Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya koma da baya tamkar babu wannan rauni a jikinsa. Da isar Shaharan inda ya baro su Haiman sai ya iskesu a cikin wani irin mugun hali. Duk wuraren da wannan Kunama ta sara a jikinsu har ya rube ya fara tsutsa kuma wajen dada girma yake yana dada zabtarewa, su duka suna ihu. Ya Koda ganin wannan bala'i sai hankalinsa ya dugunzuma ainun kuma ya cika da tsananin 188 TASKARNOVELS.COM.NG mamaki bisa yadda aka yi shi nasa raunin bai rube ba ya kama tsutsa. Abinda ya fara fado masa a rai shi ne, watakila saboda ya shiga cikin wannan kogi ne na tudun tsira shi ya sa nasa raunikan ba su yi tsutsar ba. Cikin firgici da hanzari ya cicciɓi Zarina da Shadira ya saɓa su a kafadunsa ya sake falfalawa da gudu ya nufi inda kogin tudun tsira yake. Wannan karo shi kansa ya yi matukar mamaki bisa ganin irin masifaffen gudun da yake yi don ya ninka wanda ya yi da farko. Kafin rabin-rabin sa'a ya iso bakin kogin. Da zuwa sai ya jefa Zarina da Shadira a ciki, suna fadawa cikin kogin sai raunikan nasu suka daina tsutsa kuma suka dawo kamar yadda suke da farko. Koda ganin haka sai farin ciki ya lullube Shaharan ya juya da sauri ya sake falfalawa da gudu ya koma can wajen sauran abokan tafiya. 189 TASKARNOVELS.COM.NG Haka ya rinka dauko su da bibbiyu akan kafadunsa yana gudu yana kawo su cikin kogin tudun tsira yana watsa su ciki har ya gama debo su gabadaya ya zamana cewa saura dokinsa da Aljani Marhabul Zaurus kadai. wannan lokaci shi ma dokin Kunamar ta sare shi a waje biyu kuma raunin ya zama tsutsa har ya cinye rabin jikinsa, dokin ya baje a kas har ya fara kokarin mutuwa. Koda Shaharan ya ga halin da dokinsa ke ciki kuma ya ga shi ma Aljani Marhabul Zaurus yana cikin irin wannan hali sai hankalinsa ya dugunzuma ainun tunda shi ma Marhabul Zaurus din ba zai iya koda mikewa zaune ba bare ya dauki dokin ya kai shi can bakin kogin tudun tsira. Shaharan ya sunkuya ya cicciɓi dokinsa da dukkan karfinsa amma sai ya kasa koda raba dokin da kasa ne saboda nauyinsa. Sai da 190 TASKARNOVELS.COM.NG Shaharan ya jarraba daukar dokin nasa har sau uku amma yana kasawa, kawai sai ya zauna a gefe daya yana kallon dokin yana kuka, sa'adda dokin ya fara kakarin mutuwa. Yana ji, kuma yana gani tsutsa ta baibaye gabadaya jikin dokin, wannan tsutsar ta zamo sanadin ajalinsa. Nan fa Shaharan ya kurma uban ihu sannan ya sake fashewa da matsancin kuka. Shi kuwa Aljani Marhabul Zaurus lokacin da azabar tsutsar jikinsa ta addabe shi sai ya fara ihu yana kuka yana mai cewa, "Ya kai wannan jarumi ka sani cewa ni ma mutuwa zan yi yanzu, ina mai yi maka gargadi da ka yi hankali da Boka Muzaffar domin gaba dayanku yaudararku yake yi, so yake da zarar kun isa kogon Darul Iksina ya hallaka ku, ku duka saboda shi kadai yake son ya mallaki wannan ruwan sihiri da kuma Aljani Maruful Dauwaz. 