yana juyi tare da rausayawa tamkar wata mace, Domin MD parouk irin mutanen nan ne masu raha. Aku ma daidai Nan tawagar katafarin abokanan jalaal Areef ɗin suka qariso na gida 9j da sauran qasashen ketare, nan suka shiga gaggaisawa tare da taya abokin nasu murnar samun cikon muradin sa da kuma burinsa da sukaji ta hanyar babban amininsa MD parouk. Saurin zazzaro IDANUWANSA sukayi baki ɗaya har Angon loqacin da idanunsu suka sarqe a cikin na *GENERAL MALEEK TOUFIQ* ango ga AYUSHA ABDULPHATA OMAR jadderh {littafin KAREN BANA} na AMMEY LAYLERH.
Ya zaune daga cikin motarsa ya hakimce cikin kakinsa na sojojin da suka gama haɗewa tare da amsar jikinsa, gaba ɗaya motar kewaye take da sojojinsa masu bashi tsaro, cikin sassarfa jalaal ya qariso tare da faɗawa jikin maleek toufiq ɗin, yana faɗin.
"MISKILI KAFI MAHAUKACI BAN HAUSHI, dama zaka zo baka faɗa min ba, wato surprised nawa kayi kenan? Sai kuma ya ɗago daga jikin sa yana ta sakin murmushi shi shikaɗai, domin yafi kowa sanin waye GENERAL MALEEK TOUFIQ ɗin, shi Maleek dake hakimce cikin motarsa hannu ya miqa wa JALAAL AREEF ɗin tare da faɗin,
"Congret na tayaka murnar samun RAYUWAR ka gaba ɗaya"
Shima jalaal murmushin ya saki tare da faɗin, "a to nikam ban tsaya miskilancin tsiya tamkar kai da aka aura maka, taka cikin muradin kuma Rainon ka AYUSHHH ɗinka cikin sauƙi ba, Ni bani da wannan cikakken gatan a yanxun!"
Ya qarishe maganar cikin raunin murya, sai kuma yace,
"Kaji daɗin MALEEK ni kuwa fa idan da ace na tsaya waye zai AURA min ita!? Mahaifina baya doron duniyar!, shi yasa na fito da qarfina cike kuma da yaqinin samun nasarar mallakar mahaɗin RAYUWATA kuma Raino na!, gashi kuma Allah Ubangijin talikai Mani man bayinsa ya mallaka min ita a matsayin MATAR AURENA, alhamdulillahi ala kulli halin Allah shine abin godiya"
Sharrrrr kuma hawaye suka shiga sauqo masa cike da tsananin tausayin aminin nashi MALEEK TOUFIQ ɗin ya shiga ɗan bubbuga gefen kafaɗarsa yana faɗin. "DUDE mene kake yi hakan NEEEEE, koka manta nifa da zafin nawa na dawo Domin mallakar mahaɗin nawa, amma kuma sai wata shiryayyar qaddara tazo ta gitta wa hakan, pls kayi haƙuri komi ya wuce DUDE"
Gaba ɗaya kuma sauran abokanan Angon sai jikinsu yayi sanyi.
Nan dai suka rankaya suka koma babban hotel ɗin da suka kama baki ɗayansu, don gudanar da liyafar taya ɗan uwansu Jalaal Areef muryan mallar mahaɗin rayuwarsa, wanda MALEEK TOUFIQ ne da kansa ya shirya masa wannan qwarya qwaryar liyafar, ganin irin zallar farin cikin dake shimfiɗe saman kyakkyawar fuskarshi ne yasa
suka shiga tsige jalaal ɗin tsafff, shi kuwa in banda murmushi babu abinda yake famanyi, domin shikam ayanxun bashi da bakin magana ma, tasbihi kawai yake ga subhanahu wata'ala Ubangijiin Al'arshi mai kowa mai komai.
Nan sauran jama'a suka dinga zuwa ana gaisawa tare da yi masu fatan Alkhairi, don a ɗaurin AUREN sa na farko bai gayyaci kowa ba, hakan nema masa ba kowane yasan yayi AUREN fari ba, cikin masu mashi barka kuwa da ala sanya alkhairi har da mahaifin fadeelah wato Alhaji JABBER SHETTIMA, cike da girmamawa yake wa mijin ƴar tasa fatan Alkhairi.
