tashi domin su tafi izuwa can fadar
Sarki Nashmir.
Bayan kowa ya gama kimtsawa sai sadauki
Najwar ya dubi Aljani Barukul Masnur ya ce,
"Ina mai gargadinka da kada ka kuskura ka
kaucewa umarnina ko kuma ka ce za ka tona
mini asiri saboda ka ga yanzu za mu koma fada
kana shakkar Sarki, Idan har kunne ya ji to
gangar jiki ta tsira".
Koda gama fadin haka sai Najwar ya dubi Aljani
Maruful Dauwaz ya ce, "Idan muna son mu sami
365
TASKARNOVELS.COM.NG
nasarar rushe mulkin maigidana mu kawar da
shi, dole ne mu yi abu uku. Abu na farko yanzu
zan kama ku na daure ku na kai ku wajensa a
matsayin fursunoni. Na san ba zai yi gaggawar
hallaka ku ba sai dai ya sa a kulle ku a kurkuku.
Mataki na biyu na shi ne, zan shiga tunanin
dabarar da zan yi na sace Gimbiya Ramlatul
Siyam daga turakarta a sirrance ko a dabarance
sannan na shirya matakan hallaka Dakarun
tsaro na fadar, yadda idan aka fara yakin za mu
sami nasarar kawar da su duka a cikin kankanin
lokaci.
Shi kuwa Sarki Nashmir ni ne zan tare shi mu
fafata in ya so muna cikin gumuzun sai ku kawo
mini dauki mu hada KARFI DA KARFE mu
hallaka shi. Da zarar sauran Dakarun nasa sun
ga mun ballaka shi dole ne su yi mubaya'a a
gare mu su dawo karkashin ikonmu."
Sa'adda sadauki Najwar ya zo nan a zancensa
sai Aljani Maruful Dauwaz ya dube shi ya ce, "Ya
kai wannan sadaukin sadaukai, mun ji duk
bayaninka kuma mun gamsu da shi, amma
366
TASKARNOVELS.COM.NG
muna son mu gana a tsakaninmu idan akwai
wani korafi sai mu sanar da kai".
Koda jin haka sai sadauki Najwar yai murmushi
ya ce, 'Ai babu komai ina sauraronku."
Nan take Maruful Dauwaz, Rahila da Sarki
Laffaru suka koma gefe daya suka fara
tattaunawa Inda Aljani Maruful Dauwaz ya
dubes u ya ce, "To kun ji abin da wannan
sadaukin jarumi ya zo mana da shi, anya kuwa
ba kwa tunanin cewa akwai. yaudara a cikin
al'amarin?
Ku tuna fa cewa shi ne Sarkin yakin Sarki
Nashmir tsawon shekaru, ta yaya kuke
tsammanin cewa zai bijire wa Sarkinsa a
yanzu?"
367
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda jin wannan batu sai Rahila da Sarki
Laffaru suka yi shiru kamar ba za su ce komai
ba, kuma hankalinsu ya kara dugunzuma.
Daga can sai Rahila ta yi ajiyar zuciya sannan ta
dubi Maruful Dauwaz ta ce, "Ai yanzu ba mu da
wata huija da za mu ce ba za mu yard jarumi
Najwar ba tunda inda ya so hallaka mu da tuni
ya kawar da mu.
Tunda har ya kyale mu lallai akwai kamshin
gaskiya a cikin zantukansa, sai dai ina shakku
akan batun Gimbiya Ramlatul Siyam da ya ce shi
zai san hikimar da zai yi ya sace ta. Ina ji a jikina
cewar yana da wani shiri na musamman akan
Gimbiya Ramlatul Siyam don haka dole ne mu
sa ido a kansa.
Tabbas yanzu ba mu da wani zaбi wanda fi ya
mu bi umarninsa tunda ya fi mu sanin dukkan
sirrin fadar Sarki Nashmir kuma masu iya
368
TASKARNOVELS.COM.NG
magana sun ce, 'Da dan gari akan ci gari', ko
kuwa a cikinku akwai mai wata sharar daba?"
Da jin haka sai Rahila da Laffaru suka dubi juna
sannan suka yi shiru. Rahila ta ce, "Ba mu da
wata shawara wacce ta fi kawai mu yi
kundunbala mu bi umarnin sadauki Najwar
tunda al'amarin ya zama lalube a çikin duhu, ba
a san inda za a dace ba."
