ya koma
da baya tamkar babu wannan rauni a jikinsa.
Da isar Shaharan inda ya baro su Haiman sai ya
iskesu a cikin wani irin mugun hali. Duk
wuraren da wannan Kunama ta sara a jikinsu
har ya rube ya fara tsutsa kuma wajen dada
girma yake yana dada zabtarewa, su duka suna
ihu.
Ya Koda ganin wannan bala'i sai hankalinsa ya
dugunzuma ainun kuma ya cika da tsananin
188
TASKARNOVELS.COM.NG
mamaki bisa yadda aka yi shi nasa raunin bai
rube ba ya kama tsutsa.
Abinda ya fara fado masa a rai shi ne, watakila
saboda ya shiga cikin wannan kogi ne na tudun
tsira shi ya sa nasa raunikan ba su yi tsutsar ba.
Cikin firgici da hanzari ya cicciɓi Zarina da
Shadira ya saɓa su a kafadunsa ya sake
falfalawa da gudu ya nufi inda kogin tudun tsira
yake. Wannan karo shi kansa ya yi matukar
mamaki bisa ganin irin masifaffen gudun da
yake yi don ya ninka wanda ya yi da farko.
Kafin rabin-rabin sa'a ya iso bakin kogin. Da
zuwa sai ya jefa Zarina da Shadira a ciki, suna
fadawa cikin kogin sai raunikan nasu suka daina
tsutsa kuma suka dawo kamar yadda suke da
farko. Koda ganin haka sai farin ciki ya lullube
Shaharan ya juya da sauri ya sake falfalawa da
gudu ya koma can wajen sauran abokan tafiya.
189
TASKARNOVELS.COM.NG
Haka ya rinka dauko su da bibbiyu akan
kafadunsa yana gudu yana kawo su cikin kogin
tudun tsira yana watsa su ciki har ya gama debo
su gabadaya ya zamana cewa saura dokinsa da
Aljani Marhabul Zaurus kadai.
wannan lokaci shi ma dokin Kunamar ta sare shi
a waje biyu kuma raunin ya zama tsutsa har ya
cinye rabin jikinsa, dokin ya baje a kas har ya
fara kokarin mutuwa.
Koda Shaharan ya ga halin da dokinsa ke ciki
kuma ya ga shi ma Aljani Marhabul Zaurus yana
cikin irin wannan hali sai hankalinsa ya
dugunzuma ainun tunda shi ma Marhabul
Zaurus din ba zai iya koda mikewa zaune ba
bare ya dauki dokin ya kai shi can bakin kogin
tudun tsira.
Shaharan ya sunkuya ya cicciɓi dokinsa da
dukkan karfinsa amma sai ya kasa koda raba
dokin da kasa ne saboda nauyinsa. Sai da
190
TASKARNOVELS.COM.NG
Shaharan ya jarraba daukar dokin nasa har sau
uku amma yana kasawa, kawai sai ya zauna a
gefe daya yana kallon dokin yana kuka, sa'adda
dokin ya fara kakarin mutuwa.
Yana ji, kuma yana gani tsutsa ta baibaye
gabadaya jikin dokin, wannan tsutsar ta zamo
sanadin ajalinsa. Nan fa Shaharan ya kurma
uban ihu sannan ya sake fashewa da matsancin
kuka.
Shi kuwa Aljani Marhabul Zaurus lokacin da
azabar tsutsar jikinsa ta addabe shi sai ya fara
ihu yana kuka yana mai cewa, "Ya kai wannan
jarumi ka sani cewa ni ma mutuwa zan yi yanzu,
ina mai yi maka gargadi da ka yi hankali da
Boka Muzaffar domin gaba dayanku yaudararku
yake yi, so yake da zarar kun isa kogon Darul
Iksina ya hallaka ku, ku duka saboda shi kadai
yake son ya mallaki wannan ruwan sihiri da
kuma Aljani Maruful Dauwaz.
191
TASKARNOVELS.COM.NG
Tabbas idan ya mallaki wadannan abubuwa
biyu babu abin da zai gagare shi a cikin wannan
duniya. Ni kaina sai yanzu ne na gane cewa ya
yaudare ni ya cutar da ni.
