatama iyayensa irin wannan? Lallai rayuwarsa batada wani amfani Koda basu kasheshiba yasan Baqin cikima kawai bazai barshi ganini Irin wannan Baqin ranar ba Shajini ya dafa kan nafi yace aljani lummun gyaxo ya yarda dake kuma ya eyntaki Ya baki duniya ki juyata son ranki Sannan ya nufi gun daddy ya watsa masa Wasu ruwa a take ya fad a wajen ya lullubeshi da wani farin kyalle Ya daukeshi ya daurashi saman wannan tukunya dake gabansa minti talatin Sannan ya sauko dashi Babu abinda ya canja ajikinsa illa fatar jikinsa da tai fari fat Sha jini yasa wata kwarya ya kwarfo jini aa cikinta ya dinga basu daya Bayan daya Har yaxo kan nafi Tasha Sannan yasa ta wanke fuskarta dashi Ji tai tamkar ancire mata imani da tausayi a lokavi guda Ji take zata iya aikata komai Saida Kowa ya gamasha Sannan sha jini yace nasha jinin babanki nafi. Gawarsa shine rigiyar kudinki AURE KAN AURE 8 Yace duk lokacin da kike buqatar jini sunansa kawai zaki kira amman Duk lokacin da nake buqatar jinin mutun kikaqi kawo Mana to jininki. Zan shanye Ta amsa da na amince Sury tace to amman sha jini munaso a rufe mana bakii Jama,a kar Wanda ya tambayi ta yaya ya mutu Sannan in an rufeshi asa mana alamar da idan an rufeshi zamu gane idan munje Kwakuloshi Sha jini yai wata irin daria Yace yaddah bakin gawannan ya rufe haka har abada babu wani Mai magana Akan ta yaya ya mutu Kuma zan sa muku Jan kyalle a bakin kabarinsa duk kabarin da kuka gani da Jan kyalle to anan aka binne sa Sukai godia Sannan akasa musu gawar a boot din mota Kowa ya kama Gabansa Ihun da take kwararawane ya janyo hankalin Kowa a gidan A gigice ta shiga Gidan tana kiciniya da gawar daddyn nata Mommy Tayo kanta itama a gigice ta kamata suka shga cikin gidan da gawar Hatta ma,aikatan gidan saidai suka taru akansa tuni Gidan ya kaure da koke koke Kamin kace me gidan ya cika da mutane akaima Wasu waya Akace Alhaji muftahu ya zama marigayi Lallai tsafi gaskiyar maishi daidai daidai da tambayar ya akai taga gawar babu Wanda e mata Musamman yaddah duk tafi Kowa shiga tashin hankali Kowa ita yake lallashi Saidai kausar tafi Kowa zama abin tausayi Yaddah daddyn nata yaci mata burin aurentshin kenan yanxu saidai Labarinsa Da aka sanar da aleeyu kuwa har kusan zaucewa yayi washe gari ya iso garin kano Randa aka rufeshine nafi taita Suman qarya a cikin dare dan haka sury tace Abarta ta kaita asibiti Tunda duka yanxu goma na dare da wani abune Tana daukarta a mota gidanta ta wuce Wanda babu Kowa a cikinsa Tsakiyar dare misalin qarfe biyu na dare Suka dauki mota suka nnufi maqabartan Lokacin da suka isa dukkansu da akwai tsananin tsoro a tattare dasu dukkansu suka fita Nafi ta riqe hannun sury muryarta qasa qasa take cewa Ance babu masu gadi a maqabartannan amman Kamar haske nake hangowa Surayyah ta rada mata tace ki cire tsoro sury banda magana kinsan muna cikin Hatsarine yanxufa Daganan babu Wanda ya sake magana cikin sanda suke haska toch Sunfi awa suna zagayea maqabartan duk sun hada gumi ga tsoro dake tattare dasu Sury ta riqe kugu tace na gaji nafi gaskia mu koma kawai mu fadama shajini Ya sake yin mana wata alamar dan mu gane Da sauri ta dubeta tace haba Sury ya duk bamuji wahalar abinda muka aikataba sai kawai Wahalar tono shi a kabarin nasa Cikin kasala tace inko baki gode abinda nai mikiba afi aiko ba zaki tsineminba Duba kiga