Nan take Maruful Dauwaz ya matsa gaban
sadauki Najwar ya ce, "Mun amince da dukkan
umarninka sai mu tafi kawai".
Koda jin haka sai Najwar ya bushe da dariyar
farin ciki. Nan take yai nuni da hannunsa izuwa
ga Maruful Dauwaz, Rahila da Sarki Laffaru sai
wata murtukekiyar sarkar tsafi ta kanannaɗe su
su duka ta ɗaure su tamau amma wannan karon
babu wuta a jikin sarkar.
369
TASKARNOVELS.COM.NG
Sadauki Najwar ya dubi Aljani Barukul Masnur
ya ce, "Maza ka dauki su Maruful Dauwaz ka
dora su a gadon bayanka sannan mu juya mu
koma izuwa Birnin Hindu".
Nan take kuwa Barukul Masnur ya cika wannan
umarni. Shi ma Najwar sai ya hau kan Barukul
Masnur ya zauna. Nan take Barukul Masnur ya
bude fuka-fukansa ya tashi sama ya kama tsala
azababben gudu yana mai tunkarar Birnin
Hindu.
Hakika inda ace mutum na nan a lokacin da
Aljani Barukul Masnur ya dauki su Aljani
Maruful Dauwaz ya tashi da su sama dole ne ya
cika da tsananin mamaki ya sallamawa Ubangiji
bisa wannan iko nasa, saboda shi kansa Maruful
Dauwaz girman halittar jikinsa ta isa abin
al'ajabi domin in daga nesa mutum ya hange shi
zai yi zaton ko tsauni ne amma sai ga shi Aljani
Barukul Masnur ya ninka shi girma sau uku.
370
TASKARNOVELS.COM.NG
Tabbas! Babu wanda ya san iyakar balittun ke
wannan duniya face Allah. Hakika shi ne abin
tsoro, wanda ya zamo mafi cancanta a bauta
masa tunda shi ne Ya halicci kowa da komai.
Tafiyar rabin sa'a kacal Aljani Barukul Masnur
ya yı ya iso fadar Sarki Nashmir. Koda isowarsa
bakin kofar shiga gidan sarautar sai ya tsaya cak
sakamakon ganin masu gadin kofar sun ki bude
musu kofar su shiga.
Koda ganin haka sai sadauki Najwar ya dubi
masu gadin ya daka musu tsawa ya ce, "Me kuke
jira ne ba ku bude mana kofar mun shiga ba ko
kuwa ba ku shaida mu ba ne?"
Da jin wannan tambaya sai shugaban masu
gadin kofar ya dubi sadauki Najwar cikin
girmamawa ya risina ya ce, 'Ya shugabana ka yi
hakuri muna kan umarnin Sarki ne domin da zai
fita bai gaya mana cewa za ku dawo tare da
fursunoni ba kuma ka san dokar gidan nan babu
371
TASKARNOVELS.COM.NG
wani bako da aka yarjewa shiga face da izinin
Sarki".
Sa'adda sadauki Najwar ya ji cewar Sarki baya
nan ya fita sai ya cika da tsananin mamaki gami
da tsananin farin ciki saboda sanin cewa ya
sami babbar dama da zai iya cika burinsa a
saukake, amma duk da haka dole ne ya bi
al'amarin a sannu.
Najwar ya dubi shugaban masu gadin kofar ya
sake daka masa tsawa a karo na biyu ya ce,
"Shin zan aikata wani abu ne daban ba tare da
izinin Sarki ba? Maza ka sa a bude mana kofa
kada fishin Sarki ya tabbata akanku idan ya
dawo".
Koda jin haka sai shugaban masu gadin ya
sunkui da kansa kas yai shiru kuma ya ki ya
bayar da umarnin a bude kofar saboda ya fada
cikin wasi-wasi da fargaba.
372
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda ganin haka sai sadauki Najwar ya fusata
ainun ya zare takobinsa ya dubi shugaban masu
gadin kofar ya ce, "Maza ka bayar da umarnin a
bude mana kofa ko yanzun nan na zare maka
ruhin numfashinka da dukkan jama'ar taka".