191 TASKARNOVELS.COM.NG Tabbas idan ya mallaki wadannan abubuwa biyu babu abin da zai gagare shi a cikin wannan duniya. Ni kaina sai yanzu ne na gane cewa ya yaudare ni ya cutar da ni. Tabbas wannan duniya makaranta ce kullum ana samun kima a cikinta. Ka yi hattara ya kai Shaharan, lallai ka yi iya kokarinka wajen ceton rayuwar sauran abokan tafiya. Ni kam tawa ta kare, sai dai nan gaba ku bayar da labarina idan kun tsira da rayuwarku!". Gama fadin hakan ke da wuya sai Aljani Marhabul Zaurus ya ɓingire kasa ya zama gawa. Shi kuwa jarumi Shaharan sai ya ci gaba da matsanaicin kuka sakamakon mutuwar dokinsa. Bai gushe ba yana wannan kuka har izuwa tsawon sa'a guda sannan ya mike tsaye ya juya ya nufi hanyar da za ta kai shi can bakin kogin tudun tsira. Yana tafe yana waigen dokinsa yana zub da hawaye har ya daina hango dokin nasa. 192 TASKARNOVELS.COM.NG Lokacin da Shaharan ya iso bakin kogin tudun tsira sai ya iske kowa ya dawo cikin haiyacinsa, ana ta yi wa juna magani a jikin raunika.Tun daga nesa Zarina ta hango shi sai ta mike tsaye ta ruga gare shi, suna haduwa suka rungume juna cikin tsananin farin ciki. A wannan lokaci Haiman da matarsa Lumaira na zaune a gefe daya suna ta duba lafiyar junansu kuma suna murna da ganin junansu a raye. Shadira Imran da mahaifiyarsa ma suna gefe a tare. Boka Muzaffar, Sarki Laffaru da Gimbiya Rahila na zaune a tare su ma suna ta murna da ganin kansu a raye Lokacin da Boka Muzaffar ya ga jarumi Shaharan ya dawo shi kadai babu dokinsa kuma babu Aljani Marhabul Zaurus sai ya ji a jikinsa cewa lallai Aljani Marhabul Zaurus da dokin Shaharan rai ya yi halinsa. 193 TASKARNOVELS.COM.NG Cikin hanzari Zarina ta janye jikinta daga cikin na Shaharan ta shiga duba lafiyarsa. Koda tayi arba da wannan katon rauni da ke kafarsa sai ta dimauce kuma ta fashe da kuka. Nan take ta zaunar da shi ta shiga sa masa magani akan raunin sannan ta je ta nemo tsumma mai tsafta ta nannade raunin duka ta ɗaure shi. Gama hakan ke da wuya sai ta kwantar da Shaharan a kas tana mai dora kansa akan cinyarta ta shiga tunani mai zurfi. Daga can sai ta fara rera waka cikin sanyaya kalamai masu dimauta maza alokacin da hawayenta ke diga bisa kan fuskar Shaharan. A cikin wakar tana bayani kamar haka; "Mazaje sun fadi a yayin da gumu ya kai gumu" "Ranar wuya ita ce ranar da daci ke yanke zaki" "Ranar masoya ke rasa masoyansu" 194 TASKARNOVELS.COM.NG "Daji biyar na masifa yau mazan Kwarai sun ratsaka mma basu sha da dadi ba" "Ga ďa da uwa a cikin bala'i, amma ba su iya tseratar da juna ba" "Miji da mata sun ga gararin da ba su taɓa" gani ba. "Jini da jini na hade amma bakin takobi ya raba su" "Yau fa ga ranar cika buri amma amfaninta ya gushe tunda babu masoyi" "In ban da akwai sauran masoya a doron kasa da mazaje sun zabi mutuwa akan rayuwa!" Lokacin da Shadira ta fara rera waďannan baitoci sai jikin kowa ya yi sanyi aka yi ta kuka kamar ba za a daina ba. Kuma aka yi tsit ana saurarenta har izuwa dogon lokaci. Ita kanta sai da ta ji ta gaji da yin wakar sannan ta yi shiru ta kifa kanta akan kirjin Shaharan har barci ya sace su su biyun ba su sani ba. Gaba dayan abokan tafiyar sai da suka yi baccin wuya, baccin dole saboda tsananin gajiyar da ke jikinsu. Dayansu bai farfado ba sai bayan sa'a biyu da rabi. 195 TASKARNOVELS.COM.NG Mahaifiyar Imran ce ta fara farfadowa