har uku da rabi tayifa A Kowa wane irin lokaci za,a iya ganinmu kin kuma San tamu ta qare kenan Nafi zatai magana sury taja hannunta Sukai gaba Suna shirin fita daga maqabartan kenan Kamar daga sama. Nafi ta Hango wani kabari lullube da Jan kyalle Tai saurin tabo sury tace ke duba min Kamar gashi can Tana dubawa tai saurin janta tace xo muje shine qawata Suna qarasawa suka jare Jan kyallen Sannan nafi ta zaro gatari da masassaqi Suka fara tone kabarin Saida suka dau lokaci kafin su Bude kabarin cikin tsoro da fargaba suka Bude likafanin nafi tace aikuwa daddy nane Nan daddy ya kamata Suka kinkimeshi sukakai cikin but Suna niyayyar shga motar ne aka haskosu da fitila ana kai suwaye nan? A firgice suka kwasa a guje har sukaso su wuce motar sury tai saurin fadawa Taima motar key jin haka itama nafin ta shiga kafin ta ida zama har anyo kansu Sury tabama motar wuta suka kwasa a guje Aka fara kiran jama,a ana jama,a ku taimaka ku tare barayin gawa Nafi ta runtse idonta dan ta gama fiddah raai ga nasara Suna hawa kan titin lbr ya sauya salo dan sury gudu take na Fitan hankali saida ta tabbatar Babu mai binsu Sannan ta dauki hanyar gidanta na sirri Sukai facking Sufa shge ciki Qarfe hudu da rabi daidai na asuba agogo ya buga Nafi ta fada kan gado tana fadin Allah ya taimakemu sury Da yau asirinmu. Ya tonu Damun tozarta mun wulaqanta a duniya Kuma da Allah yai wadai damu Sury tace kedai bari tawan yau ko runtsawa ban iyayi dan haryanxu hantar cikina bata daina kadawa ba Nafi tai daria tace kai sury na tsorata da tukinkifa yaddah kikasan ina cikin jirgin sama Hira suke sosai sai har akai sallar asuba. Qarfe shiddah daidai suka canja mota Sukasa gawar a cikin akwati Sukai gidan nafi mai gadi ya Bude qofa Ta Bayan gidan suka shiga boys quter gami da ciccibar Akwatin Wani bangare suka shiga Wanda ba!ama amfani dashi yanada babban falo da Qaramin bed dinsa da tailet dan haka suka kutsa ciki Nafi taja wata ajiyar zuciya mai qarfi ta Bude Akwatin da daddyn nata ke ciki ta gansa kwance Tace. Muftahu Saiga kudi na fita daga bakinsa Lol Ta duqa ta kwashe masu yawan gaske suka tafa gamida sa daria Sannan ta rufe Akwatin da Dakin da wani shirgegen kwado Suka fito Sukai gaba dan zuwa shaidama sha jini aikifa yayi D did is done Bayan sun dawone Murna ta koma ciki dan motar aleeyu ne a aje a cikin gidan da alamar ya Dawo kenan Kallon kallo suke mai dauke da fargaba gamida tsoro Dan haka Sukai fakin din motar jiki a mace suka Nufi cikin gidan Yanaa tsaye riqe da maqullin mota a hannunsa kome yake nazari Oho masa Suna shigowa yai juyo da hanzari yana kallonsu kallon daya hautsuna musu yayan Hanji yace AURE KAN AURE Chapter 9 Yace me kukaxo dauka? Ya akai kuka baro gidan gaisuwar? Nafi ta shga inda inda In....ma..... dama...' Sury tai saurin amshewa tace bata da lfy ne Shine na kaita asibiti tun jia ta rinqa suma Yanxu ta samu sauqi sosai shine nace bari na fara kawota gida Ta dauki abinda zata dauka saimu wuce Ya kada kai yace babu wani abunda zata dauka ku wuce muje Ya tasasu gaba suka wuce Yaja motarsa su kuma suka shge tasu Saida akai sadakar bakwai Sannan aleeyu ya dauki nafi suka Koma gida Aka qara daga bikin kausar har sai Bayan mommyn nasu ta gama Takaba Nafi kudi sun samu tarawa kawai take dan cewa tai ai ba zatama fara bushasha Yanxuba dan kar duniya ta tuhumeta Sunaji