Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dai ya yi 274 TASKARNOVELS.COM.NG masa dariya, domin huhun-ma'ahun ne, da wanzuwarsa a filin yaki gwara ma a ajiye dutse wanda ba shi da rai, wata kila abokin gaba ya yi tuntuɓe da shi. Lokacin da su Rahila suka gama kintsawa sai mahaifinta ya zo gare su domin su yi bankwana. Tun kafin mahaifin nata ya karaso daf da ita, ita da shi suka fara zubar da hawaye. Rahila ta karasa gare shi a guje ta rungume shi kuma ta fashe da kuka tana mai cewa, "Ya kai Abbana an zo an raba ni da kai a karo na farko bisa niyyar cewa zan tafi don cika burin rayuwata amma ga shi har yanzu burin bai cika ba. Yanzu ga shi zan sake rabuwa da kai a karo na biyu. Tabbas wannan ita ce rabuwarmu ta karshe domin idan na dawo na dwo ke nan ba za mu sake rabuwa ba. Ka kasance mai yi min fatan samun sa'a da nasara." 275 TASKARNOVELS.COM.NG Koda jin wannan batu sai shi ma ya fashe da kuka ya ce, "Ya ke 'yata, tabbas zan kasance a cikin yi miki fatan samun nasara dare da rana har ki dawo daga wannan gagarumar tafiya. Ki tuna cewa ni ma dukkan burina ya dogara akan samun nasararki saboda ke ce kadai 'yata a duniya. Ba ni da burin da ya fi na ga aurenki kafin cikar ajalina domin na sami jikoki wadanda za su yada zuri'ata a doron kasa bayan rayuwata. Yanzu ga shi ba za ki yi aure ba face kun sami nasara a wannan gagarumin yaki da za ku tafi. Babu wanda yake da tabbacin za ku sami wannan nasara amma in dai da rai, akwai rabo." Koda jin wannan batu sai Rahila ta sake kankame mahaifinta a jikinta tana mai daďa rushewa da kuka kuma ta ji kamar ta fasa wannan tafiya. Da kyar Sarki Laffaru ya janye Rahila daga jikin mahaifinta ya dora ta a kan doki shi ma ya hau wani dokin sannan wasu Dakaru suka kwashi dukkan kayan yakinsu suka yi musu rakiya izuwa bayan gari inda Aljani Maruful Dauwaz ke 276 TASKARNOVELS.COM.NG jiransu. Da zuwansu kuwa suka iske Aljani Maruful Dauwa a tsaye cikin wata irin gagarumar shigar yaki irin wacce ba su taɓa gani ba a rayuwarsu. Maruful Dauwaz na sanye cikin waɗansu bakaken kayan karfe na riga da wando. Hatta fuka- fukansa ya lulluɓe su da bakin karfen, sannan a kugunsa akwai wata zabgegiyar takobi mai tsananin tsawo, fadi da tsinin tsiya, gami da kaifin gayawa jini na wuce. Ita kadai takobin sai sheki da walwali take yi tana dallare idanun wanda duk yai arba da ita. Sannan a wuyansa ya rataya wata garkuwa wacce aka yi ta da zallar karfe Lu'u-lu'u fari tas, ita ma sai sheki da walwali take yi. Sa'adda Rahila da Sarki Laffaru suka ga Aljani Maruful Dauwaz a cikin wannan gagarumar shigar yaki sai suka cika da tsananin mamaki domin a duk tsawon tafiyar da suka yi tun daga 277 TASKARNOVELS.COM.NG kogon Darul Iksina ba su ganshi da wadannan kaya ba. Abin tambaya anan shi ne, a ina Maruful Dauwaz ya samo wadannan kayan yaki? Amsar da suka kasa bai wa kansu ke nan, amma sai suka kudurce a ransu cewa lallai nan gaba idan an sami sukuni sai sun yi masa wannan tambaya. Ba tare da ɓata wani lokaci ba aka zuba gaba dayan wadannan kayan yakin akan Aljani Maruful Dauwaz, sannan Rahila da Sarki Laffaru suka hau kan Maruful Dauwaz din suma suka zauna. Nan take Maruful Dauwaz ya bude fuka- fukansa ya tashi sama. Kafin kiftawar ido ya luluka a cikin iska ya fara tsala azababben gudu yana mai tunkarar hanyar da za ta kai shi Birnin Hindu. 