Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ya sa dabbobin suke tsorata da shi. Lokacin da Laffaru ya gaji da yawo a cikin dajin har ya ji kishirwa ta kama shi sai ya je karkashin wata doguwar bishiya ya zauna sannan ya fidda dan guzurin abincinsa ya fara ci. Abin da bai sani ba shi ne, ashe akwai abin da ya fito nema akan wannan bishiya da ya zauna a karkashinta. 460 TASKARNOVELS.COM.NG Wani murtukeken rikakken Zaki ne kwance akan bishiyar yana barci. Zakin bai dade da cinye wata barewa ba da ya make. Bayan ya ci ya koshi kuma ya je ya sha ruwa sai ya zo ya hau can saman bishiyar ya kwanta. Yana kwanciya kuwa sai barci ya sace shi. Da yake barcin nasa bai yi nisa ba ko munshari bai fara ba. Koda Laffaru ya fara cin abincin sai sautin taunarsa ya sa Zakin ya farka. Ai kuwa yana lekawa kasa ya yi arba da Laffaru sai ya kwarara uban gurnani mai tsananin firgitarwa. Gurnanin nasa ya cika dajin gaba daya da amsa kuwwa. Hatta Maruful Dauwaz da Ramlatul Siyam da ke can tsakiyar dajin sai da suka jiyo wannan ruri na Zaki. 461 TASKARNOVELS.COM.NG Cikin tsananin farin ciki Ramlatul Siyam ta daka tsalle ta fada kan Aljani Maruful Dauwaz tana mai cewa, "Na sami miji!" Bisa mamaki sai ta ga Maruful Dauwaz ya sunkui da kansa kas cikin alamun karayar zuciya sannan ya ce, "Wannan rurin Zakin da kika jiyo ba na fitar rai ba ne, ruri ne na tsoratarwa. Tabbas Laffaru ya yi MUGUN GAMO da murjejen Zaki kuma rikakken gaske domin sai zakin da ya haura shekaru talatin a duniya shi ne yake irin wannan ruri". Koda jin wannan batu sai hankalin Ramlatu!Siyam ya dugunzuma ainun ta ji kamar ta ruga da gudu izuwa cikin dajin domin ta kai wa Laffaru dauki amma sai ta dake. 462 TASKARNOVELS.COM.NG Lokacin da wannan Zaki ya yi wannan ruri sai Laffaru ya mike zumbur a matukar tsorace domin ya gudu, ai kuwa sai Zakin ya duro a kansa ya turmusheshi a kas suka kama kokawa suna mirgine- mirgine. Zakin ya fara kokarin ya kafa hakoransa akan makoshin Laffaru shi kuwa sai ya dage iya karfinsa yana gabzawa Zakin naushi suka ci gaba da turmutsutsu da birgima a kas. Nan da nan Zakin ya karkarce jikin Laffaru da faratan hannayensa da na kafafunsa. Albarkacin mirginawar da suke yi ne shi ma Zakin fuskarsa ta rinka gwaruwa a jikin duwatsu da bishiyoyi har ya sami raunika, jini ya cika fuskar tasa. Ai kuwa suna cikin birgima a kasan ne da mirginawa suka fado izuwa asan wani rami wanda ruwan kogi ne ke azababben gudu a cikinsa. Suna fadowa cikin ruwan sai kowannensu kansa ya bugu akan duwatsu duk 463 TASKARNOVELS.COM.NG suka suma. Igiyar ruwa ta tafi da su izuwa can gaɓar kogi tayi watsi da su. Sai da iska ta bugesu sannan Laffaru ya fara farfadowa. Koda ya yunkura domin ya mike tsaye sai ya ji ya kasa saboda ji ya yi kamar ba shi da kafar dama. Koda ya dubi kafar tasa sai ya ga ta karkarce kuma ta kumbura suntum! Nan take ya gane cewa karyewa ya yi. Al'amarin da ya matukar dugunzuma hankalinsa ke nan. Kwatsam! Sai wannan Zaki ya farfado daga dogon suman da ya yi. Ai