Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ce, "Ya kai Marhabul Zaurus ina son ka sauke wannan doki da ke bayanka ka tafi izuwa can inda Zarina ta fada rami ka dauko ta tare da gawar dan uwanta ka kawo su nan gare mu. 160 TASKARNOVELS.COM.NG Sa'adda Aljani Marhabul Zaurus ya ji wannan umarni sai fuskarsa ta yamutse kamar zai fashe da kuka sannan ya dubi Muzaffar cikin tsananin damuwa ya ce, "Ya shugabana shin ka dubi halin da nake ciki kuwa yanzu? Na rasa rabin fukafukina guda, daya fuka-fukin kuma ya tsage. Ina tabbatar maka da cewa yanzu ba zan iya daukarku ba ku duka har ma na yi doguwar tafiya da ku a sararin samaniya." Koda jin haka sai Boka Muzaffar ya sake dakawa Aljani Marhabul Zaurus tsawa a karo na biyu ya ce, "Ai ba cewa na yi ka dauke mu yanzu mu ci gaba da tafiya ba, cewa na yi ka je ka dauko Gimbiya Zarina da gawar dan uwanta kawai ka dawo da su nan." Da jin haka sai Aljani Marhabul Zaurus y mika hannunsa guda ya dauke dokin Shaharan daga kansa ya sauke shi a kas sannan ya bude fuka. fukansa da kyar ya yunkura ya tashi sama yana tambal-tambal kamar zai fado kasa. Kai da gani 161 TASKARNOVELS.COM.NG ka san cewa ba karamin namijin kokari ya yi ba har da ma ya iya tashi sama. A haka dai ya luluka izuwa can sama yana tsala matsanaicin gudu har ya ɓace da gani. Bayan kamar dakika dari da ashirin kacal sai ga Aljani Marhabul Zaurus ya dawo dauke da Zarina da kuma gawar dan uwanta rungume akan kirjinta ta kankame gawar tana ta kuka. Al'amarin da ya kara karya zukatansu ke nan, su duka kowa ya kamu da tsananin tausayin Gimbiya Zarina aka kama kuka. Sai a wannan lokaci ne Zarina ta lura cewa Shaharan da Haiman sun rasa hannayensu ďai ďai. Nan fa bakin ciki ya sake lulluɓe ta, ta fashe da sabon kuka, ya zamana cewa babu wanda ba ya zubar da hawaye a wajen. 162 TASKARNOVELS.COM.NG Nan dai masu sauran kuzari a jikinsu suka haka rami aka binne Sarkin Farisa sannan aka yanke shawarar a zauna a wajen har tsawon mako uku sannan a ci gaba da tafiya. Boka Muzaffar ne ya kawo wannan shawara Koda jin haka sai jaruma Rahila ta ce, "Wai shin mene ne ma amfanin ci gaba da wannan tafiya tamu? Shin har yanzu kuna sa rai ne cewa za mu isa kogon DARUL IKSINA a raye ne? Ku dubi fa halin da muke ciki a yanzu, wasunmu sun nakasa, nakasar da har abada babu warkewa don haka fiye da rabin karfinmu babu shi. Dajin da ya rage a gabanmu shi ne dajin da ya fi kowanne daji haɗari, inda wannan katuwar Kunama take mai tsananin gudun tsiya wacce babu wanda muke sa ran zai iya tsere mata a cikinmu face jarumi Shaharan, kuma ga shi shi ma ya sami nakasa ya rasa hannunsa guda. Ta yaya kuke tsammanin zai iya gudun da zai iya tserewa wannan Kunama a haka har ya ja ta izuwa cikin wannan kogi inda za ta hallaka?" 