278 TASKARNOVELS.COM.NG Duk wannan abu da ya faru tsakanin su Rahila da Aljani Maruful Dauwaz, Sarki Nashmir na Birnin Hindu ya gani a cikin madubin TSAFINSA a lokacin da yake zaune a kasaitacciyar fadarsa tare da 'yarsa Gimbiya Ramlatul Siyam, tauraruwar taurarin matan duniya na wannan zamani. Gimbiya Ramlatul Siyam ta kasance kyakkyawar mace ta gaban misali, domin babu wani mutum da zai iya fasalta ainihin kyawun fuskarta da kyan dirin jikinta daidai da Yadda Allah Ya ba ta, sai dai Ya kwatanta daidai iyawarsa. A takaice dai akan batun kyau sai dai a kira Gimbiya Ramlatul Siyam Kurun-kus! Masu bincike da masana tarihi sun tabbatar da cewa a wannan lokaci babu wata fada daga cikin dukkan fadodin duniya wacce ta fi ta Sarki Nashmir girma, ginuwa da katuwa. Domin komai arzikin BASARAKE da bunkasarsa in dai ya shiga cikin fadar sai ya zama cikakken dan kauye wanda bai taɓa shiga Birni ba. Kai! irin wannan daula da aka tanada a cikin gidan 279 TASKARNOVELS.COM.NG sarautar kuwa, sai dai a kirashi da "ALJANNAR DUNIYA. Lokacin da Sarki Nashmir ya ga su Aljani Maruful Dauwaz sun taho izuwa fadarsa domin raba shi da 'yarsa Gimbiya Ramlatul Siyam kuma su debi yawun barcinsa, sai ya bushe da mahaukaciyar dariya,gabaďaya daya Fadawansa ma da ke zaune a fadar sai suka taya shi dariyar domin sun san cewa abu ne wanda ba zai taɓa yiwuwa ba. Ita kuwa Gimbiya Ramlatul Siyam sai hankalinta ya dugunzuma har kwalla ta ciko a idanunta. Ba komai ne ya jaza ma ta hakan ba face ta dade tana yin wani mugun mafarki, kuma a cikin mafarkin ana nuna ma ta cewar an raba ta da mahaifinta Ramlatul Siyam ba ta taɓa gayawa Sarki Nashmir labarin wannan mafarki nata ba, 280 TASKARNOVELS.COM.NG domin a rayuwarta idan akwai abin da ta tsana bai wuce ta ga tashin hankalin mahaifinta ba. Lokacin da Sarki Nashmir ya ga alamun tsananin damuwa a fuskar Gimbiya Ramlatul Siyam sai ya cika da tsananin mamaki ya dube ta ya ce, "Ya ke 'yata, ina dalilin wannan damuwa taki bisa wannan al'amari da muke gani a madubin tsafina? Shin kin manta ne cewa duk duniya babu wani matsafi kama ta, kuma babu wani cikin gwarzon mayaki da ya fi ni shuhura? Na rantse da darajar tsafina da kuma kaunar da nake yi miki, inda duk mutanen duniya da aljanun duniya za su yi shirin yaki su zo nan fadata ba za su iya raba ni da ke ba!" Ya yin da Gimbiya Ramlatul Siyam ta ji wannan batu daga bakin mahaifinta sai ta yi ajiyar à sannan ta ce, "Ya kai Abbana ka sani cewa ba ni da shakkar komai bisa al'amuranka. Amma ka sani cewa, masu iya magana sun ce, "Dan Hakin da ka raina, shi ke tsone maka idanu". Ni dai abin da nake so da kai shi ne ka dauki matakin gaggawa akan wadannan makiya namu da suka 281 TASKARNOVELS.COM.NG taho. Kada ka bari su iso nan. Lallai ka tura Dakaru su tare su tun akan hanyarsu su ragargaza su". Koda jin wannan batu sai Sarki Nashmir ya sake bushewa da dariya a karo na biyu sannan ya murtuke fuska ya ce, "Ya ke 'yata ki yi sani cewa yau shekarata hamsin da hudu ke