Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dakin shaheeda tayi tsalle ta fada kan gado tamike tsaye tana rawa Yana fita sukayi ido 4 da hajiya naja'atu yajuya ze koma ta kira shi "zonan Najib yakaraso gurinta "wato ban isa nasa maka doka Kabiba ko Najib kodai kaika haifo kanka ne dukanta kayi ko dannaji tana ihu "Meyasa zan daketa mommy Yasmeen ce ta katsesu da cewa mommy angama kaimata za ayi ko Tare zatazo aci a dining table "A'a kice mata ta hado mata nata ta kai mata bance kekikai ba 'yar iya ita da aikinta Amma kina mata shishigi Toh mommy zan fada mata yaya Najib Zaka makara fa Katino Dr Abdul yace zaku hadu yau katashi katafi Yasmeen ta fada tana kanne mishi ido yana jin haka ya gane me take nufi"haka nefa niharna mantama bari naje na shirya na tafi Yatafi Yasmeen kitchen taje sukabar hajiya naja'atu baki abude "dole nayi maganinki Yasmeen kizo kisameni ina magana da dana kikirkiro karyar kisashi ya amsa dukdan karna mishi fada idan na gama da Ubanki zanji dake tafada rai a bace BabaHabiba mommy tace kikaiwa matar yaya Najib nata abincin dakinta to bari naje habiba ta hada ta tafi Yasmeen na tsaye a kitchen tana wani tinanin na daban jitayi ankira sunanta ahankali ta tsorata "Yasmeen yada tsoro haka "yaya Najib ya bazanji tsoroba nasandai nini kadaice anan senaji ankira sunana a hankali "Ki dena tsoro Yasmeen nafa gode Manta kawai yaya mommy batasan halin shaheeda ba zata fito mata a mutum bakunta take mata yanzu nina sani yan ajinsu babu wanda yake mata shedar harziki fa yaya "nasani Yasmeen kinga hadamin breakfast dina naci natafi zance "Yaya zance kuma wacce ita "watace tafi shaheeda da komai infada miki "yaushe zaka kaini na ganta "eh badai kwana kusaba kibari idan nasa rana zanfada miki "Ok toh Ta zuba mishi a kitchen yazauna yaci Baba Habiba tayi sallama shaheeda ta bode kofar sannan ta amsa "hajiya breakfast dinki na kawo miki kallon banza tayi mata "shigo medame kika dafa "potatoes salad, chips, farfesun naman rago da Tea harda biredi "kutumelisi wanadan rainin hankalinne yace ki kawo min wannan abincin talakawan farfesun rago bama na saniya ba kuma ni shaheeda problem za a kawowa Tab jan aiki kimayar kice bana ci kuma bazan zauna da yunwaba azo asan yanda za ayi dani kalas jeki mana Baba Habiba ta girgiza kai ta fita daga dakin a hanyar komawa kitchen suka hadu da hajiya naja'atu tafada mata abinda shaheeda tace bakomai yarin yace maida wannan kitchen zanje naji abin da takeso Seki dafa mata Baba Habiba tace toh tana shiga kitchen Yasmeen ta kafeta da idanu baba ya haka meyasa kika dawo dashi "Tace bata ci Najib daya gama cin abinci yace mezataci ban saniba amma hajiya taje ta jiyo "Bari nayi sauri na gudu kan ace naje na siyo se anjimanku najib ya shiga mota yabar gidan bayan hajiya naja'atu Yasmeen tabi bata shiga dakinba a kofa ta tsaya tana jinsu a kujerar dake dakin hajiya naja'atu ta zauna shaheeda na kan gado tana dan nawaya "shaheeda kallon hajiya naja'atu tayi batace komai ba Ankawo miki abinci kince bakyaci mezakici to banacin abinCinda yan aiki suka dafa nifa Inada kyankyami shiyasa ko a gidanmu