Tabbas wannan duniya makaranta ce kullum
ana samun kima a cikinta. Ka yi hattara ya kai
Shaharan, lallai ka yi iya kokarinka wajen ceton
rayuwar sauran abokan tafiya. Ni kam tawa ta
kare, sai dai nan gaba ku bayar da labarina idan
kun tsira da rayuwarku!".
Gama fadin hakan ke da wuya sai Aljani
Marhabul Zaurus ya ɓingire kasa ya zama gawa.
Shi kuwa jarumi Shaharan sai ya ci gaba da
matsanaicin kuka sakamakon mutuwar dokinsa.
Bai gushe ba yana wannan kuka har izuwa
tsawon sa'a guda sannan ya mike tsaye ya juya
ya nufi hanyar da za ta kai shi can bakin kogin
tudun tsira. Yana tafe yana waigen dokinsa yana
zub da hawaye har ya daina hango dokin nasa.
192
TASKARNOVELS.COM.NG
Lokacin da Shaharan ya iso bakin kogin tudun
tsira sai ya iske kowa ya dawo cikin haiyacinsa,
ana ta yi wa juna magani a jikin raunika.Tun
daga nesa Zarina ta hango shi sai ta mike tsaye
ta ruga gare shi, suna haduwa suka rungume
juna cikin tsananin farin ciki.
A wannan lokaci Haiman da matarsa Lumaira na
zaune a gefe daya suna ta duba lafiyar junansu
kuma suna murna da ganin junansu a raye.
Shadira Imran da mahaifiyarsa ma suna gefe a
tare. Boka Muzaffar, Sarki Laffaru da Gimbiya
Rahila na zaune a tare su ma suna ta murna da
ganin kansu a raye
Lokacin da Boka Muzaffar ya ga jarumi
Shaharan ya dawo shi kadai babu dokinsa kuma
babu Aljani Marhabul Zaurus sai ya ji a jikinsa
cewa lallai Aljani Marhabul Zaurus da dokin
Shaharan rai ya yi halinsa.
193
TASKARNOVELS.COM.NG
Cikin hanzari Zarina ta janye jikinta daga cikin
na Shaharan ta shiga duba lafiyarsa. Koda tayi
arba da wannan katon rauni da ke kafarsa sai ta
dimauce kuma ta fashe da kuka. Nan take ta
zaunar da shi ta shiga sa masa magani akan
raunin sannan ta je ta nemo tsumma mai tsafta
ta nannade raunin duka ta ɗaure shi.
Gama hakan ke da wuya sai ta kwantar da
Shaharan a kas tana mai dora kansa akan
cinyarta ta shiga tunani mai zurfi. Daga can sai
ta fara rera waka cikin sanyaya kalamai masu
dimauta maza alokacin da hawayenta ke diga
bisa kan fuskar Shaharan. A cikin wakar tana
bayani kamar haka;
"Mazaje sun fadi a yayin da gumu ya kai gumu"
"Ranar wuya ita ce ranar da daci ke yanke zaki"
"Ranar masoya ke rasa masoyansu"
194
TASKARNOVELS.COM.NG
"Daji biyar na masifa yau mazan Kwarai sun
ratsaka mma basu sha da dadi ba"
"Ga ďa da uwa a cikin bala'i, amma ba su iya
tseratar da juna ba"
"Miji da mata sun ga gararin da ba su taɓa" gani
ba. "Jini da jini na hade amma bakin takobi ya
raba su" "Yau fa ga ranar cika buri amma
amfaninta ya gushe tunda babu masoyi" "In ban
da akwai sauran masoya a doron kasa da
mazaje sun zabi mutuwa akan rayuwa!" Lokacin
da Shadira ta fara rera waďannan baitoci sai
jikin kowa ya yi sanyi aka yi ta kuka kamar ba za
a daina ba. Kuma aka yi tsit ana saurarenta har
izuwa dogon lokaci.
Ita kanta sai da ta ji ta gaji da yin wakar sannan
ta yi shiru ta kifa kanta akan kirjin Shaharan har
barci ya sace su su biyun ba su sani ba.
Gaba dayan abokan tafiyar sai da suka yi baccin
wuya, baccin dole saboda tsananin gajiyar da ke
jikinsu. Dayansu bai farfado ba sai bayan sa'a
biyu da rabi.