Koda jin haka sai jikin shugaban masu gadin ya
kama kyarma, ba shiri ya dubi yaran nasa ya
daka musu tsawa ya ce su yi maza su bude
kofar! Nan take kuwa masu gadin suka fara
kokarin bude kofar.
Ita dai wannan kofa ta shiga fadar Sarki
Nashmir tsawonta ya kai kamu dubu uku, haka
ma fadinta. Idan aka fara bude ta sai an shafe
sa'a uku ana janye ta daga sama tana shigewa
cikin karkashin kasa. Wata murtukekiyar sarkar
karfe ce guda biyu a jikin kofar a dama da
hagunta.
Kowacce sarka guda akwai aljanu dubu goma
wadanda ke rike da ita. Idan za a bude kofar
373
TASKARNOVELS.COM.NG
aljanun da ke dama ne suke jan wannan sarka
har sai sun shafe sa'a uku suna janta sannan za
ta gama budewa ta kule a cikin kasa.
Haka kuma idan za a rufe kofar aljanu dubu
goma da ke hagu ne za su yi ta jan sarkar har
tsawon sa'a ukun sannan kofar take rufewa ta
tokare da saman ginin fadar.
Kaurin wannan kofa ya kai kamu dari uku,
huma an yi ta ne da zallan karfen lu'u-lu'u, babu
wani makami da zai iya yiwa kofar lahani komai
kkarfinsa, tsininsa da nauyinsa.
Sai da su Najwar suka yi jira har tsawon sa'a
uku sannan kofar ta gama budewa suka kunna
kai izuwa cikin gidan sarautar.
Da shigarsu sai Aljani Maruful Dauwaz da Rahila
da Sarki Laffaru suka cika da tsananin mamaki
sakamakon ganin tsananin girman gidan da
374
TASKARNOVELS.COM.NG
kuma irin gine-ginen da ke cikinsa da kayan
kawar da aka shirya tamkar aljannar duniya.
Babu abin ma da ya fi ba su mamaki face ganin
yadda Aljani Baruk! Masnur ya yi ta tafiya a
cikin gidan sarautar, bai iso inda aka gina
kurkukun gidan ba sai da ya shafe tafiya mai
nisan gaske Wacce suka yi a baya tun daga dajin
Hizurul Aswad.
Nan take Aljani Barukul Masnur ya sauko kasa
ta dira a bakin kofar kurkukun.
Dirarsa ke da wuya sai sadauki Najwar
Ya dubi masu gadin kurkukun ya ce, "Ga
fursunonin Sarki ku shigar da su ciki a kulle su
har sai na dawo karbarsu"
Nan take Wadansu jibga-jibgan aljanu wadanda
sun ninka Aljani Barukul Masnur sau biyu a
girma da Kwarjini suka kama su Maruful
Dauwaz tamkar Shaho ya kama Dan tsako suka
375
TASKARNOVELS.COM.NG
shige da su izuwa cikin kurkukun aka yi ta tafiya
da su har sai da aka yi doguwar tafiya ana wuce
mugayen matakan tsaro, sannan aka jefa su a
cikin wani daki aka kulle su.
Babu abin da ya firgit su Aljani Maruful Dauwa
face ganin tsananin tsaron kurkukun da kuma
irin yanayin ginin da aka yi shi, komai
jarumtakar mahaluki da Karfin sihirinsa bai isa
ya iya guduwa daga cikin wannan kurkukun ba.
Koda suka garkame su Aljani Maruful Dauwaz a
cikin wani kuntataccen ďaki sai hankalinsu ya
dugunzuma domin ji suka yi kamar an jefa su a
cikin rijiya gaba dubu an rufe muffin rijiyar.
Cikin tsananin takaici da nadama Rahila ta dubi
Aljani Maruful Dauwaz ta ce, hakika mun yi
babban kuskure da muka yarda da sadauki
Najwar. Abin da na fahimta yanzu shi ne,
Sadauki Najwar ba ya son ya kashe mu so yake
a kawo mu gare shi a raye, wata kila don ya
376
TASKARNOVELS.COM.NG
ďanďana mana muguwar azaba ne kafin ya
hallaka mu.
ya Koda jin wannan batu sai cikin Sarki Laffaru
duri ruwa ba, ya firgita ainun bai san sa'adda ya
saki fitsari a wando ba. Al'amarin da ya sa Aljani
Maruful Dauwaz ya tuntsure da dariya ke nan,
sannan ya daka wa Laffaru tsawa ya ce, "Kai
tsohon azzalumin Sarki, shin ka manta ne da
irin bakin mulkin da ka yi wa mutane a baya?