kuwa yana bude idanunsa ya yi arba da Laffaru zaune a gabansa sai ya daka tsalle gami da wangame bakinsa zai afka masa. Cikin tsananin zafin nama Laffaru ya cisgo wata 'yar karamar bishiya da ke daf da shi yai sama 464 TASKARNOVELS.COM.NG ya tari Zakin. Bisa sa'a kuwa sai tsinin reshen bishiyar ya shige cikin hancin Zakin ya bullutso ta wuyansa. Suna fadowa kasa shi da Zakin sai Zakin ya kama matagungun da shure-shuren mutuwa. Sai da Zakin ya dade yana shure-shure sannan ya mutu. Nan fa tashi ya gagari Laffaru. Dole ya ci gaba da zama a bakin wannan koramar da wanan karamar bishiya wacce ya kashe Zakin da ita ya samu ya kakkarya rassanta ya gyara karayar tasa ya daure kafar a jikin rassan da taimakon tsumman rigar jikinsa da ya yayyage. Sai da ya kwana uku yana jinyar kafar tasa a bakin wannan kogi ya zamanacewa, ba shi da abincin ci sai danyen naman wannan Zaki da ya kashe, har ma Zakin ya rube ya fara tsutsa amma a haka yake cin naman nasa don kada yunwa ta kashe shi, tunda babup kyastu a wajen wanda zai kunna wuta ya gasa naman. Ruwan wannan kogi kuwa shi ne ya zamo ruwan shan sa. 465 TASKARNOVELS.COM.NG Al'amarin Ramlatul Siyam da Aljani Maruful Dauwaz kuwa, koda suka ga rana tafadi dare ya yi Laffaru bai dawo ba sai hankalinsu ya dugunzuma ainun suka aiyana a ransu cewa ya mutu. Koda kwana uku suka shude sai suka kara sallamawa. Abin da ya kara dugunzuma hankalinsu shi ne a wannan rana ne Rahila ta ci gaba da aman jini ba kakkautawa, ga shi sun diga mata wannan maganin barci amma ta kasa yin barcin sai numfashinta ne ke ci gaba da sarkewa. Koda ganin halin da Rahila ta shiga sai Maruful Dauwaz ya fara kuka domin ya san cewa karshen burinsa ya zo. 466 TASKARNOVELS.COM.NG Kwatsam! ba zato ba tsammani sai suka ga mutum ya tunkaro su yana dogara ice da hannunsa na dama, hannunsa na hagu kuwa na rike da wani katon kan Zaki. Koda mutumin ya matso kusa sai suka shaida shi. Ba wani ba ne face Sarki Laffaru.Cikin tsananin farin ciki Ramlatul Siyam ta mike zumbur! ta ruga wajen Laffaru ta rungume shi tana cewa, "Ka zama mijina na zama matarka". A daidai wannan lokaci ne suka ji Maruful Dauwaz ya fashe da matsanaicin kuka. A firgice suka juyo suka dube shi sai suka ga ashe Rahila ce ta mutu akan hannayensa. Ai kuwa sai su ma suka durkushe kasa suka fashe da matsanaicin kuka. Sai da Laffaru, Ramlatul Siyam da Aljani Maruful Dauwaz suka 467 TASKARNOVELS.COM.NG shafe sa'a biyar suna kuka da bakin ciki sannan suka haka kabari suka binne Rahila. A sannan ne Aljani Maruful Dauwaz ya dago kai ya dubi Sarki Laffaru da Ramlatul Siyam a lokacin da hawaye ke zubowa kan kumatunsa daki- daki ya ce, "Ya ku abokan tafiya, ku yi sani cewa lokacin rabuwa ta da ku ya yi, tabbas in ba don ina da sauran alkawari guda daya ba da yanzu take a gabanku zan kashe kaina. Alkawarin da ya rage mini kuwa shi ne na komawa kofar kogon Darul Iksina domin na gani idan sauran abokan tafiyarku na nan a raye. Alfarma daya zan iya yi musu na karanta wadannan dalasimai na tsafi na bude kofar kogon. 