Aikuwa jalaal yaji daɗin ganinsa ganin shima harda nashi ƴar tawagar ya haɗo.
Idan muka koma ceeeênnn cikin gida kuwa, Inna ladiyo ce tsaye a gaban ɗakin umman Layla tana raira waqarta, wacce ta kasance tamkar habaicine takewa umman Layla dama laylan kanta.
"Aure yayi riba ahayye coriyalle, AUREN marar asali, ahayye coriyalle, auren rashin gata, corigiyalle, auren marar ƴanci corigiyalle"
Inna ladiyo ce mai wannan Waqar, kuma saida ta dubi qofar ɗakin umma, umman kuwa sarai tasan da ita take, amma ta nuna tamkar batajin komi da take faɗa ɗin.
Kafin kuma hajja ta cafe ta faɗin, "wllh kuma auren cushe auren daqar nasha, auren SADAKA tunda babu abinda gidan mazan suka taɓa kawowa, yo ko danjin MIJIN ma bamu taɓa gani ba wama ya sani ko SHEGEEE neeee waya sani ma ko har an ɗaurooo"
"Jika na ba SHEGEEE baneeee!, shi kuwa yake da kyakkyawan tsatso mai kyau, Kana na asali na gaban kwatance, ɗaga marigayi AREEFULLAHU MUHD MAI NASARA, nasan bazaku gaza sanin shiba tsohon shugaban qasarku ba kana mariga a yanxun!"
Sukaji wata murya mai cike da karaɗi ta karaɗe gidan nasu, a razane Inna ladiyo hajja suka jiyo dan ganin mai maganar.
Da wata kyakkyawar dattijuya sukaci karo, gefe guda kuma wasu haɗaɗɗun manyan matane tsaitsaye daga gefenta.
Alhaji Yusuf mai kaba da tun farkon shigowar waɗannan mutanen daya gama ganin ana sauqesu daga cikin wasu irin manya manyan kuma haɗaɗɗun motocine yayi saurin cafe zancen matar dayaji ta qira kanta da kakar yaron da aka ɗaurawa aure da ƴarsa.
"La shakka kuwa domin ninen kattt tunda Ni!!! Aka ɗamkawa sadakin ƴata a hannuna Naira dubu ɗari biyar da mukullin mota, kuma naji na gani na shaida hakan!"
Daga bayan Alh Yusuf kuwa suma mutanen dasu inna ladiyo suka turane suka ce, "kwarai kuwa domin idan har basu yarda dakai ba mu zasu yarda mu, tunda muɗin ƴan aikensu neeee kuma wakilan da suka suka tara domin ganin Yadda ɗaurin auren ƴar SADAKA zai kaya, amma fa acewar su"
Cewar wani matashin da ganinsa ba mutunci zaiyi ba.
Wasu manya manyan haɗaɗɗu kuma ƙayatattu akwatune aka shiga, shigowa dasu tsaƙiyar tsakar gidan ana direwa, inda wasu kattan samari suka dinga shigowa dasu suna kuma jerewa a tsakar gidan.
Idan da abinda yafi mutuwa ɗaci da zafi,to kuwa shine ganin wannan abu da su Inna ladiyo suke yi tamkar almara, tamkar shirin Film, tamkar a rubutun littafi.
Domin kyakkyawan motsi ma sun gaza.
Wasu daga cikin ƴan uwan ummane sukayi buzut suka firfito tsakar gidan, Domin dama duk irin tujarar dasu inna ladiyon keyi suna jinsu, masu zafin zuciyar cikinsu ne sukayi azabut zasu fito umman ta hanesu, da farko sunƙi jin maganar ta saida suka ga umman tana hawaye kana suka haƙura suka qyale su Inna ladiyon da hajjan badan sunso ba.
Manyan taburbin amarya da umman ta gama siyen kayanta tsaffff suka firfito dasu suna makalewa a tsaƙiyar GIDAN.
Adda fatsima ce ta tashi, ta tashi ta rangaɗa wata uwar guɗa tare da soma zubar da ruwan maganganun da duk taga dama itama.
