ta juye ruwan zafin cikin tea flask ta miƙawa Ammar wanda ke tsaye yana ta santi tun kan ya ci ta abin cikin cikin food flask su ka dawo ɗakin ta, nan ya zauna suka soma ci, yana santi ya ce
"Kai da zayyu da sai ki bini mu tafi ABGANISTAN wlh"
Dariya ta yi ta ce
Kai Ammar naje nayi menene a cen.
"Uhm ki yi ta dafa min irin wannan"
Tayi murmushi, ta ce
Uhm Ammar kenan, yanzu akan abinci sai na bika cen da yake ni ce ƴar fari ko.
Dariya ya yi sosai ya ce
"Yes babbar yaya"
Ya haɗa musu tea suna sha suna fira ya tashi ya kunna tv sai suka ji ana nocking, Ammar ne ya miƙe ya buɗe, ganin ƙawar Hamra yasa shi cewa
"Shatu ki shigo mana"
Ta shigo Hamra na ganinta ta sakar mata da murmushin nayi kewar ki, ta ƙaraso ta zauna nan Ammar ya fice bayan sun gaisa. Hamra ta haɗa mata tea tare da zuba mata abinci tana
Ƙawata saukar yaushe haka, shiru babu labarin ki.
"Yau na dawo, na tambayi Nura mai shago ko yaga giftawar zuwa wajen aiki ya ce eh kin fice, shine na ce sai zuwa dare zan shigo, ji na shuru da kika yi wata ce ta sami matsala shiyasa na rasa number ki"
Ayya Shatu so sorry, ya Mama?.
"Tana nan tare muka dawo ai, da bazan zo ba ma da ƙyar aka shawo kaina"
Subhanallah! Me kuma ya faru?.
"Uhm pretty ke dai bari, abubuwa a kullum sake taɓarɓare min suke, wlh da wannan rayuwar ƙuncin da nake ciki gwamma na mutu, i hate this life, menene daɗin duniyar ma.....
Shatu.
Cewar Hamrah, tare da dafa ta ce
In dai akan jinkirin auren ki ke irin waɗannan kalaman to ki sani wannan babu kyau, kina ja ne da jarrawabar da Ubangiji ya yi miki, kuma ba a so bawa sbd yana cikin tsanani ya dinga furta irin wannan kalaman, sannan irin su ke cire mutum cikin musulunci, musulmi an fiso ya yarda da KADDARAR mai kyau ko mara kyau, sannan Ubangiji yana jarraba bawan shi ne sbd ya gwada imanin shi, amma da addu'a, hakuri da juriya sai ki ga ya yaye mana damuwar mu kamar ba a taɓa yi ba, abin da nake so dake shine ki daure ki ci gaba da addu'a Allah zai kawo mafita.
"Hamrah pretty na gode da karfafa min gwiwa, wlh matsalar da nake cikin ta, tafi ƙarfin kai na, abin ya wuce tunanin mai tunani, in taƙaita miki saura ƙiris na sami matsalar brain, sbd tunani da kuma tashin hankali"
Jikin Hamra ya yi matukar sanyi ta gyara zaman ta cikin sanyin murya ta ce
Shatu kina nufin bayan matsalar da na sani kina fama da ita akwai wacce ta fita?.
"Eh hakana nake nufi akwai wacce ta fita amma kuma kusan ita wancan ɗin ta rashin auren ce ta haifar da wannan ɗin, zan faɗa miki komai amma sai ranar da baki da aikin wuni zan shigo na sanar dake"
Sauke numfashi Hamrah tayi cikin sanyin murya ta ce
To shikenan ƙawata gobe ma night duty gareni, babu inda zan je sai kin shigo.
Sun ɗan taɓa fira sannan Shatu ta tafi, Hamrah ta dawo ta rufe ƙofarta, ta haye kan bed ta yi addu'an bacci sannan ta kwanta.
