Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ci gaba da wannan dauki ba dadi har tsawon sa'a daya da rabi, a sannan ne suka iso tsakiyar dajin. Koda Tsuntsayen suka ga su Imran na neman tsira daga sharrinsu, sai suka taru gaba dayansu suka yi musu kawanya kuma suka yi musu 103 TASKARNOVELS.COM.NG rubdugu aka ruguntsume da sabon azababben yaki mai tsananin firgitarwa da tashin hankali, domin kuwa, su tsuntsayen suna yakin ne da dukkan karfinsu don ayi ta, ta kare, su ma su Imran sun jajirce iyakar iyawarsu don kare kansu. Koda aka dan jima ana wannan bakin artabu sai al'amura suka sauya, saboda jaruman sun fara gajiya. Hatta gimbiya Rahila ma ta gaji ainun har wani tsuntsu ya cafi kugunta da 'yan yatsunsa biyu ya yunkura zai yi sama da ita ke nan sai sadauki Imran ya do ki tsakiyar kansa da sanda. Tsuntsun ya rikirkice, kuma ya yi wani uban ruri sakamakon tsananin zafi da zogin da ya ji, babu shiri ya saki Rahila ta fado kasa a matukar galabaice, saboda kugun na ta ma da ya danka da yatsun kafarsa ya yi ma ta rauni har ta kasa mikewa ta ci gaba da gudu. Koda ganin halin da Rahila ta shiga sai boka Muzaffar yai wuf ya sure ta ya goya ta a bayansa ya ci gaba da gudu, kuma aka ci gaba da gumurzun a haka. 104 TASKARNOVELS.COM.NG Kaico! Tsautsayi ba a sa masa rana. Ita kuwa masifa, idan ta zo babu makawa sai ta afku, sai dai a dauki dakon hakuri dole. Lokacin da aka sake dan jimawa a cikin wannan hali sai ya zamana cewa kayan karfen da ke jikin kowa wanda ke dan ba su kariya duka ya kekkece babu mai sauran amfani, kowa sai ya fara gajiya, ya Zamana cewa mugayen tsuntsayen sun rutsa jaruman a waje daya sun kasa ci gaba da gudu, don haka sai suka ci gaba da kai musu mugayen hare-hare. Tun suna karewa da mai da martani har ya zamana cewa sun kasa mai da martanin, sai dai kare kai. Tafiya gaba-gaba dai sai kare kai din ma ya gagara. Wayyo! A wannan lokaci ne fa Tsuntsayen suka fara yiwa jaruman mugayen rauni. Sarki Laffaru ne ya fara kifewa kasa yana mai kwarara uban ihu sa'adda wadansu tsuntsaye biyu suka yi masa rubdugun sara da faratan kafafunsu a lokaci guda. 105 TASKARNOVELS.COM.NG Saran farko a kirjinsa aka lafta masa har jini yai feshi, sara na biyu kuwa a gadon bayansa ne lafcece. Jarumi Shaharan da ke ta guje-guje da zulle- zulle a tsakankanin Tsuntsayen sai shi ma wani tsuntsu ya fake shi ya make shi a fuska. Saboda karfin makuwar sai da yai katantanwa a sama sau uku sannan ya baje a kasa sumamme. Gimbiya Rahila da Zarina kuwa, wani tsuntsu ne yai musu kwaf daya da fuka-fukansa, su ma dai suka yi ďaiďai a kasa ko kyakkyawan motsi ba su kara yi ba. Haiman, Shadira da boka Muzaffar kuwa, a kafafunsu aka laf-lafta musu sara, suka yi tsugunnon dole suna kwarara ihu sakamakon tsananin zogi da radadin da suka ji. Nan take jini ya rinka zuba a jikinsu, kuma jiri ya debe su suka kwanta a kas bisa dole suka rungumi Raddara kawai suna jiran su ji mutuwarsu domin babu abinda za su iya tsinanawa don kare kansu. 