Su kuwa hajja mama zama suka yiyyi akan tabirmin da aka shimfiɗa musu, kafin itama hajja maman ta tashi, ta rangaɗa Tata guɗar domin ta fuskanci abinda yasa jikan nata ya buƙaci da abar duk wata shidima sai bayan ɗauren Aure, Nan take ta gane nufin sa.
Kafin kace mene tuni har cika musu gabansu da fura da nono da kuma lafiyayyar Masar da suka ɗana domin gudanar da shagalin bikin, sai gashi hakan ya musu Rana gefe guda kuma ga katon katon na lemuka, da ruwan roba, bayan wasu daga cikin makwabta sun shishshigo ne aka shiga ganin kaya.
La ila ha illallahu, akwatina ne set huɗu ko wanne da colour nashi daban, akwai pitch color,akwai ruwan zuma, kana akwai red color sai waɗanda sukafi duk sauran set ɗin haɗuwa, wasu fitattun kuma ƙayattun fararen set ne na gani na faɗa na numa Sa'a, aikuwa zokaga didima kafin kace me gidan harya cika ya tinbatse, dan kowannesu yawa idanunsa damu.
Sai wajajen yamma suka ɗan sami saukin mutane, yayin dasu hajja mama suke uwar ɗakan umma bayan an wadata gabansu da kayan abinci da kuma gashin zaɓin da umma tayi sauri ta bada kuɗaɗe aka siyo musu, adda fatsima taje nan makwabta tayo musu gashi na musamman wanda suke fitar da wani irin daddaɗan ƙamshi, hajja mama dake masifar son gashin zabbice ta ciro wata dakular cinya taka bakinta, tare da nitsa musu hakwaranta Ahankali ta lumshe idanunta tare da gyara zamanta, sai kuma ta dubi jama'ar ɗakin tana faɗin.
"Kai Allah ya wa iyayen wannan YARINYA albarka, domin badai karamciba nifa kallo ɗaya nawa mahaifiyar amaryar nan naji ta kwanta min, domin da ganinta badai mutunci da iya karrama bako ba"
Lalla hafsa wacce ta kasance ƙanwa ka hajja mama ce, ta dube ta da ƙyau tare da faɗin.
"Kai aike kamm dama hajja mama idan kinsamu Gashin zabbi baki da dama"
Ta yi maganar murmushi kwance a saman fuskarta,domin ita ma kanta ta yaba da irin karamci da girmama baƙo irin na waɗan nan bayin Allah.
Haka dai suka ringa sati sun, wani abinma saidai hajja mama ta taci haɗaɗɗiyar Masar garin mu BAUCHIN Yakubu ikon Allah, wacce tayi irin har suyar nan miyar kuwa tasha uban dandakwashin naman rago, waiyo kuzo kuga santi wurin hajja mama.
Su Umma da suke parlourn a Zazzau ne sunajin duk irin yabon da suka ringa musu, kwarai suma sunji daɗin hakan da gaske, kafin kuma motocin da suka kawo su hajja mama suzo ɗaukarsu, nan dangin umma sunka haɗa musu tsarabe ² irin namu na karamci.
Nan aka koma dasu ƙaton gidan jalaal ɗin dake garin na Bauchi, wanda suna Nan harsai angama bikin zasu tafi da amaryar bisa umarnin hajja mama, itama cenñnn ummien jalaal tana tare da wasu mutanen tana nata taron.
Tunda su umma sukaji su hajja mama suna garin nasu kullum sai an kai musu kayan karin safe, da kuma na Rana dana dare, lafiyayyun abinci ake kai musu mai rai da lafiya, itadai Hajja mama tace kullum tana son wannan Masar tasu mai masifar daɗin Nan, aikuwa ummance ma da kanta take yi mata,
Haka su Umma suka shiga gudanar da bikinsu cikin kwanciyar hankali.
Wai ina labarin amaryar mune?.
Tun wannan loqacin tana nan a makwabtansu gidansu qawarta Rahama, tana kwance babu lafiya tunda taji an ɗaura mata aure, gaba ɗaya jikin ta yayi sanyi sai takejin tamkar ma ace anfasa AUREN nata ne kawai, ko ranta yayi sanyi.