tana bude idonta ta hangi danta Imran da Shadira kwance a waje daya sai ta ji ta cika da tsananin farin ciki da ta rayu ta kawo izuwa wannan lokaci da take daf da warkewa daga cutar da ta addabi rayuwarta tsawon shekara da shekaru kuma take daf da ganin auren danta. Bayan ta jima tana kallon Imran da Shadira tana ta murmushi sai kuma ta juya ta kalli inda Haiman da matarsa Lumaira ke kwance, nan take taji suma ta tayasu farin ciki ainun tunda suna daf da cika burinsu na warkewar. Lumaira daga cutar makanta. Koda ta tuno da yaro Masnur dan uwan Shadira, Sarki Farisa dan uwan Zarina da kuma dokin Shaharan ai ta fashe da matsanaicin kuka saboda ko ba komai ta shaku da su a cikin wannan doguwar tafiya da aka yi kuma ta tausayawa masoyansu matuka bisa rashin su da suka yi. 196 TASKARNOVELS.COM.NG Sautin kukan mahaifiyar Imran ne ya sa kowa ya farka daga barci.Koda Imran ya ga mahaifiyarsa na kuka sai ya mike tsaye zumbur daga jikin Shadira ya ruga "Ya ke izuwa wajen mahaifiyar tasa ya durkusa a gabanta suka rungume juna yana mai cewa, Ummina ina dalilin wannan kuka naki?" Ki yi sani cewa yanzu lokaci ne na farin ciki ba na kuka ba tunda muna daf da cika burin zuciya. Koda jin wannan batu sai mahaifiyar tasa ta janye jikinta daga cikin nasa suk fuskanci juna sosai sannan ta ce, "Ya kai dana ka yi sani cewa ba komai ne ya sani wannan kuka ba face tsananin tausayinmu gaba daya nan. Tabbas ko nan gaba idan ana bayar da labarinmu sai an yi kuka a duniya kuma labari ne irin wanda baya shafewa kuma ba za a taɓa mantawa da shi ba. Ko a iya nan labarinmu ya tsaya mun aje tarihin abin al'ajabi kuma abin alfahari". 197 TASKARNOVELS.COM.NG Sa'adda mahaifiyar Imran ta zo nan a jawabinta sai Imran ya yi ajiyar zuciya ya ce, "Ya ke Ummina ki yi sani cewa a cikin matafiyan nan gaba daya ba masu sa'a sama da mu ni da ke. Duk tsananin masifun da muka hadu da su a baya ni da ke babu wanda ya rasa wani bangare na jikinsa, amma sauran abokan tafiya kuwa daga wanda ya sami manyan raunika a jikinsa sai wanda ya rasa masoyi da wanda ya rasa wani бangare na jikinsa.Ina ji a jikina cewa har mu shiga cikin kogon Darul Iksina babu abin da zai same mu kuma sai bukatarmu ta biya." Koda jin wannan batu sai mahaifiyar tasa ta dube shi cikin firgici ta ce, "Haba ya kai dana kai kuwa mene ne tabbacinka cewa za mu sami wannan nasara alhalin har yanzu akwai sauran tashin hankali a gabanmu na shiga cikin kogon Darul Iksina?" Ya yin da Imran yaji wannan batu sai ya yi murmushi ya ce, "Ba komai ne ya sa nake da wannan yakinin ba face na san cewa a duniya babu wata soyayya mai karfi sama da soyayyar 198 TASKARNOVELS.COM.NG da ke tsakanin da da mahaifi. Ya ke Umkina ki tuna cewa tun ina cikin cikinki kike dawainiya da ni kike shan wuya har kika haife ni sannan kika shiga rainona. Sa'adda na fara zama mutum kuwa sai ya zamana cewa soyayyarki a gare ni kullum tana karuwa kuma ya zamana cewa ko kuda ba kya son ya taɓa dafiyar jikina. Ba zan taɓa mantawa ba da irin dawainiya da wahalar da muka sha ta rayuwar talauci, rashin makwanci da tsananin yunwa gami da yawo kwararo-kwararo