other abinci nakeyi daga babban gurin cin abinci shine tawani kawo min farfesun rago ni tab "yanzu ya kikeso ayi "Yanda na saba zanyi mana dan'uwana zankira ya kawo min shikadai yasan gurin cin abincin Sannan idan yazo Kugane fukarshi saboda shize dinga kawo min abinci koyazo bada wurize koma ba Ze iya zuwa shikadai kosu biyu koma fiye da haka nidai kawai kar a hanasu shigowa inba hakaba raina ze baci "bada muwa shaheeda ai da yunwanne banaso ki zauna indai wannanne bama tsala a gabanta ta daga waya ta kirashi tafa mishi ya kawo mata abin da ta saba ci yace to Hajiya naja'atu tabar dakin tana fita taga Yasmeen a gabanta " mommy wana irin ME kawo abincine idan ya kawo ze Dade kafin ya koma kuma su biyu kofiye da haka Hajiya naja'atu ta rufe mata baki seda sukai nisa da dakin nata tace Yasmeen meyasa zakiyi irin wannan maganar a kofar dakinta idan ta jikifa New writer's Hakan Take *husba'ahfama* 😍❤🤩 *'YAR kwalliya* ❤💋 👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝 👠👠👠👠👠👠👠👠👠👠 💄💅 *HEEDAYA* 💅💄 *(I KIRARI)* 👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝 👠👠👠👠👠👠👠👠👠👠 Written by *husba'ahfama* Instagram *@officiall_husba'ahfama* Facebook *Real husba'ahfama* 26-27 "Taji mana mommy waye shi Cikin yan uwanta wannene baki saniba a cikin su rainin hankaline kawai irin na shaheeda "Babu ruwanki Yasmeen banson shegen sa ido irin naki nibaki barniba yanzu itama tazo zaki koma kanta wannan ba hali bane kicanza tinyanzu kan amiki aure "OK fine nayi shiru wata rana za a gane me nake nufi Tana gama fada tabar gurin baki hajiya naja'atu ta rike "yau naga ikon Allah ka haifi da a cikinka yace shize fada maka abinda zakayi Yasmeen hmm Waje Yasmeen ta fita ta zauna tana jiran shigowar wanda ze kawo abinci ta jima a zaune a guri can setaga shigo warshi da bakar leda tana ganinshi ta gane shi shima shiri-shirine kamar shaheeda tagabanta yazo ya wuce ta bishi da kallo harya wuce kananan kayane a jikin shi riga da wando bayan shi tabi taga a ina zata sauke shi azatonta a falo zata saukeshi setaga ta shiga dashi daki Yasmeen ta gigice "meyasa ta shiga dashi ciki kota manta dacewa ita matar aurece yanzu waye shi dole nanemo Hakan Tazauna a falo tana fuskantar dakinsu "Shaheeda problem kina wuta wai nayi zaton shikenan mundena haduwa dake kuma komai ya tsaya Ashe ba haka bane gaskiya naji dadi ammadai ina fatan lbr ya canza dan yanzu kinyi aure bedace na Tsaya iya wajeba ya kamata na dinga shiga ciki shaheeda kiyi tinani "nicefa shaheeda kasan bazan iya rabuwa da kaiba duk wuya duk dadi zamu dinga haduwa akai akai Boss nafada maka haryanzu hakona be cimma ruwa ba shiyasa "ya isa bakya qaunata shaheeda duk abin da mukeyi kawai ina rage miki zafine kuma kinada wata manufa a kaina na daban haka zakice nikinga tafiyata Yanufi kofa ze bude shaheeda tarike hanun shi "karkamin haka Boss duk abin da nakeyi ina yine saboda kai sabodakai nayi wannan auren danna rufa mana asiri ba san Najib nake yiba wata manuface ta daban yasa na aure shi daga na cika burina shikenan kuma nida kai ba get "wana burine haka shaheeda "hmm burina tin wanda na fada makane bancanza ba