163 TASKARNOVELS.COM.NG Sa'adda Rahila ta zo nan a zancenta sai kowa ya yi shiru aka rasa wanda zai ce kala. Daga can sai Boka Muzaffar ya dubi jarumi Shaharan ya ce, "Ya kai abin dogaronmu a cikin daji na biyar, ka ji abinda Rahila ta ce, shin gaskiya ne ba za ka iya yin gudu ba kamar yua ya kamata sakamakon wannan nakasa da ka samu?" Koda jin wannan tambaya sai Shaharan yai ajiyar zuciya ya ce, "Ko shakka babu rashin Wannan hannu nawa sai ya rage mini karfin guduna Sosai, to amma ai mai rai ba ya fid da tsammanin sa'a da rabo. Wannan lalura da ta same ni ba za ta sa mu karaya ba. Ina son mu kasance masu juriya da karfafar juna duk da cewa masifun da suka same mu a cikin wannan tafiya sun karya mana zuciya. Yanzu ga Shadira ta rasa dan uwanta Masnur, Zarina ma ta rasa dan uwanta Sarkin Farisa. Duk da hakan yanzu mu shida muka rage masu son cika burinsu a kogon Darul Iksina. Ni ina son dokina ya warke daga cutar da ke addabar kafafunsa. Haiman yana son matarsa ta warke daga cutar makanta, 164 TASKARNOVELS.COM.NG Imran yana son mahaifiyarsa ta warke daga gurguntaka. Sarkin Laffaru da Boka Muzaffar suna son su mallaki Aljani Maruful Dauwaz, ita kuma Gimbiya Rahila tana son ta auri Sarki Laffaru bayan ya mallaki Maruful Dauwaz. Ku duba fa ku gani a halin yanzu Shadira da Zarina ba su da sauran buri a cikin wannan tafiya tamu amma hakan bai sa sun ki ci gaba da yin tafiyar ba, saboda me mu kuma za mu karaya akan ci gaba da tafiyar?" Lokacin da Shaharan yazo nan a zancensa sai kowa ya ji dukkan tsoro ya kau daga zuciyarsa, suka ji ba su ki ba ma a cigaba da tafiyar nan take in ba don akwai bukatar su yi jinyar jikkunansu ba. Haka dai aka zauna ana jinyar juna ya zamana cewa Lumaira tana matukar kula da mijinta, ba ta barinsa ya yi komai da kansa, ita ke yi masa saboda rashin hannu guda. Shi ma Shaharan Zarina ce ke dawainiya da shi. A lokacin ne soyayya mai karfi ta kara kulluwa tsakanin Shaharan da Zarina har suka ji ba za su iya rabuwa ba daidai da sa'a daya. 165 TASKARNOVELS.COM.NG Imran da Shadira ma sai suka sake shakuwa da juna ainun, ya zamana cewa dare da rana ba sa rabuwa. Mahaifiyar Imran ce kadai take shiga tsakaninsu a wasu lokutan tana yi masa hidima. A kullum sai Zarina ta shafe sama da sa'a biyar zaune a gaban kabarin dan uwanta Sarkin Farisa tana kuka da begensa. Shaharan ne kadai ke iya rarrashinta ya tashe ta daga gaban kabarin ya kai ta cikin tantinta ya zaunar da ita sannan ya ba ta abinci da hannunsa ta ci har sai ya ga ta koshi sannan shi ma yake cin abincin. A ɓangaren Gimbiya Rahila da Sarki Laffaru kuwa, suma soyayya ce ta rinka haɓaka kai kace bai girme ta ba a shekaru nesa ba kusa ba. Kuma ganin yadda take matukar kula da shi ne gami da ganin tsananin kyawunta ya sa ya dulmiye a cikin kogin kaunarta. (Laffaru tsohon ďn duniya kenan) 166 TASKARNOVELS.COM.NG Ita kuwa Rahila ba komai ne yasa sonsa ya mamaye zuciyarta ba sai don sanin cewa shi ne kadai namijin da za ta aura ta cika babban burinta na duniya, burin da babu wanda ya san shi face ita kadai. Kamar yadda aka yanke shawarar zama a cikin wannan daji na hudu har izuwa tsawon mako uku, haka al'amarin ya kasance. A ranar da mako ukun ya cika ne kowa ya sami kwarin jikinsa ya zamana babu sauran mai jinya a cikin matafiyan kuma ba sa jin ciwon komai a jikinsu sai dai tabubbuka. Da sassafe kowa ya kimtsa aka hau kan Aljani