har ta kai mu ga zaman dole a cikin daji. Na yi imani a zuciyata cewa wannan wahala da muka sha ba za ta zamo a banza ba, lallai sai mun ji dadi kafin cikar ajalinmu". Ya yin da Imran ya zo nan a zancensa sai mahaifiyarsa ta cika da dumbin farin ciki ta sake rungume shi a kirjinta tana mai bushewa da dariyar murna shi ma ya tayata dariyar. A dai-dai wannan lokaci ne Boka Muzaffar ya mike tsaye ya dubi gaba dayan abokan tafiyar daya bayan daya ya ce, "Ya ku 'yan uwana ku yi sani cewa yau ne muka kawo karshen wuya a 199 TASKARNOVELS.COM.NG cikin wannan tafiya tamu kuma daga nan zuwa kogon Darul Iksina tafiya ce ta kwana uku kacal. Ina mai tabbatar muku da cewa babu wani mugun abu da za mu sake haduwa da shi akan hanya har mu isa kogon Darul Iksina amma ku sani cewa a cikin kogon Darul Iksina akwai masifu iri-iri har kala dari tara da casa'in da tara. Gaba dayanku nan babu wanda ya san yadda za a iya tsallake masifun da ke cikin wannan kogo face ni saboda haka da zarar mun shiga cikin kogon ku kasance masu biyayya a gare ni da bin umarnina. Duk abinda na ce ku yi kawai ku yi shi cikin gaggawa kada ku yi mini gardama ko jayayya. Idan kunne ya ji, gangar jiki ta tsira. Yanzu zamu zauna anan har tsawon kwana uku domin mu yi jinyar raunikan jikinmu sannan mu ci gaba da tafiya". Koda gama wannan jawabi sai Boka Muzaffar ya koma inda yake ya zauna. Zamansa ke da wuya sai jarumi Shaharan ya dube shi ya ce, "Ya kai jagoran wannan tafiya ina da tambaya guda daya a gare ka. Wai shin me ya sa tun da muka fara wannan tafiya ba ka ceci rayuwar mutum daya ba daga cikinmu da karfin sihirinka? Ka 200 TASKARNOVELS.COM.NG tuna fa cewa ka shafe shekaru masu yawa kana bincike da hidima akan wannan tafiya tamu, ai ya ci ace ka san duk irin bala'in da za mu fuskanta a cikinta ka tanadar mana rigakafinta." Koda jin wannan batu sai Boka Muzaffar ya kyalkyale da dariya sannan ya hade fuska kamar an aiko masa da sakon mutuwa ya ce, "Ya kai Shaharan ka yi sani cewa babu wani sihirin tsafi da ya isa ya yi tasiri a cikin wadannan dazuzzuka biyar da muka ratsa fiye da shekaru dubu da suka gabata haka wannan al'amari yake amma idan muka shiga cikin kogon Darul Iksina kowannenmu sihirin tsafinsa zai iya tasiri". Koda Boka Muzaffar ya zo nan a zancensa sai Shaharan ya mike tsaye ya yi 'yar tafiya nesa kaɗan da inda sauran abokan tafiya suke ya zauna ya shiga sabon tunani. Abinda ya fara fado masa a rai shi ne, tunowa da wasiyar da Aljani Marhabul Zaurus ya yi masa kafin ya mutu cewar ya yi hankali da Boka Muzaffar lallai mayaudari ne shi kuma 201 TASKARNOVELS.COM.NG azzalumi".Shaharan na cikin wannan tunani ne yaji an dafa kafadarsa ta baya. Cikin firgici ya waigo da sauri sai ya ga ashe Zarina ce don haka sai ya yi murmushi a gare ta itama ta maida masa da martanin murmushin sannan ta zauna daf da shi suna masu fuskantar inda sauran abokan tafiya ke kwance, wato can bakin kogin tundun tsira. Tsawon 'yan dakiku dayansu bai ce uffan ba daga can sai Zarina ta yi gyaran murya ta ce, 'Ya kai masoyina, ka yi sani cewa masu iya magana sun ce, 'Ruwa baya tsami