Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tashi domin su tafi izuwa can fadar Sarki Nashmir. Bayan kowa ya gama kimtsawa sai sadauki Najwar ya dubi Aljani Barukul Masnur ya ce, "Ina mai gargadinka da kada ka kuskura ka kaucewa umarnina ko kuma ka ce za ka tona mini asiri saboda ka ga yanzu za mu koma fada kana shakkar Sarki, Idan har kunne ya ji to gangar jiki ta tsira". Koda gama fadin haka sai Najwar ya dubi Aljani Maruful Dauwaz ya ce, "Idan muna son mu sami 365 TASKARNOVELS.COM.NG nasarar rushe mulkin maigidana mu kawar da shi, dole ne mu yi abu uku. Abu na farko yanzu zan kama ku na daure ku na kai ku wajensa a matsayin fursunoni. Na san ba zai yi gaggawar hallaka ku ba sai dai ya sa a kulle ku a kurkuku. Mataki na biyu na shi ne, zan shiga tunanin dabarar da zan yi na sace Gimbiya Ramlatul Siyam daga turakarta a sirrance ko a dabarance sannan na shirya matakan hallaka Dakarun tsaro na fadar, yadda idan aka fara yakin za mu sami nasarar kawar da su duka a cikin kankanin lokaci. Shi kuwa Sarki Nashmir ni ne zan tare shi mu fafata in ya so muna cikin gumuzun sai ku kawo mini dauki mu hada KARFI DA KARFE mu hallaka shi. Da zarar sauran Dakarun nasa sun ga mun ballaka shi dole ne su yi mubaya'a a gare mu su dawo karkashin ikonmu." Sa'adda sadauki Najwar ya zo nan a zancensa sai Aljani Maruful Dauwaz ya dube shi ya ce, "Ya kai wannan sadaukin sadaukai, mun ji duk bayaninka kuma mun gamsu da shi, amma 366 TASKARNOVELS.COM.NG muna son mu gana a tsakaninmu idan akwai wani korafi sai mu sanar da kai". Koda jin haka sai sadauki Najwar yai murmushi ya ce, 'Ai babu komai ina sauraronku." Nan take Maruful Dauwaz, Rahila da Sarki Laffaru suka koma gefe daya suka fara tattaunawa Inda Aljani Maruful Dauwaz ya dubes u ya ce, "To kun ji abin da wannan sadaukin jarumi ya zo mana da shi, anya kuwa ba kwa tunanin cewa akwai. yaudara a cikin al'amarin? Ku tuna fa cewa shi ne Sarkin yakin Sarki Nashmir tsawon shekaru, ta yaya kuke tsammanin cewa zai bijire wa Sarkinsa a yanzu?" 367 TASKARNOVELS.COM.NG Koda jin wannan batu sai Rahila da Sarki Laffaru suka yi shiru kamar ba za su ce komai ba, kuma hankalinsu ya kara dugunzuma. Daga can sai Rahila ta yi ajiyar zuciya sannan ta dubi Maruful Dauwaz ta ce, "Ai yanzu ba mu da wata huija da za mu ce ba za mu yard jarumi Najwar ba tunda inda ya so hallaka mu da tuni ya kawar da mu. Tunda har ya kyale mu lallai akwai kamshin gaskiya a cikin zantukansa, sai dai ina shakku akan batun Gimbiya Ramlatul Siyam da ya ce shi zai san hikimar da zai yi ya sace ta. Ina ji a jikina cewar yana da wani shiri na musamman akan Gimbiya Ramlatul Siyam don haka dole ne mu sa ido a kansa. Tabbas yanzu ba mu da wani zaбi wanda fi ya mu bi umarninsa tunda ya fi mu sanin dukkan sirrin fadar Sarki Nashmir kuma masu iya 368 TASKARNOVELS.COM.NG magana sun ce, 'Da dan gari akan ci gari', ko kuwa a cikinku akwai mai wata sharar daba?" Da jin haka sai Rahila da Laffaru suka dubi juna sannan suka yi shiru. Rahila ta ce, "Ba mu da wata shawara wacce ta fi kawai mu yi kundunbala mu bi umarnin sadauki Najwar tunda al'amarin ya zama lalube a çikin duhu, ba a san inda za a dace ba." Nan take Maruful Dauwaz ya matsa gaban sadauki Najwar ya ce, "Mun amince da dukkan umarninka sai mu tafi kawai". Koda jin haka sai Najwar ya bushe da dariyar farin ciki. Nan take yai nuni da hannunsa izuwa ga Maruful Dauwaz, Rahila da Sarki Laffaru sai wata murtukekiyar sarkar tsafi ta kanannaɗe su su duka ta ɗaure su tamau amma wannan karon babu wuta a jikin sarkar. 