mikin dake taso masa na rashin matar nashi, ya ce.
"Why? Me ya sa!, me ya sa, me yasa kika tafi kika barni,Why does death do this to me? Why does it come to cut our love?, whyyyyy" yayi maganar wani irin hawaye na saƙko mishi.
Tamkar wanda aka zabura ya mike a zabure, kalamanta ne suka shiga dawo masa cikin brain nashi.
"Alfarma ɗaya zan nema a gareka Lovie kada ka taɓa zubar min da hawaye yayin daka tuna dani acikin zuciyarka ABU FATEEMERH!, wannan shine babban gatan da zaka min". Sune kalaman ƙarshe daga gareta, itace maganar data zama kalmar ƙarshe ɗaya ji daga gare ta.
Toilet ya faɗa yana sakar ma kansa ruwa, yana fatan abinda yake ji a chunkushe a kirjin sa ya ragu ko da kankani ne, sai dai baya jin akwai wani abu da zai rage masa yadda yake ji ɗin ko da kuwa kaso ɗaya ne cikin ɗari na abinda ya danne dukkan wani tarin farin cikin nashi, wanda yake jin ba zai taɓa dawowa daidai ba. Ganin tamkar kamar ma ƙara tunkuɗo masa abubuwan ake ne ya sanya shi nufar gyms nashi.
Da sauri-sauri yake motsa jikin duk ya hada gumi sosai, be tsaya ba sai da yaji ya gaji sosai sannan ya tsaya,wani irin bazaraten mutum ne buɗaɗɗe da baka gane hakan kai tsaye, idan har baya cikin riga. Cikin zafi-zafin da ke nuna ba'a haiyacinsa yake ba yake sarrafa machine ɗin, idanunsa a rufe ruf ya kwashe tsawon loƙaci yanayi dan sai da yay sharkaf da zufa kafin ya kashe ya koma wajen ɗaga ƙananun ƙarafe, irin na riƙewa a hannun nan ko kana daga zaune zaka ɗaga, Nan ma ya ɗebi loƙaci yana yi kafin ya ajje ya koma ɗaga ainahin ƙarfe daga kwance rigingine. Haka ya ɗin ga ringa motsi jikin tamkar baya a hayyacin sa, Saida ya kwashi wasu lokutai kafin ya kashe komai.
goran ruwa ya ɗauko yana kwankwaɗe a take ya shiga sauƙe ajiyar zuciya mai karfin gaske.
Bethroom nashi ya ƙara koma wa yana sakarma kansa ruwa, haka ya shiga ambaton sunayen Allah duk wanda yazo kan harshen sa. Directly masjid ya nufa, shine bai dawo gidan ba sai wajajen goman dare, samm yaƙi aminta ya haɗu da koda mutam ɗaya ne daga cikin ahalinsa. Cikin Sa'a kuma loƙacin da yake dawowar babu kowa a palon haka ya shige bangaren sa.
LKY SPORT PYJAMAS ya sanya tare da amless irin mara hannun Nan, luntsumeme gadonsa ya haye tare da adda'oin kwanciya barci, idanunsa a lumshe kansa a sama haka komai tiryan-tiryan na rayuwarsa da suka daɗe da zama shuɗaɗɗu suka ci gaba da bijiro masa.
★★★
★ ★★
Cikin tsantsar farin ciki na ƙara riƙe wayar da kyau, bakina tamkar ya yage nace. "Wai don Allah da gaske yaya jay ka kusan zuwa, ka taho min da aunty zeey da julaibeeb, ka taho min da kayan daɗi irin na ƴan ƴan gayun indiyawan Nan don Allah yayaaaaa jayyyy" ko Numfashi ban tsaya shaƙa ba haka na dinga ziba abuna.
Daga cen kuwa murmushin yarintar teemah yake da har yanzun bata ganin ta girma, (kodan ita kaɗai ce mace kuma oho. Ya) ya faɗi maganar yana ɗage kafaɗunsa alamar oho ɗin nan,aunty Zainab dake jin zubar da fatiman take ne ta saki murmushi tare da amsan wayan tana kara ta a kunnenta, kafin tace."ki fara shiri yarinya tunda naga kina ƙaunar India zan taho dake idan mun zo", dariya ta ƙyalkyalce tare da cewa.