Ai bai kamata a ce ka zamo matsoraci mai
gudun azaba tunda babu irin kalar azabar da ba
ka sa an yi wa mutane ba.
Hakika a da can kai Kura ne, amma yanzu
wannan Kurar ta zama Akuya. Abin da nake so
da kai shi ne ka kwantar da hankali ka. Ka sani
cewa mai rai ba ya kasa motsi. Na yi muku
alkawari ba za mu tozarta ba a cikin wannan
kurkuku, ta kowanne hali sai na ceci
rayuwarmu na fitar da mu".
377
TASKARNOVELS.COM.NG
Sa'adda Rahila da Sarki Laffaru suka ji wannan
batu sai suka cika da tsananin mamaki. Rahila ta
dubi Maruful Dauwaz ta ce, Kai kuwa ta yaya za
ka iya fitar da mu daga cikin wannan mugun
kurkuku mai tsananin tsaro haka?"
Da jin wannan tambaya sai Maruful Dauwaz yai
murmushi ya ce, Ku zuba ido kawai ku sha kallo,
nii ne fa jarumi mai sa'a da rabo wanda komai
RINTSI DA TSANANI sai ya fita daga cikin
kowanne bala'i.
Idan kuka yi la'akari da abubuwan da suka faru
a gare mu a baya za ku gane cewa sa'ata ita ce ta
kai mu ga kawowa i yanzu.
Wannan shi ne abin da ya faru ga su Aljani
Maruful Dauwaz bayan an kawo su fadar Sarki
Nashmir a matsayin fursunoni.
378
TASKARNOVELS.COM.NG
Al'amarin su sadauki Najwar kuwa, lokacin da
ya ga an shigar da su Aljani Maruful Dauwaz
cikin kurkuku an je an kulle su sai ya tafi cikin
tsananin farin ciki bisa ganin cewa duk
abubuwan da ya tsara don cika burin rayuwarsa
suna tafiya daidai.
Babu abin ma da ya kara karfafa masa guiwa
face da ya zo ya tarar da cewa Sarki Nashmir ba
ya nan. Abin da ya fado masa a rai shi ne, dole
ne yanzu ya je ya yi bincike domin ya gano inda
sakri Nashmir ya tafi da kuma lokacin da zai
dawo domin ya yi sauri ya gama kammala
dukkan shirye- shiryensa kafin Sarki Nashmir
ya dawo.
Kai tsaye sadauki Najwar ya wuce izuwa
gidansa wanda ke can ɓangare daya a cikin
gidan sarautar. Cikin tsananin farin ciki ya shiga
gidan ya wuce izuwa dakin halwar tsafinsa ya
dukufa. Nan take ya ga abin da ya matukar
girgiza masa hankali ya ga cewa ashe ma idan ya
cika burinsa a yau din ma tsugune ba ta kare ba,
akwai gagarumar masifa a gabansa.
379
TASKARNOVELS.COM.NG
Ba wani abu sadauki Najwar ya gani ba a cikin
madubin tsafinsa face rincaɓewar masifaffen
yaki tsakanin Boka Muzaffar, Sarki Nashmir da
Sharlis a can gidan Boka Muzaffar da ke Birnin
Kufa a dokar daji.
Su ukun suna yakar juna ne akan abu daya. Ba
wani abu bane face MASHIN GALILUL HARAS.
Mashin na jingine a cikin dakin tsafin Boka
Muzaffar amma an rasa wanda zai sami nasarar
daukar mashin a tsakaninsu su ukun domin sun
wanzu a cikin kai wa junansu sara da suka cikin
bakin zafin nama, juriya da jarumtaka ta gaban
kwatance kuma kowannensu yana amfani ne da
dukkan karfin dantsensa da karfin tsafinsa.
Duk sa'adda takubbansu suka hadu sai dai ka ji
tartsatsin wuta na tashi gami da hayaki.