468 TASKARNOVELS.COM.NG Lallai idan akwai wanda yai rai a cikinsu a sannan ne zai iya fitowa ni kuma sai na dauke shi na maida shi kasarsa". Koda jin wannan batu sai Laffaru da Ramlatul Siyam suka kara kamuwa da tsananin tausayin Aljani Maruful Dauwaz. Ramlatul Siyam ta dube shi ta ce, "Ya kai Sarkin sadaukai na duniya, ka yi sani cewa har abada duniya ba za ta manta da kai ba domin ka yi jarumtakar da babu wanda ya taɓa irinta. Kai ne ka fara shiga wajen da ya gagari kowa a duniya, kuma kai ne ka dauko ni daga cikin fadar mahaifina wajen da ya fi ko ina karfin tsaro a duniya. Bai kamata a ce gwarzon mayaki kamarka ya yi mutuwar banza ba. Na sani cewa bayan ka je kogon Darul Iksina babu abin da za ka sake yi face ka kashe kanka. Ina mai rokonka alfarma guda daya. 469 TASKARNOVELS.COM.NG Ina son a ranar da na haihu ka zo ka ga 'yata ka dauke ta da hannayenka masu albarka ka sa mata albarka domin ina son anan gaba ta yi alfahari da cewa Sarkin sadaukan duniya ya dauke ta da hannayensa. Ina tabbatar maka da cewa sai na sassaka gunkinka a lokacin da kake dauke da jaririyata domin ya zamo abin tunawa da kai a gare mu har abada. Kuma lallai za mu bar tarihinka a rubuce yadda jama'ar kowanne zamani za su riske shi kamar yadda aka samu kadan daga cikin tarihin naka a kundin tarihi na Birnin Lairuf wato garin su Gimbiya Rahila. Sa'adda Ramlatul Siyam ta zo nan a zancenta sai hawaye ya kara zubowa Aljani Maruful Dauwaz ya ce, "Hakika babu wata alfarma da za ki nema a wajena na ki yi miki don haka na yi miki alkawari lallai zan dawo gare ku a ranar da kika haihu." Koda gama fadin hakan sai Aljani Maruful Dauwaz ya buɗe fuka-fukansa ya tashi sama a hankali yana kallon su Ramlatul Siyam su ma 470 TASKARNOVELS.COM.NG suna kallonsa suna hawaye shi ma yana hawaye har ya luluka a cikin gajimare ya ɓace musu da gani. Maruful Dauwaz ya ci gaba da tsala gudu a sararin samaniya ba sassauci yana mai tunkarar tsibirin da kogon Darul Iksina yake. Ai kuwa a cikin sa'a biyu da rabi jal ya iso bakin wannan kogi wanda kogon na Darul Iksina ke kansa. Aljani Maruful Dauwaz na sauka a bakin gabar kogin sai ya dubi gabas da yamma, kudu da arewa ya ga wayam babu wata halitta mai numfashi a wajen, koda kuwa tsuntsu guda daya ko kwari, kuma ba a jin sautin komai face na iskar da ke kadawa a cikin dajin. Nan take Aljani Maruful Dauwaz ya tuna tsawon shekarun da ya yi a cikin kogon Darul Iksina saboda bakin cikin mutuwar masoyiyarsa, ya tuna cewa shiga yanzu ba shi da kowa a duniya domin duk zuri'arsa ma sun kare. 471 TASKARNOVELS.COM.NG Abin da yai masa saura kawai shi ne wannan wasiyya wacce masoyiyarsa ta bar masa kuma ga shi wadda ta san inda wasiyyar take ta mutu sai ya fashe da matsanaicin kuka. Sai da Aljani Maruful Dauwaz ya shafe rabin sa'a yana wannan kuka sannan ya dubi kogon Darul Iksina ya bude bakinsa ya karanta wadannan dalasimai na tsafi. Faruwar hakan ke da wuya sai kofar kogon ta bude da kanta. Aljani Maruful Dauwaz ya kura idanu izuwa cikin kofar amma sai ya ji shiru bai ji motsin tafiya ba kuma bai hango kowa ba. Tsawon kusan wata rabin sa'ar bai ga wani ya fito ba sai ya fid da rai ya aiyana a ransa cewa gabadayan abokan tafiyar su Laffaru sun mutu a cikin kogon na Darul Iksina. 