Marhabul Zaurus aka zazzauna sannan ya bude fuka-fukansa wadanda suka kasance daya da rabi ya tashi da su sama ya luluka a cikin gajimare. Marhabul Zaurus ya wanzu yana ta tsala gaudu a cikin gajimare har tsawon kwana guda da yini 167 TASKARNOVELS.COM.NG daya. Kwatsam! Sai yaji wata irin iska mai karfin tsiya ta zuko shi ta damfara shi da kasa a cikin abinda bai wuce dakika goma ba. Gaba dayan matafiyan da ke kansa suka gangaro kasa ba shiri. Al'amarin da ya fusata su jarumi Imran ke nan. Cikin fishi Imran ya dubi Aljani Marhabul Zaurus ya ce, "Wane ne ya ba ka izinin ka yi irin wannan wawar sauka ďauke da mu? Inda da tsautsayi ai da wasunmu sun karya wuya sun hallaka a yanzu". Koda jin wannan batu sai Boka Muzaffar ya yi caraf ya tari numfashin Imran ya ce, "Ka yi wa bawana uzuri domin kuwa ba laifinsa ba ne. Ina son ku sani cewa babu wata halitta da ta isa ta ratsa ta saman wadannan mugayen dazuzzuka guda biyar, shi ya sa ma tun da farko duk dajin da muka iso farkonsa sai Marhabul Zaurus ya sauko da kansa kas saboda ya san cewa bai isa ya ketare lafiya ba. Yanzu mun iso farkon daji na biyar wanda shi ne daji na karshe. Muna fita daga cikinsa za mu yi arba da kogon Darul Iksina Idan har muka ratsa ta cikin wannan daji 168 TASKARNOVELS.COM.NG lafiya lau a raye mun gama shan wuya. Daman an ce bayan wuya sai dadi". Ya yin da Boka Muzaffar ya zo nan a jawabinsa sai kowa ya shiga gyara damararsa da kayan yakinsa. A lokacin ne sadauki Haiman ya dubi hannunsa na dama wanda da shi ne yake sarrafa takobi ya ga babu hannun kuma dole sai dai ya yi amfani da hannun hagu, kawai sai ya fashe da kuka. Al'amarin da ya sa kowa ya kamu da tsananin tausayinsa kenan. Take matarsa Lumaira ta bude hannayenta ya fada kan kirjinta suka kankame juna suna masu kuka ta shiga rarrashinsa ta ce, Ya kai mijina ka kwantar da hankalinka, ka daina tunowa da abin da ka rasa. Ka sani cewa " kaddara ta riga fata, kowanne bil'adama baya sanin yadda karshen halittar jikinsa za ta kasance face ya mutu. Ka sani cewa wannan hannu naka da kar ba zai sa ka rasa dukiya ko soyayyata ba, ko kuma mulki da dukkan matsayi a wannan duniya. Zan kasance mai matukar alfahari da kai idan har ka sami 169 TASKARNOVELS.COM.NG nasarar shiga kogon Darul Iksina kuma ka debo wannan ruwan sihiri na cikinsa, koda kuwa ni ban rayu ba na kai izuwa lokacin, domin ka ajiye babban abin tarihi na sadaukantaka da jarumtaka wadda waninka bai ajiye a baya ba. Babban bakin cikina shi ne, ace mutuwa ta raba mu a wannan lokaci wanda ba mu sami haihuwa ba bare mu bar abin tunawa da juna. Bana son ka mutu ka bar ni, gwara ni na tafi na barka domin idan kai ne ka tafi, raunin zuciyata ba zai bar ni na iya ci gaba da rayuwa ba." Lokacin da Haiman ya ji wannan batu sai ya sake kankame Lumaira a kirjinsa ya ci gaba da kuka. A bangaren Shaharan da Gimbiya Zarina kuwa, lokacin da suka tsaya suna tattaunawa kamar masu yin bankwana sai Zarina ta ga Shaharan ya kura ma ta idanu har hawaye na zubowa daga cikin idanunsa. Cikin yanayin mamaki ta sa hannunta guda ta share