Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yi shiru ta shiga tunani mai zurfi. Babban tashin hankalinat shi ne, ba za ta iya tafiya ta bar danta Shaddad shi kadai akan mulki ba, domin ta bi bayan su Sarki Laffaru ta wargatsa duk shirinsu. Nan fa ta fara tunanin wata dabarar da za ta yi ta wargatsa shirin nasu ba tare da ta bi bayansu ba. Sharlis ta ce a ranta, "Yanzu dai kokarinsu shi ne su sami damar da za su isa kogon Darul Iksina su dauko aljani Maruful Dauwaz domin ya je ya 24 TASKARNOVELS.COM.NG sato musu gimbiya Ramlatul Siyam 'yar Sarki Nashmir na birnin Hindu. To ai kuwa abu ne mawuyaci su iya tsallake wadannan masifu da ke cikin dazuzzukan nan biyar har su isa kogon Darul Iksina domin fiye da shekaru dubu biyu baya ba a sami wanda ya keta ta cikin su ba face shi kansa aljani Maruful Dauwaz aljanin da aka tabbatar da cewa babu kamarsa a zafin nama, karfin gudu a sama da kuma tsananin juriyar wuya kowacce iri ce. Abu na biyu kuma shi ne, ai koda ma sun ami nasarar dauko aljani Maruful Dauwaz shiga fadar Sarki Nashmir har a dauko gimbiya Ramlatul Siyam daidai yake da tafiya neman jaki mai kaho. Domin hatta Sarki Bokayen aljanu na duniya almajirin Sarki Nashmir ne, a wajensa ya yi karatun tsafi. Tsaron da ke cikin gidan sarautar Sarki Nashmir da irin abubuwan masifun da ke cikinsa sun ninka wanda ke cikin wadannan mugayen dazuzzuka biyar na hanyar kogon Darul Iksina sau arba'in. Koda Sharlis ta zo nan a zancen zucinta sai ta bushe da dariyar murna, ta ce, "Ai babu wata hanya da burin su Sarki Laffaru zai cika, to amma duk da haka ba 25 TASKARNOVELS.COM.NG zan saki jiki ba na zuba ido kawai, dole ne na yi tunanin matakin da ya kamata na dauko, koda tsautsayi zai sa su sami nasarar daga yanzu zuwa lokacin da za su sami nasarar dauko aljani Daruful Dauwaz." Wannan shi ne abin da ya faru a birnin Kufa bayan ɓacewar Sarki Laffaru. ***** AL'AMARIN su boka Muzaffar kuwa, kamar yadda boka Muzaffar ya bayar da shawara haka aka yi, wato sai da aka kwana biyu suna jinyar jikinsu ya zamana cewa dukkanninsu sun ji kwarin jikinsu sannan suka yi shiri domin su shiga daji na farko. Bayan kowa ya gama kintsawa sai sukai cirkocirko gaba dayansu aka rasa wanda zai fara wucewa kan gaba, har ita kanta kuwa gimbiya Rahila saboda tsananin fargaba da tunanin abinda ke cikin dajin. 26 TASKARNOVELS.COM.NG Koda ganin haka sai boka Muzaffar ya dubi sadauki Haiman ya ce, Ya kai wannan jarumi mai jarumtakar ban al'ajabi ka yi sani cewa yanzu ne zamu shiga dajin Maridai, kai kadai ne za ka iya tarwatsa wadannan Maridai mu kutsa ta cikinsu mu wuce. Saboda haka kai ne za ka wuce gaba sanann gaba dayanmu mu bi ka a baya. Koda jin wannan batu sai sadauki Haiman ya zare takobinsa ya wuce gaba. Da ganin haka sai jaruma Shadira ma ta goya yaro Masnur a baya, jarumi Imran ya goya mahaifiyarsa, gimbiya Zarina ta goya dan uwanta sarkin Farisa. Al'amarin da ya dugunzuma hankalin sadauki Shaharan ke nan, domin shi ba zai iya daukar dokinsa ba. Koda boka Muzaffar ya ga hankalin Shaharan ya tashi ainun, sai ya yi dariya, sannan ya dubi aljani