banza' Tabbas akwai abinda ke damunka shi ya sa ka baro cikinmu ka dawo nan ka zauna kana tunani. Idan har son da kake yi mini na gaskiya ne kada ka ɓoye mini komai. Ka tuna cewa na rasa dan uwana Sarkin Farisa yanzu bani da sauran kowa a duniya. Kai ma ka rasa dokinka wanda da shi ne kaɗai za ka cika babban burinka na duniya, ba ka da wani abu da yai saura wanda ya fi ni daraja. Lallai ya zama wajibi a gare mu mu hada kai mu taimaki juna tunda muna bukatar junan namu". Sa'adda Gimbiya Zarina ta zo nan a cikin zancenta sai jarumi Shaharan ya yi ajiyar zuciya sannan ya 202 TASKARNOVELS.COM.NG kwashe labarin duk abinda ya faru tsakaninsa da Aljani Marhabul Zaurus ya zaiyane ma ta. Koda jin wannan labari sai hankalin Zarina ya dugunzuma ainun, ta yi shiru tana mai tunani. Daga can sai ta kawo gwauron numfashi ta ajiye sannan ta ce, "Hakika Biri ya yi kama da Mutum. Inda Boka Muzaffar ya kasance adali kuma mai gaskiya da ya nuna matukar damuwarsa bisa duk irin abubuwan da suka rinka faruwa a gare mu mu duka. Ni na rasa dan uwana amma ko jaje bai yi mini ba. Shadira ta rasa dan uwanta bai tausaya mata ba. Kai ma ka rasa dokinka bai ce da kai komai ba. Haiman da kai kun rasa hannayenku dai dai amma duk bai nuna tausayinsa ba. Wannan yana yi mana nuni da cewa Boka Muzaffar bai damu da rayuwarmu ba alhalin kuma shi ne ya dora mu akan wannan TAFARKI zuwa kogon Darul Iksina kuma mun dade muna jiransa akan yin wannan tafiya. Ko shakka babu Muzaffar yana da wata manufa a Karkashin zuciyarsa kuma yana da wani buri na musamman akan shiga cikin kogon Darul Iksina. 203 TASKARNOVELS.COM.NG Lallai ya yi amfani da mu ne kawai a matsayin Karukan farautarsa. Ya kai masoyina shawarar da zan ba mu ita ce duk irin umarmin da Boka Muzaffar zai ba mu a cikin kogon Darul Iksina kada mu yi amfani da shi kuma idan da hali mu hana sauran abokan tafiya aiki da wannan umarni nasa." Lokacin da Zarina ta zo nan a zancenta sai Shaharan yai ajiyar zuciya sannan ya ce, "Ya ke masoyiyata ki yi sani cewa abokan tafiyarmu sun yarda da Boka Muzaffar dari bisa dari, koda za mu ba su labarin wasiyyar da Aljani Marhabul Zaurus ya bayar ba za su aminta ba. Idan kuma muka sanar da su a yanzu za su yi mana tawaye, wata kila ma su hada kai su yake mu. Abin da zai fiye mana alheri shi ne kawai mu bar wannan al'amari a cikin zuciyarmu. Wanda duk yake da rabon fitowa a raye daga cikin kogon Darul Iksina lallai zai fito. Yanzu ki tashi mu koma can wajen abokan tafiya domin idan muka ci gaba da hira anan Boka Muzaffar zai iya zarginmu har ma ya yi tunanin daukar mataki a kanmu". Gama fadin hakan ke da wuya sai duk su biyun suka mike tsaye suka koma can wajen sauran 204 TASKARNOVELS.COM.NG abokan tafiya. Nan take aka shiga kafa tantuna gami da shirya abincin da za a ci. Kamar yadda Boka Muzaffar ya shirya haka al'amura suka kasance, wato sai da su Shaharan suka shafe kwana uku cur suna jinyar raunikan jikinsu a nan bakin kogin tudun tsira sannan suka kintsa aka kama hanya aka durfafi kogon Darul Iksina. Haka dai suka wanzu suna tafiya, ba sa ya da zango face idan dare ya yi