195
TASKARNOVELS.COM.NG
Mahaifiyar Imran ce ta fara farfadowa tana bude
idonta ta hangi danta Imran da Shadira kwance
a waje daya sai ta ji ta cika da tsananin farin ciki
da ta rayu ta kawo izuwa wannan lokaci da take
daf da warkewa daga cutar da ta addabi
rayuwarta tsawon shekara da shekaru kuma
take daf da ganin auren danta.
Bayan ta jima tana kallon Imran da Shadira tana
ta murmushi sai kuma ta juya ta kalli inda
Haiman da matarsa Lumaira ke kwance, nan
take taji suma ta tayasu farin ciki ainun tunda
suna daf da cika burinsu na warkewar. Lumaira
daga cutar makanta.
Koda ta tuno da yaro Masnur dan uwan Shadira,
Sarki Farisa dan uwan Zarina da kuma dokin
Shaharan ai ta fashe da matsanaicin kuka
saboda ko ba komai ta shaku da su a cikin
wannan doguwar tafiya da aka yi kuma ta
tausayawa masoyansu matuka bisa rashin su da
suka yi.
196
TASKARNOVELS.COM.NG
Sautin kukan mahaifiyar Imran ne ya sa kowa
ya farka daga barci.Koda Imran ya ga
mahaifiyarsa na kuka sai ya mike tsaye zumbur
daga jikin Shadira ya ruga "Ya ke izuwa wajen
mahaifiyar tasa ya durkusa a gabanta suka
rungume juna yana mai cewa, Ummina ina
dalilin wannan kuka naki?"
Ki yi sani cewa yanzu lokaci ne na farin ciki ba
na kuka ba tunda muna daf da cika burin zuciya.
Koda jin wannan batu sai mahaifiyar tasa ta
janye jikinta daga cikin nasa suk fuskanci juna
sosai sannan ta ce, "Ya kai dana ka yi sani cewa
ba komai ne ya sani wannan kuka ba face
tsananin tausayinmu gaba daya nan. Tabbas ko
nan gaba idan ana bayar da labarinmu sai an yi
kuka a duniya kuma labari ne irin wanda baya
shafewa kuma ba za a taɓa mantawa da shi ba.
Ko a iya nan labarinmu ya tsaya mun aje tarihin
abin al'ajabi kuma abin alfahari".
197
TASKARNOVELS.COM.NG
Sa'adda mahaifiyar Imran ta zo nan a jawabinta
sai Imran ya yi ajiyar zuciya ya ce, "Ya ke
Ummina ki yi sani cewa a cikin matafiyan nan
gaba daya ba masu sa'a sama da mu ni da ke.
Duk tsananin masifun da muka hadu da su a
baya ni da ke babu wanda ya rasa wani bangare
na jikinsa, amma sauran abokan tafiya kuwa
daga wanda ya sami manyan raunika a jikinsa
sai wanda ya rasa masoyi da wanda ya rasa
wani бangare na jikinsa.Ina ji a jikina cewa har
mu shiga cikin kogon Darul Iksina babu abin da
zai same mu kuma sai bukatarmu ta biya."
Koda jin wannan batu sai mahaifiyar tasa ta
dube shi cikin firgici ta ce, "Haba ya kai dana kai
kuwa mene ne tabbacinka cewa za mu sami
wannan nasara alhalin har yanzu akwai sauran
tashin hankali a gabanmu na shiga cikin kogon
Darul Iksina?"
Ya yin da Imran yaji wannan batu sai ya yi
murmushi ya ce, "Ba komai ne ya sa nake da
wannan yakinin ba face na san cewa a duniya
babu wata soyayya mai karfi sama da soyayyar
198
TASKARNOVELS.COM.NG
da ke tsakanin da da mahaifi. Ya ke Umkina ki
tuna cewa tun ina cikin cikinki kike dawainiya
da ni kike shan wuya har kika haife ni sannan
kika shiga rainona. Sa'adda na fara zama mutum
kuwa sai ya zamana cewa soyayyarki a gare ni
kullum tana karuwa kuma ya zamana cewa ko
kuda ba kya son ya taɓa dafiyar jikina. Ba zan
taɓa mantawa ba da irin dawainiya da wahalar
da muka sha ta rayuwar talauci, rashin
makwanci da tsananin yunwa gami da yawo
kwararo-kwararo har ta kai mu ga zaman dole a
cikin daji. Na yi imani a zuciyata cewa wannan
wahala da muka sha ba za ta zamo a banza ba,
lallai sai mun ji dadi kafin cikar ajalinmu".