Marhabul Zaurus ya ce, "Dauki dokin Shaharan ka taho da shi. Cikin matukar firgici 27 TASKARNOVELS.COM.NG aljani Marhabul Zaurus ya dubi boka Muzaffar ya ce, haba ya shugabana ya za ka ce na karawa kaina nauyi alhalin ka san irin bala'in da za mu shiga a cikin wannan daji. Cikin fishi boka Muzaffar ya dakawa Marhabul Zaurus tsawa ya ce, "Ba wai rokonka nake ba umarni nake ba ka. Bisa dole Marhabul Zaurus ya dauki dokin sadauki Shaharan ya dora shi a gadon bayansa,sannan aka ci gaba da tafiya. Sadauki Haiman na kan gaba, jaruma Shadira na biye da shi, sai Zarina, Imran da Shaharan. Boka Muzaffar, Sarki Laffaru, gimbiya da Rahila ne a karshe sai kuma aljani Marhasul Zaurus wanda ke goye da dokin Shaharan. Hakan dai suka ci gaba da tafiya har suka wuce iyakar dajin da suka baro suka shiga cikin farkon dajin gaba daya, wato dajin mugayen Maridai. Da shigarsu cikin wannan daji sai suka kamu da matukar fargaba. In ka dauke jaruman guda hudu da gimbiya Rahila da boka Muzaffar gaba daya sauran abokan tafiyar jikinsu karkarwa yake kamar wadanda aka tsoma a 28 TASKARNOVELS.COM.NG cikin ruwan kankara. Ba komai ne ya haddasa hakan ba face ganin yanayin wannan daji. Wadansu irin gabza-gabzan bishiyoyi ne a dajin dogaye masu siffofin mutane kirar mutanen farko. Babu abinda zai bai wa mutum mamaki face yadda siffofin bishiyoyin suka zama haka tunda ba sassakasu aka yi ba, a haka suka tsiro suka girma. Da zarar mutum ya kalli bishiyoyin sai ya ji zuciyarsa na dukan uku-uku saboda munin siffofinsu kuma sai ya ga kamar za su kawo masa hari a ko yaushe. Dajin ya yi tsit tamkar wani abu mai rai bai taɓa wanzuwa ba a cikinsa, amma da zarar su sadauki Haiman sun taka busassun ganyayyakin wadannan bishiyoyi sai ka ji karar ruburбushewar ganyayen ta cika dodon kunne, kuma ta cika dajin gaba daya harda amsa kuwwa. Ga shi babu inda mutum zai taka inda babu ganyayen. Abin da su Haiman basu sani ba shi ne, wannan kara ta ganyaye ita ce alamar da mugayen maridan suke ganewa cewa an shigo cikin mahallinsu. 29 TASKARNOVELS.COM.NG Kwatsam! Ba zato ba tsammani sai ga wadannan zabga-zabgan Maridai suna fitowa daga cikin wadansu ɓoyayyun ramuka a karkashin kasa tamkar an tashi matattu a makabartar da ta kunshi gawar da ba ta da dadi. Koda su Haiman suka yi arba da wadannan Maridai sai suka firgice ainun, nan take dukkaninsu suka ji sun yi nadamar baro kasashensu don cika burin kansu. Shi kansa sadauki Haiman da aka ce shi ne zai iya tarwatsa maridan sai da ya tsorata ainun ya raina kansa, domin ya tabbatarwa kansa cewa boka Muzaffar karya ya yi da ya ce da shi shi ne zai iya tarwatsa su, domin ido ba mudu ba ne amma ya san kima, kuma ko ba a gwada ba linzami ya fi karfin bakin kaza. Sadauki Haiman yaji kamar ya yar da takobinsa ya juya da baya a guje, amma da ya ga cewar tuni maridan sun yi musu kawanya babu hanyar gudu sai ya tsaya cak! Hakika masu iya magana sun yi gaskiya da suka ce, "Idan mutum ya ga mutuwa ta ritsa shi, to fa a sannan ne yake zama jaurmin dole, domin ya 30 TASKARNOVELS.COM.NG ceci rayuwarsa ta kowane hali." Lokacin da sauran