masa hawayen sannan ta ce, "Ya kai masoyina, a ina dalilin zubar wannan hawaye naka? Ka tuna cewa saboda kai fa na ci gaba da rayuwa na kawo i yanzu. Babu abin da nake son gani face farin cikinka, kuma 170 TASKARNOVELS.COM.NG babu abin da zubar da hawayenka zai haddasa mini face tsananin bakin ciki mara tukewa." (Oh ni Maiboko! Wato ana tafka gagarumar soyayya a cikin litattafan yaki) Ya yin da Zarina ta zo nan a zancenta sai hawaye ya sake zebowa akan kumatun Shabaran ya dube ta ya ce, "Ya ke masoyiyata ki yi sani cewa ba komai ne ya sa ni zubar da wanan hawayen ba face tsananin tausayinki. Abu na farko, ga shi kin rasa dan uwanki wanda kike so fiye da komai a cikin wannan duniya. Ni kuma da muka fara soyayya yanzu ga shi na zama nakasasshe. Ta ya ya kina matsayin 'yar Sarki za ki auri nakasasshe mai hannu daya? Shin ba kya tananin cewa wannan abin gori ne kuma abin zuzutawa a cikin duniya?" Sa'adda Zarina ta ji wannan batu sai ta yi murmushi sannan ta ce, "Ya kai abin begena dare da rana ina mai tabbatar maka da cewa wannan nakasa 171 TASKARNOVELS.COM.NG da ta same ka ba ta kara komai ba a tsakanina da kai face ɗumbin soyayya mara adadi. Ina so ka sani cewa babu ruwan so da kyau, matsayi ko yanayi. Shi So wani tsuro ne wanda idan ya fito a cikin zuciya baya mutuwa sai dai kullum ya ci gaba da girma har ya mamaye filin zuciyar gabdaya saboda yana samun taki da ruwa daga tafkin bege da kauna Sauyin siffar jikinka ba zai iya kankare kaunar da ta gama mamaye zuciyata ba. Inda za a yi gutsun gutsun da sassan jikinka muddin zan ganka a raye zan so na ci gaba da zama da kai a hakan har izuwa Karshen rayuwata, koda kuwa ba za ka iya tsinana mini komai ba." Koda jin wannan batu sai Shaharan ya ji ya daďa kamuwa da tsananin kaunar Gimbiya Zarina fiye da ko yaushe don haka sai ya sake rungumeta a kin kirjinsa ya kama kukan farin ciki a cikin zuciyarsa 172 TASKARNOVELS.COM.NG Kamar yadda Zarina da Shaharan da kuma Haiman da matarsa suka yi wannan tattaunawa haka ma Sarki Laffaru da Gimbiya Rahila suka yi. Shi kuwa Boka Muzaffar da aljanui Marhabul Zaurus sun yi wannan tattaunawar, sai dai su ba maganganu na alamun bankwana suka yi ba, kuma keɓewa suka yi gefe daya yadda babu mai jinsu. Boka Muzaffar ya dubi Aljani Marhabul Zaurus ya ce, "Abin da nake so da kai shi ne, da zarar mun sami nasarar shiga cikin kogon Daru! Iksina kai sauri ka hallaka gaba dayan abokan tafiyar nan tamu domin idan muka kuskura dayansu ya mallaki wannan ruwan sihiri to tamkar ya mallaki duniya ne gabadayanta domin yana shan ruwan zai iya sarrafa Aljani Maruful Dauwaz. Da ma karya nayi musu na ce ba zamu iya sarrafa Maruful Dauwaz ba face mun je masa da Gimbiya Rahila. Alkawarin da ke tsakaninmu ni da kai yana nan, tabbas sai na yi maka sarautar Sarkin aljanu na duniya 173 TASKARNOVELS.COM.NG muddin ka cika wannan umarni nawa ba tare da ka yi kuskure ba." Lokacin da Aljani Marhabul Zaurus yaji wannan batu sai ya cika da tsananin mamaki kuma ya shiga rudani da wasi-wasi don haka sai ya dubi Boka Muzaffar cikin yanayin rashin fahimta