472 TASKARNOVELS.COM.NG Aljani Maruful Dauwaz ya yunkura domin ya tashi sama sai kawai ya jiyo sautin tafiya daga can cikin kogon Darul Iksina. Cikin tsananin murna ya dakata ya sake zuba idanu izuwa cikin kogon. Sannu a hankali sautin tafiyar ya rinka karuwa har ya yi arba da masu fitowar. Ba wasu ba ne face Shaharan, Zarina, Shadira, Imran, Lumaira da mahaifiyar Haiman. Dukkaninsu da kyar suke tafiya. Zarina ta goyo mahaifiyar Imran a bayanta, ita kuma Shadira tana rike da hannun makauniya Lumaira. Imran da Shaharan kuwa sun rike kafadun junansu suna dingishi. Koda su Imran suka hango Aljani MarufulDauwaz a can bakin gaɓar kogin sai 473 TASKARNOVELS.COM.NG suka firgita ainun suka ji kamar su koma cikin kogon na Darul Iksina domin ba su taɓa ganin Aljani mai matukar kwarjini da ban tsoro ba kamarsa. Amma da suka tuna cewa ba su san wanda ya bude musu kofar kogon ba har suka fito sai suka aiyana a ransu cewa lallai wannan Aljani ne ya bude kofar kogon. Yayin da Aljani Maruful Dauwaz ya fahimci cewar sun tsorata da shi sai ya dube su cikin murmushi ya ce, "Ya ku wadannan ZARATAN JARUMAI ababan alfahari ku yi sani cewa ni ba wani bane face Aljani Maruful Dauwaz." Koda jin wannan batu sai farin ciki ya lulluɓe su Imran suka yafuto Aljani Maruful Dauwaz da hannayensu suna masu yi masa nuni da ya zo ya dauke su. Nan take kuwa Aljani Maruful Dauwaz ya ketare kogin ya sauka a gabansu. 474 TASKARNOVELS.COM.NG Ba tare da fargabar komai ba su duka suka hau kan Aljani Maruful Dauwaz suka zauna shi kuma sai ya bude fuka-fukansa ya tashi da su sama yana mai tsala gudu a cikin gajimare. Suna cikin tafiyar ne ya ba su labarin duk abin da ya faru tsakaninsa da su Laffaru tun daga lokacin da suka riske shi a cikin a cikin kogon Darul Iksina kawo izuwa sa'adda ya dauke su suka tafi izuwa fadar Sarki Nashmir suka yi wannan yake-yake, har daga karshe Rahila ta mutu ba tare da ta sanar da shi inda wasiyyarmasoyiyarsa take ba, da kuma dajin da ya baro Ramlatul Siyam da Sarki Laffaru inda za su ci gaba da rayuwarsu ta zaman aure." Koda Aljani Maruful Dauwaz ya gama bai wa su Imran labari, sai suka cika da tsananin bakin ciki da tausayi suka fashe da kuka gabadayansu. A sannan ne kuma ya yi musu albishir da cewa, Boka Muzaffar da Sarki Nashmir sun kashe 475 TASKARNOVELS.COM.NG junansu amma mashin Galilul Haras ya koma hannun Sharlis. Haka kuma ya tabbatar musu da cewa daya bayan daya sai ya mayar da kowannensu kasarsa. Koda jin wannan labari sai suka kamu da tsananin farin ciki. Amma da suka tuna cewa lokacin rabuwarsu ya zo gaba daya sai suka ci gaba da kuka saboda sabo da shakuwar da suka yi. Wannan shi ne abinda ya faru tsakanin Aljani Maruful Dauwaz, da su jarumi Imran, jaruman da su ne kadai