jaruman tafiya suka ga sadauki Haiman ya tsaya cak bai yi yunkurin komai ba sai kallon maridan yake kawai sai suma suka gyara tsayuwa suna wasa da makamansu. Su kuwa sauran abokan tafiyar tun sa'adda suka yi arba da halittun suka sume duk da cewa ana goye da su. Shaharan, Sarki Laffaru ne kawai ba su suma ba saboda su ma zuciyoyinsu na sadaukai ne A iya tsawon rayuwar wadannan Maridai a dajin shekaru dubu biyu baya ba su taɓa ganin mutane ko aljanu masu dakakkiyar zuciya ba kamar su sadauki Haiman, domin duk wanda ya yi arba da su take yake sumewa ko ya haukace, amma su ga su daram a gabansu. Sannu a hankali maridan da ke gabansu suka fara marmatsowa suna wangame manyan bakunansú masu kama da bakin rijiya da nufin su dasawa su Haiman wawaso su cinye su. 31 TASKARNOVELS.COM.NG Koda Haiman ya ga mutuwa na durfafo shi gadan-gadan sai ya ďaga takobinsa sama ya kwarara uban ihu sannan ya ruga da gudu ya durfafi maridan. Cikin hanzari sauran abokan tafiyar suka yi koyi da shi. Koda Haiman ya riski maridan sai ya hau su da sara da suka cikin tsananin zafin nama ya rinka tarwatsa su da karfin tsiya a guje yana samar musu. hanya suna wucewa, amma takobin tasa ba ta iya datsa jikinsu, sai dai mammake su suna zubewa kasa, amma da zarar sun fadi sai su mike zumbur a ci gaba da kasa tsere da su. Jaruma Shadira, sadauki Imran, gimbiya Zarina, gimbiya Rahila da boka Muzaffar ne suka rinka taimakawa Haiman suna sara da dukan maridan ta gefe da gefe, da kuma bayansu. Babban abinda ya fi dugunzuma hankalin su Shadira shi ne, a duk sa'adda maridan suka kawo musu wafta ko sara da kaifafan faratan hannayensu idan suka goce suka sami kasa sai ka ga sun haifar da katon rami, idan kuwa bishiya suka samu sai ka ga sun datsata gida biyu, in kuwa dutse ne tarwatsewa yake ya farfashe. Haka kuma zafin naman maridan ya wuce misali, 32 TASKARNOVELS.COM.NG domin a cikin dakika biyu suna iya kawo hari goma. Nan fa maridan suka ruda su suka rikirkita su. Idan ba don gimbiya Rahila na da matukar zafin nama ba da karfin dantse da tuni maridan sun gama hallaka dukkan abokan tafiyar da ke bayan sadauki Haiman, domin ita ce take wata irin gagarumar bajinta tana kare hare-harensu ta hanyar shawagi a sama, tayi gabas, tayi yamma, kudu da arewa tana saran maridan da takobinta tana karkadar da su.Duk wannan kokarin da Rahila ke yi sai ya zamo a banza, domin ta kai cewa maridan sun far make jaruman suna faduwa kasa suna dada kai wawan taku da nufin mutsittsike su amma sai ka ga Rahila na janye su daga kasan cikin zafin nama tana kubutar da rayuwarsu. A haka aka ci gaba da gudu ana daďa ratsawa ta cikin maridan. Tunda sadauki Haiman yake gumura a yaki bai taɓa tsintar kansa a cikin bala'i irin wannan ba. Hatta bala'in da suka fuskanta a wadanna dazuzzukan da suka wuce bai kai na wannan ba. Lokacin da maridan suka ga an dauki dogon lokaci suna artabu da wadannan shu'uman mutane sai suka fara wani irin ihu 33 TASKARNOVELS.COM.NG mai tsananin karfi wanda ka iya sa mutum ya kurmance. Lokaci guda su Haiman suka kasa ci gaba da gudu suka toshe kunnuwan da hannayensu, damar