369 TASKARNOVELS.COM.NG Sadauki Najwar ya dubi Aljani Barukul Masnur ya ce, "Maza ka dauki su Maruful Dauwaz ka dora su a gadon bayanka sannan mu juya mu koma izuwa Birnin Hindu". Nan take kuwa Barukul Masnur ya cika wannan umarni. Shi ma Najwar sai ya hau kan Barukul Masnur ya zauna. Nan take Barukul Masnur ya bude fuka-fukansa ya tashi sama ya kama tsala azababben gudu yana mai tunkarar Birnin Hindu. Hakika inda ace mutum na nan a lokacin da Aljani Barukul Masnur ya dauki su Aljani Maruful Dauwaz ya tashi da su sama dole ne ya cika da tsananin mamaki ya sallamawa Ubangiji bisa wannan iko nasa, saboda shi kansa Maruful Dauwaz girman halittar jikinsa ta isa abin al'ajabi domin in daga nesa mutum ya hange shi zai yi zaton ko tsauni ne amma sai ga shi Aljani Barukul Masnur ya ninka shi girma sau uku. 370 TASKARNOVELS.COM.NG Tabbas! Babu wanda ya san iyakar balittun ke wannan duniya face Allah. Hakika shi ne abin tsoro, wanda ya zamo mafi cancanta a bauta masa tunda shi ne Ya halicci kowa da komai. Tafiyar rabin sa'a kacal Aljani Barukul Masnur ya yı ya iso fadar Sarki Nashmir. Koda isowarsa bakin kofar shiga gidan sarautar sai ya tsaya cak sakamakon ganin masu gadin kofar sun ki bude musu kofar su shiga. Koda ganin haka sai sadauki Najwar ya dubi masu gadin ya daka musu tsawa ya ce, "Me kuke jira ne ba ku bude mana kofar mun shiga ba ko kuwa ba ku shaida mu ba ne?" Da jin wannan tambaya sai shugaban masu gadin kofar ya dubi sadauki Najwar cikin girmamawa ya risina ya ce, 'Ya shugabana ka yi hakuri muna kan umarnin Sarki ne domin da zai fita bai gaya mana cewa za ku dawo tare da fursunoni ba kuma ka san dokar gidan nan babu 371 TASKARNOVELS.COM.NG wani bako da aka yarjewa shiga face da izinin Sarki". Sa'adda sadauki Najwar ya ji cewar Sarki baya nan ya fita sai ya cika da tsananin mamaki gami da tsananin farin ciki saboda sanin cewa ya sami babbar dama da zai iya cika burinsa a saukake, amma duk da haka dole ne ya bi al'amarin a sannu. Najwar ya dubi shugaban masu gadin kofar ya sake daka masa tsawa a karo na biyu ya ce, "Shin zan aikata wani abu ne daban ba tare da izinin Sarki ba? Maza ka sa a bude mana kofa kada fishin Sarki ya tabbata akanku idan ya dawo". Koda jin haka sai shugaban masu gadin ya sunkui da kansa kas yai shiru kuma ya ki ya bayar da umarnin a bude kofar saboda ya fada cikin wasi-wasi da fargaba. 