Amma gefe guda kuma tana maqale da son sanin ainihin wanene shi, shin wayeeeee wannan CEO ɗin na Companyn su, wanda yake mata kama da wanda ta taɓa sani acikin rayuwarta, amma an datse mata burinta nadin ainihin sanin waye shi, ta hanyar ɗaura mata Aure.
Tunda aka soma shirin bikin da ya kasance nata ta tattare nata ya nata ta koma gidansu Rahama, don a ganinta hakan zaifi ita dama cenñnn ba qawaye gareta, bare tayi gayyata hakan da tayi kuwa shine mafi sauqinta, kullum kamar Rahama na bata wasu abubuwan itama acewarta na gyara ne dana sanyi kuma, haka ma kullum adda fatsima tana zuwa ta kawo mata wasu haɗaɗɗun zumummuka masu amfani, wanda itace take haɗa mata su da hannuwanta, irinsu tsimi ɓaure, tsimi rake, zumar ɓaure wacce akeyinta da ɓaure da marke da kuma malmo da dabino da ɗan bashanana, da kukkuki sai kanun fari da minanas sai citta sai kuma uwa uba zumar, wohoho HAJIYATA idan har kina irin wannan zumar kin wuce Raini wurin MIJI, Sai kuwa haɗaɗɗen DAKA na musamman wanda Ni Ammey laylerh nice nakeyin duk wannan abubuwan, iya kuɗinki iya shagalinki kai harda ma sauran kayan mata masu amfani na gargajiya ina haɗawa Amare uwayen gida, haɗine masu matuqar amfani da sauqar da NI'IMA nan take.
Shi kuwa ɗakan ɗaya kasance na dabino, Aya mazar ƙwaila, kanun fari, minanas, aswakin mata, geron mata sai gadalin ma'aurata gadalin daka kai abindai kammm ba'a magana, domin na musamman ne ina haɗawa mace ko wanne irin abu da take buƙata.
*DOMIN SAMUN CIKAKKIYAR DAMARKU KUSA Move information
WhatsApp number AMMEY LAYLERH
090-65-78-25-69
Mu koma bangaren su Inna ladiyo, zuwa wannan loqaci Idan hankalisu yayi dubu toya tashi, ganin irin MIJIN da laylan ta aura, hakan shine dalilin da ya qara rura wutar tsanar su gasu umman, inda suka nazama gurin bokaye domin a warware wannan aure, saidai ko ina maganar ɗayace.
Wannan aure babu abinda ya isa rabashi, domin tabbatacce ne tun daga tun ran gini tun ran zane.
Ruwa, iska kai koda za'a haɗe duniyar baki ɗaya babu mahalukin daya isa raba wannan auren.
Hakan ne ya qara fusata su Inna ladiyo da hajja amma ko ina sukaje maganar ɗaya ce babu sanji.
Ɓangare momin Fadeelah kuwa itama hakan take, domin haka suka fantsama
bin bokaye bayan farfaɗowar Fadeelahn
amma duk maganar ɗayace bata sanja zani ba, amma kuma ita ko ɗar bataji ba dangane da hakan, domin tasha jin irin wannan maganganun AUREN fadeelah da kuma jalaal da taso haɗa wa a wancen loqacin.
Haka manyan malamai da bokaye suka ringa faɗin wannan aure ba tabbacce bane ba mai iyuwa bane, sai gashi kuma auren ya yiyu, wannan shine dalilin da yasa sammm bata tsorata kota girgiza ba.
★★★★★
yau Litinin wanda yayi daidai da kwanansu uku kenàn a garin na BAUCHIN Yakubu, kuma yau suke shirye² tafiya kuma tare da amaryarsa
★★★
Zaune take gaban mahaifiyar nata tana kuka tamkar wacce akace mata sun rabu kenan, inda gaba ɗaya duk jikin ƴan parlourn yin sanyi da irin kukan da laylan take, sanye dake cikin wani ɗanyen farin leshi wanda akawa ɗinkin doguwar riga halp bubu.
Cikin son qarfafawa ƴar nata gwiwa Umma ta shiga yi mata nasiha mai matuƙar ratsa jiki. Umman ta shiga faɗin.