"Gaskiya bazan biku ba, idan na biku ummiena kuma ga zauna da waye?, kawai dai ku taho min da kayan daɗi na ƴan gata" baki ɗaya dariya suka fashe su dukansu yana zare wayar tare da kashe abarsa. Domin yasan tsabbb shirmen fatima zasu iya kwana suna wayar ma ita bata ƙiba. Tana jin ya kashe wayar ta nufo palonsu da tsananin zafin ciki don sanar da ummiensu jinin jiki ya kusa zuwa.
Turus taja birki ganin yaya Nurien a harɗe a parlourn yana zaune ƙafa ɗaya kan ɗaya. A take duk annurin dake kan kyakkyawanr fuskarta ya gushe, ko inda yake bata kuma kallo ba ta shige bedroom ɗin ummie, shi kuwa yaya Nurien bai ma san da shigowar ta palon ba don hankalin sa kachokam yana kan laptop nashi da yake video call shiɗa ɗan uwansa jay. Ahankali yake sakin murmushi sai kamarsa da fatima ta bayyana sakk. Ban san mene aka ce masa ba amma har yanzun murmushin na kwance saman kyakkyawar fuskarshi mai kama data Fatima, "kasan mutumiyar ka da rashin ji. Idan akace babu mai taka mata birki to birkicewar nata sai yafi haka, sammm ba'a son raina nake mata wasu abubuwan ba!, kasan ɗazu marinta ta sanya nayi!"
Ya faɗa a marairaice tare da dunkule hannuwansa yana harbin iska alamun shi ma marin ya taɓa ransa.
Cikin dariyar diramar su jay ya shiga ƙyaƙyata dariya yana tafa hannayensa, idonsa har wani ɗan ruwa ruwa suka tara tsabar dariyar.cikin yin dariyar yace, "wllh irinsu Fatima sune maganin masu halin ALIEYO Naaaaaa". Wata kafurar dariya yaya Nurien ya saki shima yana cewa "Ai a fannin mugunta kai BOSS ne babban yaya, yo in banda tsabar mugunta taya kake tunanin masu rawar kai irin su Fatima ka haɗa su da wannan murɗaɗɗen abokin naka, yo ai da sunan sa sorry indai kuwa haka ne babban yaya ".
Yayi maganar yana tuno abokin yayan nasu, da yake Nan tamkar me zuciyar ifiritan farko. Shifa zai iya rantsewa tunda ya mallaki hankalin kansa tare ya sansu da ƴaƴansu, amma zai iya rantsewa bai taɓa ganin koda farin haƙorinsa bane, tamkar wanne aka ma wahayi da shiga wuta. Yo shiga wuta mana mutum kullum ba fara'a.
Kallon sa kawai yaya jay ya tsaya yi, "ka gama dariyar naka ko akwai wata?" Yayi maganar da alamar tambaya. Shi kuwa dariyarsa yaci gaba dayi domin har ya hasko haukar da za'a buga, "Dan ƙari" ya faɗa yana sake sakin wata dariyar.
"Wllh zan kashe tunda hauka zaka min dan ubanka" yaya jay ya faɗa a fusace domin shima wani murɗaɗɗen ne ai, idan yaso ayi wasa da dariya idan kuwa bai soba yanxune yaci uban mutum.
Kimtse dariyar yayi (amma fa wllh zanso ganin wannan games ɗin) ya yi maganar a cikin zuciyarsa. wllh ya tabbata rana ɗaya sai ya kusan kashe ta da duka, don Fatima ba ƙaramar ƴar takife bace, ta wajen shegen tsokanar masifa da shiga shiri ba shanu, kata samm samm bata da yafiya ko kaɗan.
Haka dai suka ci gaba da firansu sama² domin shi gaba ɗaya ya tafiya duniyar tunanin zancen yayan nasu. (Wato yaya Jabeer ba ƙaramin mugu bane yaseen) ya yi maganar azuciyarsa. Ganin bakinsa kamar yana motsi ne ya sanya shi faɗin, "kace mene akie?"