da maridan suka samu ke nan suka ritsa su a waje daya suka ci gaba da kai musu sara da suka da faratansu. Saboda karfin harin maridan da zafin namansu ya zamana cewa tun jaruman na iya kare kansu da makamansu har sun fara gajiya. Boka Muzaffar aka fara cakawa tsinin farce a saman kafadarsa. Farcen maridin ya faso ta bayansa, Muzaffar ya kwarara uban ihu sakamakon mugun zafin da yaji. Maridan na zare farcen nasa daga cikin kafadar Muzaffar sai jini yai tsartuwa, Muzaffar ya fadi kasa sumamme. A sannan ne hankalin sauran jaruman ya dugunzuma ainun domin sun zata ma boka Muzaffar ya mutu. Shi kuwa Sarki Laffaru da ya ga abin da ya faru ga boka Muzaffar abin dogaronsa sai yai sauri ya kwanta a kasa ya yi kamar ya mutu saboda sanin cewa ba zai iya tsinana komai ba a wannan gumurzu. 34 TASKARNOVELS.COM.NG A dai-dai wannan lokaci sadauki Imran ba karamin kokari ya yi ba yana ta bubbuge kawunan maridan da sandarsa kuma yana samin damar tarwatsa su amma jaruma Shardira ta fi shi kokari domin a duk sa'adda ta dana kibiyoyinta ta harba sai dai ka ga kibiyoyin na cakewa akan maridan suna faduwa kasa amma saboda taurin ransu da nacinsu sai dai ka ga sun sa hannu sun zare kibiyar sun mike tsaye sun ci gaba da kai mugun hari duk da cewa jini na zuba a jikinsu. Ita kuwa jaruma Zarina abin da ya taimake ta kawai shi ne, ta iya zulliya matuka. Duk ta inda maridan suka kawo ma ta farmaki sai ka ga ta goce ba sa samunta, amma tashin hankalinta shi ne ta fara gajiya, don haka a ko yaushe komai zai iya faruwa. Sadauki Shaharan ma karfin gudunsa ne ya cece shi domin a tsakiyar dodannin yake ta tsala gudu yana shiga karkashinsu, wani lokacin har jikinsu yake hawa yana gudu suna kawo masa mangari yana gocewa. Inda matsalar take shi ne, shi ma ya fara gajiya su kuwa maridan ko alamar gajiya ba sa yi, kamar ma kara kuzari suke. Ana cikin haka 35 TASKARNOVELS.COM.NG ne wani maridi mai shegen naci ya shammaci Imran ya yi masa dundu a take Imran ya baje a kasa da ruf da ciki a lokacin da ya ji kamar kasusuwan bayansa sun kakkarye, don haka sai ya kasa mikewa. Maridin ya daga hannu zai caka faratansa a gadon bayan Imran. Koda Shadira ta hango abinda ke shirin faruwa sai ta daka wawan tsalle daga inda take ta dira a inda Imran ke kwance da nufin ta dauke shi, da yake zafin naman Maridin ya fi nata, sai ya sami nasarar kartar hannunta a lokacin da ta sami nasarar janye Imran har ya juyo da fuskarsa ya ga irin ceton da ta yi masa. Nan take hannun Shadira ya dare jini ya yi feshi, itama ta kwala ihu kuma ta fadi kasa a galabaice. Koda Imran ya ga yadda Shadira ta ceci rayuwarsa kuma ya ga abinda ya faru gare ta, sai ya fusata ainun ya daka tsalle sama tamkar an cilla shi daga cikin baka ya narkawa wannan maridi sanda aka. Take kan maridin ya tarwatse ya kife a kasa matacce. 