nan akan karagar mulki, kuma duk shekara sai na yi yaki da babbar kasa wacce gagarumin matsafi ke mulka, amma ba a taɓa ci na da yaki ba. Ban taba zuwa filin yaki da kaina ba sai sau daya, sa'adda gaba dayan Sarakaunan duniya suka hada KARFI DA KARFE domin su kawar da ni. Ina zuwa filin dagar na ci su da yaki a ciikin sa'a uku kacal. A wannan lokaci kina yarinya karama ba ki fi shekara hudu ba a duniya. Ki yi duba izuwa ga Madubin tsafina domin ki ga abin da ya faru a filin yakin a wancan lokaci". 282 TASKARNOVELS.COM.NG Koda gama fadin hakan sai Sarki Nashmir ya yi nuni da hannunsa izuwa ga wani katon farin Allo na zinare da ke fadar. Nan take filin yaki ya baiyana cike da abokan gaba kimanin Dakaru miliyan dubu daya. A gefe daya kuma Dakarun Sarki Nashmir ne basu fi su miliyan goma ba. Koda Dakarun Sarki Nashmir suka ga tsananin yawan abokan gabarsu sai suka firgice suka juya da baya suka zaburi dawakansu domin su gudu, amma sai abokan gabar suka taso su a gaba a kan dawakai suna kure musu gudu suna rafke su. Wohoho! Nan fa aka fara cinikin daukar rai, ihun mazaje ya cika dodon kunne, sannan jikin bil'adama ya rinka shawagi a sararin sama, jini kuwa ya dinga feshi da fantsama yana malala a kas kai ka ce kogin jini ne ya ɓalle. 283 TASKARNOVELS.COM.NG Kafin cikar sa'a guda an kashe sama da kaso biyu cikin kaso uku na Dakarun Sarki Nashmir. Ana tsaka da wannan masifaffen yaki ne aka ga wata dunkulalliyar guguwa ta fado daga can kololuwar sama. Nan take ta tarwatsa dukkan wadannan abokan gaba. Duk wanda yake bisa kan doki sai da ya fado kasa, wanda ke kasa kuwa sai da ya baje.Nan take wannan dunkulalliyar guguwa ta rikide ta zama Sarki Nashmir, sai ga shi ya baiyana a cikin gagarumar shigar yaki ta farin sulke sama da kasa yana rike da wadansu tagwayen takubba sihirtattu masu matukar kwarjini da ban tsoro. Sarki Nashmir ya kasance gabjejen katon mutum, ga tsawo kuma ga kauri tamkar Basamude. Gabadayan jikinsa a murde yake kamar curin nakiya, kuma cike yake da jijiyoyi da kwanji. 284 TASKARNOVELS.COM.NG Kaico! Kallo daya mutum zai yi masa ya san cewa yana da karfin Allah Ya isa! Koda baiyanar Sarki Nashmir sai gabadayan wadannan Dakarun abokan gaba kimanin su miliyan dubu daya suka yi dauki kansa shi kadai. Kaico! Tsautsayi ba a sa masa rana. Ita kuwa masifa idan ta taho babu hijabin da ya isa ya tare ta. Koda Sarki Nashmir ya ga wadannan miliyoyin Dakaru sun rugo izuwa kansa sai shi ma ya falfala da azababben gudu na gaban kwatance izuwa kansu ya ratsa ta cikinsu da karfin tsiya ya hau saransu da sukarsu. Sai dai ka ga yana tsarga gangar jikin bil'adama tamkar takardu yake kekketawa. Duk inda ya sa gabansa maza faduwa suke tamkar ana sassabe a gona. Kafin cikar sa'a uku cif gabadayan filin yakin ya cika da gawarwakin abokan gabar babu dayansu a raye.Kai ba ma su ba hatta dawakansu sun zama gawarwaki domin Sarki Nashmir ya daddatsa su kai ka ce mahauta ce. 285 TASKARNOVELS.COM.NG Filin yakin ya yi tsit! Tamkar wani mahaluki bai taɓa wanzuwa ba a wajen, in ban da sautin iska da ke kadawa babu abin da kunne ke iya ji. A dai-dai wannan lokaci ne ragowar Dakarun Sarki Nashmir da suka tsere