Ya yin da Imran ya zo nan a zancensa sai
mahaifiyarsa ta cika da dumbin farin ciki ta sake
rungume shi a kirjinta tana mai bushewa da
dariyar murna shi ma ya tayata dariyar.
A dai-dai wannan lokaci ne Boka Muzaffar ya
mike tsaye ya dubi gaba dayan abokan tafiyar
daya bayan daya ya ce, "Ya ku 'yan uwana ku yi
sani cewa yau ne muka kawo karshen wuya a
199
TASKARNOVELS.COM.NG
cikin wannan tafiya tamu kuma daga nan zuwa
kogon Darul Iksina tafiya ce ta kwana uku kacal.
Ina mai tabbatar muku da cewa babu wani
mugun abu da za mu sake haduwa da shi akan
hanya har mu isa kogon Darul Iksina amma ku
sani cewa a cikin kogon Darul Iksina akwai
masifu iri-iri har kala dari tara da casa'in da
tara. Gaba dayanku nan babu wanda ya san
yadda za a iya tsallake masifun da ke cikin
wannan kogo face ni saboda haka da zarar mun
shiga cikin kogon ku kasance masu biyayya a
gare ni da bin umarnina. Duk abinda na ce ku yi
kawai ku yi shi cikin gaggawa kada ku yi mini
gardama ko jayayya. Idan kunne ya ji, gangar
jiki ta tsira. Yanzu zamu zauna anan har tsawon
kwana uku domin mu yi jinyar raunikan jikinmu
sannan mu ci gaba da tafiya".
Koda gama wannan jawabi sai Boka Muzaffar ya
koma inda yake ya zauna. Zamansa ke da wuya
sai jarumi Shaharan ya dube shi ya ce, "Ya kai
jagoran wannan tafiya ina da tambaya guda
daya a gare ka. Wai shin me ya sa tun da muka
fara wannan tafiya ba ka ceci rayuwar mutum
daya ba daga cikinmu da karfin sihirinka? Ka
200
TASKARNOVELS.COM.NG
tuna fa cewa ka shafe shekaru masu yawa kana
bincike da hidima akan wannan tafiya tamu, ai
ya ci ace ka san duk irin bala'in da za mu
fuskanta a cikinta ka tanadar mana rigakafinta."
Koda jin wannan batu sai Boka Muzaffar ya
kyalkyale da dariya sannan ya hade fuska kamar
an aiko masa da sakon mutuwa ya ce, "Ya kai
Shaharan ka yi sani cewa babu wani sihirin tsafi
da ya isa ya yi tasiri a cikin wadannan
dazuzzuka biyar da muka ratsa fiye da shekaru
dubu da suka gabata haka wannan al'amari yake
amma idan muka shiga cikin kogon Darul Iksina
kowannenmu sihirin tsafinsa zai iya tasiri".
Koda Boka Muzaffar ya zo nan a zancensa sai
Shaharan ya mike tsaye ya yi 'yar tafiya nesa
kaɗan da inda sauran abokan tafiya suke ya
zauna ya shiga sabon tunani. Abinda ya fara
fado masa a rai shi ne, tunowa da wasiyar da
Aljani Marhabul Zaurus ya yi masa kafin ya
mutu cewar ya yi hankali da Boka Muzaffar
lallai mayaudari ne shi kuma
201
TASKARNOVELS.COM.NG
azzalumi".Shaharan na cikin wannan tunani ne
yaji an dafa kafadarsa ta baya. Cikin firgici ya
waigo da sauri sai ya ga ashe Zarina ce don haka
sai ya yi murmushi a gare ta itama ta maida
masa da martanin murmushin sannan ta zauna
daf da shi suna masu fuskantar inda sauran
abokan tafiya ke kwance, wato can bakin kogin
tundun tsira.