"Ban ce komi ba babban yaya" katse video call ɗin kawai jay yayi daga cenñnn ganin baki ɗaya kamar hankalin ɗan uwan nasa baya jikinsa. Ware ido Nurien yayi ganin sha biyu saura.
"Ashe mun ɓata loƙaci haka ban sani ba" ya faɗa yana tashi tare da nufar bangaren sa.
★Washe gari★
Da farin ciki ta tashi ba kaɗan ba tayi missing na yayan nasu, kasancewar juma'a ne kuma ta fita daga makarantar Sakandire ya sanya ta fara gyaran gidan, bayan ta kammala gyara ko ina ta shiga kitchen ta haɗa musu dinner cikin abinda bai gaza 50 mini ba ta kammala komai.
Kasan cewar soyayyan dankelen turawa ta soya musu da ƙwai, sai lemon kwakwa data haɗa musu.
*******
******"Jay pls ka dawo gida haka nan mana, koba komi kazo kayi azumi a gida kusa da ummie" tamkar wanda aka sanya irin dolen nan ko aka matsa mishi yayi maganar.
"Hhhhh tunda yau ga wanda baida ra'ayin kansa ba, to duk na gano wayonka malam. Ka fito fili kawai kace kana son in dawo kayi missing kunun gyaɗar queen teemah 🥰 muna fhiki kawai" ya faɗa yana sakin dariya wanda ya tunzura aliey ya datse kiran baki ɗaya tamkar ba shine yayi ƙiran ba (da gaske ya rantoni fa) ya faɗi maganar acikin zuciyarsa.
Amnah dake jikinsa a kwance ne taɗan zame tare da ɗago kanta tace "laaa papiey uncle jay ɗin kane kayi waya dashi, amma shine koka sanmin shi!" Ɗan ɓata fuska yayi tare da kawar da kansa gefe yana yamutse kyakkyawanr fuskarsa tare da ce mata. "Mun ɓata ne ai yanzun, sai gobe damu shirya"
"To akan mene kuka ɓata papiey?"
"Sunanta daya ambata min"
"Sunan waye?"
"Shiiiiiiiiiiiiiii " ya ɗora hannunsa saman bakinta domin harya gaji da surutun da Amnah ta sanya shi, gashi shi ɗin ba ma'abocin zance bane.
Badon taso ba haka ta haƙura ta ƙyale papieyn nata don tasan ba ƙaramin aikin sa bane ya yace ta tafi wurin ammiey, anan wurinsa tayi barci kwantar da ita yayi akan gadonsa toilet ya shi Yaɗan watso ruwa tare da ɗaure alwula,wanda hakan al'adarsa ne baya kwanciya ba tare da ɗaura alwula ba. Hasken ɗakin ya kashe yana kunna Electric kindle a take ɗan haske kaɗan ya bayyana.
****
Itafa tunda taji masoyinta farin cikin ta mai ƙaunarta yayanta jay zai dawo ta kasa zaune ta kasa tsaye, Allah Allah kawai take ya zo domin ba ƙaramin missing nashi tayi ba. saidai duk yadda takai ga nacinta yaƙi bata mata ranar da zai zo.
Dan dole haka ta haƙura ta zauna zaman zuba idon zuwansa ko yaushe.
Duk da ba wani shiri take da yaya Nurien ba, amma Saida ta tambaye shi ko yasan ranar da yayan nasu zai dawo.
A firgice ya tashi sakamakon wani irin mummunan famarki da yayi, Rumtse Idanunsa yayi qamm tare da qara qanqame jikinsa wuri guda,a ƙalla yaɗau minti biyu zuwa uku kafin ta yaki ajiyar zuciya.amma ba baiyi motsin kirkiba balle kuma ya iya furta wata magana.
Sosai mafarkin ya firgita shi, in banda tsuma babu abinda jikinsa ke faman yi sai uban zufar dake yanko masa.
kai tsaye bathroom nashi ya shige jin zuciyarsa na masa wani irin luguɗen masifa.
Shower kawai ya sakarma kansa yana daya kunna na dukan jikin sa yana fatar samun sassauci daga abinda yake ji acikin zuciyarsa.