ya ce, "Ya shugabana lallai zan kasance mai cika umarninka, amma ina tsoron abu biyu. Abu na farko shi ne, ta yaya zan iya kawar da wadannan abokan tafiya tamu alhalin duk sun fi ni karfin sihirin tsafi, Sarki Laffaru ne kadai ba shi da sihirin komai a yanzu. Abu na biyu ina shakkar Gimbiya Rahila domin tun a farkon wannan tafiya tamu na lura da cewa kai kanka ta fi ka karfin sihiri da jarumtaka, shin ba ka tunanin cewa ita kadai za ta iya wargatsa dukkan shirinmu?" Tambayar ta biyu da nake son na yi a gare ka ita ce, tun a farko ka gaya mini cewa kana son ka mallaki rabin kasar Sarki Laffaru da rabin dukiyarsa bayan ka taimake shi ya auri Gimbiya Ramlatul Siyam, to shin yanzu ba ka bukatar 174 TASKARNOVELS.COM.NG komai daga gare shi ne shi ya sa ka ba ni umamin na hallaka shi?" Sa'adda Aljani Marhabul Zaurus ya zo nan a zancensa sai Boka Muzaffar ya tuntsure da dariya har sauran abokan tafiyar suka tsargu da jin dariyar amma sai ya wayance ya dubi Aljani Marhabul Zaurus cikin murmushi da kara kaskantar da murya ya ce, "Kai dai kawai ka zuba ido ka sha kallo kuma ka bi umarnina zan warware maka duk abin da ya shige maka duhu anan gaba". Ba tare da ɓata lokaci ba Shaharana ya wuce kan gaba, sadauki Haiman na biye da shi goye da matarsa Lumaira, sannan Imran da Shadira, Imran na goye da mahaifiyarsa, Zarina na take musu baya, sai kuma Gimbiya Rahila, Boka Muzaffar da Sarki Laffaru. Aljani Marhabul Zaurus ne na karshe yana tafe yana waige-waife cikin alamun tsoro kamar ace kyat ya fita da gudu. 175 TASKARNOVELS.COM.NG Sai da aka shafe sa'a guda cif-cif ana tafiya a cikin wannan daji na biyar ba su ga koda giftawar dan karamin kwaro ba, kuma ba su ji motsin komai ba. Gashi a wannan lokaci rana ta kwalle kuma guzurin nasu na ruwa da abinci duk ya kare don haka yunwa da kishirwa sun fara addabarsu Wani abin takaici kuma shi ne, gaba daya wannan daji a cike yake da rairayin sahara babu bishiyoyi ma bare a sami inuwar da za a fake, kuma babu kogo ko korama inda za a sha ruwa, dole sai an isa karshen dajin anan ne akwai kogin da ake kira TUDUN TSIRA yake'. Lokacin da Boka Muzaffar ya ga sun shafe wannan doguwar tafiya amma ba su hadu da wannan katuwar Kunama ba sai hankalinsa ya dugunzuma ya aiyana a ransa cewa lallai a ko yaushe Kunamar za ta iya baiyaną a gare su ta kawo musu MAMAYAR BAZATO. 176 TASKARNOVELS.COM.NG Ana cikin tafiyar sai Muzaffar ya bude muryarsa da karfi ya ba da umarnin a tsaya. Da yake Shaharan ne akan gaba sai ya tsaya cak! A inda yake. Ai kuwa sai kowa ma ya tsaya. Boka Muzaffar ya dubi gaba dayan abokan tafiyar daya bayan daya ya ce, 'Ya ku abokan tafiya ku yi sani cewa rayuwarmu tana cikin mugun hadari tunda har yanzu wannan muguwar Kunamar ba ta baiyana a gare mu ba kuma ba mu ci rabin tafiya ba izuwa karshen wannan daji. Idan muka ce zamu ci gaba da tafiya ko kuma mu koma da baya inda zamu nemi ruwa da abincin da zamu ci ba zamu kai ba, yanwa da kishirwa za su kashe mu. Haka kuma idan ma muka ce za mu ci gaba da tafiyar a haka a ko yaushe Kunamar za ta iya baiyana a gare mu ta hallakavmu gaba daya, saboda haka yanzu meye abin yi? Tabbas muna cikin TSAKA MAI WUYA kuma GABANMU TSINI NE, BAYANMU SIYAKI. 