suka tsira da rayuwersu a cikin kogon Darul Iksina bayan sun fid da rai ga tsira da rayuwa. ***** 476 TASKARNOVELS.COM.NG AL'AMARIN Sharlis kuwa, lokacin da ta ga ta mallaki mashin Gul Haras sai ta cika da tsananin farin ciki ta koma Birnin Kufa. Tana isa gida ta iske danta Sarki Shaddadu a zaune cikin matukar damuwa saboda rashin ganinta. Koda ta baiyana a gabansa rike da mashin Galilul Haras sai ya mike zumbur! Ya ruga gare ta suka rungume juna cikin tsananin farin ciki. Nan take ta ba shi labarin darajar mashin Galilul Haras ta tabbatar masa da cewa, za ta koya masa yadda ake sarrafa Mashin amma sai bayan ya girma ya mallaki hankalin kansa don kada kuruciya tasa ya je ya yi wani abin da bai dace ba. Daga wannan rana Sharlisa ta ci gaba da koya wa Shaddad yaki dare da rana ya zamana cewa jarumtakarsa kullum karuwa take yi. 477 TASKARNOVELS.COM.NG Wani lokacin tausayinsa ne yake kama ta idan ta ga irin bakar wahalar da yake sha wajen karɓar horon yaki, har ma ya kan suma sai dai Sharlis ta ji kwallah ta zo mata saboda tsananin tausayinsa amma duk da haka ba ta daina ba shi horon ba. Ba komai ne yasa Sharlisa take bai wa Shaddad wannan horo mai tsanani ba face saboda ta yi bincike ta gano cewa Sarki Laffaru ya auri Gimbiya Ramlatul Siyam kuma suna nan a cikin wani daji suna zaman rayuwar aure. Babu yadda Sharlisa ba ta yi ba domin ta shiga dajin Rauful Mausur amma abu ya gagara. Sau goma sha daya tana yin gagarumin shiri ta je har bakin dajin domin ta shiga amma sai ta kasa, bisa dole ta hakura ta koma da baya. A cikin binciken da ta yi ne ta ga cewa lallai Sarki Laffaru da Gimbiya Ramlatul Siyam za su haifi 'ya mace kyakkyawar da babu kamarta a duk duniya, kuma za ta taso da gagarumar jarumtaka irin wacce babu wani jarumi mai irinta. 478 TASKARNOVELS.COM.NG Babu wanda zai iya tararta da fada ko yaki face danta Shaddadu. Shi kansa Shaddadun ba zai iya hallaka ta ba face yai amfani da mashin Galilul Haras. Lokacin da ta daďa zurfafawa a cikin binciken nata ne, sai ta gano cewa babban abin da zai janyo rashin nasarar Shaddadu akan 'yar Sarki Laffaru shi ne SOYAYYA. Ko shakka babu in dai ya yi arba da 'yar Sarki Laffaru sai ya kamu da tsananin sonta, in kuwa ya kamu da tsananin sonta ba zai iya kashe ta ba. Koda Sharlisa ta gano wannan al'amari sai ta rinka cusawa Shaddad kiyayyar mata a zuciyarsa, ta rinka nuna masa cewa sharrin mata ya fi na bakin kumurci. 479 TASKARNOVELS.COM.NG A haka Shaddad ya taso da tsananin kiyayyar mata, ya zamana cewa ya tsane su ainun komai kyan mace ba ta birge shi. Kai hatta sha'awa ma irin wacce kowanne da namiji ke yi wa mace sai da Sharlis ta cire wa Shaddad ita da karfin sihiri, a matsayin ba za ta dawo masa da sha'awar ba sai bayan ya kashe 'yar da Laffaru ya haifa sannan ya kamo Laffarun ye kawo mata shi sun gana masa muguwar azaba tsawon kwanaki sannan su yi masa kisan gilla. A kwana a tashi, sai jarumi Shaddad ya cika shekaru ashirin da daya a duniya. A sannan ne kirar jikinsa ta ginu sosai, kai