"Kiyi haƙuri! Kiyi haƙuri!! Kiyi haƙuri!!!, Innallaha ya, Allah yana tare da masu haƙuri me yakai wannan daɗi, A cuceki kiyi haƙuri,wanda kikayi haƙurin danshi kuma yana tare dake, in Allah yana tare dake yana kula da duk al'amurranki, yana cikin duk sha'aninki, yana kuma sane dake a komai!
Amma sammmm wasu matan basa ganewa, gani suke da ance suyi haƙurin an cucenesu.
Allah ya e dukkan masu haƙuri zasu shiga aljanna ba tare da hisabi, mai yakai wannan daɗi?
Me kiki so bayan wannan Allah yana sane da wand zasu fara haƙuri suce sun gaji, sai yace fasbir, kayi haƙuri sabaran jameela, haƙuri kyakkyawa kinga kenan akwai haƙurin da bai kai haƙuri ba ko?, kince haƙurin ki ya qare kin ɗauki mataki toh me kenàn kikayi?, wahalar da kikai a banza kenan ya ta shi?"
Cike da rauni da kuma kwallar dake qoqarin sakko mata, domin wani miki ne na daga sahin zuciyarta itama. Taci gaba da faɗin.
" MIJI! MIJI!! Miji!!!
Miji ba abin wasa bane abin girmamawa ne, ki sani cewa mijinki yafi iyayenki haqqi akanki,,bani na faɗa ba addinin Musulunci ne yace.
Amma da an faɗa wasu zakaga kunfar baki, to ba haka Mata masu ilimi suke ba.
Daga ranan da aka ɗaura igigiyin auren wani a wuyanki, iyayen ki sun sauqe nauyin su akanki sai abinda miji yace.
GIRMAN da musulunci ya bawa MIJI ba kaɗan bane.
Manzon Allah S. a.w yace da mace zata lashe gyambon na kuraje a jikin mijinta daga kai har zuwa qafar mijinta wallahi da bata biyarshi!.
Ki kalla fa sujjadar da Allah kaɗai ake yiwa amma ace wai da za'a yiwa wani ba'a ce Annabi ba, ba'a ce iyayenki ba , ba'a ce malaminki ba sai akace mijinki,kunga kuwa lallei ana so a nuna mana ne bayan Allah da Manzonsa babu wanda ya chanchanci biyayya da total devotion irin mijinki!"
Tuni wasu har sun fara zuba ruwan hawaye, gaba ɗaya jikin kowa ya kuma yin sanyi fiye da farko, umman kanta xuwa wannan loqacin ruwan hawaye take sharɓewa, amma cikin dauriya Tasan in banda mahaifiyar data zamar maka dole babu wanda ya isa ya maka irin wannan gatan, a zamanin nan da komi ya taru ya gama lalacewa haka taci gaba da faɗin.
"UWAR MIJI! UWAR MIJI!! Da ƳAN uwan mijinki, UWAR MIJI dolenkice wallahi baki da yadda zakiyi da ita! , ta zame miki dole a rayuwa indai kinason zama da ɗanta.
Zata zame miki ba dole ba ne idan kin shirya rabuwa da ɗanta.
Dukkan namijin da kuka gani a duniya da mahaifiyarsa da ƴan uwansa sunsha gwagwarmayar rayuwa tare har girma.
Kar ki shigo ki ringa nuna kin fisu tausayi dason ɗan uwansu, zasu tsaneki sosai!.
Ko ya kawo miki laifinsu ki qoqari ki nuna masa sunfi kusa ke babu ruwanki ciki maganar.
Idan da hali ki qoqari wurin sulhunta su tare da nuna masa ko wani AHALI ana samun saɓani ba wani abu bane¡!¡"
Zuwa yanxun gaba ɗakin yayi tsittt tamkar ruwa yaciyensu, hajja mama dasu lalla hafsa da tun fara wannan nasihar da umman laylan ta fara har qarshen ta a kann kunnensu, sosai Hajja mama ta sake tabbatarwa sai yanxu jikan nata zaiyi Aure mai sunan aure, ba irin auren fadeelah ba ƴar tselan uwa.
Da sallama Hajja mama da lalla hafsa sai ƙanwar mahaifiyar ummien jalaal ɗin dama aka bari duk sauran sun tafi, su uku kawai aka dage iyaka.