Ina godiya da addu'oin ku, jina da ku kayi kwana biyu banyi Update ba na shiga rubibi ne amma Alhamdulillah yanzu ina free.
Comments and share
[1/10, 19:31] SAYYADA ✍️ Barrister: *MUJARRABI*
By SAYYADA ✍️ Barrister UMMUL UMMU ABIHA
09021706569
PG 11 & 12
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
_WASHEGARI_
_______ Da ƙyar ta iya buɗe idanuwan ta da suka yi mata nawi sbd bacci da kuma gajiya dake tattare da ita, a hankali ta karanta addu'ar farkawa daga bacci, ta yi miƙa ta sauko daga bed ta shige toilet a daidai lokacin ake kiran assalatu ta asubar fari, ta ɗauro alwala ta idar da raka'atainil farjir, raka biyu ta na fila sannan ta idar da ta farillah, ta bima tana addu'oi nta sannan ta yi azkar na safe ta ɗan taɓa karatun Alkur'ani sann ta koma bed ta ci gaba da bacci sbd night duty gareta. Sosai ta sha bacci sai kusan 11:00am ta tashi, ta shige toilet nan ta watsa ruwa ta fito daure da towel ta shafe jikinta da mai da kuma turare sannan ta gyara gashin kanta, ba laifi yau kam har da shafa powder da lipstick ta shirya cikin riga da skart wacce ta sake fito da coca cola shape nata, tayi normal ɗauri sannan ta fito ta wuce ɗakin Ammie, ta tadda tana kwance cikin sanyin murya ta gaida ta, ta amsa tare da ce mata yau bata jin daɗin jikinta, ta taimakawa mai'aikinsu su gyara gidan tare da girki, ta amsa da to Allah ya baki lfy sannan ta fito, ta wuce kitchen ta tadda ta har ta soma aikin nan Hamra ta ce da ita ta bari ita zata girka abinci ta je ta gyara palour, nan ta wuce, Hamrah gwanan son girki ta fara sharyawa musu abinci tam kala biyu zata yi, Daddyn su ya fi cin biski da miyar ganye Mommyn su kuma ta fi cikin cin tuken shinkafa da miyar ganye, sbd girkin na rana ne yasa suke da fa abinci mai nawi ita hamra ba kasafai ta ke ƙaryawa ba shiyasa breakfast bai dame ta ba, ta daura ruwan farar shinkafa sannan ta daura ruwan biski (tsaki) a cikin ruwan ta zuba gishiri da mai ta barshi ya tafaso, sannan ta zuba biskin a hankali har ya haɗe kanshi sannan ta rufe shi, ta komawa ruwan shinkafar ganin ya tafaso yasa ta wanke farar shinkafa ( ɗanya) ta zuba ta rufe ta barshi, ta buɗe fridge ta fito da nama da kayan miya nan ta soma haɗa miyar ganyen ta wacce tasha gyaɗa sannan ta koma ta bude tukunyar shinkafa ta tuƙa shi, ta kashe gas ta dawo wajen biskin ta da yayi warawara sbd mai da ta zuba mashi ta kwashe ta zuba cikin food flask, ganin miyar ta dahu yasa ta juye ta, tare da sauke shinkafar ta mulmulata cikin, leda nan ta kammala.....
"Wow, what a nice delicious!"
Ta juyo ganin Ammar ya sa ta ce
Yauwa zo ka taimaka min ka kaiwa Ammie nata sannan wannan zan kai dining area sbd anjima.
"To na ji kin ce na Ammie da Daddy ina nawa kuma?"
Kashe nan sai ka ɗiba, ai nayi mai wuyan tun da na girka.
"Nasan zayyi daɗi duk ƙamshi ya baje gidan"
To ɗauka dai sojo.
Dariya yayi ya ɗau basket da ta jerawa Ammie duk abin da zata buƙata ya kai mata, ita kuma ta dawo palour ta ajiye, ta koma ta ɗauko nata ta fito dashi, shima Ammar ɗin ya wuce ya ɗauko plate ta zuba mashi tare da ɗauko goran ruwa ya ajiye musu, suna ci suna fira yana santi ya ce
"Kai zan yi missing na girkin ki da na tafi"
Murmushi ta yi ta ce
To ka zauna mana.