36 TASKARNOVELS.COM.NG Koda ganin haka sai Imran ya buďu baki ya buɗe muryarsa gaba daya ya yiwa sauran abokan tafiya bushara da su yi kokarin dukan kan maridan domin anan lagonsu yake. Kamar maridan sun fahimci abinda Imran ya fadawa 'yan uwansa sai suka daina sunkuyo da kawunansu. Nan fa bala'i ya kai bala'i, masifa ta yi masifa, turnuku ya kara tsanani. Zarina na cikin yin zilliya a karkashin maridan sai wani maridi ya tarfa ta ya naushe ta a kirji ta baje a kasa tana numfashi sama- sama, kuma tana gani dishi-dishi. Kawai sai maridin ya daga kafarsa zai tatsileta. Cikin bakin zafin nama Shaharan ya janyeta daga kasan amma kafin ya bar wajen kafar maridin ta take tasa kafar, fit sai babban dan yatsansa ya fice ya tsandara ihu, amma saboda juriya bai yarda ya fadi ba sai ya sungumi Zarina ya goya ta a bayansa ya ci gaba da gudu a tsakankanin maridan. Sai da aka shafe sa'a guda cur ana wannan bakin gumurzu ya zamana cewa babu wanda maridin ba su yi wa rauni biyu zuwa uku ba face Sarki Laffaru da kuma 'yan uwan jaruman wadanda dama tuntuni su tsoro ya sumar da su. Shi kuwa Laffaru don ya бuya ne a kasan boka Muzaffar wanda shi ma tunda ya suma bai farfado ba. A 37 TASKARNOVELS.COM.NG wannan lokaci ita kanta Rahila ta gaji ainun har ta fara sarewa ta sallama cewa lallai duk hallaka za su yi. Sadauki Haiman ma ya karaya, domin ta kai cewa da kyar yake iya ci gaba da tarwatsa maridan kuma ga shi tunda maridan suka kewaye su a waje daya ake ta gumurzun sakamakon ihu da maridan suke ta yi ba su fasa ba. A wannan lokaci aljani Marhabul Zaurus ne kadai bai gaji ba, amma shi ma ya san cewa in dai aka kara 'yan dakiku a haka shi ma ba zai kai labari ba Lokacin da aljani Marhabul Zaurus ya ga mutuwa muraran na shirin afko masa sai ya tuna cewa shi aljani ne yana da fuka-fukai da zai iya tashi sama ya dunga dukan kan maridan, kawai sai yai kundunbala yai sama yana mai surar sadauki Haiman da gimbiya Rahila suka kama shawagi akan maridan suna saran kawunansu. Ai kuwa sai ga shi maridan na zubewa kasa matattu kamar ana sassabe a gona. Damar da suka samu ke nan suka sauko kasa cikin zafin 38 TASKARNOVELS.COM.NG nama suka kwashe, dukkan abokan tafiyar tasu sannan suka ci gaba da ragargazar maridan. Al'amarin da ya dugunzuma hankalin maridan kenan domin su kansu ba su taɓa shiga bala'i ba irin na wannan rana domin ba su taɓa haduwa da shaidanun da har suka sami damar iya hallaka koda daya daga cikinsu ba. Ya yin da maridan suka ga mummunar 6arnar da aka yi musu kuma ana daďa ci gaba da yi musu sai suka fara guduwa suna shigewa cikin ramukan da suka firfito. Kafin a jima wajen ya zama babu irinsu face matattunsu. Koda ganin hanya ta samu sai farin ciki ya kama su Rahila, nan take Rahila ta umarci aljani Marhabul Zauwas da ya yi sauri ya kai su karshen iyakar wannan daji inda za su iya tsayawa su yi jinyar raunikansu ba tare da fargabar kada maridan su sake kawo musu farmakin sumame ba. Nan take kuwa aljani Marhabul Zauwas ya cika wannan umarni bai sauka a ko ina ba sai a gaban wata korama da ke karshen dajin Maridai! 