Cikin girmama juna suka shiga gaisawa tare da qara yiwa juna ban gajiyar biki, Layla da har zuwa wannan loqacin take shirɓar kukane, yasa Aunty Maryam ɗan rungumo laylan tana ɗan tsokanarta tare da cewa.
"Bafa adam mai irin wannan sunan da ragwanta ba, atoh qara ki gyara Ta kwara na, kada ki ɓata mana suna "
Hakan yasa gaba ɗaya paulourn suka saki murmushi loqaci guda.
Bayan an basu abinci su ci suka fara shirye shiryen tafiya gudun kada yamma tayi.
Inda aka ware mutum huɗu ƴan rakiyar amarya Inna ladiyo, hajja, adda fatsima, sai kuma babar Rahama, ganin irin kukan rabuwar da suke da junane yasa akace a bar Rahman ma taje.
Haka suka haɗa nasu ya nasu suka fito, suna shishshiga cikin motocin da zasu kai su filin jirgi, amma kafff ɗin su babu wanda yasan a jirgin zasu tashi, sai iya su hajja maman, Nan fa kuwa ya dawo sabo domin bayan an kaita wurin baffanta ya mata ƴar nasiharsa da bata taka kara ta karya ba, daƙyar umman ta lallamata bayan ta rakata har cikin mota, Alh Yusuf mai kaba kuwa da shima ya fito ganin dan qara dan qaran motocinsu, da zasu kai sune ya sashi cewa Wallahi saiya raka ƴarsa har gidan aurenta, hajja mama tace ba laifi haknma ai sunnar annabinmu ne Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama, haka motocin suka kula zuwa filin jirgin, wai zoka ga yadda Alh Yusuf mai kaba yayi loqacin dawai yaji a jirgin za'a kai ƴarsa gidan aurenta, hhhhhhhh ciki sai yayi ciwo wllh a gaba, haka jirgin su ya keta sararin samaniya.........
Saida mu yiwa amaryarmu fatan sauuƙa lafiya
Sai mun haɗe a shafi na gaba
By *AMMEY LAYLERH*
https://chat.whatsapp.com/FZOG6TDjDid2W63LyRn3XP
____________________________
*💐🌼 JALAAL AREEF 🌼💐*
~💸 THE BILLIONAIRE 💸~
A story of pure love that touches the ♥️
*NA AMMEY LAYLERH*
Page 19&20
08104493215
____________________________
♥️🤍♥️
Haka jirgin su ya keta hazo, dab da sallar la'asr jirgin su ya sauqa,inda wasu irin Narkakkun motoci suka zo ɗaukarsu daga gidan su jalaal, guda goma sha ɗaya ne ciff inda suka sanya laylan a motar da tafi ko wacce haɗuwa acikinsu da ɗaukar hankali. Biyar suna gaba biyar suna baya wacce duka sauran motocin matakan tsaro ne a cikin su. Baffa Yusuf mai kaba kuwa in banda faman raba idanu a saman titi babu abinda yake, Ahaka har suka isa qatuwar anguwar GUZAPE ASOKORO DISTRICT ABUJA, data kenàn shiru tamkar yadda kuka sani,
kafin suyi hong a qaton get ɗin estate ɗin gidan su jalaal ɗin.
Wohoho zoka ga idanuwan su Inna ladiyo ganin motocin da suke a ciki sun faka gaban qaton get ɗin estate ɗin su jalaal.
Hong motocin suka shiga dannawa, da sauri get man yazo ya buɗe musu get ɗin farko na cikin estate ɗin, kafin su kuma shimgiɗa motocin saman kwaltar dake malale a gaba ɗaya kata fanin gidan.
Gaban get na biyu suka kuma danna hong shima get man yazo ya buɗe musu, sojojin dake harabar wurin ne suka sara musu tare da cira bindugunsu sama, kai wannan gida dai kam inhar ba sani kayi tabbas zaka daɗe kana qiransa da SOLDIER'S HOUSE ne.
Domin irin sojojin dake ta kai kawo a harabar wurin, nan suka nausa kansu cikin get na uku sunyi tafiya mai nisa kafin suka Isa wurin hasalin cikin gidan, direct parking lot suka nufa suna paka motocin nasu.