ana maganganun anshga maqabarta an sace gawa hardasu cikin Masu zagin masu irin wannan halin lol Don haka aka qara gyara maqabarta da masu gadi Bayan Momy ta gama Takaba ne aka Fara shirye shiryen bikin kausar tare da rabon gado Aka raba akabama Kowa nasa Sun samu kudi da qasarori bata wasaba dan Alhaji muftahu ya tara Dukiya da qaddarori. Bata wasaba Hakan yasa kausar ta ciro tata aka shiga bagajajr duniya wajen bikinta shikansa aleeyun yayi iya bakin qoqarinsa wajen ganin kausar din ta samu Abimda takeso Bangaren nafi kuwa aleyu ne matsalarta tanason bushasha amman da zarar ta Fara zai taka mata birki Babu kuma yaddah ta iya Ammanfa dukda haka saida ta sai irin jeep jeep din da sury ke dasu saidai Aleeyu bai barta ta saka securties ba dan aboyema tasai wani katafaren Fili ba tare da ya saninsaba Duniya kuda ta fara tamfatsa gini Nafi ta rinqa Jan ra,ayin aleeyu da ya shiga harkar siyasa Amman sai yace mata ba yanxuba da sauran lokaci Shi kansa yanasan cikama daddy burinsa Nason zama dan siyasa Qarshen wata ya shirya ya tafi qauye Domin duba iyayensa Ya gyara musu gidansu dan dama tuni yasa aka rusheshi akai musu na zamani Sunajin dadin rayuwarsu a ciki dan ya zuba musu kayan alatu Dan har mai aiki ya aje musu yana biyanta kasancewar girma ya fara Jan iyayen nasa Anan ya samu innar tasa ta dauko dandan marigayyah maria Wacce ta rasu tabar yaya hudu inna ta dauko daya Babban cikinsu Wanda ake kira da suna adnan Aleeyu ya taisaya masa mutuwar mahaifiya aiba wasa bane Da zai tafine yacema innar tasa ta bashi adnan din ya tafi dashi da farko taqi dan tasan iskancin matarsa Saida malam yasa baki Sannan tabar masa shi suka tafi Haka kawai aleeyu yaji Yaron ya shiga ransa Kyakkyawane jajur dashi kaikace balarabe Suna tafe aleeyu ya dafa kan yaran tausayinnsa ya game masa jiki Wanda a qalla bazai wuce shekara goma a duniya ba A haka har suka iso gidan Nafi na kwance a falo tana game a wayarta Aleeyu ya shgo riqe da hannun adnan Nafi ta bishi da kallo harya samu wuri ya zauna Ta wurgo ido tana kallonsa a yamutse Kamin tace wannan Yaron kumafa mai kamada zabiya? Ina ka samoshi kko almajiri ka samo mana? Ya qarajan Yaron jikinsa kamin yace ya miki kama da me neman taimako? Ta tabe baki tana fadin aiko mai Maganar bai wuce neman taimakoba Yace eh amman ba anan ba ko? Tace na nawa ai saidai kuma kar,a kuma Yace wasa kike yarinya kinji dubeninan daga sama har qasa na wuce na nemi taimako a wajenki Wannan da kike ganinsa Yaron diyar yayar mahaifiyatace Dan mamansa ta rasu nakeson riqeshi na bashi kyakkyawan kulawa Tashi tai kamin tace Wlh baka isaba Aikin banza gayyar arna a idi Dole ka dauke yaronnan ka maidashi inda ka daukoshi Aika gane ko? Yace a,a saidai idan naji saukar bugu zan gane kinji uwata Ta qara harzuqa tace kaga malam ba neman magana nakeba umarni nake baka bawai shawara ba Bazan zauna da dan wai wata gawa ba Inko kace saiya zauna Wlh to saiya kwammace yawon barance da zaman gidannan Dan saina mayar dashi abin tausayi Aleeyu ya miqe tare da Yaron ya kalleta sama da qasa Sannan yace To fadama kaji dansu tattabaru tashi suke Bai saurari abinda zata fadaba ya wuce abinsa yana kwallama ladidi mai aiki Kira Ta fito a guje yace ina binta? Tace tana ciki yace kirata itama kuxo tare Batafi minti biyarba suka dawo sai kwasar gaisuwa suke Ya amsa yace musu