Tsawon 'yan dakiku dayansu bai ce uffan ba
daga can sai Zarina ta yi gyaran murya ta ce, 'Ya
kai masoyina, ka yi sani cewa masu iya magana
sun ce, 'Ruwa baya tsami banza' Tabbas akwai
abinda ke damunka shi ya sa ka baro cikinmu ka
dawo nan ka zauna kana tunani. Idan har son da
kake yi mini na gaskiya ne kada ka ɓoye mini
komai. Ka tuna cewa na rasa dan uwana Sarkin
Farisa yanzu bani da sauran kowa a duniya. Kai
ma ka rasa dokinka wanda da shi ne kaɗai za ka
cika babban burinka na duniya, ba ka da wani
abu da yai saura wanda ya fi ni daraja. Lallai ya
zama wajibi a gare mu mu hada kai mu taimaki
juna tunda muna bukatar junan namu". Sa'adda
Gimbiya Zarina ta zo nan a cikin zancenta sai
jarumi Shaharan ya yi ajiyar zuciya sannan ya
202
TASKARNOVELS.COM.NG
kwashe labarin duk abinda ya faru tsakaninsa
da Aljani Marhabul Zaurus ya zaiyane ma ta.
Koda jin wannan labari sai hankalin Zarina ya
dugunzuma ainun, ta yi shiru tana mai tunani.
Daga can sai ta kawo gwauron numfashi ta ajiye
sannan ta ce, "Hakika Biri ya yi kama da Mutum.
Inda Boka Muzaffar ya kasance adali kuma mai
gaskiya da ya nuna matukar damuwarsa bisa
duk irin abubuwan da suka rinka faruwa a gare
mu mu duka. Ni na rasa dan uwana amma ko
jaje bai yi mini ba. Shadira ta rasa dan uwanta
bai tausaya mata ba. Kai ma ka rasa dokinka bai
ce da kai komai ba. Haiman da kai kun rasa
hannayenku dai dai amma duk bai nuna
tausayinsa ba. Wannan yana yi mana nuni da
cewa Boka Muzaffar bai damu da rayuwarmu ba
alhalin kuma shi ne ya dora mu akan wannan
TAFARKI zuwa kogon Darul Iksina kuma mun
dade muna jiransa akan yin wannan tafiya. Ko
shakka babu Muzaffar yana da wata manufa a
Karkashin zuciyarsa kuma yana da wani buri na
musamman akan shiga cikin kogon Darul Iksina.
203
TASKARNOVELS.COM.NG
Lallai ya yi amfani da mu ne kawai a matsayin
Karukan farautarsa. Ya kai masoyina shawarar
da zan ba mu ita ce duk irin umarmin da Boka
Muzaffar zai ba mu a cikin kogon Darul Iksina
kada mu yi amfani da shi kuma idan da hali mu
hana sauran abokan tafiya aiki da wannan
umarni nasa." Lokacin da Zarina ta zo nan a
zancenta sai Shaharan yai ajiyar zuciya sannan
ya ce, "Ya ke masoyiyata ki yi sani cewa abokan
tafiyarmu sun yarda da Boka Muzaffar dari bisa
dari, koda za mu ba su labarin wasiyyar da
Aljani Marhabul Zaurus ya bayar ba za su
aminta ba. Idan kuma muka sanar da su a yanzu
za su yi mana tawaye, wata kila ma su hada kai
su yake mu. Abin da zai fiye mana alheri shi ne
kawai mu bar wannan al'amari a cikin
zuciyarmu. Wanda duk yake da rabon fitowa a
raye daga cikin kogon Darul Iksina lallai zai fito.
Yanzu ki tashi mu koma can wajen abokan
tafiya domin idan muka ci gaba da hira anan
Boka Muzaffar zai iya zarginmu har ma ya yi
tunanin daukar mataki a kanmu".
Gama fadin hakan ke da wuya sai duk su biyun
suka mike tsaye suka koma can wajen sauran
204
TASKARNOVELS.COM.NG
abokan tafiya. Nan take aka shiga kafa tantuna
gami da shirya abincin da za a ci.
Kamar yadda Boka Muzaffar ya shirya haka
al'amura suka kasance, wato sai da su Shaharan
suka shafe kwana uku cur suna jinyar raunikan
jikinsu a nan bakin kogin tudun tsira sannan
suka kintsa aka kama hanya aka durfafi kogon
Darul Iksina.
Haka dai suka wanzu suna tafiya, ba sa ya da
zango face idan dare ya yi sannan su tsaya a
kafa tantuna a kwanta ayi barci.