sannan su tsaya a kafa tantuna a kwanta ayi barci. Wani abin mamaki da ya faru shi ne, a iya tsawon kwana ukun da suka yi wannan tafiya ko maciji ba su kara gani ba akan hanyarsu bare ya kawo wa dayansu hari. Da la'asar sakaliya suka iso bakin kogon Darul Iksina. Kogon na Darul Iksina ya kasance abin al'ajabi ga dukkan wanda ya yi arba da shi, domin ya wanzu ne tamkar ginin gida akan wani 205 TASKARNOVELS.COM.NG dan karamin tsuburi, wanda ruwa ya kewaye shi kuma ruwan ba shi da zurfi domin komai gajartar mutum bai fi ya kawo masa iya kaurin kafarsa ba. Kogon na Darul Iksina an yi shi ne cikin siffar gida na ginin jan dutse na Murjani, wanda tun daga nesa mutum zai ga yana ta kyalkyali da daukar ido sannan haskensa ya haskake dajin gaba daya. Girman gidan ya kai na dan karamin gari yana da fadi da tsawo sosai domin idan aka fuskance shi ba a iya hango karshen katangarsa. Idan mutum ya daga kai ya dubi saman ginin kogon sai ya ga kamar bashi da karshe kwai dai ya lmtokare da sararin samaniya ya kule a cikin gajimare. Ko kadan babu alamar kofa ko taga a jikin gidan kuma ko ina a mulmule yake a shafe tamkar wani abu bai taɓa shiga cikinsa ba. 206 TASKARNOVELS.COM.NG Lokacin da su jarumi Shaharan suka iso daf da kogon Darul Iksina sai gabadayansu suka ja suka yi cirko-cirko suna kallon kogon cikin tsananin al'ajabi. Shi kansa Boka Muzaffar an batar da tunaninsa domin yadda duk yake tsammani zai ga kogon ba haka ya gan shi ba. Bayan sun dan ɓata dakiku masu yawa suna kallon kogon sai Boka Muzaffar ya wuce kan gaba ya shiga cikin wannan ruwa ya durfafi tsuburin da kogon Darul Iksina ke kai ba tare da fargabar komai ba yana ta kyalkyala dariyar farin ciki kuma yana yafito sauran abokan tafiya da hannu. Koda ganin haka sai Haiman ya bi bayansa yana goye da matarsa Lumaira, sannan Imran dauke da mahaifiyarsa, Shadira na binsu daf da daf Shaharan da Zarina na biye sannan Gimbiya Rahila, Sarki Laffaru ne na karshe. 207 TASKARNOVELS.COM.NG Kamar yadda Shaharan da Zarina ke da shakku akan Boka Muzaffar, haka Sarki Laffaru ya kasance domin shi ma ya lura da take-takensa tun daga farkon tafiyar tasu har izuwa sa'adda suka iso bakin tekun tudun tsira don haka sai ya aiyana a ransa cewa duk irin umarnin da Boka Muzaffar ya bayar a cikin kogon Darul Iksina ba zai yi aiki da shi ba koda kuwa zai rasa rayuwarsa. Bayan kowa ya haye wannan ruwan sai aka hau kan tsuburin aka iso daf da kogon Darul Iksina aka tsaya aka yi cirko-cirko kowa ya zubawa Boka Muzaffar idanu. Yayin da Muzaffar ya ga shi kaɗai ake sauraro sai farin ciki ya lulluɓe shi nan take ya shiga yi wa kansa kirari yana mai cewa; "Ni ne Bokan zamani wanda ya gagari dukkan Bokaye. 