"Uhm ai ba zayyu ba, kema rigima ta ki ke nema tafiya babu fashi"
Ah to ashe kana da sense.
Murmushi yayi yana kallonta, ganin ta yi kwalliya ya sa shi cewa
"Unguwa za ki tafi?"
A'a meka gani?.
Naga kinyi kwalliya ne.
To ai sai kace bana kwalliya sai zani unguwa, shikenan na fahimta.
Ya yi murmushi ya ce
"To ai naga baki cika yin shi ba ne shiyasa"
To yau nayi is that okay.
"Uhm Allah baki hakuri"
Wayarta ta yi ringing ganin sunan Ayshe yasa ta ɗauka suka gaisa Ayshe ta ce
"Shuru tun da ki ka baro mu, na so kiranki amma ban samu na kira ki ba, ya mutan gida ina Ya Ammar?"
Uhm uwargida a gidan Alay Bukar, kowa yana lafiya ga nan Ammar ma.
"Umm uwar gidan dole ba an kama an mai dani babba, to na ƙarba ya zan yi, ki baiwa ya Ammar mu gaisa"
Hamrah ta miƙawa Ammar wayar ya karɓa suka gaisa ta ke masa ƙorafin ya ƙi gidan ta yaran ma na tambayar shi, ya sauke numfashi tare da cewa
Ba haka bane Ayshe abubuwan ne sun min yawa, na ji kuna batun uwar gida, ki na nufin Alay Bukar zai ƙara aure?"
"Eh ya Ammar zai ƙara nan da upper Saturday"
"Ok ina gari ma, zan shigo kamin lokacin"
"To Ya Ammar thank you"
Ya miƙawa Hamrah wayar suka ci gaba da firar su, Ayshe ta ce
"Yaya Hamrah ankawo min set na ɗaki fah"
Barakallah na taya ki murna.
"Na gode, jiya aka kawo"
To asufar lafiya.
"Na gode"
Ya su namecy ta?
"Suna nan lafiya, sun tafi skul"
My regards to them.
"Zasu ji"
Sukai sallama.
HAMRA ta sauke numfashi ta kalli Ammar da ya kammala cin abinci shi yana ƙoƙarin tashi ta ce
Har ka kammala sai ina kuma?.
"Eh fah office na Daddy zan je yau akwai waɗanda za suzo su ɗauki kaya"
To ya yi kyau.
Ya fice hamra ta dawo cikin ɗakinta, ta kwanta ɗaya saura amma ta ɗan kwanta zuwa da rabi sai ta tashi. Ta ɗan sami bacci ta farka, ta shige toilet ta ɗauro alwala ta idar da sallah azahar, ta miƙe ta fito ƙarƙashin bishiyar darbejiya ta zauna, sai taji duk gajiyar babu, tana nan zaune ne sai ga Shatu ta shigo, da sallamarta ta ƙaraso ta zauna, daman anan suke wuni su sha firar su sannan ta tafi, ta ce
"Tun ɗazu fa nake ta son na shigo amma kuma aiki ya shige min gaba"
Sai a hankali ƙawata nima sai bacci bai jima ba na farka, kin san akwai gajiya kema haka daga tafiya ki ke sai kin sami hutu na ƴan kwanaki.
"Hakane ƙawata to ni ina naga wani hutu ai hutu ba na irin mu bane"
Murmushi Hamrah ta yi ta ce
Shatu you have to say Alhamdulillah, tun da kina da rai da kuma lafiya kin fi dubi.
"Alhamdulillah ala kulli hali, hakane kam Allah yasa mu dace"
Ameen.