106 TASKARNOVELS.COM.NG Lumaira mahaifiyar Imran da Sarkin Farisa kuwa, tuni duk sun suma, ba don samun rauni ba, sai saboda tsananin firgita bisa ganin wannan gagarumar masifa da suka tsinci kansu a ciki wacce tafi karfin jaruman da ke kokarin kare lafiyarsu. Nan dai ya zamana cewa babu sauran jarumi guda daya da ke tsaye a cikinsu face sadauki Imran, shi ma albarkacin iya sarrafa wannan sanda da ke hannunsa ne yasa ya kai labari. Koda Tsuntsayen suka ga saura jarumi Imran shi kadai a tsaye yana fafatawa da su, sai suka ja da baya gaba dayansu suka tsaitsaya a sama cak! Cikin iska kamar hadin baki, kai kace hutawa suke. A lokacin ne shi ma jarumi Imran ya tsaya cak! Ya gyara tsayuwa rike da sandarsa gamgam da hannu biyu, yayin da jini ke satatowa ta kan gefen hannunsa na hagu sakamakon wani lafcecen yanka da ke kan kafadarsa. 107 TASKARNOVELS.COM.NG Imran ya dudi gabadayan jarumai abokan tafiyarsa ya gansu gabadaya a kwance a kas cikin mugu hali kamar ma wasunsu sun mutu, domin babu alamar rai a jikinsu. A sannan ne ya tuno da mahaifiyarsa, wacce ke goye a bayansa, kawai sai ya kira sunanta, ai kuwasai ya ji shiru. Cikin firgici! Ya taɓo kanta da hannunsa guda, sai yaji kan ya langabe alamar babu rai a tare da ita. Cikin gagarumin fushi Imran ya takarkare ya kwarara uban ihu ya falfala da matsanaicin gudu izuwa kan wadannan Tsuntsayen da dukkan fushinsa da karfinsa da nufin a yi ta, ta kare ko shi ko su! Ai kuwa su ma Tsuntsayen sai suka taso masa gaba dayansu suna yin wannan ruri mai iya kurmantar da bil'Adama, amma shi bai ma san suna yi ba. 108 TASKARNOVELS.COM.NG Kafin ya hade da Tsuntsayen tuni ya daka wawan tsalle sama tamkar an cilla shi daga cikin baka ya tari Tsuntsayen ya hau dukansu da sandarsa a cikin bakin zafin nama da dukkan iyakar karfin dantsensa. Bisa tsautsayi kuwa sai ya sami daya daga cikinsu Tsuntsayen a ido. Nan take idon tsuntsun ya fashe, ya sulalo kasa. Ji ka ke tim! kamar giwa ta fadi, don har sai sa dakasa ta yi girgiza. Tsuntsun ya baje matacce a kas ko shurawa bai yi ba. Koda Imran ya ga ya sami wannan nasa ta gano lagon Tsuntsayen sai ya ci gaba da dukan idanun Tsuntsayen da sandarsa. Ai kuwa sai ga shi yana karkaɗosu kasa suna mutuwa. Babu abin da zai yi matukar burge mutum a wannan gumurzu face yadda Imran yake daka tsalle sama tamkar fuka-fukai ne a jikinsa, wato 109 TASKARNOVELS.COM.NG a sama yaci gaba da gumurzun da Tsuntsayen. Wani lokacin ma sai dai ka ga yana tattaka Tsuntsayen tamkar yana taka matattakalar bene. Abinka da Sarkin yawa ya fi Sarkin karfi, a hakan ne wasu Tsuntsayen suka rinka kai masa sara da suka. Wani loakcin ka ga sun same shi jini na tsartuwa da feshi a jikinsa yana kwarara uban ihu, amma saboda bakin naci da dakewar zuciya da juriya shi ma bai fasa ragargazar su ba. Abin da ya ayyana a ransa shi ne, koda wadannan Tsuntsayen za su kashe shi sai ya tabbatar da cewa shi ma ya yi musu muguwar бarna da yawansu tun da dai ya gano lagonsu. Haka dai aka ci gaba da wannan mummunan artabu tsakanin jarumi Imran da mugayen tsuntsayen har izuwa tsawon sa'a guda, ya zamana cewa ya kashe fiye da kaso biyu cikin 110 TASKARNOVELS.COM.NG