kunga yarone gashi dan uwanane na jini mahaifiyarsa Ta rasu nakeaon dan Allah ku bashi kulawa yaddah ya kamata duk wani abu da ake buqata kumin magana Suka amsa da to amgama ranka shi Dade insha allahu zamu riqeshi bisa aman da gaskia. Gamida kulawa Binta taja hannun Yaron tana fadin meye sunanka yace adnan Tace yaro mai kyau dashi kuwa tubarkallah tamkar balarabe taja Yaron suka wuce ciki Shima ya wuce bangarensa Ba tare daya ya qara waiwayentaba abin ya qular da ita A zuciyata tace hum lallai aleyu. Dani kake zaune da kasan da wacce kake Zaune da baka isa nai Maka umurni ka takeba Wlh sai kayi nadamar kawo yaronnan cikin gidannan daan Yanxune zaka gane cewaa nafisan daka sani ashe kwallon shegiyace baka saniba Sati guda da kawo adnan aleeyu ya samar masa makarantar kudi Da take tare da islamiyyah Inya tafi tun bakwai bai dawowa sai 6na yammah Makarantar tsadaddar gaskece amman akwai karatu Nafi ta dauki tsana ta daurama adnan musamman dataga ya dauki son duniya ya daurama dan Daga office da kansa yake Wucewa ya dauko adnan din Kasancewar duk sai shidah suke tashi Dasun dawo zaisa Binta ta canja masa kaya su nufi masallaci indan Sukai magrib da isha,i sai su nufi cikin gari yawo Sai misalin goma suke dawowa Hakan ba qaramin baqantama nafi rai yakeba ganin ta rasa samun hanyar gallazama Yaron Yasa ta zari wayarta ta kira sury dan ta bata shawarar yaddah zata raba aleeyu Da adnan budan bakin sury sai cewa tai kibama sha jini shi kawai Take ke surayyah kina ganin ba za,a iya samun matsalaba kuwa tace wannne Matsa karki kawo wata matsala a xuciyarki tundai dai biyan buqatarki kike nema Tace to ai matsalar Yaron koda yaushe suna tare da aleeyu ne ta yaya za,ai mu iya Bama sha jini shi sury ta kyalkyale da raria tace nafi kenan Sbd ke sabon shga ce shiyasa bakisan taqadirancin shajini ba kedai kawai Allah e kaimu gobe kawai A haka nafi ta koma kan gadonta cike da murnan raba aleeyu da adnan......... Chapter10 Washe gari shine ranan da suka tunkari shajini da Buqatarsu tason bashi adnan amman ina Buqatarsu bata cimma Ruwaba dan cewa yai ya masa qanqanta ta barshi ya tasa Hakan bai mata dadiba Dan haka tasa musu ido tana kallonsa ya gama wahalarsa a banza ba moriyarsa Zaiciba Kwanci tashi ba wuya adnan ya gama primary Aleeeyu ya samar masa gurbin karatu na ajin gaba da primary a haka nafi ta samu Ciki Murna wajen aleeyu ba,a magana Don haka ya shga tattalinta da rainon cikin Soyayyah kuwa tamkar zai hadiyeta Hakan ba qaramin yin mata dadi yaiba dan daman Abinda takeso kenan Saidai kausar ta rigata haihuwa ta haifi danta namiji Alokacin cikin nafi baifi wata shiddah ba Gama Makarantar adnan ta primary taxo masa Da sauyin yanayi Dan nafi tamkar wata dama ta samu na shga Rayuwar yaron Qarfe biyu ake tashiinsu ya dawo gida sai hudu ya wuce islamiyyah Adnan yarone mai hazaqa ga farin jini Kowa sonsa yake Dalibai da malamai Ita kuwa nafi wani tsana ta dauka ta qara Dora masa Shiyasa yaron babu abinda yake tsoro sama da ita Dan shi kansa aleeyun ya fara fahimtar hakan Adnan tun yana yaronsa ya taso mai tsoron Allah da yawan addu,o.i na neman kariya Misalin qarfe hudu na yaMma nafi na kwance saman doguwar kujera A falo chartin kawai take da kawayenta Adnan ya fito daga Bangaren masu aiki sanye da kayan islamiyyah Army Kalo sun haska fatarsa saika rantse dan larabawane