"Na shigo ne akan maganar da na ce zamu yi jiya, ƙawata ina cikin damuwa duk hankalina a tashe"
Sauke numfashi Hamrah ta yi sannan ta ce
Ina jin ki Shatu, Allah ya bamu mafita.
"Ameen ƙawata, to cikin matsalolina wanne da wannene ki ka san su ina yaso na san yadda zan miƙi bayani ki fahimta har ki bani shawara"
Shatu mun jima tare tun muna yara ke mace ce mai juriya da kuma zurfin ciki hakan yasa ba komai ake iya sani naki ba ko a fahimta amma abin da na sani shine, kina fama da matsalar rashin aure da wuri hakan har ya kai ga mijin mahaifiyar ki takure ki, ya kai ga ko ya yi cefanen gida baya so ki taɓa, kai har ya kai ga kwanan gidan ma yana so ya hanaki, wai kina takure shi.
Sauke numfashi Shatu ta yi a hankali hawaye ke zubo mata cikin sanyi murya ta ce
"Ƙawata, duk abin da ki ka faɗa haka ne amma kuma kusan akwai asalin abin da yasa hakan ya ke faruwa, mijin mahaifiya ba mutumin ƙirƙi bane fatsiki ne, kuma so yake ya lala tamin rayuwata ƙin amincewa da hakan ya sa yake takure min ba tare da kowa yasan dalili ba, ake ganin laifina ne sbd ƙin gaishe sa da na keyi kuma bazan taɓa yarda da shi ba a matsayin uba ba har abada ko da hakan zai zame silar rabuwata da mahaifiyata"
Innalillahi wa inna ilaihi rajiun, ya hayyu Ya Qayyum, Shatu me ki ke shirin sanar dani, dan Allah ce min mafarki nake, what Alhaji Yusuf mijin mahaifiyar ki shine ke son lalata miki rayuwa, Shatu Please kada ki ce dani gaskiya ne.
"Uhm kin fi kowa sanin yanda nake son mahaifiyata kuma kin san irin shaƙuwa da kuma soyayyar dake sakanin mu, bayan rasuwar mahaifina kowa ya juya mata baya amma ban dani, sannan kin san irin gwagwarmayar da aka sha kamin ta aure Alhaji Yusuf, to kuwa yakamata ki sani ba zan taɓa yi masa ƙazafi ba, abin da na ke shirin sanar dake gaskiya ne"
Jikin Hamrah ya matukar sanyi, lallai rayuwa ba tabbas kuma duk irin damuwar da ka ke ciki akwai wanda na shi ya fi naka, wai duk irin nata damuwar ga wacce ta dameta....
"Hamrah, bayan Alhaji Yusuf ya auri mahaifiyata ya ci gaba da kulawa damu tamkar ƴaƴan da ya haifa, ya jamu jikin shi, har muke ji kamar ma bamu rasa mahaifin mu ba, barin ma ni wacce duk abin da zayyi sai ya shawarce ni, hatta abinci ni ke girka mashi, hakan nayiwa mahaifiyar ta daɗi sbd ganin na saki raina daga tunanin rashin mahaifina saboda shaƙuwar da mu kayi. Da farko ban fahimci manufar shi ba yana kirana a duk inda ya ke ina zuwa kamawa office nashi zuwa guest House nashi Ina kai mashi saƙo ko abinci sannan ko yana gida ma haka sai ya kira ni ɗakin shi wai na haɗa mashi tea, ban taɓa zato ko sammanin yana ɗauke da FUSKA BIYU ba kuma har ga Allah kallon uba na ke yi mashi. Wata rana da bazan taɓa manta da ita ba wacce tasa na yi da na sanin haiho ni a duniya, wata safiyar Laraba mahaifiyarta ta sanar damu zata tafi cen Cameroon anyi mata rasuwa cikin dare aka sanar da ita, mu kayi ban kwana ta tafi Alhaji Yusuf ne ya yi mata rakiya zuwa Airport, ba dawo ba sai kusan 10:00pm ya dawo ya kirani a waya a lokacin har na fara bacci, na ɗauka ya ce na same shi a side nashi, na taso na fito duk ƙannena ƙananun sun yi bacci ni kaɗaice ban yi ba, shuru gidan nayi nocking ya bani izinin shigowa na shigo sai dai ganin yanayin shigar shi yasa na juya zan fice ya ce