ukunsu, amma fa a wannan lokaci ya gaji ainun, har ba ya iya yin tsalle sama a kasa yake yakin. Wani lokacin ma idan suka make shi sai ya baje a kasa kamar ya mutu, amma da zarra sun yi caa! a kansa za su yagalgala shi sai su ga ya mike zumbur! Ya ci gaba da ragargazar su tamkar ma a sannan ya fara yakin. Kai wani lokacin ma har lambo yake yi wa tsuntsayen ya yi kamar ya mutu, sai dai kawai su ga ya sake mikewa ya ci gaba da kashe su. Su kansu wadannan mugayen Tsuntsayen a iya wanzuwarsu a cikin wannan daji ba su taɓa haduwa da takadarin bil'Adama mai taurin rai ba kamar Imran. Koda Tsuntsayen suka ga Imran ya yi musu gagarumár ɓarna, kuma ga shi sun kasa kashe shi sai suka karaya, suka dauka cewa ba za su iya kashe shi ba, don haka ba shiri su duka suka 111 TASKARNOVELS.COM.NG yi sama suka luluka izuwa can kololuwar sama, suka bar nahiyar dajin gaba daya. A dai-dai wannan lokaci ne Imran ya kama layi da tangadi kamar wanda ya sha giya ya bugu, sakamakon jinin da ke zuba a cikin sassan jikinsa. Bai ma san sa'adda sandarsa ta suбuce daga hannunsa ba. Tabbas a wannan lokaci inda Tsuntsayen na kusa da salin-alin za su sa masa wawa su cinye shi, ko ruburbushin jikinsa ma ba za su rage ba, domin ba zai iya kare kansa da komai ba, saboda dukkan karfinsa ya kare. Inda Tsuntsayen sun san cewa haka za ta faru da tabbas basu gudu ba! Nan take Imran ya kife kasa sumamme. In da ace akwai mutum tsaye a filin da aka yi wannan bakin gumurzu da dole ya ce kowa ya mutu, domin babu wanda yake numfashi daga cikin su Imran. 112 TASKARNOVELS.COM.NG Wajen gaba daya ya yi kaca-kaca da jini da kuma gawarwakin wadannan tauntsaye abin ba kyan gani. Sai bayan kusan sa'a biyu lokacin da wata irin iska mai tsananin sanyin gaske ta fara kadawa sannan jaruna Shadira ta farfado ita kadai. Tana bude idanunta ta ji gaba daya jikinta yai ma ta nauyi tamkar an danne ta da katon dutse, don haka sai ta kasa mikewa tsaye. Koda ta dubi filin yakin ta ga gabadayan abokan tafiyarta a kwance babu mai numfashi, sai ta fashe da kuka, domin a zatonta kowa ya mutu babu sauran mai rai. Nan fa ta fara jan jiki tana tafiya a hankali da kyar har ta isa inda jarumi Imran ke kwance. Shadira ta dago da kan Imran ta ga baya motsi, kuma babu alamar numfashi a jikinsa, sai kawai ta rungume kansa a kirjinta ta dada fashewa da matsanaicin kuka na bakin ciki. 113 TASKARNOVELS.COM.NG Ruwan hawayenta da ke zuba akan fuskara ne ye zamo sanadin farfadowarsa daga dogon suman da yayi. Nan take Shadira ta ji Imran ya rike kafadarta da hannunsa guda. Koda ta ji haka ta gane cewa bai mutu ba sal ta bushe da dariya ta sake rungume shi a kirjinta cikin tsananin farin ciki. Shi ma sai ya kama dariyar murna. Sai da suka daďe a kankame da juna suna ta dariya kamar ba za su saki juna ba. Bayan sun dawo cikin haiyacinsu ne duk su biyun suka dubi sauran abokan tafiyarsu, suka ga cewa har yanzu fa su biyu ne rak! Suka mike, sai hankalinsu ya dugunzuma ainun. Imran ya dubi Shadira a lokacin da hawaye ya subuto masa, ya ce, "Yanzu mu biyu ne rak ke nan muka tsira da rayuwarmu a wannan daji?" Koda jin wannan tambaya sai ita ma hawaye ya zubo ma ta ta ce, "Haka dai yanayi ya nuna, amma zai fi kyau mu tashi mu duba kowa, babu mamaki akwai sauran mai rai, domin kaicma na fitar da rai da kai, amma kuma sai ga shi ka mike". 