yanzuma shizan sake fada maka "tin ina karama babu namijin da nake sha'awa irin Najib nayi duk yanda zanyi akan na bashi kaina a waje amma yaki amincewa dole yasa na aure shi Najib naiwa tanadin budircina shinakeso na fara sani ina saninshi zan kara fadada harkallata fiye dada "har yaushe zakikai kina wannan mafarkin "baze dau lokaciba boss Macecenifa kada ka gaji dani ta fada tana shafa mishi fuska kwana kusa komai ze canza zeyi magana ta hada bakinshi da nata suna shafa jikin juna a haka har suka raba kansu da suturar dake jikin su suka shiga tafka Masha a wa'iya zubillah Yasmeen na zaune tanata jimamin shigar dashi ciki da tayi mommy tazo inda take ta zauna "Yasmeen ina shaheeda yazaki barta ita kadai kice ta fito kinsan kewane yake damunta kiringa janta a jiki dan Allah Yasmeen "kewadai mommy tanada me debe mata karki damu dan yanzu haka suna tare "Allah sarki Najib din naciki kenan "wana yaya Najib wanda ya fishine a ciki Tana gama fada tabar falon bayan mommy tabi da kallo "ikon Allah kodai Yasmeen bakin ciki take da shaheeda ne Allah ya kyauta gaba kadan zan gane haka Shaheeda nakan kirjinshi a kwance boss yace shaheeda nizan koma yanzu kar inyi jinkiri yadawo yamin akuya Ba yanzu zedawo ba kadan bari zuwa anjima niban gaji da kaiba tana kokarin hada bakinshi da nata boss yarufe bakin ta "shaheeda mutanenemu ba dabbobiba yakamata muyi abin da ya dace a dan lokacinda Allah ya ara mana karmuyi zire a lokacinda ba namuba mufada cikin wata cakwakiyar ya sauke shaheeda daga kirjinshi ya maida kayan shi "nizan tafi gawannan harda maganinki yau sabone a ciki zetemaka miki gurin jawo hankalin Najib towel fari ta daura tatashi danta raka shi ta bude mishi kofa harze fita ta janyo shi ta hada bakinshi da nata ganin shaheeda naniyar zarcewa boss ya fusge bakin shi daga nata "kar a kamamu nakula Kekin kuna bakya soran kauri nina tafi yana fita taga hajiya naja'atu a falo ya gigice yana niyar komawa ciki hajiya naja'atu tana murmurshi tace harka karaso Kenan sannu da zuwa Shaheeda cikin muryar rada take cewa kafita kugaisa tana turashi waje ka fita mana hakanda kakeyi zesa ta zargi wani abu Da kyar ya fita itama tabi bayanshi a yanda take kai ba dan kwali balle hijabi suka isa gurinta yasunkuya "ina wuni "lpy kalau y gida da mutanen gidan "lpy klau duk suna gaida ku "muna amsawa "hajiya nizan koma gashi ba samu gaisawa da angoba "Allah sarki idan ya dawo a fada mishi kazo ba wani abu ai dake be jima da fita ba a gaida mutan gida Yasmeen ce ta dawo falon cak idanta ya gane mata shaheeda daga sama har kasa ta kare mata kallo tana mamaki daurinkirji ko cinya be Gama rufe mata ba balle ayi maganar gwaiwa a haka tafito a gabanshi kuma Yasmeen ta fada a zuciyar ta zama tayi tadan matso murmushi me kama da yake "zasuji da kyau natafi Shaheeda tace ka gaida su mama yace to shaheeda ta koma daki hajiya naja'atu tabi Bayanta da kallo tana dariya "haryanzu shaheeda yarinta na kanta kokulata Yasmeen batayi ba Tana shiga ta janyo ledar da boss yazo mata dashi ta ciro kwalbar maganin ta bude takafa kai ta shanye gaba daya ta yarda kwalbar ta kwanta cikin