208 TASKARNOVELS.COM.NG Ni ne murucin kan dutse ban fito ba sai da na shirya. Ina matsafa da jaruman duniya, yau ga Bokan farko da zai zamo sanadin da za a shiga kogon Darul Iksina. Na bata hankali Dare na sami suna da daukaka, kuma na samu. In banda Aljani Maruful Dauwaz babu wanda zai riga ni shiga kogon Darul Iksina, lallai na bar wa duniya abin tarihi. Ko yanzu na mutu na kasaita kuma na gawurta, lallai duniya ba za ta manta da ni ba." (OH ni Maiboko! Ka ji ďan egiya mayaudari macuci) Gama fadin hakan ke da wuya sai Muzaffar ya fiddo wata 'yar karamar wuka daga jikinsa ya 209 TASKARNOVELS.COM.NG kama suturar jikinsa dai-dai ciayarsa ya kwaye ta, sai ga wadansu dalasiman tsafi rubuce akan ciyar Nan take ya fara karanto dalasiman tsafin cikin daga murya. Faruwar hakan ke da wuya sai wata irin iska mai karfi ta fara kadawa tana zagaye gaba dayan kogon na Darul Iksina, gaba daya yanayin sararin samaniya ya sauya daga fari fat ya koma kore shatar. Al'amarin da ya firgita gaba dayan abokan tafiyar ke nan, dukkaninsu suka ji tsigar jikinsu ta tashi, kuma tsoro ya baibaye su. Boka Muzaffar na gama karanto wadannan dalasiman tsafi sai wannan iska ta dauke dif, yanayin sararin samaniyar ya dawo dai-dai yadda yake a da. 210 TASKARNOVELS.COM.NG Ba zato ba tsammani sai suka ga wata katuwar kofa ta bakin mulmulallen karfe ta baiyana akan ginin kogon Darul Iksina, sannan sai suka ji karar zare sakatu a jikin kofar har guda casa'in da tara. Daya bayan daya sakatun suka rinka zare kansu. Ta casa'in da taran na gama fita sai kofa ta bude wanwar. Koda suka yi arba da cikin kogon sai gaba dayansu suka cika da tsananin al'ajabi. Ba komai ne ya haddasa hakan ba face ganin abin da ke cikin kogon. Wadansu gidaje ne kala-kala a cikin kogon har guda bakwai. Kowanne gida guda daya ya kai girman unguwa guda, kuma dukkan gidajen anginasu ne daga dangin su Zinare, Lu'u-lu'u, Jauhar, Murjani da sauransu. Duk wanda ka kalla sai ka ga kamar ya fi wanda ke kusa da shi kyau da ginuwa 211 TASKARNOVELS.COM.NG Ba tare da fargabar komai ba Boka Muzaffar ya kuna kai izuwa cikin kogon suma sauran abokan tafiyar sai suka bivshi da sauri duu! Da yake Sarki Laffaru ne na karshe yana shiga sai kofar gidan ta rufe kanta wadansu sakatu guda casa'in da tara suka mayar da kansu cikin ramukansu, sanann kofar ta sake rufe kanta. Faruwar hakan ke da wuya sai Boka Muzaffar ya bushe da dariyar mugunta. Lokaci guda kuma ya hade rai ya ce, "Ni ne kadai zan iya sake bude muku kofar wannan gida ku fito in ba haka ba kuwa sai dai ku mutu a cikinsa". Gama fadin hakan ke da wuya sai Boka Muzaffar ya sanya hannunsa a cikin aljihunsa ya fiddo wata 'yar karamar jemammiyar fata. Babu. komai a jikin fatar face taswirar gidajen da ke cikin wannan kogo gaba dayansu guda casa'in da taran. A jikin kowanne gida akwai rubutun wadansu kalmomin tsafi. 212 TASKARNOVELS.COM.NG Nan take Boka Muzaffar ya ajiye wannan jemammiyar fata a kasa, gaba dayan abokan tafiyar suka kewaye ta suna kallonta cikin mamaki. Muzaffar dube su daya bayan daya ya ce, Shin a cikinku akwai wanda zai iya karanta mini kalma daya daga cikin kalmomin da aka rubuta a jikin wannan fata?" Koda jin wannan tambaya sai kowa ya duruduru aka rasa wanda zai ce kala. Da ganin haka sai Boka Muzaffar ya sake bushewa da dariya sannan ya ci gaba da kuri yana mai cewa, "Ku duka a yanzu rayukanku a hannuna suke. Wanda duk ya bi umarnina zai kuɓuta ya sami cikar burinsa. Wanda kuma duk ya bijire mini kuwa zai hallaka anan cikin kogon Darul