suka fara dawowa filin yakin. Koda suka ga gagarumin aikin da Sarki Nashmir ya yi sai dukkaninsu suka zube kasa a gabansa suna masu yi masa sujjada. Nan take Sarki Nashmir ya rikide ya zama wannan gagarumar guguwar, Guguwar ta yi sama ta ɓace ɓat a cikin gajimare. Lokacin da Gimbiya Ramlatul Siyam ta gama ganin wannan al'amari a cikin madubin tsafin mahaifinta sai ta ji hankalinta ya kwanta matuka, ba ta san sa'adda murmushi ya kwace ma ta ba. 286 TASKARNOVELS.COM.NG Ta dubi Sarki Nashmir ta ce, "Tabbas yanzu na gamsu cewa babu wani mahaluki da zai iya cinka da yaki. Amma dai duk da haka ina son ka tura Dakaru su tari wadannan abokan gaba namu tun kafin su iso domin mu ga irin jarumtakarsu da karfin sihirinsu". Ya yin da Sarki Nashmir ya ji wannan batu sai ya yi murmushi ya ce, "Ya ke 'yata ki yi sani cewa, babu wata alfarma da za ki nema awajena na ki yi miki ita. Saboda haka lallai zan yi yadda kika bukata. Nan take Sarki Nashmir ya kirawo waɗansu zakwakuran mayakansa su uku wadanda ya yarda da jarumtakarsu, kuma shi da kansa ya tsuma su da tsumin tsafinsa ya umarce su da su hau kan daya daga cikin manyan hadiman aljanunsa su je su tari su Aljani Maruful Dauwaz tun gabannin su iso Birnin Hindu. kuma su tabbatar da cewa sun yanko kan Aljani Maruful Dauwaz da na abokan tafiyarsa sun zo da su". 287 TASKARNOVELS.COM.NG Nan take mayakan uku suka yi shiri suka hau kan wani Aljani wai shi SHARKAMUZA ya tashi da su sama ya luluka a cikin gajimare. Aljani SHARKAMUZA ya kasance narkeken kato wanda girmansa ya ninka na Aljani Maruful Dauwaz sau uku. A bangaren kwarjini da kira ta sadaukantaka kuwa, Aljani Maruful Dauwaz jariri ne akansa. Su kuwa wadannan zakwakuran mayaka guda uku da aka tura su kashe su Aljani Maruful Dauwaz sun kasance tagwayen sadaukai, domin uwarsu daya ubansu daya, kuma rana daya aka haife su. Tsawonsu da kaurinsu yazo daidai da na Sarki Nashmir, kawai abin da ya fi su shi ne sadaukantaka da karfin sihiri. , 288 TASKARNOVELS.COM.NG Ana kiran wadannan tagwayen sadaukai da suna, SHARMAL, ZARHUF da HAZWAN. Shi kansa Sarki Nashmir akwai wata rana da ya umarci su Sharmal da su hada karfi su ukun su yake shi domin ya jarraba iyakar jarumtakarsu. Ai kuwa da ya fafata da su sai da ya sha bakar wuya, kuma sai da suka yi masa rauni sau biyu. Da kyar ya sami nasarar bazar da su kas ya sumar da su Tun daga wannan ranar ya kara musu matsayi babba a cikin Dakarunsa babu wanda ya fi su face Sarkin yakinsa wanda ake kira RAJWAN BIN SAMMAR. Sarkin yaki Rajwan ya kasance barden jarumi, FASA TARO mai TARWATSA MAZA. 289 TASKARNOVELS.COM.NG Ya kasance gawurtaccen Sadauki wanda jarumtakarsa kiris ya rage ta zo dai-dai da ta Sarki Nashmir. Domin kuwa a ranar da suka gwada 'yar kashi sai da suka kusan yin RAGAS. Da kyar da sidin goshi Sarki Nashmir ya sami rinjaye akan Rajwan. In ba don ma ya nuna masa kwarewa da sanin makama ba da ba zai yi nasara a kan shi ba. Gabadaya mutane Birnin Hindu babu mutumin da suke tsoro sama da Sarkin yaki Rajwan domin ya fi Sarki Nashmir rashin imani da zalunci, sannan kuma shi ne wazirin Sarki Nashmir don haka ana tsoron kada Sarki Nashmir ya riga Rajwan mutuwa, muddin