muryar me alamar somi somin buguwa take cewa boss idan inadakai bani ba damuwa kwata kwata takarasa da dariya Bangaren Kareema kuma yau akasa ranar aurensu da Alhaji Ibrahim gadara ansa 21 ga wata ranar a sabar ya kama daurin aure sati daya aka saka umma murna da farinciki kawai take da habaici lubabatu da umma suka shiga saka abin da zasu karawa Kareema dashi Lubabatu ce tace da farkodai umma dole a kafeshi akuma bude mishi aljihu tayanda da munce a bamu kudi tana tambaya ze bata yazama minjin tace se yanda tayi dashi hajiya naja'atu kuma asamata tsoran Kareema ita kuma Kareema akara mata kwarjini tayanda babu me rainata damunyi wannan shikenan yauwa lubabatu kinyi daidai ni AI banyi wanna tina ninba ko kadan ta kunce zani ta ciro kudi ta mika mata gashi afara aikin da wannan kinsandai bamuda lokaci ko eh nasani umma bari naje yanzu sosamu Kareema tazo muje tare taji komai da kanta idan da abin da takeso a kara mata dashi seta fada "bakomai Kareema tashi kidauko hijabi ku tafi "ga hijabina a hannuna mutafi kawai lubabatu "umma semun dawo "saikun dawo nima zandan fita amma bazan dade ba zan dawo "to umma kice kema wani kunge kungen Zakiyi "Eh wlh abin seda haka naja'atu kuje kudawo karkuyi jankiri Suna tafiya umma ta ciro kudi a cikin filo ta matse a zani tasa hijabi ta fita Adam daya fito daga dakin mami yana ganin fitar ta yabi bayan ta Tafiya kawai takeyi bata waige saida ta ankara ana binta sai ta waigo bataga kowa ba takara tafiya ta kuma wai gowa kayan da yasa ta gani bata ganshiba Adam umma ta fada kamar kayan da yasa yaukenan dole na canza hanya adam na labe awani kango kanya fito tini ta bace mishi yana fitowa yaga bata nan ya shiga waige waige kozega inda tabi amma be ganiba tafiya kwai umma takeyi me nisa da takai dai-dai wani kango me get ta duba taga ko wani ya ganta amma bataga kowaba seta shiga kango se kanshin wiwi da taba ke tashi a gurin tadanyi tafiya kadan san nan tajiyo hirarsu tasa kai zata shiga taji suna cewa "Oga zaki garifa yaci wuta yaza ayi da kudin dake kurin uwar budurwarka tayi alkawari zata kawo amma shiru koda muka fito daga gurin kwalawa bata nememuba kose munje munyi tonan siririne danmu ba a rufe tsiya damu sedai arziki Zaki ya cire tabar dake bakinshi ya busa hayakin "kwari me kake ganin za ayi yanzu kaifa na bukatar caji baze yiyu da kudinmu a wani guri mukuma muzauna bamu hau online ba Kwari yace muje muyi mata eh yane idan taki bamu semu mika gaisuwa ta hanyar Dara mata na jaki kungane ai muje kawai gaba dayansu suka mike zasu fita umma tace abin bekai haka ba gani nazo zaki yace barka da zuwa dafatan Tare kike da kudinmu "Dashi nazo ta bude zani ta ciro ta bashi gashi nan kirga kagani kosun cika Kwairi ya ansa ya kirga "suncika "madallah ga wannan zaki ya ansa yace na meye shikuma "yauwa wani aiki nakeso kumin nan da kwana uku masu zuwa "wakike so a kashe "ba kisa za ayi ba zaki ta rage murya ta yanda koni bazan san metake cewa ba ta gama fada mishi komai suka bushe da dariya kwari yace kina bamu aikin mata bazaki bamu kisaba se Kana nan aiki irin wannan kar a kira mana kwalawa kamar wancan