114 TASKARNOVELS.COM.NG Koda jin wannan batu sai Imran yaji ya sami kwarin zuciya gami da farin ciki. Kawai sai ya yunkura ya mike tsaye da kyar yana tangadi kamar ba zai iya taku daya ba. A haka ya nufi inda sauran abokan tafiyar ke kwance yana harde kafafu kamar zai fadi, domin har a sannan bai daina jin jiri ba. Ita kuwa Shadira sai ta sake yunkurawa domin ta mike tsaye amma sai ta kasa. Imran ya je kan kowa daya bayan daya ya girgizavsu amma har ya gama duba su duka bai ga mai alamar rai ba. Koda ganin haka sai ya durkushe kasa bisa guiwoyinsa ya fashe da kukan bakin ciki. Koda Shadira ta hango halin da yake ciki sai ta ci gaba da jan ciki har ta riske shi sannan ta kwanta akan kirjinsa ta ci gaba da tayavshi kukan. Da ma Imran mahaifiyarsa ce wadda ya duba daga karshe don haka, yana kankame da ita 115 TASKARNOVELS.COM.NG yana ta kuka, a lokacin da ya ji ya tsani kansa, kuma ya tsani duniyar gaba daya. Bayan sun yi kuka har sun gaji sai Shadira ta dago da kanta daga kan kirjinsa ta dube shi ta ce, "Ya kai masoyina, wai shin yanzu mene ne amfanin rayuwarmu a doron kasa? Na rasa dan uwana Masnur, kai skuma ka rasa mahaifiyarka. Dukkan burinmu na duniya ya yanke. Yanzu ga shi abokan tafiyarmu kaf ďinsu sun mutu. Mene ne amfanin zuwanmu kogon Darul Iksina tunda wadanda za mu je dominisu babu su? Sa'adda Shadira ta zo nan a jawabinta sai Imran ya sake fashewa da matsanaicin kuka, ya ce, "Hakika rayuwarmu ba ta da wani amfani, gwara ma ace mu ma duk mun mutu" Koda jin wannan batu sai Shadira ta yi murmushi ta ce "Ai kuwa ni yanzu farin cikin da ya rage mini a nan duniya kawai shi ne, na mutu akan kirjinka, ko ba komai na mutu tare da masoyina na biyu wanda na so shi fiye da komai. Ka sani cewa in ban da dan uwana Masnur da na rasa babu wanda zuciyata ta aminta da shi kuma take kauna da gaskiya sama da kai! Koda jin haka sai hawayen farin ciki ya zubowa Imran daga can 116 TASKARNOVELS.COM.NG kuma sai ya ce, ba shakka kin zo da shawara to amma ta yaya za mu mutu a tare ba tare da ďaya ya riga ďaya mutuwa ba? Shadira ta, mu nausa cikin daji watakila mu haďu da wata muguwar dabbar, sai mu sallama mata kanmu ta cinye mu ko kuma mu nemi katon tsauni mu hau karshensa sai mu rukunkume juna mu sallamo kasa bisa duwatsu mu hallaka. Koda jin haka sai Imran ya ce, "Tabbas kin zo da shawara mafi kyau". Nan take Imran ya ajiye mahaifiyarsa a gefe daya ya kura mata idanu sa'adda hawaye ya ci gaba da shatata bisa kan kumatunsa har izuwa tsawon 'yan dakiku, sannan ya ce, "Ya ke Ummina ki gafarce ni, hakika zan mutu da tsananin bakin ciki bisa rashin samun nasarar cika burin zuciyata. Na so a ce na mutu akan hannunki domin na nemi gafararki bisa abin da na kasa cikawa, 117 TASKARNOVELS.COM.NG amma idan har akwai wata rayuwar bayan wannan na yi miki