hakan ta faru sai Rajwan ya dora kansa akan karagar mulki da karfin tsiya, ko ana so ko ba a so ba zai bari Gimbiya Ramlatul Siyam ta hau ba. A bangaren karfin sihirin tsafi kuwa, Rajwan da Sarki Nashmir sun yi kunnen doki kuma kowa na shakkar kowa. 290 TASKARNOVELS.COM.NG Sarkin yaki Rajwan bai taɓa yin aure ba kuma a duniya babu macen da yake mutuwar so sama da Gimbiya Ramlatul Siyam, amma sai ya bar abin a cikin zuciyarsa saboda ya san cewa Wutsiyar Rakumi ta yi nesa da kasa. A kullum Rajwan ba shi da wani buri a cikin zuciyarsa wanda ya fi ya ga Sarki Nashmir ya mutu domin ya sami damar haye karagarsa, kuma ya aure 'yarsa Gimbiya Ramlatul Siyam. Bisa wannan dalili ne Sarkin yaki Najwar ya kasance mai tsananin biyayya ga Sarki Nashmir don kada ya gane abin da ke zuciyarsa kuma bai taɓa yarda ya nunawa Gimbiya Ramlatul Siyam alamun soyayya ba. Haka ya danne abin a zuciyarsa ya zamana cewa yana fama da tsananin begenta dare da rana. 291 TASKARNOVELS.COM.NG Saboda kwarjinin Gimbiya Ramlatul Siyam da kuma tsoron mahaifinta ba a taba samun wani dan Sarki ko dan Boka da ya taɓa fitowa ya nuna yana sonta da aure ba saboda a dalilin hakan ma an kashe sama da samari dubu wadanda suka yi gangancin nuna soyayya a gare ta. Dangane da ita kanta Gimbiya Ramlatul Siyam kuwa, ba ta taɓa son wani da namiji ba, kuma babu namijin da ya taɓa koda yin hira da ita tsawon dakiku sittin face mahaifinta. Tsakaninta da maza sai kallo da marmari daga nesa, amma babu wanda ya isa ya kusance ta. Hadimanta ma gabadaya mata ne. Kai idan ta dauro Gimbiya Ramlatul Siyam tana shekara ba ta ga da namiji ba face a cikin fadar mahaifinta. Wannan al'amari yana matukar daurewa mutanen Birnin Hindu kai domin suna wasiwasi a cikin zuciyarsu bisa tunanin cewa Gimbiya Ramlatul Siyam ba ta da cikakkiyar lafiya. 292 TASKARNOVELS.COM.NG Domin a matsayinta na baligar mace ya kamata a ce ta bukaci namiji.' Abin da ba su sani ba shi ne; Mahaifinta ya yi amfani da karfin sihirin tsafi wajen cire mata sha'awa, kuma an rasa wanda zai iya karya wannan sihiri Lokacin da su Sharmal suka ci gaba da tafiya bisa kan Aljani Sharkamuza a sararin samaniya sai suka kagu ainun akan su riski su Aljani Maruful Dauwaz domin sun dade basu yi kan mai uwa da wabi ba. Bisa wannan dalili ne Sharmal ya dakawa aljani ysawa Sharkamuza ya ce, "Wai shin wacce irin tafiya ce wannan kake yi ne har yanzu mun kasa cim ma abokan gabar ta mu?" Koda Aljani Sharkamuza ya ji wannan batu sai numfasa ya ce, "Ka yi mini uzuri ya shugabana. ya Shin kun manta ne cewa ku uku ne a zaune bisa kaina. Nauyin kowanne daya daga cikinku 293 TASKARNOVELS.COM.NG ya kai na giwa fa. Dole ne karfin guduna ya ragu ainun, amma ina tabbatar muku da cewa nan da sa'a biyu kacal lallai za mu riski su Aljani Maruful Dauwaz a kusa da wani daji da ake kira HIRZUL ASWAD." Koda jin wannan batu sai Sharmal ya ce, "Ni kuwa na taɓa ganin siffar wannan Aljani Maruful Dauwaz a cikin madubin tsafina a wani lokaci can baya da na yi nazari akan kogon Darul Iksina. Wai shin ya ya karfin jarumtakarsa da karfin sihirinsa yake ne?". Sa'adda Aljani Sharkamuza ya ji wannan tambaya sai ya bushe da dariya ya ce, Tabbas Maruful Dauwaz ya cika gawurtaccen jarumi kuma ya yi suna sosai a cikin jaruman aljanu na duniya amma fa na fi shi komai, abin da ya ya fi ni shi ne daukaka. A halin yanzu babu wani Aljani mai tsananin karfin gudunsa a sararin samaniya. Sannan yana da matukar juriya da naci a filin yaki da shanye wuya komai tsananinta. 