lokacin ba haka mukayi da keba baki san kiran kwalawa ya sabawa dokar aikin muba ki kula indai kinaso mudinga miki aiki Umma tace Shima kisan a kwai lokacinshi Nidai fatana kuyi yanda nace sannan wanda zeje aiwatar da aikin dan Allah karya bugu sadoda kar a samu matsala bani na kira yansan daba bazan Bari a kira suba kushirya komai da kanku ni zanji da komai taciki ya aikai Kuka fito duk nashiga da muwa da aka kulle ku "mune fa munada daurin gindi ta inda bakya tinani lbr Kawaiya samu yasa aka sakemu kwananmu 1 a can karki kara shigowa inda muke kai tsaye akwai matsala ki kiyaye ware kawai ki baza ido kisha kallo cewar kwari "To na tafi sekun zo tana fita sukayi ido 4 da Adam rai a hade ko alamar dariya babu umma ta dabar-barce tana niyar komawa ciki New writer's Hakan Take *husba'ahfama* 😍❤🤩 *'YAR kwalliya* ❤💋 WhatsApp number 📱 07036891952 👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝 👠👠👠👠👠👠👠👠👠👠 💄💅 *HEEDAYA* 💅💄 *(I KIRARI)* 👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝 👠👠👠👠👠👠👠👠👠👠 Written by *husba'ahfama* *Instagram @officiall_husba'ahfama* Facebook *Real husba'ahfama* Follow me on wattpad *@Real husba'ahfama* 28-29 Umma ta dabar barce tarasa mezata cewa Adam saboda karya barota ta kakalo dauriya da dakiya tace Adam meya kawo ka nan kuma Cikin kallo me ciki da tuhuma Adam yace umma kezan tambaya meya kawoki nan ke kadai bakiga yanda gurin yake bane "Yimin shiru ina ruwanka da yanda gurin yake kasan meya kawo ni gurin wuce mu tafi " kije kawai zan taho Abu zan gani a cikin gurin nan Ina mamakin abinda kika zoyi nan Gigicewa tayi da taji ze shiga tarasa inda zata sa kanta tini Adam yasa kai ze shiga ta rike shi "Adam karka shiga nace kasan dai Nina haifeka ko bakada wata uwar bayanni kana sane da cewa ba a sake uwa to indai ka yarda da haka karka shiga wuce mutafi " na yarda ammafa sena shiga senaga suwaye a ciki da ganin gurin nan ba gaskiya a ciki danme gaskiya baze zauna a nanba matsa na wuce Tokare kofar umma tayi "nace karka shiga ko Adam kana shiga zan tsine maka zan daga maka nono tinda ka rabi hafsa nasan shikenan kuma tajika ta baka bazaka saurari maganataba shiyasa tinwuri narabaku saboda bokanta ya iya aiki sekai watsi da maganata ga hanya shiga kadai ji me nace Umma tabar jikin kofar Adam jikinshi ya mutu yafasa shiga yajuya ya fara tafiya gida Umma tayi murmushin keta tabi bayan shi da sauri saida ta tarar dashi Tace Adam kajini da kyau karna sake naji maganar nan a wani guri inba hakaba zan tsine maka wlh da gaske nake ba wasa ba kaji na fada maka To kawai yace harsuka Karasa gida fada kawai take yi mishi kin shiga daki yayi dakin su heedaya ya shiga Umma tayi salati " Allah na gode maka in haifi da a cikina ya fifita wata a kaina nida shi se kallo ba a isaba wlh sena dauki mataki umma ta fada da karfi a tsakar gida Mami da Adam dake zaune afalo suna jinta mami tayi murmushi wani hirar Adam ya dauko yana yiwa mami sunata Dari umma takasa zaune ta kasa tsaye se tafito da niyar yi musu magana seta fasa ta koma daki shakuwar Adam da mami da yaranta na bata mata rai yanke shawarar yinta ta kare umma tayi