alkawari sai na cika miki burinki.. Haka dai Imran ya ci gaba da surutai barkatai ba tsari. Koda Shadira ta fuskaci alamun yana neman zautuwa sai ta yunkura da kyar ta kama hannayensa suka mike tsaye tare ta jan shi suka kama dingishi suna tafiya har suka yi dan nisa da wajen. Ai kuwa nan take suka yi arba da wani rami mai zurfin gaske a gabansu. Kawai sai suka dubi juna suka yi murmushi. Ba tare da jiran komai ba suka durfafi wannan rami ko kallon gabansu ba sa yi, sai kallon fuskokinsu suna yi wa juna murmushin karshe. Saura taku uku kacal tsakaninsu da ramin sai kawai Imran ya ji an kwala masa kiran. Cikin dimauta da razani ya juyo baya. Koda ya ga wanda ya kira sunan nasa sai ya cika da 118 TASKARNOVELS.COM.NG tsananin mamaki gami da farin ciki mara misaltuwa. Ba wani ya hango ba face mahaifiyarsa tana rarrafe ta tunkaro su kuma hawaye na zuba daga idanunta. Nan take Imran ya ruga da gudu izuwa gare ta ya sure ta ya rungumeta a kirjinsa. Shi da ita suka bushe da dariyar murna, ya kama sumbatar ko ina a fuskarta yana mai cewa, Ashe ba ki mutu ba ya Ummana, ashe ba ki mutu ba" Mahaifiyar tasa ta rike fuskarsa da hannayenta biyu ta ce, "Ya za a yi na mutu alhalin kana raye a doron kasa, kuma akwai alkawari a tsakaninmu? Ya kai dana, kayi sani cewa na dade ina mafarkin cewa burinmu ya cika, ina tabbatar maka da cewa ban taɓa yin mafarki bai tabbata ba. Lallai ina ji a jikina cewa, komai wuya, komai rintsi sai na sami lafiya na taka kafafuna ka gani da idanunka. Koda mahaifiyar Imran ta zo nan a zancenta sai Imran ya sake rungume ta a kirjinsa ya fashe da kukan farin ciki, tana mai tayavshi kukan. 119 TASKARNOVELS.COM.NG Jaruma Shadira da ke tsaye a can bayansu tana kallonsu cikin tsananin murna sai ta taho gare su ita ma ta rungume su ta taya su kukan farin cikin. Ba zato ba tsammani sai suka ji motsi yai yawa a bayansu. Koda suka waigo sai suka ga ashe sauran abokan tafiyar su ne suka farfado daga dogon suman da suka yi daya bayan daya. Cikin tsananin farin ciki suka karaso gare su suna tashinsu zaune. Nan fa aka shiga taimakon juna. Masu manyan raunika a jikinsu aka rinka dinke musu raunin, raunin da za a sa masa magani aka sa masa maganin. Zarina ce ta dinkewa Shaharan manyan raunika guda biyu da ke jikinsa da hannunta, ita kuma dan uwanta Sarkin Farisa ya dinke nata raunin da kansa. 120 TASKARNOVELS.COM.NG Lokacin da Zarina ke dinkewa Shaharan rauninsa ne Sarkin Farisa ya lura da cewa Zarina da Shaharan suna satar kallon juna suna murmushi, don haka sai ya gane cewa lallai akwai soyayya mai karfi a tsakaninsu. A iya sanin da Sarkin Farisa ya yi wa Zarina ba ta taɓa koda taɓa wani da namiji ba face shi, kuma bai taɓa ganin ta yi wa wani murmushi ba sai shi, amma yau gavshi ta damu bisa ranin da ke jikin Shaharan har ta yi masa magani da hannunta, kuma tana yi masa murmushi. Koda Zarina ta ga cewa dan uwanta ya fuskanci tana son Shaharan sai kunya ta kama ta kuma hankalinta ya dugunzuma, domin ta karya alkawarin da ta dauka cewa ba za ta yi aure ko soyayya ba face ta samowa dan uwanta maganin