294 TASKARNOVELS.COM.NG Haka kuma yana da matukar sa'a bisa duk abin da ya sa a gabansa. Saboda haka ina yin arba da shi zan yi kokari na yi masa kwaf daya cikin shammata yadda zan hallaka shi da wuri, in ba haka ba kuwa zai iya wahalar da ni matuka ko kuma idan na yi wasa mu yi RAGAS!" Koda jin wannan batu sai Sharmal, Zarhuf da Hazwan suka bushe da dariya. Hazwan ya ce, "Yaya ma za a yi mu bari har Maruful Dauwaz ya sami nasara akanka? Ai tuni za mu gama da shi. Rahila da Sarki Laffaru kuwa ta farat daya za mu gama da su, babu abin da Laffaru zai iya tsinanawa". Gabadayansu sai suka bushe da dariyar mugunta, sautin dariyar tasu ya cika sararin samaniya gaba ldaya har yana amsa kuwwa. * 295 TASKARNOVELS.COM.NG AL'AMARIN Aljani Maruful Dauwaz kuwa lokacin da suka iso tsakiyar dajin Hirzul Aswad za su gifta sai Rahila ta yi gyaran murya ta ce "Bukata ta kama ta don haka tana son a sauka kasa domin ta kawar da bukatar" Koda Aljani Maruful Dauwaz yaji haka sai ransa ya baci, ya yi tsaki ya ce, "Ai ka ji irinta! Shi ya sa bana son tafiya ta hada ni da mace, saboda ku ba kwa iya jure bukata. Inda za ki yi hakuri nan da rabin sa'a za mu isa daf da Birnin Hindu, in yaso sai nа sauka a bayan gari ki biya bukatar taki". Rahila ta ce, "In ban da abinka ai cikin dakiku kadan na hattama. Bawali kaɗai zan yi'. Koda jin haka sai Aljani Maruful Dauwaz ya saki fuka-fukansa ya yi kasa. Nan da nan ya dira akan turba cikin dajin Hirzul Aswad. Daji ne mai matukar kwarjini da ban tsoro, domin yana dauke da manya-manyan bishiyoyi 296 TASKARNOVELS.COM.NG masu yawan ganyaye a samansu, sannan akwai makeken fili wanda sama da mutum miliyan dubu za su iya yin yaki a cikinsa. Akwai manyamanyan duwatsu da tsaunika. Da saukar Aljani Maruful Dauwaz sai Rahila a yi wuf ta dirga kasa sannan ta ruga izuwa bayan Wata bishiya. Sai da ta dubi gabas da yamma, kudu da arewa ta yi nazarin wajen sosai sannan ta sugunna domin tayi bawalin. A daidai wannan lokaci ne wata irin gagarumar iska ta taso daga sararin sama ta dugunzuma hankalin su Aljani Maruful Dauwaz, domin ji suka yi kamar iskar za ta sure su ta yi sama da su, har ma sai da Sarki Laffaru ya fado kasa daga kan Aljani Maruful Dauwaz. Cikin firgici Maruful Dauwaz da Sarki Laffaru suka daga kawunansu sama. Itama Rahila ba shiri ta mike tsaye zumbur! tana mai daga kanta sama. 297 TASKARNOVELS.COM.NG Koda duk su ukun suka yi arba da abin da ke shirin faruwa sai suka firgice suka ji kamar su ruga da gudu. Ba komai suka gani ba face jaruman nan uku, wato su Sharmal bisa Aljani Sharkamuza. Aljani Sharkamuza na dira bisa turba sai dajin gaba daya ya yi girgiza da tambal-tambal kamar kasa za ta koma sama saboda tsananin nauyinsa. Sharlisa ta ruga da gudu ta dane kan Maruful Dauwaz shi ma Sarki Laffaru ya yi sauri ya koma kan Maruful Dawaz, du