Wani abin mamaki da ya faru shi ne, a iya
tsawon kwana ukun da suka yi wannan tafiya ko
maciji ba su kara gani ba akan hanyarsu bare ya
kawo wa dayansu hari.
Da la'asar sakaliya suka iso bakin kogon Darul
Iksina. Kogon na Darul Iksina ya kasance abin
al'ajabi ga dukkan wanda ya yi arba da shi,
domin ya wanzu ne tamkar ginin gida akan wani
205
TASKARNOVELS.COM.NG
dan karamin tsuburi, wanda ruwa ya kewaye
shi kuma ruwan ba shi da zurfi domin komai
gajartar mutum bai fi ya kawo masa iya kaurin
kafarsa ba.
Kogon na Darul Iksina an yi shi ne cikin siffar
gida na ginin jan dutse na Murjani, wanda tun
daga nesa mutum zai ga yana ta kyalkyali da
daukar ido sannan haskensa ya haskake dajin
gaba daya.
Girman gidan ya kai na dan karamin gari yana
da fadi da tsawo sosai domin idan aka fuskance
shi ba a iya hango karshen katangarsa. Idan
mutum ya daga kai ya dubi saman ginin kogon
sai ya ga kamar bashi da karshe kwai dai ya
lmtokare da sararin samaniya ya kule a cikin
gajimare. Ko kadan babu alamar kofa ko taga a
jikin gidan kuma ko ina a mulmule yake a shafe
tamkar wani abu bai taɓa shiga cikinsa ba.
206
TASKARNOVELS.COM.NG
Lokacin da su jarumi Shaharan suka iso daf da
kogon Darul Iksina sai gabadayansu suka ja
suka yi cirko-cirko suna kallon kogon cikin
tsananin al'ajabi. Shi kansa Boka Muzaffar an
batar da tunaninsa domin yadda duk yake
tsammani zai ga kogon ba haka ya gan shi ba.
Bayan sun dan ɓata dakiku masu yawa suna
kallon kogon sai Boka Muzaffar ya wuce kan
gaba ya shiga cikin wannan ruwa ya durfafi
tsuburin da kogon Darul Iksina ke kai ba tare da
fargabar komai ba yana ta kyalkyala dariyar
farin ciki kuma yana yafito sauran abokan tafiya
da hannu.
Koda ganin haka sai Haiman ya bi bayansa yana
goye da matarsa Lumaira, sannan Imran dauke
da mahaifiyarsa, Shadira na binsu daf da daf
Shaharan da Zarina na biye sannan Gimbiya
Rahila, Sarki Laffaru ne na karshe.
207
TASKARNOVELS.COM.NG
Kamar yadda Shaharan da Zarina ke da shakku
akan Boka Muzaffar, haka Sarki Laffaru ya
kasance domin shi ma ya lura da take-takensa
tun daga farkon tafiyar tasu har izuwa sa'adda
suka iso bakin tekun tudun tsira don haka sai ya
aiyana a ransa cewa duk irin umarnin da Boka
Muzaffar ya bayar a cikin kogon Darul Iksina ba
zai yi aiki da shi ba koda kuwa zai rasa
rayuwarsa.
Bayan kowa ya haye wannan ruwan sai aka hau
kan tsuburin aka iso daf da kogon Darul Iksina
aka tsaya aka yi cirko-cirko kowa ya zubawa
Boka Muzaffar idanu.
Yayin da Muzaffar ya ga shi kaɗai ake sauraro
sai farin ciki ya lulluɓe shi nan take ya shiga yi
wa kansa kirari yana mai cewa;
"Ni ne Bokan zamani wanda ya gagari dukkan
Bokaye.
208
TASKARNOVELS.COM.NG
Ni ne murucin kan dutse ban fito ba sai da na
shirya.
Ina matsafa da jaruman duniya, yau ga Bokan
farko da zai zamo sanadin da za a shiga kogon
Darul Iksina.
Na bata hankali Dare na sami suna da daukaka,
kuma na samu.
In banda Aljani Maruful Dauwaz babu wanda zai
riga ni shiga kogon Darul Iksina, lallai na bar wa
duniya abin tarihi.