177 TASKARNOVELS.COM.NG Sa'adda Boka Muzaffar ya zo nan a jawabinsa sai hankalin kowa ya dugunzuma aka yi tsit aka rasa wanda zai ce kala. Daga can sai Rahila ta ce, "Ni a tawa shawarar mu tsaya anan mu huta sosai domin mu sami kwarin jikinmu koda kuwa ba mu sami ruwa mun sha ba. Idan muka huta din sai mu ci gaba da tafiya in ya so da zarar mun ga Kunamar ta fito sai jarumi Shaharan ya janye ta da gudu ya kai ta har can kogin Tudun Tsira inda za ta hallaka sannan mu bi bayansa hankali kwance. Nan take aka taru waje daya aka zazzauna ana hutawa duk da cewa zafin rairayi ya addabi kowa. Kash! Inda su Haiman sun san abin da zai biyo baya da ba su yi gangancin zama domin su huta ba. Ashe ita wannan Kunama ta ga shigowar su Haiman cikin dajin tun a farkon zuwansu, kawai sai ta kama haka rami ta shige izuwa can karkasin kasa, rairayi ya rufeta ruf, ta ci gaba da tafiya a can karkashin rairayin ba tare da ana jin motsinta be har ta sha kansu taje wannan wuri 178 TASKARNOVELS.COM.NG daidai inda suka zazzauna suna hutawa. Abin da ba su sani ba shi ne akan Kunamar suka zazauna. Ba zato ba tsammani sai suka ji wani katon abu ya yi sama da su gaba dayansu suka rikito kasa. Koda suka yi arba da abin da yai watsi da su sai suka dimauce ce har sun yi yunkurin guduwa, sai Shaharan ya daka musu tsawa ya ce, "Su tsaya, duk wanda kuwa ya gudu tamkar ya sayi ajalinsa ne". Nan fa aka fara kallon-kallo tsakanin jaruman da wannan shirgegiyar Kunama wacce idan daga nesa mutun ya hangota sai ya yi zaton ko tsauni ne saboda girmanta kuma ta kasance baka wuluk har shekin baki take yi ba kyan gani. Kafafuwanta gasu nan birjik zankala-zankala masu dauke da muggan yatsu masu farata ma'abota TSINI DA KAIFI. 179 TASKARNOVELS.COM.NG Shaharan ya dubi sauran abokan tafiya a lokacin da kowa jikinsa ya kama kyarma ya ce, "Babu batun guduwa a yanzu tunda wannan Kunama ta shammace mu ta baiyana tsulum! a gabanmu. Na tabbata idan ma muka ce zamu yi gudun da yawanmu ba za su tsira ba Kunamar za ta riske su ta hallakasu. Ni kaina ba ni da tabbacin zan iya tsere ma ta tunda babu tazara a tsakanina da ita. Ku sani cewa ba mu da wani zabi wanda yabfi mu tunkare ta da yaki muna yakarta muna karawa gaba da gudu. Ina mai gargadinmu da kada dayanmu ya yi sakaki har Kunamar ta soke shi da farcenta domin da zarar hakan ta faru za ta sa masa dafi wanda zai narkar da shi nan take". Kafin Shabaran ya gama rufe bakinsa tuni Kunamar ta afko musu su duka tana mai kawo musu SARA DA SUKA da dukkan kafafunta su kuwa sai suka wanzu suna masu kare harin da garkuwoyi kuma suna mai da martani da saran takubba gami da ja da baya cikin gudu. Kunamar ta ci gaba da binsu tana kuntata su. Duk sadda takubbansu ya haďu da jikin Kunamar sai ka ga 180 TASKARNOVELS.COM.NG tartsatsin wuta gami da hayaki na tashi kuma ko kwarzanewa jikinta ba ya yi. Al'amarin da ya dugunzuma hankalin jaruman kenan musamman Haiman da Shaharan wadanda