tafito ranta a bace tazo saitin kofar taji mami na cewa Adam abin da hauwa'u takeyi betaba bata min raiba ko kadan hasalima nibana kulawa da haka komai lokacine watarana zata gane gaskiya karka damu ba komai inda sabo ai yaci ace na saba Mami na sani amma ki kara hakuri konace ki rinka hakuri kan hakuri Dan umma bazata taba canza haliba Nina sani Umma na labe tana jinsu girgiza kai tayi ta rike baki "wato gulmata sukeyi idan sun hadu yau naga lalacewa a hada baki da danka anayidakai tsabar ranshin kishi ko a kanshi gaba se a hada baki dashi a bani guba yazama dole na rabasu dangaba bansan meze biyo baya ba umma tafada a hankali tayanda bawanda ze jita "Allah ya Toni asirinki hafsa kisa Dana a gaba kina yidani shikuma yana biye miki tsabar ranshi kishin koda yake ba laifin sa bane shanye shi kikayi Umma na tsaye a waje ta inda take shiga batanan take fita ba jin basu kula taba suncigaba da,hira ta bankade labilen tana kallon su Adam da kofin Lemo a hannun shizekai baki umma ta shigo a fusace ta bige kofin ya fadi lemon yazube Kofi ya fashi ta daga kofin tangaran da aka Zibo lemon ta doka da kasa ya fashe cikin kankanin lokaci dakin ya fita daga haiyacinshi "hafsa dahaka kika samu kika malla kemin da tsaka Nina dashi se kallo baki isaba tashi kabar dakin nan bake bashi ke kallo idan yashiga tsaka ninki dashi wlh zakisha maki wuce kafita "Umma karkice haka mana idan nafita inazani gurin wa gurina man nice uwarka ba itaba kuma kaf gidan babu wani dakin sewannan ne fita nace kosena fita dakai dakaina Mikewa yayi kamar zefita ya koma bayan mami " niba inda zani anan zan zauna kome zefaru sedai ya faru Ikon Allah shikenan kinrabani dashi kinji dadi Adam zoka fita Na dawo kanta Dan dakata zanyi a gidan nanyau tura takai bango Mami ta kalli Adam "kaga fita kamar yanda ta umarce ka kuma ka bata min rai wannan ba tarbiyar Dana mukubace tace ka fita amma kaki gaskiya banji dadi ba kabata hakuri kuma kafita Umma yi hakuri bazan karaba mami yafada yasunkuya har kasa kiyafeni bazan iya jure wabane bazan iya rabuwa dakeba umma da tace infita ba iya fitaba kawai dakinma seta hanani shigowa "Yawuce Adam karka kara yin haka ba halin dana gari bane Nagode Mami insha Allah zanzama Dana gari Umma tazare ido tana huci jitayi kafafunta narawa afusace ta fisgi Adam ta watsa shi waje ya mike ya fita daga gidan umma tamatsa tana nuna mami da Dan yatsa "Baki isaba ba a haifi me rabani da Dana ba wace ke ba a haifaba wlh Mami tace hauwa'u kishiga han kalinki i na raga mikine saboda Adam idan kikace zaki zake kiwuce Gona da iri tofa bazan dauka ba idan kika sake nuna mini yatsa sena karya hannun nan idan kina musu gwada ki gani "Idan nayi mezaki yimin eh fadi " ki gwada mana idan kikayi jikin ki da idanki zasu fada miki abinda ze faru "Yau koni koke hafsa sena koya miki hankali kin mallake malam kinrabani dashi "au hauwa tanan kika fito to jamuje idan kin gaji da tsayuwa kya fita nikinga ta fiya ta " kekin isa wlh ba a haifaba dawo dawo nace ko Mami taki juyowa umma taje ta janyo ta tana nuna ta mami a fusace ta watsar da umma tana dukanta ta riko hannun data nunata