380
TASKARNOVELS.COM.NG
Duk wanda aka sari jikinsa kuwa sai ka ji kamar
karfe aka sara, makamin bay a tasiri haka uma
babu wanda yake da alamar gajiyawa a cikin
yakin alhalin kwanansu goma sha hudu ke nan
suna wannan masifaffen yaki a waje ďaya har ta
kai cewa sun rugurguza gaba dayan ginin gidan
na Boka Muzaffar tamkar ginin bai taɓa
wanzuwa ba Komai dake cikin gidan ya kone ya
zama toka, Mashin Galilul Haras ne kadai ko
kwarzanewa bai yi ba.
Sadauki Najwar ya ci gaba da bincike domin ya
gano wanda zai sami nasarar daukar mashin na
Galilul Haras a tsakanin matsafan uku, amma sai
abu ya gagara.
Ya sake yin bincike akan sa'adda yakin nasu zai
zo karshe amma abu dai ya gagara. Al'amarin da
ya dugunzuma hankalin sadauki Najwar ke nan
ainun fiye da ko yaushe ya fusata har ya maka
madubin tsafin nasa a kas ya tarwatse.
381
TASKARNOVELS.COM.NG
Nan fa ya zauna ya yi tagumi yana tunanin abin
da ya kamata ya yi. Sai da ya daɗe a zaune cikin
wannan hali sannan ya yanke shawarar cewa
duk yadda zai yi dole ne a cikin wannan dare ya
mallaki Gimbiya Ramlatul Siyam kuma ya
mallaki karagar mulkin Sarki Nashmir.
Ko a yau din ne kadai ya sadu da Gimbiya
Ramlatul Siyam kuma ya zauna akan karagar
mulki ai ya gama cika burinsa na duniya bai ki
ba ma Ajalinsa ya riske shi tun da ya yi abin da
babu wani mahaluki da ya isa ya yi shi a doron
kasa. Ko ba komai ba zai yi mutuwar banza ba
wacce za a manta da shi.
Dole ne a rinka tunawa da shi a cikin tarihin
MAZAN JIYA wadanda suka yi gagarumar
bajintar da ba za a taɓa mantawa ba.
Koda sadauki Najwar ya gama aiyana hakan sai
ya mike zumbur! ya fita daga cikin gidansa, bai
382
TASKARNOVELS.COM.NG
zame a ko ina ba sai inda Aljani Barukul Masnur
yake a cikin gidan sarautar.
Irin su Aljani Barukul Masnur sun kai su miliyan
daya da rabi a cikin Dakarun da ke tsaron fadar
Sarki Nashmir kuma dukkaninsu sun fito ne da
ga wata zuri'a ta aljanu a Birnin Hindu.
Tunda zuri'ar tasu ta wanzu a doron kasa, suka
kasance bayi, ba su taɓa samun 'yancin kansu ba
a wajen 'yan uwansu ajlanu da manyan Bokayen
duniya na jinsin Bil'adama.
Wani babban abin takaici a gare su shi ne, sun
kasance 'yan tsiraru a cikin al'ummar aljanu na
Birnin Hindu, kuma an kafa musu karan-tsana,
shi ya sa ake karar da dukkan rayuwarsu a cikin
bauta.
Iyaye da Kakanninsu da wannan bakin ciki suka
tsufa suka mutu, domin sun san cewa har abada
383
TASKARNOVELS.COM.NG
ba za su iya yin tawaye ba don su kwaci 'yancin
kansu. Lokacin da sadauki Najwar ya riski Aljani
Barukul Masnur sai ya ja shi izuwa cikin wani
daki suka kadaita a inda babu wanda zai ji abin
da za su tattauna.
Najwar ya dubi Barukul Masnur ya ce, "Na ji
dadi da ka rufa mini asiri ba ka gayawa kowa
sirrina ba, bisa wannan dalili yanzu zan yi wa
zuri'arku gabadayanta gatan da ba a taɓa yi
muku ba. Ka sani cewa a cikin shekara guda sau
daya jal ake ba ku hutun aikin bauta.
To ni yanzu na ba ku hutu na tsawon wata uku,
kuma a yau na shirya muku walima ta
musamman a cikin fadar maigirma sarki
Nashmir".
Koda jin wannan batu sai idanun Barukul
Masnur suka zazzaro ya cika da tsananin tsoro
ya ce, "Haba ya shugabana, ai idan ka yi haka
Sarki ya dawo sai ya sa a hallaka mu gaba
384
TASKARNOVELS.COM.NG
dayanmu. Kai kanka ba za ka tsira ba daga
sharrinsa".