Yanayin yanda ruwan ke dukan jiki da kuma kansa kaɗai, ya Isa bayyana maka cewar lallai ba'a cikin tunani da kuma hayyacinsa yake ba. Domin duk yanda yaso da yayi zeroying mind nashi abun yaci tura. Ahankali yakai hannunsa ya kashe showern, tare ɗaukar wata kakkaurar bathrobe ɗin dake gefensa ya sanya a jikinsa.
Hannunsa ya ɗaura akan handle ɗin qofar, ya buɗe yayin da yake jin qirjinsa na amsawa aduk wani taku da zai yi.
idanunsa da suke a lumshe ya ware tare da ƙurama wuri ɗaya ido tamkar Anan ne za'a faɗa masa fassarar mafarkin da yai.
Ahankali ya riƙe kansa da Hannuwansa biyu da yake jin tabbas yana gaf da samun matsala, indai har zaici gaba da shiga irin wannan attack ɗin. kwanciya yayi daga jikin sopa domin yana ganin, tamkar daya koma ɗin mafarkin da yai zai kuma maimatuwa ne. "Ya Ilahi" ya faɗa yana ci gaba da tasbihi acikin ransa.
Ƙarar shigowar message cikin woyar sane ya sanya shi fuɗe idonsa, da suka gama galabaituwa sosae, Ahankali ya janyo wayar tare da shafa screen nata. Yake p
Kyakkyawa Pics ɗin Safiyya ya bayyana ganin sunan jay ne ya sanya shi buɗe saƙon ya karanta saƙon.
Duk da yanayin da yake ciki hakan bai hana ya ɗan yi murmushin gefen baki ba, (Tijara kawai, malam da sanya mutum aiki)
Shi kaɗai ya ƙaraci mitar shi kafin ya kife jikin kujerar wani irin barci yazo yayi awon gaba dashi. Washe gari haka ya tashi daɗan sassauci yau kamm ko ina ha gaza fita haka yayi wunin gida sai Bayan sallar isha'i,ya ɗauki ɗaya daga cikin fitattun motocin ƙirar Lexus Rx baƙa wuliƙ. Wanda mutun ganin farko zai yi mata yasan ehhhhhhhhh lallei nera ba ƙaramin kuka tayi ba, wajen siyar wannan rantsatstsiyar mota.
Suna zaune kamar kullum a farfajiyar gidan ita da masoyinta rayuwarta Aliyu shureim nurul qalb ɗin ta. Sassanyan murmushin farin ciki dake saki domin daddaɗan zancen da yazo mata dashi, na cewar Nan da ƴan watan Ni ƙalilan zata zama mallakin sa, Uwar ƴaƴan sa Insha Allah.
Hannuwanta cikin nashi yaci gaba da dubanta yana jin tamakar ya buɗe zuciyarsa ya zire ta kawai a ciki, domin ya huta da azabtar dashi da soyayyarta take matuƙar yi. Dai-dai wannan loƙacin rantsatstsiyar mota baka wuliƙ ta sanyo kanta cikin haraban gidan. dummmm haka kawai zuciyarta taji tayi wani irin bala'in bugawa da ƙarfin masifa.
Baki ɗaya ita shi motar suka zubama ido ganin irin wannan motar har cikin gidansu, cikin tsananin farin ciki zeey ta fara yowa waje. Wani irin ware ido Fatima tayi ganin aunty zeey ɗinta. Ai da wani irin bala'in gudu ta nufeta wata iriyar kyakkyawar runguma ta mata, tare da buga tsalle ta sake ta Tana nufar gaban motar. Babu tunanin komai a ranta ta ta buɗe gaban motar Ba tare data san waye a mazaunin driver ba ta wani faɗa jikinsa.
Tare da ƙanƙame sa tana sakin dariyar farin ciki tare da cewa.
"I miss you fiye da billions dollers my JININ JIKI ♥️🤍♥️"
Wani irin ɗaukewa numfashinsa yayi ganin mace kwance ɗare-ɗare acikin jikinsa. Cikin wani irin masifar ɓacin rai da zallar takaicinta ya buga mata wata razananniyar uwar tsawar data sanya ta buɗe Idanunt, tare da toshe kunnawanta da duka hannayen ta. Tarrr idanunta masu kama dana mage suka faɗa cikin na mutumin da bata taɓa ganin irinsa akaf cikin duniya. Da wani irin bala'in ƙarfi tayi ƙoƙarin janye jikinta.