372 TASKARNOVELS.COM.NG Koda ganin haka sai sadauki Najwar ya fusata ainun ya zare takobinsa ya dubi shugaban masu gadin kofar ya ce, "Maza ka bayar da umarnin a bude mana kofa ko yanzun nan na zare maka ruhin numfashinka da dukkan jama'ar taka". Koda jin haka sai jikin shugaban masu gadin ya kama kyarma, ba shiri ya dubi yaran nasa ya daka musu tsawa ya ce su yi maza su bude kofar! Nan take kuwa masu gadin suka fara kokarin bude kofar. Ita dai wannan kofa ta shiga fadar Sarki Nashmir tsawonta ya kai kamu dubu uku, haka ma fadinta. Idan aka fara bude ta sai an shafe sa'a uku ana janye ta daga sama tana shigewa cikin karkashin kasa. Wata murtukekiyar sarkar karfe ce guda biyu a jikin kofar a dama da hagunta. Kowacce sarka guda akwai aljanu dubu goma wadanda ke rike da ita. Idan za a bude kofar 373 TASKARNOVELS.COM.NG aljanun da ke dama ne suke jan wannan sarka har sai sun shafe sa'a uku suna janta sannan za ta gama budewa ta kule a cikin kasa. Haka kuma idan za a rufe kofar aljanu dubu goma da ke hagu ne za su yi ta jan sarkar har tsawon sa'a ukun sannan kofar take rufewa ta tokare da saman ginin fadar. Kaurin wannan kofa ya kai kamu dari uku, huma an yi ta ne da zallan karfen lu'u-lu'u, babu wani makami da zai iya yiwa kofar lahani komai kkarfinsa, tsininsa da nauyinsa. Sai da su Najwar suka yi jira har tsawon sa'a uku sannan kofar ta gama budewa suka kunna kai izuwa cikin gidan sarautar. Da shigarsu sai Aljani Maruful Dauwaz da Rahila da Sarki Laffaru suka cika da tsananin mamaki sakamakon ganin tsananin girman gidan da 374 TASKARNOVELS.COM.NG kuma irin gine-ginen da ke cikinsa da kayan kawar da aka shirya tamkar aljannar duniya. Babu abin ma da ya fi ba su mamaki face ganin yadda Aljani Baruk! Masnur ya yi ta tafiya a cikin gidan sarautar, bai iso inda aka gina kurkukun gidan ba sai da ya shafe tafiya mai nisan gaske Wacce suka yi a baya tun daga dajin Hizurul Aswad. Nan take Aljani Barukul Masnur ya sauko kasa ta dira a bakin kofar kurkukun. Dirarsa ke da wuya sai sadauki Najwar Ya dubi masu gadin kurkukun ya ce, "Ga fursunonin Sarki ku shigar da su ciki a kulle su har sai na dawo karbarsu" Nan take Wadansu jibga-jibgan aljanu wadanda sun ninka Aljani Barukul Masnur sau biyu a girma da Kwarjini suka kama su Maruful Dauwaz tamkar Shaho ya kama Dan tsako suka 375 TASKARNOVELS.COM.NG shige da su izuwa cikin kurkukun aka yi ta tafiya da su har sai da aka yi doguwar tafiya ana wuce mugayen matakan tsaro, sannan aka jefa su a cikin wani daki aka kulle su. Babu abin da ya firgit su Aljani Maruful Dauwa face ganin tsananin tsaron kurkukun da kuma irin yanayin ginin da aka yi shi, komai jarumtakar mahaluki da Karfin sihirinsa bai isa ya iya guduwa daga cikin wannan kurkukun ba. Koda suka garkame su Aljani Maruful Dauwaz a cikin wani kuntataccen ďaki sai hankalinsu ya dugunzuma domin ji suka yi kamar an jefa su a cikin rijiya gaba dubu an rufe muffin rijiyar. Cikin tsananin takaici da nadama Rahila ta dubi Aljani Maruful Dauwaz ta ce, hakika mun yi babban kuskure da muka yarda da sadauki Najwar. Abin da na fahimta yanzu shi ne, Sadauki Najwar ba ya son ya kashe mu so yake a kawo mu gare shi a raye, wata kila don ya 376 TASKARNOVELS.COM.NG ďanďana mana muguwar azaba ne kafin ya hallaka mu. ya Koda jin wannan batu sai cikin Sarki Laffaru duri ruwa ba, ya firgita