"Shatu ba damuwa ai ki ƙaraso mana, tea zaki haɗa min"
Jikina ya matukar sanyi babu riga a jikin shi gajeren wondo ne da shi, kai na a ƙasa na wuce inda food flask na ruwan zafi ya ke na soma haɗa mashi, na kammala sannan na kawo mashi, kai na har yanzu still a ƙasa ya ke na miƙa mishi, sai da abin da naji ne yasa na ɗago cikin sauri na kalle shi hannuna ya haɗa da cup ɗin ya rike yana jifata da wani mayen kallon da ya sanya zuciya ta harɓawa, jikina ya soma rawa ganin yanda idanuwan shi ya kanza kala yana fidda numfashi na yi saurin ja da baya ina mai mashi kallon me ka ke nufi ne, ya yi saurin riƙe mun hannu ya dawo dani tare da zaunar dani bakin bed ya yi saurin cewa
"Magana zamu yi, meyasa naga kina jan jiki dani yau Shatu ni ne fah Daddyn ki"
Na sauke numfashi har zuwa wannan lokacin na kasa sakin jiki dashi ina waro idanuwa waje cikin tsoro, ina jin shi yana ƙurɓan tea na shi bayan ya kammala ne ya ajiye tare da riƙe mun hannu yana murza su a hankali jikina ya soma rawa ina tunanin anya Daddyn mu ne ko dai wani ne mai kama dashi, na ɗago kaina sbd na tabbatar da cewa shine ko kuma ba shi ɗin bane sai naga shine yana min wani irin kallo, na yi sauri zan miƙe da niyyar na bar ɗakin ya dawo dani tare da janyo ni jikin shi yana shafa ni tare da sauke numfashi cikin sauri² jikina na rawa na hankaɗe shi na miƙe duk ƙafafuwana sun shanye tafiyar ma neman gagarata take nayi bakin kofa ya yi sauri ya biyo ni, na tsaya tare da juyowa na nuna shi da yatsa na ce
"Daddy kada ka iso in da nake, wlh zan yi maka abin da ba zaka tabaɓa mantawa dashi ba, wlh ka bani mamaki i have never imagine you'll do this to me, har a kullum ina yi maka kallon uba ne wanda ya zai tarbiyyar ta damu ya ɗaura mun a kan hanya madaidaiciya shine ka ke so ka rusamin rayuwata.
Ajiyar zuciya ya sauke ya yi magana a hankali yadda kada wani ma ya jisu, ya ce
"Be wise please Shatu, I'm not your real father, it I'll never be, nothing will ever change from that, I'm only the husband of your mom, don't be confused about our new relationship. It's normally happening in our nowdays so this is nothing.......
Wani ihu na yi da ya sanya shi ya yi baya cikin tashin hankali, yana kallona kamar wata sabuwar shafar aljanu, na nuna shi da yatsa sannan na ce
Ka cuce mahaifiyata, sai Allah ya saka mata sbd cin amanar ta da ka ke yi bata sani ba, tana farin cikin samun ka a matsayin miji, a kullum ƙara alfahari ta ke da kai ashe bata sani ba 2 face gare ka, you showed me your true color and don't ever let her knows, you will regret everything.
Ta sowa ya yi ya iso dab da ni babu kunya babu tsoron Allah ya ce
"Do you mean za ki faɗa mata komai"
Ai ya zama dole tasan wa ta ke aure.