suka kasance miskinai masu hannu dai dai. Imran da Gimbiya Rahila, Shadira da Zarina ne kawai suke gagarumin kokari sai kuma Boka Muzaffar da ke taimaka musu amma Sarki Laffaru buya yake yi kawai a bayansu yana gudu. Sai da aka shafe sa'a daya da rabi ana wannan bakin gumurzu, ya zamana cewa kurar rairayin ta tashi ta bulbule dajin gaba daya har ma basa iya ganin junansu sosai kuma duk da cewa suna ja dabaya cikin gudu suna yakin amma ba su isa kogin Tudun Tsira ba. A daidai wannan lokaci ne jaruman suka fara gajiya ya zamana cewa da kyar suke iya kare harin Kunamar, kuma a sannan ne Kunamar ta 181 TASKARNOVELS.COM.NG fara kawo musu suka da tsinin faratan hannayenta. Da zarar sun kare sukar da garkuwa sai ka ga farcen Kunamar ya burma garkuwar tamkar an buda ganga da wuka. Al'amarin da ya kara dugunzuma hankalinsu ke nan. In ba don ma jaruman sun kasance masu matukar juriya da na ci ba da tuni Kunamar ta gama yin fata-fata da sassan jikinsu tun a farkon fara gumurzun. Ya yin da Kunamar ta ga an jima ana wannan dauki ba dadi amma ba ta sami nasarar suka koda jikin daya daga cikinsu ba sai ta fusata ainun, ta kara kaimi, ta mai da hankalinta akan kai musu munanan sara. Ai kuwa nan da nan ta lalata dukkan garkuwoyinsu suka yi ta jifa da su, bisa dole suka ci gaba da yakarta da takubba. Kaico! Tashin hankali ba a sa masa rana. A wannan lokaci ne Kunamar ta sami lagon jaruman ta fara samun nasarar saran jikinsu. A 182 TASKARNOVELS.COM.NG lokaci guda ta sari Shadira da Zarina a damtsen hannayensu wurin ya yi rami mai zurfi jini yai feshi suka kwalla ihu suka fadi can gefe daya a matukar galabaice. Haiman, Imran da Zarina, Rahila da Shaharan kuwa a kafafunsu ta sassaresu ta yi watsi da su can gabanta. Boka Muzaffar da Sarki Laffaru gami da Aljani Marhabul Zaurus kuwa wani irin wawan mangari tayi musu suka yi sama kamar an cilla su daga cikin Baka sannan suka fado a kasa a sume kuma a warwatse. Nan take Kunamar ta ruga izuwa inda su Shaharan ke zube a kas domin ta karasa hallaka su. Suna ji suna gani aka rasa wanda ai iya mikewa tsaye ya kare kansa. Tuni a wannan lokaci mahaifiyar Imran, Lumaira da dokin Shahara sun dade da suma sakamakon mummunar buguwar suka yi a kas. 183 TASKARNOVELS.COM.NG Koda ya rage bai fi saura taku goma ba tsakanin Kunamar da su Imran, Shaharan ya ga mutuwa muraran ta taho gare su sai ya kwarara uban ihu, duk da cewa akwai Raton rauni a kafarsa wanda naman wajen ya zabtare yana reto har ana ganin kashin Kafar sai ya daka wawan tsalle sama kamar kibiya aka harba ya dira akan tsakiyar Kunamar yana rike da takobi da hannu daya. Daya dungulmin hannun nasa kuwa ya naushi idon kunamar da shi. Saboda karfin naushin sai da dungulmin hannun nasa ya nutse a cikin idon Kunamar. Yana zaro hannun nasa sai ga jini yana feshi. Duk da haka Kunamar ba ta daina kawo masa sara da suka ba da dukkan sauran hannayenta, shi kuwa ya wanzu yana mai kade hannayen na ta da takobinsa cikin bakin zafin nama wanda ko a mafarki bai taɓa zaton zai iya yin hakan ba. A hakan Kunamar ta ci gaba da matsawa