ainun bai san sa'adda ya saki fitsari a wando ba. Al'amarin da ya sa Aljani Maruful Dauwaz ya tuntsure da dariya ke nan, sannan ya daka wa Laffaru tsawa ya ce, "Kai tsohon azzalumin Sarki, shin ka manta ne da irin bakin mulkin da ka yi wa mutane a baya? Ai bai kamata a ce ka zamo matsoraci mai gudun azaba tunda babu irin kalar azabar da ba ka sa an yi wa mutane ba. Hakika a da can kai Kura ne, amma yanzu wannan Kurar ta zama Akuya. Abin da nake so da kai shi ne ka kwantar da hankali ka. Ka sani cewa mai rai ba ya kasa motsi. Na yi muku alkawari ba za mu tozarta ba a cikin wannan kurkuku, ta kowanne hali sai na ceci rayuwarmu na fitar da mu". 377 TASKARNOVELS.COM.NG Sa'adda Rahila da Sarki Laffaru suka ji wannan batu sai suka cika da tsananin mamaki. Rahila ta dubi Maruful Dauwaz ta ce, Kai kuwa ta yaya za ka iya fitar da mu daga cikin wannan mugun kurkuku mai tsananin tsaro haka?" Da jin wannan tambaya sai Maruful Dauwaz yai murmushi ya ce, Ku zuba ido kawai ku sha kallo, nii ne fa jarumi mai sa'a da rabo wanda komai RINTSI DA TSANANI sai ya fita daga cikin kowanne bala'i. Idan kuka yi la'akari da abubuwan da suka faru a gare mu a baya za ku gane cewa sa'ata ita ce ta kai mu ga kawowa i yanzu. Wannan shi ne abin da ya faru ga su Aljani Maruful Dauwaz bayan an kawo su fadar Sarki Nashmir a matsayin fursunoni. 378 TASKARNOVELS.COM.NG Al'amarin su sadauki Najwar kuwa, lokacin da ya ga an shigar da su Aljani Maruful Dauwaz cikin kurkuku an je an kulle su sai ya tafi cikin tsananin farin ciki bisa ganin cewa duk abubuwan da ya tsara don cika burin rayuwarsa suna tafiya daidai. Babu abin ma da ya kara karfafa masa guiwa face da ya zo ya tarar da cewa Sarki Nashmir ba ya nan. Abin da ya fado masa a rai shi ne, dole ne yanzu ya je ya yi bincike domin ya gano inda sakri Nashmir ya tafi da kuma lokacin da zai dawo domin ya yi sauri ya gama kammala dukkan shirye- shiryensa kafin Sarki Nashmir ya dawo. Kai tsaye sadauki Najwar ya wuce izuwa gidansa wanda ke can ɓangare daya a cikin gidan sarautar. Cikin tsananin farin ciki ya shiga gidan ya wuce izuwa dakin halwar tsafinsa ya dukufa. Nan take ya ga abin da ya matukar girgiza masa hankali ya ga cewa ashe ma idan ya cika burinsa a yau din ma tsugune ba ta kare ba, akwai gagarumar masifa a gabansa. 379 TASKARNOVELS.COM.NG Ba wani abu sadauki Najwar ya gani ba a cikin madubin tsafinsa face rincaɓewar masifaffen yaki tsakanin Boka Muzaffar, Sarki Nashmir da Sharlis a can gidan Boka Muzaffar da ke Birnin Kufa a dokar daji. Su ukun suna yakar juna ne akan abu daya. Ba wani abu bane face MASHIN GALILUL HARAS. Mashin na jingine a cikin dakin tsafin Boka Muzaffar amma an rasa wanda zai sami nasarar daukar mashin a tsakaninsu su ukun domin sun wanzu a cikin kai wa junansu sara da suka cikin bakin zafin nama, juriya da jarumtaka ta gaban kwatance kuma kowannensu yana amfani ne da dukkan karfin dantsensa da karfin tsafinsa. Duk sa'adda takubbansu suka hadu sai dai ka ji tartsatsin wuta na tashi gami da hayaki. 