Murmushi ya yi ya ce
"Na sani ba zaki iya ba, kuma in kina ganin za ki iya to bismillah"
Na buɗe ƙofar na fito ina kuka na iso ɗakina cikin tashin hankali, na so a ce wannan abin mafarki ne amma kuma duk inda na waiga ganin a zahiri ne ya faru ina ta juyi har gari ya waye, na tashi da ciwon kai, ban fito ba har yara suka tafi skul ina jin yana tambayar su ina na ke su ka ce dashi ciwon kai na ke yi, sai bayan ya fice daga cikin gidan na samu na fito, haka mu kayi wasan ɓoya na tsawon kwanaki uku, a rana ta huɗe ce ina zaune a palour gidan shuru yara duk suna skul naji sallamar shi, ganin ina zaune a palour yasa ya iso ya zauna kusa dani na yi saurin miƙewa ya dawo dani ta hanyar janjoni ya kwantar bisa kujera ina ta kiciniyar kwace kaina abin ya gagara sbd yadda yake da ƙarfi, ya yi magana
"Shatu bana jin daɗin irin gujemin da ki ke yi kin san yanda na ke son ki kuwa amma ki ke wulakanta ni"
Sabar baƙin ciki da takaici ma kasa magana na yi sau hawaye, jin ya ɗaura hannun shi bisa gashin kaina yana shafa ya sa na ce dashi
Allah ya isa sakanina da kai, ka rusa mana farin cikin gidan mu, sai Allah ya saka mana.
"Uhm Shatu kina bani wahala menene a ciki ina kin ja shekaru baki yi aure ba, kuma a kullum cikin son yi ki ke yi to tunda babu mashinshin ki saki jiki dani zan baki kuɗaɗe daga dubu ɗaya zuwa 100 million, zan miki gatan da ba zaki taɓa da kin sanin aikata hakan ba kuma za kiji daɗin rayuwar.....
Ya Allah ga bawan ka nan yana son cutar da ni da kuma mahaifiyata, Allah ya shiga sakanina dashi, Allah ka maida mashi sharrin sa kan shi.
Cikin ƙarfi na hankaɗe shi na tashi a guje na shige ɗaki na kulle, na fashe da kuka kamar raina zai fita, what anya kuwa Daddy ne wannan, to akan ta zai fara ko kuma daman halin shi ne, tun daga wannan lokacin na tsiri zaman ɗaki har Mommy ta dawo, aranar da ta dawo ta fahimci duk na sauya na rame kuma bana son zama a palour, ta ke tambaya ta ganin tana cikin farin ciki yasa na ki faɗa mata na danne ko ganin idonta zai sauya tunani, amma kuma sai ya nemo wata hanyar da yana bukatar abu sai ya kwalla min ƙira ganin bata san komai ba sai na fito ya ce na dafa mashi abu kaza ko na haɗa mashi tea, amman bana sake mashi, rannan ta fita unguwar ina kwance cikin ɗakina ya shigo tare da sakawa ƙofar key, na miƙe cikin tashin hankali zan sauko daga kan katifata ya yi saurin riƙe ni ya danne ni, tare da rufe min baki ina, na kasa magana ma ballantana na ihu, ya jima yana kallona nima shi nake kallo ina jiran naga ta inda zai fara sai kuma naga kawai kallona ya ke, a hankali ya yi magana
"Shatu ba zan daina bibiyar ki ba har sai kin amince da ƙudirina kuma a nan zamu dinga haɗuwa ba a cen guest House nawa zamu dinga haɗuwa, ina son ki....