Koda jin wannan batu sai Najwar ya bushe da
dariya ya ce, "Ka san dai idan Sarki ba ya nan
babu mai ba da umarni a gidan nan sai ni ko ba
haka ba ne?"
Barukul Masnur ya ce, Haka yake". Najwar ya ce,
Maza ka je ka sami ragowar yan uwanka su
duka ka gaya musu cewa ina nemansu yanzuyanzu a fada. Koda gama fadin hakan sai Najwar
ya 6ace fat. Bai baiyana a ko ina ba sai a fadar
Sarki Nashmir inda karagar mulki take.
Baiyanarsa ke da wuya ya bai wa Barori da
Kuyangi umarnin su je su kawo abinci da abin
sha iri-iri wanda za a yi walima da shi.
Nan take kuwa Barorin da kuyangin suka cika
wannan umarni cikin 'yan dakiku kadan.
Faruwar hakan ke da wuya sai ga gabadayan
385
TASKARNOVELS.COM.NG
zuri'ar su Aljani Barukul Masnur sun baiyan a
fadar.
Al'amarin da ya matuka bai wa gabadayan
Dakarun tsaro na gidan maraki ke nan, domin
hakan ba ta taɓa faruwa ba tunda Sarki Nashmir
ya hau karagar mulki.
Bayan zuri'ar su Aljani Barukul Masnur sun
gama hallara gaba dayansu kimanin su miliyan
daya da rabi sai sadauki Najwar ya daka tsawa
ga sauran Dakaru, barori da bayi da ke cikin
fadar ya ce kowa ya fita ya bar su da zuri'ar su
Barukul Masnur. Nan take kuwa aka bi wannan
umarni.
Bayan kowa ya gama fita ne sai Najwar ya sa
aka kulle dukkan kofofi da tagogin fadar don
kada ma wani ma ya ji abin da za su tattauna.
386
TASKARNOVELS.COM.NG
Ba tare da 6ata wani lokaci ba Najwar ya bai wa
su Aljani Barukul Masnur umarni suka fara
walima.
Saboda tsananin fari ciki da mamaki ba su san
sa'adda suka kama bushasha ba har ma wasu
suka rinka kade-kade da raye-raye, wasu ma
suka yi ta shan ruwan barasa kai ka ce a cikin
gidajensu suke ba a fadar mai girma Sarki
Nashmir ba. Shi kansa Najwar sai ya shagala ya
yi ta rawa a cikinsu yana nishadi.
Bayan kowa ya ci ya gyatse sai sadauki Najwar
ya tafi kai tsaye izuwa kan karagar Sarki
Nashmir ya zauna akanta ya harde kafafuwansa.
Koda ganin haka sai gaba dayan aljanun suka
firgice suka kama kuka suna rokon Najwar da ya
ba su umarnin su fice daga fadar don kada Sarki
Nashmir ya dawo a yanzu ya ga abin da ke
faruwa ya sa a hallaka su su duka.
387
TASKARNOVELS.COM.NG
Koda jin wannan batu sai Najwar ya bushe da
dariya, lokaci guda kuma ya murtuke fuska ya
ce, 'Ya ku wannan zuri'a ta aljanu da ba su da
gata a wannan kasa tamu, shin kun yi imani
cewa ni ne Wazirin Sarki Nashmir?"
Su duka suka amsa da "Na'am". Najwar ya
cigaba da bayani yana cewa. "Fiye da shekaru
dubu arba'in ba ku taɓa samun 'yancin kanku
ba, Iyayenku da Kakanninku duk a cikin kangin
bauta suka mutu. Yau ni Najwar zan kwato
muku 'yancinku. Koda jin haka sai gabadayan
aljanun suka rude da shewa cikin tsananin
murna har sai da Najwar ya daga hannunsa
sama sannan suka yi tsit tamar mutuwa ta gifta.
Najwar ya ci gaba da cewa, "Ku sani cewa da
kadan Sarki Nashmir ya fi ni jarumtaka da
karfin shirin tsafi. To ni ma na gaji da yi masa
bauta babu ci gaba. Yau ne ranar da na sami
damar da zan yi masa tawaye, amma sai idan
kun ba ni hadin kai sannan ni da ku za mu samu
'yancinmu.