380 TASKARNOVELS.COM.NG Duk wanda aka sari jikinsa kuwa sai ka ji kamar karfe aka sara, makamin bay a tasiri haka uma babu wanda yake da alamar gajiyawa a cikin yakin alhalin kwanansu goma sha hudu ke nan suna wannan masifaffen yaki a waje ďaya har ta kai cewa sun rugurguza gaba dayan ginin gidan na Boka Muzaffar tamkar ginin bai taɓa wanzuwa ba Komai dake cikin gidan ya kone ya zama toka, Mashin Galilul Haras ne kadai ko kwarzanewa bai yi ba. Sadauki Najwar ya ci gaba da bincike domin ya gano wanda zai sami nasarar daukar mashin na Galilul Haras a tsakanin matsafan uku, amma sai abu ya gagara. Ya sake yin bincike akan sa'adda yakin nasu zai zo karshe amma abu dai ya gagara. Al'amarin da ya dugunzuma hankalin sadauki Najwar ke nan ainun fiye da ko yaushe ya fusata har ya maka madubin tsafin nasa a kas ya tarwatse. 381 TASKARNOVELS.COM.NG Nan fa ya zauna ya yi tagumi yana tunanin abin da ya kamata ya yi. Sai da ya daɗe a zaune cikin wannan hali sannan ya yanke shawarar cewa duk yadda zai yi dole ne a cikin wannan dare ya mallaki Gimbiya Ramlatul Siyam kuma ya mallaki karagar mulkin Sarki Nashmir. Ko a yau din ne kadai ya sadu da Gimbiya Ramlatul Siyam kuma ya zauna akan karagar mulki ai ya gama cika burinsa na duniya bai ki ba ma Ajalinsa ya riske shi tun da ya yi abin da babu wani mahaluki da ya isa ya yi shi a doron kasa. Ko ba komai ba zai yi mutuwar banza ba wacce za a manta da shi. Dole ne a rinka tunawa da shi a cikin tarihin MAZAN JIYA wadanda suka yi gagarumar bajintar da ba za a taɓa mantawa ba. Koda sadauki Najwar ya gama aiyana hakan sai ya mike zumbur! ya fita daga cikin gidansa, bai 382 TASKARNOVELS.COM.NG zame a ko ina ba sai inda Aljani Barukul Masnur yake a cikin gidan sarautar. Irin su Aljani Barukul Masnur sun kai su miliyan daya da rabi a cikin Dakarun da ke tsaron fadar Sarki Nashmir kuma dukkaninsu sun fito ne da ga wata zuri'a ta aljanu a Birnin Hindu. Tunda zuri'ar tasu ta wanzu a doron kasa, suka kasance bayi, ba su taɓa samun 'yancin kansu ba a wajen 'yan uwansu ajlanu da manyan Bokayen duniya na jinsin Bil'adama. Wani babban abin takaici a gare su shi ne, sun kasance 'yan tsiraru a cikin al'ummar aljanu na Birnin Hindu, kuma an kafa musu karan-tsana, shi ya sa ake karar da dukkan rayuwarsu a cikin bauta. Iyaye da Kakanninsu da wannan bakin ciki suka tsufa suka mutu, domin sun san cewa har abada 383 TASKARNOVELS.COM.NG ba za su iya yin tawaye ba don su kwaci 'yancin kansu. Lokacin da sadauki Najwar ya riski Aljani Barukul Masnur sai ya ja shi izuwa cikin wani daki suka kadaita a inda babu wanda zai ji abin da za su tattauna. Najwar ya dubi Barukul Masnur ya ce, "Na ji dadi da ka rufa mini asiri ba ka gayawa kowa sirrina ba, bisa wannan dalili yanzu zan yi wa zuri'arku gabadayanta gatan da ba a taɓa yi muku ba. Ka sani cewa a cikin shekara guda sau daya jal ake ba ku hutun aikin bauta. To ni yanzu na ba ku hutu na tsawon wata uku, kuma a yau na shirya muku walima ta musamman a cikin fadar maigirma sarki Nashmir". Koda jin wannan batu sai idanun Barukul Masnur suka zazzaro ya cika da tsananin tsoro ya ce, "Haba ya shugabana, ai idan ka yi haka Sarki