Ƙarfi ne ya zo min na hankaɗe shi ya faɗi na tashi zan gudu ya janyo ni na faɗi ƙasa har naji ciwo, ganin na ji ciwo yasa ya buɗe ƙofar a lokacin kuma Mommy ta dawo jin ihu na yasa ta iso ɗakin ganin mu biyu bata ce komai ba sai ma tambayar shi da take akan meyasa meni, cikin kwanciyar hankali ya ce da ita wai faɗuwa nayi ya ji ihu na shiyasa ya iso ƙofata, nan tayi ta masifa ta fice na kalleshi cikin ɓacin rai ya sakar min murmushi ya fice. Tun daga wannan ranar na daina gaidashi na fita harkar shi ko ya kirani bana amsawar, abin ya yiwa mahaifiyar ta ciwo har da marina wai ina raina mata miji ta ya zan je bazan gaida shi ba, ai shima ubane gareni dole na yi mishi biyayya kuma ai da amincewar mu ta aure shi to maisa ni zan fara raina shi, na rasa ta inda zan fara faɗa mata shine na fara gaishe sa, to amma kuma na ƙudirin niyyar faɗa mata komai na shigo ɗakinta na tadda ta zaune ina shigowa ta ce
"Kamar kin san neman ki nake, to menene kuma naga fuskar a dame, wai ma meyake damun ki ne duk kin rame?"
Na sauke numfashi cikin sanyin murya na ce
Mommy magana na ke so muyi akan Daddy.
"To naji kamin ki fara na ki maganar bari na faɗi nawa"
Fito min ta yi da key motar ta ce wai ya bata kyautar ta a ranar hankalina ya matukar tashi kenan babu yadda zan faɗa mata kuma ta amince kawai na ce da ita zan tafi cen Cameroon na zauna, nan ko ta tashi hankali tana ta masifa wai tasani sbd mijinta na ke haka, dan haka bazan je ko ina ba kuma na cire miji na yi aure sannan ya zama dole na girmama shi, kuma na bashi hakuri. Cikin sanyin jiki na dawo ɗakina, kawai na barwa Ubangiji komai na saduda, shikenan mijin mahaifiya ta zai ci galaba a kaina. Bayan ya dawo da daddare ne ta tisani gaba wai na bashi hakuri na bashi. Tun daga wannan lokacin na ɗan sauko ganin kamar ya sauya kwasam ranar Mommy ta ce na ɗau abinci shi na kai mashi guest House nashi zayyi baƙi driver ya kaini, bana son ja in ja da ita na shirya na fito a lokacin kuma babu ita da Rahama sun jera manya manyan kuloli cikin Boot na motar na shiga driver ya kai ni guest House na Alhaji Yusuf mijin mahaifiya ta..........
Comments and share
*MUJARRABI*
By SAYYADA ✍️ Barrister UMMUL UMMU ABIHA
09021706569
PG 13 & 14
*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*
_________ Muna isowa ya taimaka min muka sauke kulolin abincin, sun kai kala 7 kuma ko wannensu da irin abincin da ya ke ciki duk kuma babu na ƙi, Mommyna gwana ce ta fannin girki, shiyasa Alhaji Yusuf ba ya shakkar gayyatan baƙi cin abinci guest House nashi, ko kala nawa ne Mommy zata girka mashi. Driver ya kalleni ya ce
"Zan iya tafiya ne ko na jiraki?"
A'a ka tsaya mu koma tare....
"Ah har kun iso to sannunku da ƙoƙari"
Banyi mashi magana ba, na juya zan shige motar ya ce
"Shatu taimaka min mu shigar mana"
Ban ƙi ba na taimaka muka shigar sai dai a lokacin da na fito babu driver na dube na ce
Ina driver kuma ya tafi.
"Oh na aike shi ba zai jima ba zai dawo"
Na sauke numfashi na ɗau rogowar kula na shige dashi ciki, sai dai ina ƙoƙarin fitowa kuma na ji ƙofar a kulle, na yi na yi na buɗe abin ya gagara, sai jin takun shi naji na bayana, na juyo ganin babu kaya a jikin shi yasa na ja da baya na haɗe da jikin ƙofar ina waro idanuwa waje, ya matso kusa dani daga shi sai gajeren wondo ya kai hannunsa zai taɓa ni nayi ƙasa tare da matsawa gefe guda na haɗe jikina waje guda ina addu'ar Allah ya kamin ɗauki, daga inda yake tsaye ya kuramin idanuwan shi da suka sauya kala soka koma red da su ya ce
"Ki amince mana ko da na wannan ranar ce, ni
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 19