cutar da ke jikinsabCikin tsananin takaici da damuwa Zarina ta mike tsaye tsam! daga gaban jarumi Shaharan ta koma can gefe daya ta yi tagumi a yayin da idanunta suka ciko da kwalla tana mai bakin cikin saba alkawarin da ta yi. 121 TASKARNOVELS.COM.NG A can gefe daya kuwa, gimbiya Rahila ce take sa wa Sarki Laffaru magani akan raunikan da ke jikinsa, ita kuma boka Muzaffar na sanya mata. Shi kuma aljani Marhabul Zaurus ne yake sa masa maganin. Abin da ya daurewa kowa kai a wajen shi ne aljani Marhabul Zaurus ya fi kowa samun yawan raunika a jikinsa a wannan bakin gumurzu da aka yi a daji na uku, amma kuma yafi kowa jure raunikan kuma da kansa ya yi wa kansa magani. Dokin Shaharan kuwa, shi kadai ne bai sami rauni ko daya ba sakamakon kariyar da aljani Marhabul Zaurus ya ba shi, ya lulluɓe shi da dukkan fuka-fukansa, don haka duk harin da aka kawowa dokin akan Marhabul Zaurus yake karewa. Lokacin da Sarkin Farisa ya ga 'yar uwarsa Zarina ta koma can gefe daya ta zauna sai ya dubi jarumi Shaharan ya ce, "Ya kai ma'abocin 122 TASKARNOVELS.COM.NG gudu, ka yi sani cewa kai ne saurayi na farko da 'yar uwata ta nunawa soyayya a duniya. A dalilin son da samari ke yi mata, da yawansu sun hallaka bisa kamuwa da cutar begenta a zukatansu. A tunanina, har abada babu wani mahaluki da zai iya bai wa 'yar uwata farin ciki face ni kaina, amma yanzu na karyata kaina kuma na yi imani cewa kai za ka iya ba ta dukkan farin cikin rayuwa. Na sani cewa ka dade kana begen 'yar Sarkin garinku a cikin zuciyarka, kuma ka baro kasarku ne domin ka yi gasar tseren doki ta neman auren 'yar Sakin naku. Ina mai tabbatar maka da cewa 'yar uwata tafi 'yar Sarkinku kyau, ta fita karfin mulki da arziki. Ina ji a jikina cewa abu ne mawuyaci na rayu a cikin wannan tafiya tamu har burina ya cika, wato samo mini maganin cutar da ta addabe ni 123 TASKARNOVELS.COM.NG ta hana ni yin aure. Bisa wannan dalili daga yau na ba ka amanar 'yar uwata. Idan har rai ya yi halinsa ina son ka aure ta domin ka debe mata kewa ta tunda kaivne za ka iya ba ta farin cikin da take samu daga gare ni. Ka sota, So na hakika, irin wanda dan uwa ke yi wa dan uwansa, ba wai So irin wanda saurayi ke yi wa budurwa ba. Idan da hali ka So ta kamar yadda na ga mahaifiyar imran ke son danta Imran." Sa'adda sarkin Farisa ya zo nan a jawabinsa sai tausayinsa ya kama jarumi Shaharan har hawaye ya subuto masa nan take suka rungume juna. Shaharan ya ce, "Ni kuwa na yi maka alkawari lallai zan rike 'yar uwarka bisa amana da soyayya mara misaltuwa. Koda jin haka sai Sarkin Farisa ya kara Kankame Shaharan a kirjinsa yana mai yi masa godiya. 