dashi ta murde umma ta fara ihun neman te mako "Adam ina kake ne zoka janye min ita Adam Adam kojiyo ta beyi ba yana fita ya hadu da Ali sukayi zaman su mansir ma yazo suka zauna tare da malam Nazifi A waje suna hira Mami dukanta take kamar an aikota umma nata kiran Adam kamar daga sama Adam yaji ana kiranshi jin sautin kiran kamar nameyin kuka yasa suka shiga gaba dayan su suka samu mami akan ruwan cikin umma cak suka tsaya aka rasa me rabasu kareema da lubabatu suka Shigo suka tarar dasu a haka ciki suka shiga da kyar suka iya rabasu umma tashima ta kasa a " dagani kareema inada magana Kareema ta daga ta "Malam kana cikin gidannan matar ka ta dakeni kaki daukar mataki Mansir yace meya kawo ki dakinta "Ina ruwanka eh da ubanka nake bakaiba " bakarya yayi ba ai tambayace me kyau meya kawo ki dakinta cewar malam Nazifi Adam yace mantawa nayi ban fada muku ba nan ya sanar dasu komai da abin da yasa ta shigo kunji abin da na sani "hauwa bakida gaskiya meye naki na rabasu kinsan zaki haka meyasa bakiyi tin yana karamiba se yanzu kina sane kike turo mata shi ta shiraya shi ya zauna a dakinta ita taci kashin shi sakaiyar dazaki mata kenan kincika butulo hauwa tashi kibar mata daki " malam haka zakace eh tashi mana idan kika Bari nasake magana dube-dube ya fara bashiri kareema da lubabatu sukamata suka kaita dakinta Umma garin yaya meya kaiki cewar lubabatu Umma tace tsautsayi da rabon shan duka "Allah ya kare gaba nizan koma kareema zata miki bayani Kai ta daga mata lubabatu ta koma gida umma kwana tayi tana jinyar jikinta Bayan kwana 2 Hajiya naja'atu yasmeen da shaheeda na zaune a falo suna kallo sukaga yan aikin gidan na shigo da akwatina a falo suka ajiye Alhaji Ibrahim gadara ya shigo da wasu mutane yana nuna musu wani sashe na gidan kirjin naja'atu ya buga amma ta dake bayan sungama ya dawi falo "kunga inda za ayiwa gyaran gobe kuzo kufara aiki Dan da wuri nake so " Alhaji koyau kace kanaso zamuyi maka kaidin namune ba abin da zamuce dakai se godiya Allah ya rabaka da duniya lpy wani ya fada daga cikin su da alama shine babba "Ameen Dan lami gawannan kukara Kudi yamika musu Dan lami ya ansa yana godiya "Kuje se goben inkunzo sukace to Kan kace me hajiya naja'atu ta jike dagumi jikinta yadau zafi Ma aikatan suka gaidata dakyar ta amsa tana kallon Alhaji Ibrahim sukayi sallama sukatafi zama yayi akan kujera ya cire hular kanshi Ruwa yaga anmiko mishi ya ansa yana kallon Wanda ya bashi ruwan Yasmeen ya gani "Daddy sannu da zuwa "Yauwa yasmeen kai ammafa kin kyauta kamar kinsan INA bukatar ruwa "Mommy ya haka meya sameki kinganki kuwa lokaci daya kincanza gaba daya Kasa magana tayi shidai kallonta kawai yakeyi Yasmeen nashiga ciki Bin shi tayi da kallo naja'atu na ganin haka tabi bayan shi shaheeda ta dawo kusada yasmeen "A ganinki akwati nannan nameye cewar shaheeda "Oho "Na fadar kishiyane shiyasa kikaga mommy ta zama mara lpy ta gano hakan aganinki meyasa daddy yakawo mutanen da suka fita kinga inda yanuna a gyara na kishiyar mommyne Yasmeen ta kalli shaheeda " kishiya wa mommy New writer's Hakan take *husba'ahfama* 😍❤🤩

Chapter 6 of 21