Ko yanzu na mutu na kasaita kuma na gawurta,
lallai duniya ba za ta manta da ni ba." (OH ni
Maiboko! Ka ji ďan egiya mayaudari macuci)
Gama fadin hakan ke da wuya sai Muzaffar ya
fiddo wata 'yar karamar wuka daga jikinsa ya
209
TASKARNOVELS.COM.NG
kama suturar jikinsa dai-dai ciayarsa ya kwaye
ta, sai ga wadansu dalasiman tsafi rubuce akan
ciyar
Nan take ya fara karanto dalasiman tsafin cikin
daga murya. Faruwar hakan ke da wuya sai
wata irin iska mai karfi ta fara kadawa tana
zagaye gaba dayan kogon na Darul Iksina, gaba
daya yanayin sararin samaniya ya sauya daga
fari fat ya koma kore shatar.
Al'amarin da ya firgita gaba dayan abokan
tafiyar ke nan, dukkaninsu suka ji tsigar jikinsu
ta tashi, kuma tsoro ya baibaye su.
Boka Muzaffar na gama karanto wadannan
dalasiman tsafi sai wannan iska ta dauke dif,
yanayin sararin samaniyar ya dawo dai-dai
yadda yake a da.
210
TASKARNOVELS.COM.NG
Ba zato ba tsammani sai suka ga wata katuwar
kofa ta bakin mulmulallen karfe ta baiyana akan
ginin kogon Darul Iksina, sannan sai suka ji
karar zare sakatu a jikin kofar har guda casa'in
da tara. Daya bayan daya sakatun suka rinka
zare kansu. Ta casa'in da taran na gama fita sai
kofa ta bude wanwar.
Koda suka yi arba da cikin kogon sai gaba
dayansu suka cika da tsananin al'ajabi. Ba komai
ne ya haddasa hakan ba face ganin abin da ke
cikin kogon.
Wadansu gidaje ne kala-kala a cikin kogon har
guda bakwai. Kowanne gida guda daya ya kai
girman unguwa guda, kuma dukkan gidajen
anginasu ne daga dangin su Zinare, Lu'u-lu'u,
Jauhar, Murjani da sauransu. Duk wanda ka
kalla sai ka ga kamar ya fi wanda ke kusa da shi
kyau da ginuwa
211
TASKARNOVELS.COM.NG
Ba tare da fargabar komai ba Boka Muzaffar ya
kuna kai izuwa cikin kogon suma sauran abokan
tafiyar sai suka bivshi da sauri duu! Da yake
Sarki Laffaru ne na karshe yana shiga sai kofar
gidan ta rufe kanta wadansu sakatu guda casa'in
da tara suka mayar da kansu cikin ramukansu,
sanann kofar ta sake rufe kanta.
Faruwar hakan ke da wuya sai Boka Muzaffar ya
bushe da dariyar mugunta. Lokaci guda kuma ya
hade rai ya ce, "Ni ne kadai zan iya sake bude
muku kofar wannan gida ku fito in ba haka ba
kuwa sai dai ku mutu a cikinsa".
Gama fadin hakan ke da wuya sai Boka Muzaffar
ya sanya hannunsa a cikin aljihunsa ya fiddo
wata 'yar karamar jemammiyar fata. Babu.
komai a jikin fatar face taswirar gidajen da ke
cikin wannan kogo gaba dayansu guda casa'in
da taran. A jikin kowanne gida akwai rubutun
wadansu kalmomin tsafi.
212
TASKARNOVELS.COM.NG
Nan take Boka Muzaffar ya ajiye wannan
jemammiyar fata a kasa, gaba dayan abokan
tafiyar suka kewaye ta suna kallonta cikin
mamaki.
Muzaffar dube su daya bayan daya ya ce, Shin a
cikinku akwai wanda zai iya karanta mini kalma
daya daga cikin kalmomin da aka rubuta a jikin
wannan fata?"
Koda jin wannan tambaya sai kowa ya duruduru aka rasa wanda zai ce kala. Da ganin haka
sai Boka Muzaffar ya sake bushewa da dariya
sannan ya ci gaba da kuri yana mai cewa, "Ku
duka a yanzu rayukanku a hannuna suke.
Wanda duk ya bi umarnina zai kuɓuta ya sami
cikar burinsa. Wanda kuma duk ya bijire mini
kuwa zai hallaka anan cikin kogon Darul Iksina.