Gaba ɗaya Jama'ar gidan baki ɗayansu suna Zazzau ne bisa wasu fararen kujeru irin na bikan, suna ganin motocin sun daidai parking nasu ne wasu daga cikin su suka nufi motocin.
Ummie ce akan gaba yayin da sauran abokan zamanta, suka rufa mata baya daidai kuma loqacin da aka fara buɗe musu motocin, motar da ummien jalaal ta tabbatar a ita Layla take ta buɗe motar da Bismillah, tare da sanya hannuwanta ta kamo na laylan, Layla kuwa da xuwa loqacin tama dena kukan baki ɗaya sai shan zuciya kawai take, jin an kamo hannuwanta ne ya sata ɗago kanta don ganin waye mai taɓa tan, da wata kyakkyawar mata taci karo wanda tashi ɗaya laylan taji kamar tasan fuskar,ko kuma mai irin fuskar.
Wani tattausan murmushi ummien ta sakamar laylah ɗin, domin kallon farko yaji yarinyar ta masifar kwanta mata arai, Layla kanta tayi qasa dashi domin haka nan taji matar ta mata kwarjini haɗi dajin kunyarta.
Ummie kuwa dake riƙe da hannun laylan har yanzu ganin tayi qasa da kanta ne, ya sanya ta ɗan sunkuyo da kanta cikin motar tare da raɗa mata.
"Ki fito da Bismillah atare dake, kana ki fara fitowa da qafar dama"
Kamar yadda ta buƙata ɗin hakan kuwa Laylan ta fito da adda'oi a bakinta bama iya Bismillah ba.
Ahankali ummien ta ɗan rungumo mota jikinta.
Again tana kuma sakar mata woni sabon murmushin, baffa yusif tun loqacin da suka shigo get ɗin farko ya rumtse idanunsa, yanajin wasu abubuwa na masa yawo acikin jikinsa, bai qara tsinkewa da labarin ba saida yaga waɗan nan kattin sojojin, tuni yaji cikinsa ya harmutsa da qarfin balaki. Domin gani yake shi kenàn tasu tazo qarshe, Su Inna ladiyo kuwa zuwa wannan loqaci an shiga taitaiyi, Ahankali ummie ta zare jikinta daga na laylan tana kama hannunta, da hamzari Hajiya Hafsat tayi saurin kama ɗayan hannun layan, da wata kafurar harara Hajiya Turai ta raka bayansu, tana jan kwafa Aranta, su adda fatsima kuwa hajja mama ce ta zame musu jagora, suna tafiya suna ƴar firarsu taɗan sabon daya shiga tsakan kaninsu, na ƴan kwanakin da suka yi gari ɗaya kuma dama adda fatsiman itane mai kaima su hajja maman abinci.
Kai tsaye ummie ɓangarenta ta nufa da ita, kasancewar loqacin anata qiraye qirayen sallar la'asr ne yasa ta nufar ɓangarenta kai tsaye, inda su hajja mama cenñnn suka nufa, xuwa wannan loqacin kamm babu mai yiwa wani magana tsakaninsu hajja da Inna ladiyo, sai wani irin tukukin hassadar dake cinsu.
Cikin mutum taka akai su adda fatsima masauƙi mai ƙyau,kasancewar dama ana ta qiraye qirayen sallar la'asr ne yasa kai tsaye sallah suka fara gabatarwa, kana aka shiga lode musu abincin cika kala da iri, take aka ƙayata gabansu da dinner.
Wai ina labarin baffanmu?.
Ɗaya daga cikin soldier na gidan ummie tawa umarni daya kaishi masallaci yayi Sallah, haka cikin ɗari² yabi bayan soldier ɗin tamkar woni marar gaskiya.
★★★★★★
Bayan sun tabbata kowa ya kammala duk woni uzurinsa, suka faɗa musu akwai WALEEMA ƙarfe biyar na yamma, bangaren amaryarmu kuwa bayan ummie ta zaunar da ita bakin gado ta kawo mata peoee meat da piatist pototo irin na Yaren nan, amma fa in kaci da azabar daɗi yake da kwai da Nama da da yalanbobo da da ikkiti, amma fa inhar ba sanin sa kayi ba kai tsaye kallon ƙamata na zaka ma abin, saidai a wurin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 22