su biyun suka zare makamansu a lokacin da jikinsu ya kama karkarwa kai ka ce daga cikin ruwan kankara aka tsamo su. Tabbas su Rahila sun firgita ainun bisa ganin yanayin surar su Sharmal da kuma mugayen kayan yakin da suke dauke da şu. A bangaren Aljani Marufu! Dauwaz kuwa, shi ma ya razana matuka da ganin Aljani 298 TASKARNOVELS.COM.NG Sharkamuza, domin ko ba a gwada ba linzami ya Karfin bakin kaza. Tabbas ya san cewa Sharkamuza ya fi shi karfi, girma da duk abin da yake takama da shi, amma saboda taurin rai irin na Maruful Dauwaz firgitar da ya yi ba ta sa jikinsa ya kama karkarwa ba. Nan fa aka fara kallon-kallo tsakanin su Aljani Maruful dauwaz da su Aljani Sharkamuza. Ana cikin haka ne Maruful Dauwaz ya ce da su Rahila, "Duk irin bala'in da za a yi kada ku yarda ku sauka daga kaina. Kai Laffaru ka maida takobinka ka dauki kwari da baka domin babu abind a za ka iya yi a wannan gumurzu face harbi. Ni kam zan yi iya kokarina na ga cewa ba su tarfa mu ba a waje daya domin idan har suka tarfa mu kashinmu ya bushe sai sun hallaka mu. Koda gama fadin hakan sai Aljani Maruful Dauwaz ya bude fuka-fukansa ya tashi sama kadan ya tsaya cak a cikin iska sannan ya dubi Aljani Sharkamuza ya daka masa tsawa ya ce, "Ya kai wannan ma'abocin karfi da kwarji mene ne dalilinka na zuwa gare mu?" 299 TASKARNOVELS.COM.NG Koda jin aljani Sharkamuza ya ji wannan tambaya sai ya bushe da dariya, lokaci guda kuma ya murtuke fuska ya ce, "Sunana Sharkamuza ibini Zarlala na kasance daya daga cikin manyan hadiman Serki Nashmir na Birnin Hindu. Waďannan jaruman da ke tare da ni kuwa Sharmal, Zarhuf da Hazwan kenan, manyan Dakarun yaki na Sarki Nashmir. Sarkinmu ya aiko mu ne a gare ku domin mu ragargaza ku mu yi filla-filla da sassan jikinku domin kun kasance manyan abokan gabarsa masu son raba shi da 'yarsa da kuma wani sirrin tsafinsa. Idan kuna da wasiyya ta karshe ga iyalanku sai ku furtata yanzu kafin mu zare muku ruhin numfashi. Lallai za mu isar da wasiyarku. Wannan shi ne iyakar alfarmar da za mu iya yi muku." Kafin Aljani Sharkamuza ya gama rufe bakinsa sai Aljani Maruful Dauwaz ya tari numfashinsa yana mai kara daka masa tsawa a karo na biyu ya ce, "Ya kai tsohon azzalumi ka yi sani cewa karyarku ta sha karya ba ku isa ku ida nufinku 300 TASKARNOVELS.COM.NG ba akanmu. Ina tabbatar maka da cewa da cewa sai mun yi fata-fata da ku mun maishe ku gawa sannan mun dangana da fadar Sarkin naku mun kawar da shi kuma mu dauke 'yar tasa gami da sihirin tsafin nasa." Koda jin wannan batu sai Aljani Sharkamuza da su jarumi Sharmal suka fusata ainun jikinsu ya kama tsuma. Cikin bakin zafin anma Sharkamuza yai sama ya kawowa Maruful Dauwaz wawan naushi da zabgegen hannunsa. Maruful Dauwaz yai wuf ya sunkuya hannun Sharkamuza ya naushi iska amma sai iskar hannun nasa ta yi fatali da Maruful Dauwaz ta dauke shi ta makashi a jikin wani tsauni ya sulale kasa a matukar galabaice. A zaton Sharkamuza kasusuwan bayan Maruful Dauwaz sun kakkarye amma bisa mamaki sai ya ga ya mike tsaye zumbur kamar babu abin da ya same shi sannan ya zare takobinsa yana mai gyara tsayuwa. 