Wani irin riƙi tsintsiyar hannunta yayi tare da dawo ita dab dashi har hucin Numfashinsa na bugar nata, babu zata babu tsammani taji sauƙar wani irin lafiyayyan mari a saman fuskarta.
Tare da tunkoɗa waje da wani irin azababben ɓacin rai ya figi motarsa ya fice daga harabar gidan baki ɗaya. Su kuwa yaya jay zeey tana fita shima ya fito yana fita ita kuma Fatima iyayen hankali ta banka kanta cikin motar da tajaza ma kanta shan mari a karon farko.
Duk cikin su babu wanda yasan abinda ya faru, kawai dai sunji ƙarar saukar mari ne, cikin sauri jay ya juyo gareta yana tallafarta ganin sai tangal tangal take tana Neman faɗuwa. Tana jin ta jikin mutum ya wani irin fashe da kukan azabar raɗaɗin marin data sha daga ALIEYO. "Allah ya isana, Allah yasaka min!, Allah bazai taɓa barin ka haka ba saiya biya min haƙƙin na, shege tsinan.........
Tsittttt ta gimtse bakinta jin wani irin bugu da akamawa bakin nata......
FAN'S CLUB ƘAUNA BIYU
Nake cewa sai kuma Allah Ubangijii ya kaimu bayan sallah da aran rai da kuma lafiya, zamuci gaba daga inda muka tsaya.
INSHA ALLAH
*AMMEY LAYLERHNKU* mai ƙaunarku mai ƙaunar farin cikin ku take ce muku bye bye bye bye saimun haɗe Insha Allah.
Duk wanda yaji daɗin littafin yama mahaifina adda'a Ubangijii ya jaddada rahamarsa a gareka mahaifin da bana da kamar ka. Adda'oi Na ba zasu taɓa dena zuwa gareka, har nima sai randa Ubangijii na ya amshi tawa rayuwar.
Bissalam 🙏🙏🙏🙏🙏
Allah Ubangijin talikai ya sadamu daduk wani Alkhairinsa dake cikin wannan wata na RAMADAN
*~ALLAHUMMAH BALLIGNA RAMADAN KAREEM 🤲🤲👋~*
08104493215
*💘🌺ƘAUNA BIYU 🌺💘*
~Heart touching love, with love a side 🤍🤍~
Page 11&12
*BY*
*AMMEY LAYLERH*
✯ *~🌠 OFFICIAL MIRRAH 💫~*
*Alhamdulillah forever and always 👏*
_________________________
♥️🤍♥️
Ɗago kanta tayi don ganin waye ɗalle mata baki, idonta ta sauƙe akan yaya jay kansa ya jinjina mata alamar ehh shine mai bugun. Da sauri Aliyu shureim ya ƙara so wurin yana kama hannuwanta cikin nashi, fuskarta ya ɗago da niyar share mata hawayen dake kwance saman fuskarta, da wani irin sauri yaja baya ganin shatin kwanciyar yatsun hannu kwance a saman fuskarta. Ganin yadda ya yine ya sanya yaya jay dubansu su duka.
"What happens" ya tambaya yana mastowa gare su, cikin firgici Aliyu ya shiga nuna masa fuskar Queen kafin cikin in'ina ya shiga faɗin. "Waye shi?, akan wane dalili zai maran min fuskarn matata?, dubi yadda ya kumbura mata fuska, dubi yaya jay!" Yayi maganar yana juya masa fuskar Queen. Shima sosae zanen yatsun hannun alieyon daya gani kwance saman fuskar fatiman ya taɓa shi. Sai dai Samm bai bari hakan ya bayyana a zahirance ba, yasan kaɗan kenan daga cikin aikin alieyonsa da aka ci ma Sa'a bai tattaka taba, domin zai iya rantse wa yafi kowa sanin halayen Alie karan kataf.