124 TASKARNOVELS.COM.NG Bayan gimbiya Rahila ta gama sa wa Sarki Lafaru magani sai ya dube ta cikin mamaki ya ce, "Ya ke wannan ma'abociyar kyawu da jarumtaka, ke kuwa me ya sa kike nuna kauna da damuwa a gare ni?" Koda jin wannan tambaya sai Rahila ta bushe da dariya. Al'amarin da ya bai wa Lafaru da boka Muzaffar mamaki ke nan. Rahila ta hade fuskarta sannan ta ce, "Shin ka manta ne cewa dukkan burina na duniya ya ta'allaka ne akanka? Kamar ydda naka ya ta'allaka akan auren gimbiya Ramlatul Siyam. Dole ne na fara nuna maka kauna tun a yanzu domin ta kowanne hali sai na aure ka sannan burina zai cika. Ni yanzu babbar matsalata shi ne, ba ni da tabbacin za mu isa can kogon Darul Iksina gabadayanmu nan a raye, domin na karaya bisa irin yanayin da muka tsinci kanmu a ciki. Da farko dai na san cewa gaba dayanmu nan babu mai jarumtakata amma sai ga shi na kasa tsinana komai a cikin wannan daji na uku da muka shigo. Ko shakka ba na yi jarumi Imran ne 125 TASKARNOVELS.COM.NG ya kashe tsuntsayen nan kuma bai isa ya kashe su ba gaba daya ina kyautata zaton dai guduwa suka yi da suka ga barnar de yake musu ta yı yawa. Ku tuna cewa yanzu fa saura mugayen dazuzzuka guda biyu a gabanmu kuma masifar da ke cikinsu ta fi wacce muka wuce a baya." Koda Lahira ta zo nan a zancenta sai jikin kowa yai sanyi kuma hankali ya dugunzuma aka yi tsit ana tunanin zuci. Tsawon 'yan dakiku dayansu bai ce uffan ba. Daga can sai sarki Laffaru ya dubi boka Muzaffar ya ce, "Ya kai abin dogaronmu wai shin yanzu idan muka ratsa ta cikin wadannan dazuzzuka biyu muka wuce lafiya, ya ya batun shiga cikin kogon Darul Iksina ya ke? Shin babu wata matsala da za mu fuskanta a cikinsa?" Koda boka Muzaffar ya ji wannan tambaya sai yai ajiyar zuciya sannan ya ce, "Ni kam dukkan ilimina ya tsaya iya nan ban san ma yadda za mu iya shiga cikin kogon Darul lksina ba kuma ban san irin matakan tsaron da ke cikinsa ba". 126 TASKARNOVELS.COM.NG Koda jin wannan batu sai ran sarki Laffaru ya ya dubi boka Muzaffar a fusace ya ce, "Ashe kai wawa ne ba ka san ciwon kanka ba! Yanzu kai da ba ka ma san yadda za mu shiga cikin kogon Darul Iksina ba amma ka debo mu muka sha wannan bakar wahala?" Kafin sarki Laffaru ya gama rufe bakinsa boka Muzaffar ya daka masa tsawa wacce ta firgita shi ainun ya ji kamar an kaɗa hantar cikinsa. Boka Muzaffar ya ce, "Ai kaine babban wawa wanda rashin hangen nesansa ya jefa shi a cikin bala'i. Ai wanda yake cikin ruwa ko bakin takobi masa kamawa zai yi. Shin ka manta da bala'in da kake ciki ne na abokiyar gabarka Sharlis? Ai da ka zauna ka jira ranar da ɗanta zai girma ya yi maka gisan gilla ya haye kan mulkinka da dukiyarka gwara ka taho neman maganin wannan barna koda kuwa ba za ka samu ba. Ka 127 TASKARNOVELS.COM.NG tuna cewa rai ba a bakin komai yake ba muddin akwai biyan bukata. Sai da Sharlisa ta sai da rayuwarta ta sha bakar wahala tun tana yarinya karama har ta girma sannan ta sami nasarar hawa kan tafarkin daukar fansa a kanka. Saboda me kai yanzu ba za ka sallama rayuwarka ba don ganin ka kubuta daga sharrinta? Gabadayan abokan tafiyar nan tamu sun sallama rayuwarsu ne don cika burin zuciyoyinsu, ga shi har daya daga cikinsu ta rasa dan uwanta, dukkan burinta ya rushe, amma duk da haka ba ta fasa ci gaba da yin wannan tafiya ba. Ai ko ba komai mun ajiye abin tarihi wanda babu wani mahaluki da ya taba yinsa, koda kuwa a iya nan tafiyarmu ta yanke. Lokacin da boka Muzaffar ya zo nan a jawabinsa sai sarki Laffaru ya shiga taitayinsa har ya