388
TASKARNOVELS.COM.NG
Ina tabbatar muku da cewa Sarki Nashmir ya
tafi wani gagarumin yaki shi kadai yakin da ba
zai taba tsira da rayuwarsa ba. Yanzu zan nuna
muku zahiri ku gani da idanunku".
Koda gama fadin hakan sai ya yi nuni da
hannunsa izuwa ga jikin bangon fadar. Nan take
suka ga taswirar hoton gumurzun da ake yi
tsakanin Sarki Nashmir da su Boka Muzaffar.
Al'amarin da ya matukar ba su mamaki ke nan.
Najwar ya sake nuna bangon da hannunsa
hoton komai ya dauke sannan ya ce, na yi
bincike a cikin tsafina na gano cewa za a kashe
Sarki a wannan yaki, saboda haka a daren yau
ina son ku ba ni hadin kai mu yi juyin mulki
cikin shammace domin idan muka bari har
dakakarun gidan nan suka san cewa Sarki
mutuwa zai yi, to kuwa za su dora 'yarsa ne
akan karagarsa. Idan kuwa hakan ta faru
'yancinku da nake son na karɓo muku ya suбuce
ke nan har abada, domin da zarar Ramlatul
389
TASKARNOVELS.COM.NG
Siyam ta zauna akan karagar mulki za ta sami
dukkan karfin sihirin tsafi irin na mahaifinta,
kun ga kenan ba zan taɓa iya yi mata juyin
mulki ba.
Lallai da zafi-zafi akan bugi karfe, idan kuwa aka
bari ya huce shi ke nan ba zai lankwasu ba.
Sa'adda Najwar ya zo na nan a jawabinsa sai
gaba dayan aljanun suka rude da shewa suna
masu cewa sun ba shi hadin kai dari bisa dari.
Nan take farin ciki ya lulluɓe Najwar ya sallame
su akan cewa, da zarar dare ya raba su dawo
nan fadar yana nemansu. Nan take aljanun gaba
daya suka tafi suka bar shi shi kadai tare da
Aljani Barakul Masnur.
Aljani Barakul Masnur ya dubi Najwar cikin
murmushi ya ce, "Tabbas yanzu na gamsu cewa
duk abin da ka tsara zai tabbata. Amma muna da
matsala guda daya. Yaya za mu yi da su Aljani
Maruful Dauwaz wadanda su ma sun zo ne
390
TASKARNOVELS.COM.NG
domin su mallaki Gimbiya, kuma ta yaya za ka
iya fito da Gimbiya daga cikin gidanta alhalin
kasan cewa ba za mu iya kawar da Dakarun da
ke tsaronta ba?
KAKA-KARA-KAKA!
Lokacin da sadauki Najwar ya ji wannan batu
sai ya bushe da dariya har da faɗowa kasa daga
kan karagar mulkin, ya yi ta dariyar kamar ba
zai daina ba. Daga can sai ya tsagaita da dariyar
tare da nutsuwa ya dubi Aljani Barakul Masnur
ya ce, Ai ni ba na yin Kwaina sai da Zakara.
Tuni na yi bincike akan yadda zan sami wannan
nasara, kuma na ga mafita don haka ka zuba ido
za ka sha mamaki. Nan da cikar sa'a daya jal zan
zo maka da Gimbiya Ramlatul Siyam kuma a
cikin gidanka za mu ɓoye ta har sai mun sami
nasarar juyin mulki sannan za a fito da ita a
daura aurena da ita."
391
TASKARNOVELS.COM.NG
Gama fadin hakan ke da wuya sai Najwar ya
6ace ɓat. Koda ganin haka sai shi ma Aljani
Barukul Masnur yai sauri ya bar cikin fadar.
Al'amarin sauran Dakaru, Bayi da Barori da
Kuyangin da ke hidima a cikin gidan sarautar
Sarki da Nashmir kuwa, lokacin da suka ga
Najwar ya zo da Sababbin al'amura a gidan
sarautar sai suka cika da tsananin mamaki,
amma da yake sun san cewa yana matukar
shakkar Sarki kuma yana matukar biyayya a
gare shi sai suka za ta cewa abin da yake da
sanin Sarki yake yi.