da ganinsa ka ga gawurtaccen jarumi saboda murdewar da jikin nasa ya yi da kuma tarin kwanji da jijiyoyi. Ga shi Allah Ya yi masa tsananin kyan fuska da kyan surar jiki. Karfin dantsensa kuwa ya wuce a misalta saboda komai girman bishiya idan ya 480 TASKARNOVELS.COM.NG naushe ta da hannu daya take ta ke tunɓukowa daga cikin kasa ta fadi kasa. Kuma komai yawan mayaka shi kadai yana iya tarwatsa su ya kashe na kashewa, masu sauran kwana su gudu. Idan kuwa yana yaki zai iya kwana da yini bai gaji ba A ranar da Shaddad ya cika shekara shirin da daya ne, Sharlis ta kimtsa shi ta damka masa mashin Galilul Haras sannan ta gargade shi akan kada ya yi amfani da mashin face ya gamu da 'yar Sarki Laffaru. Koda jin haka sai Shaddadu ya dubi mahaifiyarsa Sharlis cikin tsananin damuwa ya ce, 'Ya ke Ummina yanzu ya za a yi na gane wannan babbar mikiya tawa alhalin ban santa ba, kuma ban taɓa ganin irin fuskarta ba? 481 TASKARNOVELS.COM.NG Ke da kanki ma kin yi iya bincike a cikin tsafi domin ki ga fuskarta amma abu ya gagara saboda tana cikin dajin da ba a iya ganin komai". Sa'adda Shaddadu ya zo nan a zancensa sai Sharlis tayi ajiyar zuciya har kwalla ta zo ma ta a cikin idanunta, sannan ta yi murmushi ta ce, "Kada ka damu ya kai dana, yanzu-yanzu zan ba ka wata layar tsafi. Duk Macen da ka hadu da ita in dai ka ga tana da jarumtaka gami da tsananin kyau da zarar ka kara layar a jikinta za ka ga layar ta sauya launi daga baka zuwa ja jawur. Kana ganin haka ka yake ta da mashin Galilul Haras ka hallaka ta. A jikin wata sarka da ke wuyanta za ka ga hoton dajin da mahaifinta yake. Ka cire sarkar ka tafi da ita har can inda mahaifin nata yake ka kamo shi ka kawo shi wajena domin mu cika burinmu a kansa." 482 TASKARNOVELS.COM.NG Koda gama fadin hakan sai Sharlisa ta rungume Shaddadu ta fashe da kuka saboda ba ta son rabuwa da shi koda na tsawon dakika daya. Al'amarin da ya karya zuciyar Shaddad ke nan shi ma ya kama kuka. Sai da suka dade a kankame da una sannan suka yi bankwana ta ba shi Tsuntsunta na tsafi, ya hau kan tsuntsun ya zauna. Nan take tsuntsun ya bude fuka-fukansa ya tashi da shi sama. Sharlisa ta daga kanta sama tana kallonsu har sai da suka kule a cikin gajimare sannan ta sauke kanta a lokacin da hawaye ya zubo mata ta wuce kai tsaye izuwa fada ta zauna akan karagar mulki aka ci gaba da tafiyar da harkokin mulki kamar yadda aka saba, wato ta rikewa Shadaddu karagar mulki kafin ya dawo. ******* 483 TASKARNOVELS.COM.NG A can dajin Rauful Mausur kuwa, Gimbiya Ramlatul Siyam da mijinta Laffaru sun ci gaba da rayuwa cikin matukar farin ciki da kwanciyar hankali har tsawon watanni. A sannan ne Ramlatul Siyam ta sami juna biyu, al'amarin da ya jefa Laffaru cikin tsananin farin ciki ke nan ya ci gaba da kulada Ramlatul Siyam ainun har cikin na ta ya tsufa. A ranar da cikin ya cika wata tara ciť nakuda ta zo wa Ramlatul Siyam ta fara ihu da shureshure. Nan fa Laffaru ya dimauce ya rasa abin da zai yi domin bai san ma yadda zai taimaka mata ba ta haihun. Ana cikin haka ne kwatsam! Suka ga Aljeni Maruful Dauwaz ya baiyana. Nan take Maruful Dauwaz ya rinka umartar Laffaru bisa yadda zai taimakawa Ramlatu Siyam, shi kuwa sai ya himmatu yana mai bin umarnin. 