39 TASKARNOVELS.COM.NG A wannan lokaci ne Sarki Lafaru ya tsugunna a gaban boka Muzaffar ya kara kunnensa a dai-dai hancinsa sai ya ji yana numfashi, cikin tsananin farin ciki Sarki Laffaru ya ruga cikin wannan korama ya debo ruwa ya watsa wa Muzaffar nan take Muzaffar ya farfado daga dogon suman da ya yi yana mai ajiyar numfashi. Nan dai aka watsawa duk wadanda suka suma ruwa suka farfado. Koda Zarina ta dawo haiyacinta sai ta je gun Shaharan ta durkusa a gabansa ta dube shi cikin tsananin mamaki ta ce, "Me ya sa ka sallama rayuwarka domin ceton tawa?". Da jin wannan tambaya sai Shaharan ya yi murmushi ya ce, "Zuciyar da ta kamu da soyayyar gaskiya ba ta shakkar mika rai da jikinta ga abin kaunarta?". Koda jin wannan batu sai Zarina ta turbune fuska ta ce, "Kaiconka ya kai wannan jarumi...Ina mai shawartarka da ka yi kokari ka goge wannan kauna daga cikin zuciyarka har sai izuwa lokacin da bukatarmu ta biya muka sami abin da muka je nema akogon Darul Iksina, amma daga yanzu har izuwa wannan lokaci ba 40 TASKARNOVELS.COM.NG za ka sami amincewar abin da kake so ba. Na yi matukar bakin ciki da ka rasa babban dan yatsanka na kafa guda daya, amma idan har ba ka sami muradin zuciyarka ba ina yi maka fatan samun madadinta. Koda gama fadin haka sai Zarina ta mike tsaye ta koma inda take. Shi kuwa sadauki Imran lokacin da ya dawo cikin haiyacinsa sai suka kama kallon-kallo tsakaninsa da Shadira. Ga shi dai ya san cewa ta ceci rayuwarsa kuma yana son ya yi ma ta godiya, amma sai ya kasa. Ba tare da ɓata lokaci ba aka shiga yi wa masu rauni magani. Mahaifiyar Imran da kanta ta sawa Imran magani. Koda ta ga yadda ya samu manyan raunika sai ta fashe da kuka. Al'amarin da ya matukar dungunzuma hankalin Imran ke nan ya rike kafadunta suka fuskanci juna sannan ya ce, "Ya ke Ummina ina dalilin wannan kuka naki?" Koda jin wannan tambaya sai mahaifiyar tasa ta yi ajiyar zuciya gami da goge hawayenta sannan ta ce, "Ya kai ďana, ka yi sani cewa ba wani abu ba ne ya sa ni wnanan kuka ba face ganin yadda 41 TASKARNOVELS.COM.NG ka sami wadannan raunika saboda kawai ka cika mini burina. Hakika wannan tsautsayi da ya same ka ya sa na yi nadama bisa neman maganin nan. In da na san cewa wannan tsautsayi zai same ka da na hakura da wannan bukata tunda dai ni na tsufa, ba lallai ba ne na kara shekaru masu yawa a duniya". Koda jin wannan batu sai kwalla ta ciko a idanunsa ya rungume mahaifiyar tasa yana mai cewa, "Ya ke Ummina ki yi sani cewa raina da lafiyata ba a bakin komai suke ba muddin zan sami damar faranta miki rai. A duk sa'adda na tuno irin tsananin wahalar da kika sha a kokarin ganin na rayu sai na ga cewa har abada babu abin da zan yi miki na saka miki da shi. Ya za a yi na kasa yin wannan tafiya alhalin na san cewa ba ki da burin da ya fi ki ga kin mike da kanki kin taka kafafunki? Sa'adda Imran ya zo nan a zancensa sai mahaifiyarsa ta sake kankame shi a jikinta, a lokaci guda duk su biyun suka fashe da kuka. 42 TASKARNOVELS.COM.NG Koda ganin wannan al'amari sai gaba dayan abokan tafiya suka kamu da tsananin tausayinsu. Wasu suka yi kwallah, wasu kuwa sai da suka zubar da hawaye. A wnanan loakci Sarkin Farisa na sa wa gimbiya Zarina magani, lokacin da shi ma ya ga raunikan da ke jikin 'yar uwar tasa sai ya kasa ci gaba da sa ma ta maganin ya kama zubar da hawaye. Da ganin haka sai Zarina ta yi murmushi ta ce "Haba