A can kurkuku kuwa, hankali Rahila da na Sarki
Laffaru ya dugunzuma ainun sun kasa zaune
sun kasa tsaye, sai kai kawo suke yi a cikin
kurkukun domin gani suke kamar shi ke nan
sun shiga inda ba za su taɓa fita ba, sai dai a fitar
da gawarsu.
392
TASKARNOVELS.COM.NG
Shi kuwa Aljani Maruful Dauwaz ko a jikinsa
wai an mintsini kakkausa. Da ma ya ga su Rahila
sun damu ainun sai kawai ya kishingida ya
kama rara wata waka. Koda yai nisa a cikin
wakar sai ya fashe da kuka saboda ya tuno da
masoyiyarsa marigayiya Rashmin.
Koda Rahila da Laffaru suka ga Aljani Maruful
Dauwaz ya kama kuka sai su ma suka fara
kukan domin a zatonsu zuciyarsa ce ta karaya
bisa samun kuбutarsu.
Suna cikin wannan hali ne wani Badakkare ya
durfafo dakin da suke ciki dauke da abincin su
Rahila. An kawo musu abincin ne saboda sanin
cewa su mutane ne idan ba a ba su abinci ba za
su iya shiga mugun hali ko ma su rasa
rayuwarsu gabaki daya.
Da isowar Badakkaren sai ya buɗe wata 'yar
karamar taga ya zuro kwanon abincin. Kafin ya
janye hannunsa tuni Aljani Maruful Dauwaz ya
393
TASKARNOVELS.COM.NG
rike shi. Nan take Badakkaren ya zama dan
minini ya shige cikin kurkukun.
Faruwar hakan ke da wuya sai Maruful Dauwaz
ya rikide siffarsa gabadaya ta koma irin ta
wannan Badakkare. Yana dafa Rahila da Laffaru
sai suka zama 'yan mini-mini. Nan take ya dauke
su ya dora su akan kafadarsa sannan ya fice
daga cikin kurkukun kamar yadda danshi ke
ratsa kasa suka bar wannan Badakkare kulle a
cikin kurkukun yana kwance ya kasa koda
motsawa.
Maruful Dauwaz ya ci gaba da tafiya a cikin
kurkukun a siffar wannan Badakkare duk inda
ya je sai ka ga an bude masa kofa ya wuce.
Rahila da Laffaru kuwa sai tsalle-tsalle suke
akan kafadarsa suna tsananin murna bisa ganin
sun fito daga cikin wannan kurkuku.
394
TASKARNOVELS.COM.NG
Saboda kankantar Rahila da Laffaru girmansu
bai wuce na tsayin babban dan yatsa ba babu
wanda ya gan su akan kafadar Maruful Dauwaz
har suka fice gabadaya daga cikin kurkukun,
sannan suka isa wani sako inda babu kowa.
A sannan ne Maruful Dauwaz ya ďaga tafin
hannunsa dai kafadarsa, Rahila da Laffaru suka
dirgo kan tafin hannunsa, sannan ya sauko da su
Kasa daidai fuskarsa ya ce da su, "Kun gasgata
maganata cewar zan iya kubutar da mu?".
Rahila da Laffaru suka gyada kai a tare cikin
murmushi. Rahila ta ce, "Tabbas mun gamsu,
Yanzu kuma mene ne abin yi na gaba?" Maruful
Dauwaz ya ce, "Na ji a jikina cewar Najwar
yaudararmu zai yi ba zai yarda mu mallaki
Gimbiya Ramlatul Siyam ba. Dole ne yanzu mu
nemi inda gidan Gimbiya Ramlatul Siyam yake
domin mu je mu sace ta mu gudu gabadaya, da
jin wannan batu sai farin ciki ya lullube Rahila
da Laffaru suka ce, "Kawai a tafi".
395
TASKARNOVELS.COM.NG
Har Aljani Maruful Dauwaz ya yunkura zai fita
daga cikin sakon da suka бuya sai ya dawo da
baya ya tsaya. Al'amarin da ya bai wa su Rahila
mamaki ke nan. Rahila ta dubevshi cikin firgici
ta ce m, ya kai Sarkin sadaukan aljanu, mene ne
dalilin da ya sa ka dawo da baya?" Cikin alamun
tsananin damuwa Aljani Maruful Dauwaz ya
dubi Rahila kamar zai yi kuka ya ce, "Ya
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 18