484 TASKARNOVELS.COM.NG Duk da haka sai da ta shafe sa'a biyar tana nakudar sannan ta haifo santaleliyar jaririya mai tsananin kyau na ban al'ajabi. Aljani Marufl Dauwaz ne da kansa yaje ya wanke jaririyar. Koda ya dubi fuskarta sai ya ga a duniya bai taɓa ganin mai tsananin kama da masoyiyarsa Gimbiya Rashmin sama da wanann jaririya ba. Nan take ya ji ya kamu da tsananin son jaririyar kuma yaji kamar an yaye masa dukkan bakin cikinsa naduniya. Nan take ya rungume jaririyar a kirinsa ya fashe da kukan farin ciki. (BARKA DA DAWOWA SADAUKIN SADAUKAI BABBAN MASOYI GA GIMBIYA RASHMIN) Daga wannan rana Aljani Maruful Dauwaz ya zauna tare da su Sarki Laffaru a cikin dajin Rauful Masnur ya taya su rainon jaririyarsu. 485 TASKARNOVELS.COM.NG Da aka kwana bakwai sai aka radawa jaririyar suna ZIYA'UL HAK. Haka dai Laffaru, Ramlatul Siyam da Aljani Maruful Dauwaz suka ci gaba da renon Ziya'ul Hak har ta fara girma ta shekara bakwai a duniya. A wannan lokaci Ziya'ul Hak ta shaku ainun da Aljani Maruful Dauwaz fiye da ma iyayenta domin kodayaushe tana tare da shi dare da rana. Sau tari sai ta yi barci a kan kirjin Maruful Dauwaz sannan Ramlatul Siyam take zuwa ta dauke ta ta kai ta cikin tanti ta kwantar da ita. Lokacin da Ziya'ul Hak ta cika shekara bakwai ne Aljani Maruful Dauwaz ya fara koya mata yaki da kansa kuma ya dinga ba ta horon fada. 486 TASKARNOVELS.COM.NG Kullum sai ya ba ta horon sau uku. Nan da nan Ziya'ul Hak ta taso da gagarumar jarumtaka. Tun ba ta fi shekara tara ba ta ke fita farauta daji ita kadai ta kaso manyan dabbobin daji, sai dai ka ga ta ratayo Zaki ko Damisa a kafadarta ta zo gida da shi. Shi kansa Aljani Maruful Dauwaz sai da ya cika da tsananin mamaki bisa ganin irin tsananin jarumtakar Ziya'ul Hak. Babu abin da ya fi ba shi mamaki face karfin gudunta, domin shi kansa da suka kasa tsere a kasa, kasa wuce ta ya yi, nan take ta ba shi tazara mai yawan gaske. Sa'adda Ziya'ul Hak ta shekara goma sha takwas a duniya sai karfin dantsen nata ya wuce gaban misali, shi kansa Aljani Maruful Dauwaz idan yana yaki da ita da kyar yake iya kare hareharenta. Akwai lokacin da ta doki kirjinsa da kafarta guda sai da ya fadi can gefe guda ya ji 487 TASKARNOVELS.COM.NG kamar janye shi aka yi da majajjawa aka kwala shi a kasa. Tun daga ranar ya dada sallamawa jarumtakarta, domin in ban da Aljani Sharkamuza da sadauki Najwar ba, to babu wanda ya taɓa yi masa irin wannan duka sai Ziya'ul Hak. A ranar da Ziya'ul Hak ta cika shekara goma sha takwas ne Aljani Maruful Dauwaz ya kira Laffaru da Gimbiya Ramlatul Siyam gefe daya suka kadaita ya shaida musu cewa jiya ya fita daga cikin wannan daji na Rauful Masnur ya yi rangadi a cikin daji na gaba. Anan ne ya yi bincike ya gano cewa Shaddadu ya girma ya zama gawurtaccen jarumi kuma Sharlisa ta mallaka masa mashin Galilul Haras ya fito farautar Ziya'ul Hak domin ya kashe ta sannan ya zo har nan dajin Rauful Masnur ya kama Sarki Laffari". 