Nafi ta yinkura da qaton cikinta dan wata tara Ta kalleshi Kai zonan jiki a sanyaye ya nufi inda taken Kafinma ya qaraso wajenta din ta fincikoshi gami da daukeshi da wani Gigitaccen mari Wanda ya ratsa dodon kunnensa Yasa wata qara tasa hannu ta tashe masa baki tana Cewa. Rufemin baki munafikin banxa wato ka Maidani wata dodonka ko? Inna kiraka ka hau rawar jiki dan uwarka Ni abin tsoroce iye? Kuka kawai yake jikinsa sai rawa yake dan ko magana Ya kasa Tace eh lallai ba zakai maganaba kenan ko Ta shaqo wuyarsa gamida zaunar dashi Wanda har yakejin numfashinsa na fita Daqar. Tace to fara tsallen kwado ta lura bai iyaba dan haka Ta duma masa dundu ta nnuna masa yaddah zaiyi ya fara Ta koma ta kwanta duk ya hada gumi Qafafunsa suka shga karkarwa tamkar mai masassara Masu aiki suna kalllonsa saidai babu yaddah zasuyi Duk Wanda ya kalli Yaron saiya tausaya masa Har saida Yaron ya fadi Sbd Whl numfashinsa na fita daqar Ta miqe ta rankwasheshi akai tace Gobema idan na kiraka kamin rawan jiki Tai gaba abinta da sauri ladi mai aiki Taxo ta sureshi ta nufi bangarensu dashi Ta cire masa kayan jikinsa gami da watsa masa ruwa a toilet Bayan ta fito dashi ta dinga masa fifita harta samu ya dawo hayyacinsa Misalin magrib aleeyu ya dawo yana kiran adnan su tafi Masallaci Ladidi mai aiki ta fito tace ai baida lfy Hankalinsa tashe ya shga Dakin da sauri ya samesa kwance Yanacin biscuit Ya rungumeshi jikinsa yanajin kaunar Yaron a cikin xuciyarsa Ya tambayesa meke masa ciwo yace ba komai Saidai qafafuwansa da bai iya tsayawa dasu Ya dafa kai yace bari na kira likita Binta tace a,a yallabai ai Bama sai ankiraba mun gasa masa nanda Wani dan lokaci zai watstsake Ya dafakan Yaron yace meke Maka ciwo yanxu yace ba ko ina Sannan yace to me kake buqata na siyo Maka yace chocolate yace to Shikenan bari na fito daga masallaci Dan haka ya miqe ya fita Kowa yatafi domin yai sallah Daga masallaci osis ya nufa yai masa siyayyah Ya kawo masa dan yaita murna bashi ya baroshiba sau goma saura ya nufi nasa Sashin Ji yake tamkar ya kwana kusa da dan nasa Ashe can kuma nafi nacan tana ta faman naquda Ba sosaiba tanata faman kiransa yaqi daga wayar Don haka yana fitowa daga Sashin masu aiki bangarenta ya nufa Hankalinsa ya tashi matuqa ya gigice ya kwashesa sai asubiti Naqudace doguwa dan haka ya kirasu Momy cikin daren suka iso asibitin Kowa na mata addu,a Saida Momy taida gaske Sannan yabar asibitin Har washe gari nafi bata haihuba nafi ta shiga tashin hankali Tunda yai sallahr asuba ya iso asibitin dan haka likitoci Suka yanke shawarar ai mata aiki a ciro jaririn kawai Don haka aleeyu yasa hannu likitoci suka duqufa aiki Cikin ikon Allah aka ciro abinda ke cikin nata qatuwar jaririya Mai kyawun gaske Tunda aka gyara mai jego da jaririya Kowa yake rigerigen daukar yar Harda nursisi Don yar taxo da farin jini Aleeyu kuwa tankar yasa rawa aka sallamosu daga asibitin ya taci sunan Mahaifiyar aleeyun Wato hafsa don haka ya laqaba mata suna afnan Sunan Kwata Kwata baima anafi dadiba dan haka aka Shiga rikici ita aleeyu Wai yasama yarta tsohon suna irinna kauyawa gidadawa jahilai Baice mata komaiba Sbd Momy na gidan ya fice abinsa Washe gari akasha suna Kowa ya warwasa aka gasa yatsu Da da,am inji larabawa lol Don har walima akai maai qayatarwa Aleeyu ya daukoma mai jego da jaririya wacce