Iksina. Koda gama fadin hakan sai Boka Muzaffar ya Kurawa wannan fata idanu sannan ya dago kai ya dubi Haiman da Imran ya ce, "Ku je ku bude 213 TASKARNOVELS.COM.NG kofar wancan gida na uku ku shiga cikinsa kai tsaye. Lallai a cikinsa ne za ku riski ruwan albarka da za ku yiwa masoyanku magani da shi su warke". Ba tare da gardamar komai ba kuwa Haiman da ke goye da matarsa Lumaira ya nufi kofar wannan gida. Imran goye da mahaifiyarsa ya mara masa baya. Nan take suka bude kofar wannan gida na uku suka kunna kai ciki. Suna shiga sai kofar gidan ta rufe kanta. (Allah wadaran mai hali irin na boka Muzaffar) Daga nan sai Boka Muzaffar ya dubi Zarina da Shadira ya ce, "Ku kuma kun rasa masoyanku don haka ba ku da sauran bukatar ruwan albarka. Kai ma jarumi Shaharan baka da bukatar wannan ruwa, saboda haka ka bi Zarina da Shadira ku shiga cikin gida na biyu. Duk abin da kuke so na duniya wanda ya dunganci dukiya 214 TASKARNOVELS.COM.NG za ku samu a cikin wannan gida, ku shiga ku debo iya muradinku akwai hadiman da za su yi muku dako har izuwa kasashenku." Koda jin wannan batu sai Shadira ta nufi wannan gida na biyu, amma sai Shaharan da Zarina suka toge. Al'amarin da ya matukar bai wa Boka Muzaffar mamaki ke nan ya dube su ya ce, 'Me kuka tsaya jira? Ko kuwa kuna so ku bijirewa umarnina ne?" Sa'adda Shaharan ya ji wannan tambaya daga bakin Boka Muzaffar sai ya yi murmushi ya ce, "Ya kai wannan Boka ka yi sani cewa ni yanzu tsakanina da kai babu sauran yarda da amana, saboda jikina ya ba ni cewa so kake ka yaudare mu ka cutar da mu. Ina tabbatar maka da cewa duk inda ka shiga ni ma nan zan shiga tunda na san cewa ba za ka kai kanka inda za ka hallaka ba". 215 TASKARNOVELS.COM.NG Koda jin wannan batu sai Boka Muzaffar ya bushe da dariya ya ce, "Tabbas ka yi dabara ya kai wannan jarumi, b." amma ka kama hanyar da ba za bulle ba Boka Muzaffar ya dubi Sarki Laffaru ya ce, ya kai abokina, maza ka ruga izuwa cikin daki na hudu domin anan ne za ka sadu da Aljani Maruful Dauwaz wanda zai cika maka burin rayuwarka. Sarki Laffaru ya toge ya ce, "Kai ba zai yiwu ba. Haba abokina! Ai ilimin tsafi ka fi ni amma ba wayo ba ko sanin tuggun duniya. Ina tabbatar maka da cewa kafarka-kafata. Duk inda ka shiga nan zan shiga. Idan har ma gaskiya ne cewar zan sadu da Aljani Maruful Dauwaz a cikin gida na hudu ta ya ya zan iya sarrafa shi ya aminta da ni har ya biya mini bukatata?" Koda jin wannan tambaya sai Boka Muzaffar ya ce, "Ai ga Gimbiya Rahila nan amfanin tahowa da ita kenan a cikin wannan tafiya muddin Aljani Maruful Dauwaz zai yi arba da ita duk abin da kake so zai yi muku tunda kamanninta 216 TASKARNOVELS.COM.NG iri daya ne sak da na masoyiyarsa wadda ya rasa." Kafin Muzaffar ya gama rufe brakinsa tuni Gimbiya Rahila ta tari numfashinsa ta ce, "Kai! dakata tsohon banza! Mayaudari, ai kama da wane ba ta wane. Ni mutum ce, masoyiyar Aljani Mauruful Dauwaz kuwa aljana ce, kuma ta mutu. Wanda duk ya mutu ba zai dawo ba, Mauruful Dauwaz ya san da haka. Abin da na ke so da kai kawai ka kai mu inda Maruful Dauwaz yake mu gana da shi ni na

Chapter 8 of 18