tana kokarin isa inda su Haiman ke kwance sun kasa tashi domin ta turmushe su. 184 TASKARNOVELS.COM.NG Koda Shaharan ya gane nufin Kunamar sai ya sake dankara ma ta wawan naushi a daya idon nata. Take shi ma idon ya burme, jini ya kama ɓulbulowa ta zama makauniya. Wohoho! Nan fa Kunamar ta haukace ta yi wata uwar girgiza ta jeho Shaharan kasa daga kanta. Dai-dai inda ya fadin ta kai wawan suka da dukkan hannayenta, cikin matsanancin bakin zafin nama ya goce, kafafuwan na ta suka cake a cikin kasa suka lume can kasa. Kafin ta zaro kafafun na ta Shaharan ya mike zumbur ya falfala da masifaffen gudu. Duk da cewar Kunamar ta makance, sai ta yi amfani da sautin takun sawayensa ta bi shi a guje, suka kasa uban tsere. Tabbas in ba don Shaharan ya yi wannan dabara ba ya dauke hankalin Kunamar daga wajen abokan tafiyar tasa da sai ta hallaka dukkan abokantafiyar a lokaci guda. 185 TASKARNOVELS.COM.NG Sai da aka shafe rabin sa'a ana wannan tseren gudu tsakanin Shaharan da wannan Kunama, duk sa'adda ya waiga bayansa sai ya ga tazarar da ke tsakaninsa da ita bai wuce kamu biyar ba, don haka a ko yaushe za ta iya luma masa faratanta. Da zarar ya yi yunkurin sauya wurin da ya nufa sai ya ga itama Kunamar ta sauya ta bi shi. Al'amarin da ya kara dugunzuma hankalinsa ke nan musamman da ya ga cewar har a sannan ba su iso kogin tudun tsira ba. Baya ga wannan tashin hankali da yake ciki abin da yai ta fado masa a rai shi ne, rashin sanin halin da su Zarina ke ciki a yanzu. Shi dai ya san cewa gabadayansu suna cikin mugun hali, babu mamaki ma wasunsu sun mutu bai sani ba, don haka, kokarinsa shi ne yai sauri ya kai kunamar cikin wannan kogi domin ta hallaka sannan ya dawo baya a guje domin ya kaiwa su Zarina agajin gaggawa. Haka dai Shaharan ya ci gaba da gudu iyakar karfinsa. 186 TASKARNOVELS.COM.NG Hakika idan masifa ta kai masifa mutum na iya mantawa da wani bala'in. Saboda tsananin tsoron wannan Kunama wacce ke biye da Shaharan, ya manta da lafcecen raunin da ke kafarsa har ma gudan tsokar da ya zabtaro a jikin kafar ya gutsure da kansa ya fadı kasa amma bai sani ba. Da kyar da siďin goshi Shaharan ya riga wannan Kunama isa cikin wannan kogi na tudun na tsira, amma kafin ya faɗa cikin kogin sai da ta sare shi da kaifin faratanta sau uku a gadon bayansa. Duk sa'adda ta sare shi sai ya tsandara ihu ya gantsare kamar zai fadi kuma sai jini ya yi feshi daga jikinsa. Yana fadawa cikin kogin ne ita ma Kunamar kafafunta suka tsunduma a cikin ruwan kogin. Nan take jikin Kunamar ya kama narkewa, kafin cikar dakika sittin gaba dayan jikin nata ya narke ya zama ruwa. A sanann ne jarumi 187 TASKARNOVELS.COM.NG Shaharan ya fito daga cikin ruwan da kyar yana dingishi da mai da numfashi kamar zai mutu. A dai-dai wannan lokaci ne ya ji raunin kafarsa ya dame shi da tsananin zogi. Koda ya dubi raunin ya ga yadda tsokar naman kafarsa ya zabtare sai ya kwarara uban ihu ya fadi kas. Yana faduwa ya tuno da halin da ya baro abokan tafiyarsa, sai ya sake mikewa zumbur! Ya falfala da irin wannan azababben gudun nasa

Chapter 7 of 18