zata dingaa kula dasu Ba wata tsohuwa bace dan ba zata wuce shekaru arba,in ba Aleeyu ya sallami Binta dan girma yaxo mata sosai ya bata jarin isasshe Daman ita Ladidi aure zatai Dan haka gaba daya yadau dawai niyar kayan daki da sauran abinda za,a Buqata Riqon adnan ya dawo hannun baba hausa ta iya rainon yara da basu kulawa Rikicine ya balle tsakanin aleeyu da nafi wai ita ba zata shayar da afnan ba Dan baa zata yarda nonota ya zube a banza a wofi ba yaddah tanaji tana gani zai watsar da ita yaje ya dauko yarinya mai nonuwa a tsaitsayeba Kunji jahila lol Ransa ya baci yai lallashin duniyarnan nafi taqi ta watsar dashi Ganin yar zata shga wani haline yasa ya tattara yar yabama baba hauwa suka nufi asibiti Aka ruButo musu madarar daya cancanta a dinga Bama jaririyar Tare da shawarwari Ko wane jariri a duniya yana buqatar nonon uwa Wanda nonon nada matuqar mahimmanci kwarai a gurin yaro Har shi. E sa likitoci basason anama Yaron daya wuce wata shiddah mix da madara Yaron daya rasa nonon uwa kan ya rasa rayuwarsa Sannan shayar da jinjira kansa shaquwa Sannan ta nonone jinjirai ke daukar kyakkyawar halayyar iyayensu ko Mummuna Itadai afnan ta rasa wannan gata na shayarwa saidai tana samun kulawa yaddah ya kamata Adnan ya samu abin wasa koda yaushe yana like da afnan baison matsawa kusa Da ita ko yaya Shaquwace sosai ta shiga tsakaninsu Kwatakwata bata da Wanda tafi sabawa dashi irin adnan Sai kuma babarta hausa da mahaifinta aleeyu A haka adnan tai wayo Saidai nafi na cikin tashin hankali Sbd shajini yace wai jinin afnan yake buqata A wannan karon gaskia saidai komeai zai faru ya faru Dan gaskia bazata iya bada yartava dan tanasonta Damadai ya sake dan ko waye zata iya badawa amman Baddah yar tilon yarta Don haka ta kira qawarta kuma abokiyar batancinta domin su Tattauna Akan lamarin Don haka cikin rudani ta kirata a waya tana shaida mata Abinda ke faruwa tace kyakkyawar yarta kaman afnan bai kamata Ace wai shajini na buqatar jininta ba. Kuma inma hakane Ai tayi qanqanta da yawa dan koda naje masa da zancen Inason na bashi adnan Cemin yaai yayi qanqanta da yawa Sury tai daria tace nafi kenan haryanxu bakisan Shajiniba akwai abinda ya hango shiyasa kikaji yace miki Adnan ya masa qanqanta. Ai hannunka mai sanda yai miki Domin shajini. Indai akace miki jini ne to koda yaushe a buqace yake Sannan da kike Maganar afnan tayi qanqanta Kinganni nan lokacin Dana haifi sadiya ko suna ba,aiba shajini ya buqaci Jininta na nuna rashin amincewata Kuma naqi yarda yai juyin duniyarnan naqi yarda nace saidai ya shanye nawa Jinin ganin haka yace to saidai na zaba zai barmin yar tawa amman duk cikin. Dana sama a duniya nasune kuma basu yarda duk girman da nai na Tsaya da haihuwa ba Shiyasa da zarar na samu ciki wata shiddah nake juwa ya dauke jinjirin Anyi haka yakai sau uku dan duk shekara nake samun ciki Da zaran an tambaya ina cikinki sai nace Bari nai Kema inaganin wannan hanyar kawai Zakibi domin kubutar da yarki. Don shajini bai mising din target Indai Akan jini Ne Nafi tai shiru kamin tace amman kina gani zai amince Sury tace. Eh to kinsan ke sabon shgace saidai karki damu Ina ganin gobe da yammah akwai jama a majalisa Zan taimaka miki wajen nemann wannan alfarman Ba qaramin dadi tajiba tai daria gamida rungume qawar tata Tace. Kemafa qawata kin kawo

Chapter 3 of 16