Kama hannuwanta yayi zuwa ciki Aliyu ne yabi bayansu da jakankunan kayansu, zuciyarsa na masa wani irin zafi. Sosae yaji yana jin haushin wannan abokin yaya jay ɗin, duk da kuwa bai ga koda mai kama da fuskarsa bane. Amma yaci alwashin duk randa suka haɗu saiya rama mata marin fuskar Queen ɗin shi da yayi wannan alkawarin sane.
Ita kuwa dama tuni aunty zeey ta shige ciki domin kukan da julaibeeb ke mata, dole tayi cikin gidan ta barsu tsaitsaye a wurin. Suna dab da shiga main Parlour yaya Nurien da bai san da xuwan yayan nasu bane, Saida aunty zeey ta shiga aikuwa da gudu ya fito cikin tsananin murnarn zuwan ɗan uwan nasa, hannun teemah ya saki yana buɗewa ƙanin nasa hannayensa, rungume juna sukayi cikin tsananin murna da farin ciki. Kai tsaye teemah kan ummie tayi tana faɗawa jikinta tare da sakin wani sabon kukan. "Auta miye hakan?, me saya samm baƙya sanin kin girma ne?" Ummien tayi maganar tana janyeta daga jikin ta, da sauri kuma ta dawo da ita ganin zanen yatsu kwance saman fuskarta, "me ya same ki haka?, waye ya miki irin wannan marin?" Cike da kaɗuwa ummien take tambayar ta.
Kukanta taci gaba dayi, yaya Nurien ne ya matso kusa da ummien yana tambayar abinda ya faru shima, ganin yadda fuskar Shalelen nasu yayi wani irin jaaa da kumburi.
"Nima ban san shi ba!, don kawai na faɗa jikinsa nasha yaya jay shine ya buga min marin, ya hankaɗoni waje". A tare ummie da yaya Nurien suka dubi yaya jay, shi Nurien irin kallon da yake duban shi daban sakamakon ummie da take buƙatar ƙarin bayani. Sumar kansa ya ɗan shafa kaɗan.
"Rashin hankali ta masa shine ya buge ta"
"Wai waye ka faɗamin mana kake min wata kwana-kwana"
Ɗan risinar da kansa yayi tare da faɗin.
"Ummie ALIEYO Naaaaaa ne"
Ajiyar zuciya mai ɗan qarfi ummie taja tana komawa zaune, don ko kaɗan bata kawo shi ɗin bane "Yana ina?" Kai tsaye ta tambayi jay ɗin.
"Ya fice a zuciye"
"Kuma shine ka bar shi ya tafi dan kaima baka da hankali!, bayan kafi kowa sanin halin sa, amma ka barshi ya fita a irin wannan yanayin" tayi maganar tana duban yaya jay.
"Afwan ummienmu, wllh kafin ma musan abinda ya faru harya bar gidan babu damar na bishi kuma"
"Shikenan Allah ya kiyaye "shine kawai abinda ta iya faɗi tana Adda'ar Allah ya ya tsare shi acikin zuciyarta. Domin bata manta irin halin daya shiga ba a loƙacin mutuwar matarsa.
Kasancewar ita da ammiensa aminai ne sosae ta dalilin abokantar dake tsakanin ƴaƴansu mai girman gaske. Yaya Nurien ne ya dubi queen tare da sakin dariya tuno da zancen yayansu na ranar, sai gashi tun ba'a je ko ina ba haɗuwarsu na farko ya kasance duka ne, ido kawai yaya jay ya zuba masa suna haɗa ido ya kuma sakin dariya yana barin parlourn a guje ganin irin kallon da yaya jay yake mishi.
Aliyu da tun ɗazu yake zaune kansa a ɗage ne ya ɗago kansa tare da duban yaya jay.
"Yaya amma dai ba za'a barshi haka ba dole a ɗau mataki,Wllh bai daki banza ba dole nabi mata haƙƙinta" ummie ta dube shi a tsanake tace "kayi haƙuri Aliyu duk bazai kaimu ga haka ba, shiɗin babban abokin yayan kune, kuma daɗi da ƙari kasan mutuniyarka ba hankali ke gare ta".
Ajiyar zuciya kawai ya saki yana ficewa a parlourn.