bai wa Laffaru hakuri. Al'amarin da ya janyo jikin kowa ya yi sanyi ke nan. Boka Laffaru ya ce, "Ya zama wajibi mu zauna anan har tsawon mako biyu domin mu yi jinyar 128 TASKARNOVELS.COM.NG jikinmu sosai kafin mu shiga daji na biyar saboda idan muka yi gangancin ci gaba da tafiya a haka, cikin kankanin lokaci mu duka zamu hallaka". Nan take kowa ya aminta da wannan shawara ta boka Muzaffar. Ba tare da ɓata lokaci ba suka kafa tantuna sannan aka ci abinci. Bayan kowa ya huta sai suka shiga janye gawarwakin wadannan tsuntsaye suna jefa su a cikin ramin nan mai zurfi don kada su dame su da doyi, kuma kananan tsuntsaye masu cin mushe su adabbe su a wajen. Suna gama watsa tsuntsayen a cikin ramin sai suka kunna wuta suka jefa a cikin ramin. Nan take gaba dayan gawar tsuntsayen ta kama ci da wuta. Haka dai su Imran suka ci gaba da zama a cikin wannan daji suna jinyar kansu har tsawon mako biyu amam kullum a tsorace suke domin gani 129 TASKARNOVELS.COM.NG suke kamar ko yaushe ragowar wadannan tsuntsayen za su iya kawo musu MAMAYAR BAZATO. Ai kuwa tsuntsayen sun sha zuwa su yi shawagi a samansu amma wani Iko na Allah ko sau daya tsuntsayen ba su yi yunkurin kai musu hari ba. Daga karshe ma sai tsuntsayen suka ɓace ɓat tamkar ba su taɓa wanzuwa ba a dajin. A ranar da kwanaki goma sha hudu suka cika ne kowa ya ji ya sami karfin jikinsa sai dai tabon raunika kawai a jikinsu. Nan fa suka yi shiri kowa ya kimtsa sannan aljani Marhabul Zaurus su duka ya tashi da su sama aka ci gaba da taifya suka durfafi daji na hudu wanda ke dauke da muggan dabbobin daji iri-iri masu matukar hadari Da isowarsu farkon dajin sai aljani Marhabul Zaurus ya saki fuka-fukansa ya sauko kas ya tsaya cak bai motsa ba. Kowa sai ya noke ya ki 130 TASKARNOVELS.COM.NG saukowa daga kan aljani Marabul Zaurus aka kama kallon- kallo. Al'amarin da ya sa boka Muzaffar ya bushe da dariya ke nan ya ce, "Me kuke tsoro kowa ya kasa sauka kasa? Ba a sami wanda ya iya amsa masa wannan tambaya ba. Koda ganin haka sai boka Muzaffar ya sauka kas sannan ya dubi gimbiya zarina ya ce, "Gaishe ki ya mai ilimin daji ki yi sani cewa yau ne ranarki domin muna bakin daji na huďu da ke dauke da mugayen dabbobi. Ke kaɗai ce za ki iya kuбutar damu a cikin wannan daji don haka sai ki sauko ki yi mana jagora har mu isa karshen dajin". Koda jin wannan batu sai Zarina ta yunkura za ta sauko kas. Cikin hanzari sarkin Farisa ya ruko ta dube ta cikin alamun firgici da tashin hankali a lokacin da idanunsa suka ciko da kwallah ya ce, "Ya ke 'yar uwata ki yi sani cewa a halin yanzu zuciyata tana bugawa da karfi kuma ina ji a jikina cewa in dai muka shiga cikin wannan daji karshen zamanmu tare ya zo. Ni kam na hakura da wannan buri da ke gabanmu saboda 131 TASKARNOVELS.COM.NG haka mu yanke wannan tafiya tamu daga nan mu zauna anan mu jira mu ga abin da hali zai yi ko abokan tafiya za su isa can kogon Darul Iksina su dawo lafiya. Idan kuma ba su dawo ba sai mu juya da baya mu koma kasarmu. Gwara mu koma gida mu ci gaba da rayuwarmu a cikin mulkinmu muna

Chapter 5 of 18