ya dawo sai ya sa a hallaka mu gaba 384 TASKARNOVELS.COM.NG dayanmu. Kai kanka ba za ka tsira ba daga sharrinsa". Koda jin wannan batu sai Najwar ya bushe da dariya ya ce, "Ka san dai idan Sarki ba ya nan babu mai ba da umarni a gidan nan sai ni ko ba haka ba ne?" Barukul Masnur ya ce, Haka yake". Najwar ya ce, Maza ka je ka sami ragowar yan uwanka su duka ka gaya musu cewa ina nemansu yanzuyanzu a fada. Koda gama fadin hakan sai Najwar ya 6ace fat. Bai baiyana a ko ina ba sai a fadar Sarki Nashmir inda karagar mulki take. Baiyanarsa ke da wuya ya bai wa Barori da Kuyangi umarnin su je su kawo abinci da abin sha iri-iri wanda za a yi walima da shi. Nan take kuwa Barorin da kuyangin suka cika wannan umarni cikin 'yan dakiku kadan. Faruwar hakan ke da wuya sai ga gabadayan 385 TASKARNOVELS.COM.NG zuri'ar su Aljani Barukul Masnur sun baiyan a fadar. Al'amarin da ya matuka bai wa gabadayan Dakarun tsaro na gidan maraki ke nan, domin hakan ba ta taɓa faruwa ba tunda Sarki Nashmir ya hau karagar mulki. Bayan zuri'ar su Aljani Barukul Masnur sun gama hallara gaba dayansu kimanin su miliyan daya da rabi sai sadauki Najwar ya daka tsawa ga sauran Dakaru, barori da bayi da ke cikin fadar ya ce kowa ya fita ya bar su da zuri'ar su Barukul Masnur. Nan take kuwa aka bi wannan umarni. Bayan kowa ya gama fita ne sai Najwar ya sa aka kulle dukkan kofofi da tagogin fadar don kada ma wani ma ya ji abin da za su tattauna. 386 TASKARNOVELS.COM.NG Ba tare da 6ata wani lokaci ba Najwar ya bai wa su Aljani Barukul Masnur umarni suka fara walima. Saboda tsananin fari ciki da mamaki ba su san sa'adda suka kama bushasha ba har ma wasu suka rinka kade-kade da raye-raye, wasu ma suka yi ta shan ruwan barasa kai ka ce a cikin gidajensu suke ba a fadar mai girma Sarki Nashmir ba. Shi kansa Najwar sai ya shagala ya yi ta rawa a cikinsu yana nishadi. Bayan kowa ya ci ya gyatse sai sadauki Najwar ya tafi kai tsaye izuwa kan karagar Sarki Nashmir ya zauna akanta ya harde kafafuwansa. Koda ganin haka sai gaba dayan aljanun suka firgice suka kama kuka suna rokon Najwar da ya ba su umarnin su fice daga fadar don kada Sarki Nashmir ya dawo a yanzu ya ga abin da ke faruwa ya sa a hallaka su su duka. 387 TASKARNOVELS.COM.NG Koda jin wannan batu sai Najwar ya bushe da dariya, lokaci guda kuma ya murtuke fuska ya ce, 'Ya ku wannan zuri'a ta aljanu da ba su da gata a wannan kasa tamu, shin kun yi imani cewa ni ne Wazirin Sarki Nashmir?" Su duka suka amsa da "Na'am". Najwar ya cigaba da bayani yana cewa. "Fiye da shekaru dubu arba'in ba ku taɓa samun 'yancin kanku ba, Iyayenku da Kakanninku duk a cikin kangin bauta suka mutu. Yau ni Najwar zan kwato muku 'yancinku. Koda jin haka sai gabadayan aljanun suka rude da shewa cikin tsananin murna har sai da Najwar ya daga hannunsa sama sannan suka yi tsit tamar mutuwa ta gifta. Najwar ya ci gaba da cewa, "Ku sani cewa da kadan Sarki Nashmir ya fi ni jarumtaka da karfin shirin tsafi. To ni ma na gaji da yi masa bauta babu ci gaba. Yau ne ranar da na sami damar da zan yi masa tawaye, amma sai idan kun ba ni hadin kai sannan ni da ku za mu samu 'yancinmu. 