301 TASKARNOVELS.COM.NG Duk wannan abu da ke faruwa Rahila da Sarki Laffaru na rike da gashin wuyan aljanu Maruful Dauwaz suna reto ba su yarda sun fado kasa ba. Koda ganin abin da ya faru sai Aljani Sharkamuza da su jarumi Sharmal su ma suka zare takubbansu suka sake rugawa izuwa kansa aka ruguntsume da sabon azababben yaki ya zamana cewa suna kai wa junansu sara da suka cikin zafin nama, juriya da bajinta. Shi kuwa Sarki Laffaru wanda ya fara kokarin kai harbi da kibiya sai Sharmal ya daka wawan tsalle sama daga kan Sharkamuza ya doki kirjinsa da kafa daya. Kamar ya daki tamaula haka Laffaru ya lula can baya ya gwara kai a jikin wani dutse. Nan take kan nasa ya dare jini tsa jini yai tsartuwa ya fado kasa sumamme ko motsin kirki bai yi ba. Nan fa gumurzu ya dawo tsakanin rai biyu da rai hudu. 302 TASKARNOVELS.COM.NG Wohoho! Hakika idan mutum ya ga mutuwa muraran a sannan ne yake iya yin abin da shi kansa bai taɓa tsammanin zai iya ba. Nan take Rahila da Maruful Dauwaz suka fusata ainun sakamakon ganin abin da ya faru ga Laffaru ya zamana cewa sun kara ZAGE DANTSE iya karfinsu aka cigaba da bakin artabu. Duk sa'adda takubba suka haɗu sai dai ka ga tartsatsin wuta da hayaki na tashi. Da yake su Sharmal sun kasance sadaukai masu karfin Allah Ya isa, nan da nan suka fara jigita Rahila da Maruful Dauwaz har ta kai cewa ba sa iya mai da martani sai dai kokarin kare kai. Koda aka sake dan jimawa a haka sai su Sharmal suka sami nasarar buge takobin Rahila ta fadi can gefe daya kafin ta yi wani yunkuri tuni Sharmal, Zarhuf da Hazwan sun kai ma ta hari a lokaci guda. 303 TASKARNOVELS.COM.NG Sharmal ya dankara ma ta sara a gadon bayanta, Zarhuf ya sare ta a cinyarta, shi kuma Hazwan ya soke ta a gefen kirjinta 6angaren hagu Take Rahila ta kwarara uban ihu a lokacin da jini yai feshi da tsartuwa daga jikinta sannan ta subuto daga kan Maruful Dauwaz ta baje a kas wanwar babu alamar rai a jikinta. Koda Maruful Dauwaz ya ga abin da ya faru da Rahila sai ya fusata ainun irin fusatar da bai taɓa yi ba a rayuwarsa, kawai sai ya kurma wawan ihu ya sake afkawa su Aljani Sharkamuza su duka hudun ya hau su da SARA DA SUKA ba ji ba gaji. Duk da cewa su hudun suka tarar masa sai ga shi ya zame musu alakakai domin sun kasa koda kwarzanar jikinsa. Abin da ya tayar wa da Mauruful Dauwaz hankali shi ne shi ma ya kasa yivwa koda 304 TASKARNOVELS.COM.NG dayansu rauni. In ba don ma yana da matukar naci da juriya ba da tuni sun hallaka shi. Ana cikin wannan gumurzu ne Aljani Sharkamuza ya shammaci Maruful Dauwaz ya durma masa wawan dundu a gadon baya. Saboda tsananin zafi da zogin da Maruful Dauwaz ya ji bai san sa'adda ya saki takobinsa ba ta fadi kasa kuma ya durkushe bisa guiwoyinsa ya kama amai da gudan jini. Har Sharmal, Zarhu da Hazwan sun daga takubbansu na sihiri sama za su gididdiba Aljani Maruful Dauwaz sai Sharkamuza ya yi musu nuni da su tsaya, sai suka saurara. Sharkamuza ya dubi su Sharmal ya ce, "Haba! ai abin kunya ne a ce mun kashe wannan Aljanin da makami, da karfin dantsena zan kashe shi. Gama fadin hakan ke da wuya sai aljani Sharkamuza ya cafi makoshin Maruful Dauwaz da hannun hagu sannan ya shiga gabza masa naushi da hannunsa

Chapter 11 of 18