A tsanake yaya jay ya shiga gaisawa da ummien nashi, cikin fara'a dajin daɗi ummine ta amsa shi tana faɗin, "ai nasha wannan karon ma bazaka zo mana azumin ba kamar wancen karon"
Da murmushi a saman fuskarsa yake faɗin...."ba dole na dawo ba tunda wannan uban ƴan miskilancin yayi missing kunun gyaɗar queen, kinsan a duniya babu abinda yake burgeshi a fannin abinci sama da kunun markaɗaɗɗiyar gyaɗa" ƴar dariya kawai ummie tayi tana faɗin. "Shi kuma gashi da ƙin kai, kace badan mu kazo Bama mu daina murnarn zuwan ka"
"A ahhhh na tuba ummiena nace Allah,wllh dama nayi zuwan shi kuma ya isheni da ƙarafin na dawo, kuma nasan duk akan kunun nan ne"
Dariya ummie taci gaba dayi domin lallei alieyo halinsa sai shi. "Kuma wai kin san wani abu ummie"
"A ahh saika faɗa babana" ummien ta faɗa tana ƙara dubansa.
"Wllh taka nas ya sanya ammienmu gaba Saida yasa ta markaɗa masa gyaɗar, amma data dama mishi ɗan iska sai yaƙi sha wai babu daɗi kamar na gidan nan".
Sosae suke cin dariyarsu su biyu ita kuwa teemah tana jinsu duk haushin su ya ishe ta, ganin babu wanda ya kuma bi ta kanta duk cikin su. Kwafa taja a ranta tace (aikuwa zaici ubansa wllh bazai ƙara sha mana kunu ba, kuma ai dama nice mai so!, kuma nice mai damawar to Nima na daina son kunun daga yau). Duk acikin zuciyarta take wannan maganganun, kafin ta tashi tabar musu parlourn tana nufar ɓangaren aunty zeey.
♥️🤍♥️
Cikin matsanancin ɓacin rai yake sheƙe uban gudu tamkar ya tashi sama, gaba ɗaya zuciyarsa wani irin hautsinin bala'i take masa, wani irin raɗaɗi yakeji acen ƙasar zuciyarsa.
Kasancewar sa mutan mai tsananin zuciyar bala'i da ɗaukar abu da zafine ya sanya a take tsananin tashin hankali ya sashi tsats-tsafo da zufa, sabida yadda zuciyarsa ke bugawa da Masifaffen ƙarfi yayin da numfashinsa ke fusga tamkar zai bar ganganar jikinsa, cikin tsanananin tashin hankali da wani irin masifaffen juyi da kansa keyi ya ƙara matse kansa da hannu bibbiyu, da ƙyar ya iya taka birki daga gefen shimfiɗeɗen titin.
Wani irin tsanar yarinyar yake ji yana
ratsa ilahirin gangar jikinsa da kuma zuciyarsa baki ɗaya, idanunsa sun juye sun kaɗa sunyi Jawur, kab ilahirin jikinsa rawa yake kar-kar-kar tamkar mazari haka jikinsa ya shiga kakkarwar cikin wani irin sauri zuciyarsa ke bugawa da kaso Cassa'in da tara cikin ɗari, tana mai wanzar da tsantsarn tsanar yarinyar. Samm shi mutum ne daya tsani rashin kamun kai, in banda rashin kamun kai taya zata masa uban wannan rungumar, duk da kuwa cewar yayantane jinin tane amma aibe kamata ta masa uban iriyar wannan rungumar ba.
A take zuciyarsa tayi masa wani irin nauyi, kafin yaji duk wata kafa ta jikinsa na sagewa, da ƙarfin masifa yaja motar ko ganin gabansa baya yi, ikon Allah ne kawai ya kaishi gida lafiya, wani irin mahaukacin hong daya danna kuwa kai kace baya a hayyacin sa ne. Su kansu soldier's ɗin dake tsaron get ɗin Saida suka tsorata da irin hong ɗin ɗaya ringa bugawa.
Cikin azama da rawar jiki suka buɗe get ɗin, yana qara cilla kansa asalin get ɗin gidan. A tsakiyar
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 4 Chapter of 23