388 TASKARNOVELS.COM.NG Ina tabbatar muku da cewa Sarki Nashmir ya tafi wani gagarumin yaki shi kadai yakin da ba zai taba tsira da rayuwarsa ba. Yanzu zan nuna muku zahiri ku gani da idanunku". Koda gama fadin hakan sai ya yi nuni da hannunsa izuwa ga jikin bangon fadar. Nan take suka ga taswirar hoton gumurzun da ake yi tsakanin Sarki Nashmir da su Boka Muzaffar. Al'amarin da ya matukar ba su mamaki ke nan. Najwar ya sake nuna bangon da hannunsa hoton komai ya dauke sannan ya ce, na yi bincike a cikin tsafina na gano cewa za a kashe Sarki a wannan yaki, saboda haka a daren yau ina son ku ba ni hadin kai mu yi juyin mulki cikin shammace domin idan muka bari har dakakarun gidan nan suka san cewa Sarki mutuwa zai yi, to kuwa za su dora 'yarsa ne akan karagarsa. Idan kuwa hakan ta faru 'yancinku da nake son na karɓo muku ya suбuce ke nan har abada, domin da zarar Ramlatul 389 TASKARNOVELS.COM.NG Siyam ta zauna akan karagar mulki za ta sami dukkan karfin sihirin tsafi irin na mahaifinta, kun ga kenan ba zan taɓa iya yi mata juyin mulki ba. Lallai da zafi-zafi akan bugi karfe, idan kuwa aka bari ya huce shi ke nan ba zai lankwasu ba. Sa'adda Najwar ya zo na nan a jawabinsa sai gaba dayan aljanun suka rude da shewa suna masu cewa sun ba shi hadin kai dari bisa dari. Nan take farin ciki ya lulluɓe Najwar ya sallame su akan cewa, da zarar dare ya raba su dawo nan fadar yana nemansu. Nan take aljanun gaba daya suka tafi suka bar shi shi kadai tare da Aljani Barakul Masnur. Aljani Barakul Masnur ya dubi Najwar cikin murmushi ya ce, "Tabbas yanzu na gamsu cewa duk abin da ka tsara zai tabbata. Amma muna da matsala guda daya. Yaya za mu yi da su Aljani Maruful Dauwaz wadanda su ma sun zo ne 390 TASKARNOVELS.COM.NG domin su mallaki Gimbiya, kuma ta yaya za ka iya fito da Gimbiya daga cikin gidanta alhalin kasan cewa ba za mu iya kawar da Dakarun da ke tsaronta ba? KAKA-KARA-KAKA! Lokacin da sadauki Najwar ya ji wannan batu sai ya bushe da dariya har da faɗowa kasa daga kan karagar mulkin, ya yi ta dariyar kamar ba zai daina ba. Daga can sai ya tsagaita da dariyar tare da nutsuwa ya dubi Aljani Barakul Masnur ya ce, Ai ni ba na yin Kwaina sai da Zakara. Tuni na yi bincike akan yadda zan sami wannan nasara, kuma na ga mafita don haka ka zuba ido za ka sha mamaki. Nan da cikar sa'a daya jal zan zo maka da Gimbiya Ramlatul Siyam kuma a cikin gidanka za mu ɓoye ta har sai mun sami nasarar juyin mulki sannan za a fito da ita a daura aurena da ita." 391 TASKARNOVELS.COM.NG Gama fadin hakan ke da wuya sai Najwar ya 6ace ɓat. Koda ganin haka sai shi ma Aljani Barukul Masnur yai sauri ya bar cikin fadar. Al'amarin sauran Dakaru, Bayi da Barori da Kuyangin da ke hidima a cikin gidan sarautar Sarki da Nashmir kuwa, lokacin da suka ga Najwar ya zo da Sababbin al'amura a gidan sarautar sai suka cika da tsananin mamaki, amma da yake sun san cewa yana matukar shakkar Sarki kuma yana matukar biyayya a gare shi sai suka za ta cewa abin da yake da sanin Sarki yake yi. A can kurkuku kuwa, hankali Rahila da na Sarki Laffaru ya dugunzuma ainun sun kasa zaune sun kasa tsaye, sai kai kawo suke yi a cikin kurkukun domin gani suke kamar shi ke nan sun shiga inda ba za su taɓa fita ba, sai dai a fitar da gawarsu. 