ya kai dan uwana akan wane dalili zuciyarka za ta karaya bisa abinda ya samevni? Ka sani cewa farin cikinka farin cikina ne, haka ma bakin cikinka nawa ne. Har abada ba zan taɓa samun nutsuwa da kwanciyar hankali ba face na ga ka yi aure har ka haihu, sannan ne ni fa zan fara tunanin yin auren. Ka tuna cewa tun muna yara da muka taso tare komai a lokaci guda muke yi, wani ba ya riga wani, don haka har abada ina kan wannan baka ba zan sauya ba. Lokacin da gimbiya Zarina ta zo nan a zancenta sa sai Sarkin Farisa ya kara kamuwa da tsananin tausayinta ya ce, "Ya ke 'yar uwata rabin jikina 43 TASKARNOVELS.COM.NG ki ya sani cewa idan har kina son na yi aure to fa sai dai mu yi a rana daya Ina nufin a ranar da na sami lafiya. Idan kuwa ba ki amince da hakan ba to har abada ba zan yi aure ba. Koda jin haka sai hankalin Zarina ya dugunzuma ta yi shiru tana tunani, daga can sai ta lok daga kai ta dubi Sarkin Farisa ta ce, "Haba ya kai dan uwana saboda me za ka fadi haka? Sarkin Farisa ya ce, "Saboda na fuskanci cewa ko soyayyar ma ba kya so ki yi. Idan har za mu yi aure a rana guda dole ne ki nemi masoyi da wuri tun yanzu kafin lokaci ya yi domin hankalinki da shi ki tabbatar da soyayyarsa ta gaskiya yake yi miki ko saboda matsayinki yake yi miki ita ba. Tun a yanzu na fuskanci cewa kin sami wannan masoyi." Cikin matukar mamaki Zarina ta dubi dan uwanta Sarkin Farisa ta ce, "Wa kake nufi?" Sarkin Farisa ya ce, "Wanda ya ceci rayuwarki dazu a can inda muka fafata da maridai, wato sadauki Shaharan. Tabbas sadauki Shaharan ya kamu da matukar kaunarki, kuma ta kauna ta gaskiya, domin inda da akwai algus a cikin son da yake yi miki da ba zai iya sallama rayuwarsa ba da ceton taki. Koda jin wannan batu sai jikin gimbiya Zarina ya yi sanyi, ta sunkui da kanta kas kuma ta yi shiru tana tunani. Daga can sai ta 44 TASKARNOVELS.COM.NG dago kai ta dubi Sarkin Farisa ta ce, "Ya kai dan uwana ka sani cewa na yi alkawari cewa ba zan taɓa yin soyayya ba face na ga ka sami lafiya Tabbas har yanzu ina nan akan wannan batu ba zan sauya ba, saboda haka zai fi kyau ka daina yi mini batun soyayya daga yanzu har izuwa lokacin da bukatarmu za ta biya.' Da jin haka sai Sarkin Farisa ya ci gaba da sawa Zarina magani akan ciwonta, yai shiru bai kara cewa uffan ba. A ɓangaren Lumaira da mijinta sadauki Haiman kuwa, lokacin da ta farfado daga dogon suman da tayi sai ta ji ta a jikin mijinta. Cikin dimauta ta rungume shi ta kama shafa jikinsa, ai kuwa sai taji ta tabo jini a wuri biyu. Nan take hankalinta ya dugunzuma ta rasa abin da ke ma ta dadi. Kawai sai ta janye jikinta daga cikin nasa ta fashe da kuka. Cikin matukar tausayi Haiman ya ruko hannayenta ya danka mata garin magani ya ce, "Ya ke matata kukan me za ki yi kuma alhalin muna daf da samun biyan bukata? Kawai ki shafa mini wannan magani akan raunin da navji, domin ba komai 45 TASKARNOVELS.COM.NG ba ne face alamun masu tabbatar da cewa zamu sami nasarar samun abinda muka fito nema". Koda jin wannan batu sai hawaye ya zubowa Lumaira ta ce, "Ya kai mijina ka yi sani cewa zan iya zama da kai