488 TASKARNOVELS.COM.NG Koda jin wannan labari sai hankalin Laffaru da na Ramlatul Siyam ya dugunzuma ainun. Ramlatul Siyam ta fara zubar da hawaye ta ce, "Yanzu ya za a yi mu yi maganin faruwar wannanal'amari?" Aljani Maruful Dauwaz ya yi ajiyar zuciya sannan ya ce, "Hanya daya ce za mu bi mu yi maganin wannan matsala. Dole ne ita ma Ziya'ul Hak ta yi shiri ta tafi farautar jarumi Shaddadu domin ta hallaka shi, amma fa idan yana tare da Mashin Galilul Haras ba ta isa ta iya yi masa komai ba, amma tunda shi yaro ne ai mun fi shi wayo da dabara. Ni zan yi wa Ziya'ul Hak rakiya a cikin wannan tafiya domin na zamo mai ba ta kariya da 489 TASKARNOVELS.COM.NG shawarwari akan yadda za mu sami nasara akan Shaddadu koda kuwa zan rasa rayuwa ta. Ku sani cewa wanzuwar Ziya'ul Hak a doron kasa shi ne abin da ya hana ni kashe kaina, saboda ta dauke mini kewar masoyiyata. Yanzu sai ku shirya mana wannan tafiya ku yi bankwana da ita." Nan take Ramlatul Siyam ta kirawo Ziya'ul Hak ta sanar da ita duk abin da ake ciki. Ba tare da ɓata lokaci ba Ziya'ul Hak ta yi bankwana da iyayenta tana kuka su ma suna kuka suka rabu suna masu yi mata fatan nasara. Nan take Ziya'ul Hak ta hau kan bayan Aljani Maruful Dauwaz shi kuma ya bude fuka-fukansa 490 TASKARNOVELS.COM.NG ya tashi da ita sama suka luluka a cikin gajimare! A nan muka kawo karshen littafin MAZAN JIYA na uku (3) ***************** WANNE IRIN BAKIN GUMURZU ZA A YI IDAN JARUMI SHADDADU DA JARUMA ZIYAUL HAK HAR SUKA HADU? SHIN SHARLISA ZA TA CIKA BURINTA AKAN SARKI LAFFARU? YAYA KARSHEN RAYUWAR JARUMI SHADDAD ZA TA KASANCE? SHIN ZAI YI SOYAYYA KUWA A RAYUWARSA? 491 TASKARNOVELS.COM.NG YAUSHE NE ZA A JI LABARIN SADAUKI HULKAS NA BIRNIN ROMANIYA WANDA SHI NE CIKON JARUMI NA UKU DAGA CIKIN MAZAN JIYA? Mu hadu a littafin MAZAN JIYA 4 (Kashi na hudu) don jin ci gaban wannan kasaitaccen labari mai matukar kayatarwa. Muna neman afuwa ga makaranta bisa tsayin labari, hakan ya faru ne sakamakon tsayin da hikayar take da shi. Daga mai debe muku kewa a kullum da ko yaushe. ABDUL'AZIZ SANI MADAKIN GINI (The King of Adventure Story) 492 TASKARNOVELS.COM.NG Ni Maiboko, ina rokon makaranta wannan gawurtaccen littafin, da mu yi kokari mu tasirantu da kyawawan dabi'un da suka siffantu a cikin wannan hikayar. Mu kalli dalilan da suka sa Maruful Dauwaz ya yi nisan kwana sannan kuma yake samun nasara a kan duk abin da ya sa a gabansa, sabanin gagarumar nadama da tashin hankalin da sarki Lafaru yake a ciki Rayuwar aljani Maruful Dauwaz abar nazari ce da kwaikwayo duk da ta kasance a cikin hikaya ne. Aljani Maruful Dauwaz, yana daga cikin dalilan da suka sa nake wannan posting ďin. A karshe, yiwuwar cigaba da littafi na huďu na alakanta hakan da lissafin lokaci. 493 TASKARNOVELS.COM.NG 494 An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels

Chapter 17 of 18