392 TASKARNOVELS.COM.NG Shi kuwa Aljani Maruful Dauwaz ko a jikinsa wai an mintsini kakkausa. Da ma ya ga su Rahila sun damu ainun sai kawai ya kishingida ya kama rara wata waka. Koda yai nisa a cikin wakar sai ya fashe da kuka saboda ya tuno da masoyiyarsa marigayiya Rashmin. Koda Rahila da Laffaru suka ga Aljani Maruful Dauwaz ya kama kuka sai su ma suka fara kukan domin a zatonsu zuciyarsa ce ta karaya bisa samun kuбutarsu. Suna cikin wannan hali ne wani Badakkare ya durfafo dakin da suke ciki dauke da abincin su Rahila. An kawo musu abincin ne saboda sanin cewa su mutane ne idan ba a ba su abinci ba za su iya shiga mugun hali ko ma su rasa rayuwarsu gabaki daya. Da isowar Badakkaren sai ya buɗe wata 'yar karamar taga ya zuro kwanon abincin. Kafin ya janye hannunsa tuni Aljani Maruful Dauwaz ya 393 TASKARNOVELS.COM.NG rike shi. Nan take Badakkaren ya zama dan minini ya shige cikin kurkukun. Faruwar hakan ke da wuya sai Maruful Dauwaz ya rikide siffarsa gabadaya ta koma irin ta wannan Badakkare. Yana dafa Rahila da Laffaru sai suka zama 'yan mini-mini. Nan take ya dauke su ya dora su akan kafadarsa sannan ya fice daga cikin kurkukun kamar yadda danshi ke ratsa kasa suka bar wannan Badakkare kulle a cikin kurkukun yana kwance ya kasa koda motsawa. Maruful Dauwaz ya ci gaba da tafiya a cikin kurkukun a siffar wannan Badakkare duk inda ya je sai ka ga an bude masa kofa ya wuce. Rahila da Laffaru kuwa sai tsalle-tsalle suke akan kafadarsa suna tsananin murna bisa ganin sun fito daga cikin wannan kurkuku. 394 TASKARNOVELS.COM.NG Saboda kankantar Rahila da Laffaru girmansu bai wuce na tsayin babban dan yatsa ba babu wanda ya gan su akan kafadar Maruful Dauwaz har suka fice gabadaya daga cikin kurkukun, sannan suka isa wani sako inda babu kowa. A sannan ne Maruful Dauwaz ya ďaga tafin hannunsa dai kafadarsa, Rahila da Laffaru suka dirgo kan tafin hannunsa, sannan ya sauko da su Kasa daidai fuskarsa ya ce da su, "Kun gasgata maganata cewar zan iya kubutar da mu?". Rahila da Laffaru suka gyada kai a tare cikin murmushi. Rahila ta ce, "Tabbas mun gamsu, Yanzu kuma mene ne abin yi na gaba?" Maruful Dauwaz ya ce, "Na ji a jikina cewar Najwar yaudararmu zai yi ba zai yarda mu mallaki Gimbiya Ramlatul Siyam ba. Dole ne yanzu mu nemi inda gidan Gimbiya Ramlatul Siyam yake domin mu je mu sace ta mu gudu gabadaya, da jin wannan batu sai farin ciki ya lullube Rahila da Laffaru suka ce, "Kawai a tafi". 395 TASKARNOVELS.COM.NG Har Aljani Maruful Dauwaz ya yunkura zai fita daga cikin sakon da suka бuya sai ya dawo da baya ya tsaya. Al'amarin da ya bai wa su Rahila mamaki ke nan. Rahila ta dubevshi cikin firgici ta ce m, ya kai Sarkin sadaukan aljanu, mene ne dalilin da ya sa ka dawo da baya?" Cikin alamun tsananin damuwa Aljani Maruful Dauwaz ya dubi Rahila kamar zai yi kuka ya ce, "Ya

Chapter 14 of 18