babu idanu har izuwa karshen rayuwata muddin zan rinka jin numfashinka a kusa da ni gami da koshin lafiyarka, duk da cewa ina matsayin makauniya. Ka yi sani cewa ba don komai na damu na warke daga cutar makanta ba sai dan kawai na ga irin fuskarka kafin ajálina ya riske ni, duk da cewa ina ayyana fuskarka a zuciyata. Da jin haka sai Haiman ya ji ya kara kamuwa da tsananin tausayinta. Kawai sai ya rungume ta ya kama zubar da hawaye. Duk wannan abu da ke faruwa Shadira da Masnur sun nutsu suna kallon Lumaira da Haiman. Koda yaro Musnur ya ga abin da ya faru tsakanin Lumaira da mijinta sai shi ma ya dauki garin magani ya kama sa wa 'yar uwarsa Shadira a jikin raunikanta, yana yi yana zubar da hawaye. Ga shi dai akwai alamun cewa akwai maganganu a bakinsa amma saboda ba shi da 46 TASKARNOVELS.COM.NG bakin maganar sai yai shiru kawai. Lokacin da Shadira ta fuskanci halin da dan uwanta ke ciki sai ta fashe da kuka kuma ta rungume shi a kirjinta ta kamu da tsananin tausayinsa tana mai cewa, "Ya kai dan uwana kada ka damu da wannan matsayi da ka gan ni a ciki, domin ina ji a jikina cewar bukatarmu na daf da biya. Tabbas akwai alamun cewa zamu iya shan tsananin wuya a cikin wannan tafiya, wata kila ma wasunmu su rasa rayuwarsu, amma ni dai fatana shi ne ka sami lafiya, koda zan rasa rayuwa ta. Da jin haka sai yaro Masnur ya janye jikinsa daga cikin na Shadira suka fuskanci juna ya fara bayani a gare ta cikin yaren bebaye, wato amfani da hannu ya ce, "Ya ke 'yar uwata kin sani cewa tun da iyayenmu suka mutu kika ci gaba da kula da rayuwa ta ya zamana cewa ke ce uwata, kuma ke ce ubana. Babu wani mutum wanda na shaku da shi a duniya sama da ke. Yaya kike zaton zan kasance idan babu ke? Lallai idan kika rasa rayuwarki a cikin wnanan tafiya ni ma tawa ba ta da amfani, domin ba zan taɓa samun sukuni da kwanciyar hankali ba. Duk abincin da zan sa a bakina komai dadinsa ďaci zai yi mini. Yadda na ga rana haka zan ga dare, domin bazan iya rintsawa ba. A takaice dai 47 TASKARNOVELS.COM.NG komai na duniya zai dagule mini har bakin ciki ya haddasa mini cutar ajali. Da jin wannan bayani na hannu da Masnur ya yi mata, sai Shadira ta yi sauri ta janye jikinta daga cikin nasa suka fuskanci juna. Bisa mamaki sai ya ga ta yi masa murmushi sannan tasa hannu ta share masa hawaye ta ce, "Kwantar da hankalinka ya kai dan uwana, albarkacin kaunar da ke tsakanina da kai ba zan mutu ba a cikin wannan tafiya har bukatarmu ta biya mu koma gida lafiya. Sa'adda Masnur ya ji haka sai ya cika da farin ciki, fuskarsa ta cika da murmushi. Ba shakka soyayya tana cikin litattafan yaki. ********************* Al'amarin Shaharan kuwa, lokacin da ya ga Zarina ta ki yarda ma su yi wata magana duk da cewar ya ceci rayuwarta, sai hankalinsa dugunzuma ya rasa abin da ke masa dadi, domin shi hankalinsa dai ya san cewa ya kamu da tsananin kaunarta kuma ba zai iya sarrafa zuciyarsa ba ga barin abin da take so, amma da ya dubi dokinsa ya gan shi a raye sai zuciyarsa ta yi sanyi, ya ji, dadi a ransa, saboda ko ba 48 TASKARNOVELS.COM.NG komai dai har yanzu

Chapter 2 of 18