Koda gama fadin hakan sai Boka Muzaffar ya
Kurawa wannan fata idanu sannan ya dago kai
ya dubi Haiman da Imran ya ce, "Ku je ku bude
213
TASKARNOVELS.COM.NG
kofar wancan gida na uku ku shiga cikinsa kai
tsaye. Lallai a cikinsa ne za ku riski ruwan
albarka da za ku yiwa masoyanku magani da shi
su warke".
Ba tare da gardamar komai ba kuwa Haiman da
ke goye da matarsa Lumaira ya nufi kofar
wannan gida. Imran goye da mahaifiyarsa ya
mara masa baya.
Nan take suka bude kofar wannan gida na uku
suka kunna kai ciki. Suna shiga sai kofar gidan
ta rufe kanta. (Allah wadaran mai hali irin na
boka Muzaffar)
Daga nan sai Boka Muzaffar ya dubi Zarina da
Shadira ya ce, "Ku kuma kun rasa masoyanku
don haka ba ku da sauran bukatar ruwan
albarka. Kai ma jarumi Shaharan baka da
bukatar wannan ruwa, saboda haka ka bi Zarina
da Shadira ku shiga cikin gida na biyu. Duk abin
da kuke so na duniya wanda ya dunganci dukiya
214
TASKARNOVELS.COM.NG
za ku samu a cikin wannan gida, ku shiga ku
debo iya muradinku akwai hadiman da za su yi
muku dako har izuwa kasashenku."
Koda jin wannan batu sai Shadira ta nufi
wannan gida na biyu, amma sai Shaharan da
Zarina suka toge. Al'amarin da ya matukar bai
wa Boka Muzaffar mamaki ke nan ya dube su ya
ce, 'Me kuka tsaya jira? Ko kuwa kuna so ku
bijirewa umarnina ne?"
Sa'adda Shaharan ya ji wannan tambaya daga
bakin Boka Muzaffar sai ya yi murmushi ya ce,
"Ya kai wannan Boka ka yi sani cewa ni yanzu
tsakanina da kai babu sauran yarda da amana,
saboda jikina ya ba ni cewa so kake ka yaudare
mu ka cutar da mu. Ina tabbatar maka da cewa
duk inda ka shiga ni ma nan zan shiga tunda na
san cewa ba za ka kai kanka inda za ka hallaka
ba".
215
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda jin wannan batu sai Boka Muzaffar ya
bushe da dariya ya ce, "Tabbas ka yi dabara ya
kai wannan jarumi, b." amma ka kama hanyar
da ba za bulle ba
Boka Muzaffar ya dubi Sarki Laffaru ya ce, ya kai
abokina, maza ka ruga izuwa cikin daki na hudu
domin anan ne za ka sadu da Aljani Maruful
Dauwaz wanda zai cika maka burin rayuwarka.
Sarki Laffaru ya toge ya ce, "Kai ba zai yiwu ba.
Haba abokina! Ai ilimin tsafi ka fi ni amma ba
wayo ba ko sanin tuggun duniya. Ina tabbatar
maka da cewa kafarka-kafata. Duk inda ka shiga
nan zan shiga. Idan har ma gaskiya ne cewar zan
sadu da Aljani Maruful Dauwaz a cikin gida na
hudu ta ya ya zan iya sarrafa shi ya aminta da ni
har ya biya mini bukatata?"
Koda jin wannan tambaya sai Boka Muzaffar ya
ce, "Ai ga Gimbiya Rahila nan amfanin tahowa
da ita kenan a cikin wannan tafiya muddin
Aljani Maruful Dauwaz zai yi arba da ita duk
abin da kake so zai yi muku tunda kamanninta
216
TASKARNOVELS.COM.NG
iri daya ne sak da na masoyiyarsa wadda ya
rasa."
Kafin Muzaffar ya gama rufe brakinsa tuni
Gimbiya Rahila ta tari numfashinsa ta ce, "Kai!
dakata tsohon banza! Mayaudari, ai kama da
wane ba ta wane. Ni mutum ce, masoyiyar Aljani
Mauruful Dauwaz kuwa aljana ce, kuma ta
mutu. Wanda duk ya mutu ba zai dawo ba,
Mauruful Dauwaz ya san da haka. Abin da na ke
so da kai kawai ka kai mu inda Maruful Dauwaz
yake mu gana da shi ni na
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 18