agidan malam wajan takwas nadare su adam sukazo da mansur daga wajan aikinsu Abuja sunzo hutu sukatarar da abin dayake faruwa
malam yace sukwantar da hankalinsu babata tayiba du inda taje zata dawo karsu damu Allah yashiryeta yace bazantaba yimata bakiba Dan abin nata kuma se addu'a kuje kuhuta in lokacin rufe gidayayi kuje kurife
sukace to
umma dai babakin magana se Ido tamaji da inuu da yadameta
hakakuwa akayi dasukaji shuru suka rufe gidan umma nadaki anyi kwanan zaune gari nawayewa kareema zata dawo gida tahadu da us sukai fada saboda abin dayimata dakuma mahaifiyarta gashi yabarta da yaro yasamu wata sukayi fada kacakaca har marinta sedayayi Haka sukarabu baranbaran Kuma Kareema tayimasa alkawarin kaiwa iyayansa dansa tinda hakane yacuceta yaci amanarta yasata muguwar hanya Harda da sabo da bacinran da tashiga takoma gidan da takwana hankali atashe tabude jaka tafito da Kayan Mayan da tasamu akabata takafakai tahau Sha sedataji tayi yanda takeso sannnan tatashi tatafi gida Haka tahau adedaita tana bugen tafada Masa inda zata harsuka iso tasauka batabashi kudiba zata shige gida
meadaidaita yace kinma Isa yarinya nafiki tashanci wlh sekinbani kudina kankishiga gida
harsunfara tarawa kansu mutane su Adam sukajiyo hahaniya awaje suka fita sukaga meyake faruwa suka sallami mutumin sukajata zuwa gida sunashiga suka rufeta da duka seda sukayimata dukan fitar hankali malam nawajan bece komaiba se mami datahana tace karsu lahantata subarta Haka
ummu se hawaye taketayi hartayi watarama tace kareema ina kikaje
abuge cinkin muryar wahala take magana Haka umma tajata daki sukashige
Malam yace kunyimin dedai nagama yanke hukunci kanyaran da yake zuwa wajanta kusan Kullin seyazo zance danyacemin shiyaji yagani yanaso Kuma ze aureta yanzu yakirani awaya yace a idanshi kareema tadawo Kuma yacemin in yazo zefadamin wata magana bansan meneneba Kuma yacemin Dan Allah du inda heedaya take akirata tazo agabanta zefada Dani da ita da mahaifiyarta Allah yasama sundawo daga kasar wajan da sukaje hutu mijin yakirani zasuzo gaishemu zansamusu lokaci sesuzo yanda zasu hadu da yaran
Dasafe bayan ankarya kareema tatashi jiki duyayi tsami duciwo yake yimata Haka taje tai abinda zatayi bawanda yakulata kowa fishi yakeyi da ita
Ali Zaki yasawa malam ranar da zezo malam yafawa najip Suma suzo ranar Yana gida sesu gaisa zokiga murna wajan heedaya yaune ranar da zatafara zuwa gida tinda akamata aure har tausayi tabawa najip ko bancin kirki batayiba dasafe dazasu taho dakyar taci abinci shima seda najip yace inbataciba anfasa zuwa sannan taci wajan Tara da rabi tadameshi sukataho saboda asabarce bakaramin tsaraba tayowa yan gidansuba atafiyar da sukayi akwati biyu tayomusu natsaraba kowa da sunanshi kansukarasa gidansu heedaya seda najip yabiya da ita akayiwa su Mami sayaiyar Kayan abinci masu yawa
heedaya harcewa tayi sunyi yawa
yace inban musuba wazanyiwa suda sukabani yarinya guda mehankali da tarbiya gidan mutunc
i damotar tayi kadan Kiran direban gidan su hajiya naja'atu yayi awaya yazo yakwashi sauran heedaya ita tama kasa magana
sedariya najip yakeyimata yace karkimantafa yaune rana tafarko da zakifara zuwa gida aiyadace mufaranta musu Susan yau yarinyarsu tazo gaishesu
Dahaka suka karasa har kofar gidansu heedaya dasauri takama murfin mota zata fita
najip yarukota yace inbakibi ahankaliba zamu koma adai Kinga gidan
dasauri tanutsu tace nadenato
yace tare zamu shiga zaashigo da Kayan
sukashiga dasallama dauke abakinsu kowa da yake gidan fitowa sukayi sunamusu oyoyo
umma daga daki tace ke tashi mufita muga yatakoma dannasan kilama wahala takesha ninasan kudin da nakashe Akan zaman auransu dankarsu zauna lfy yaringa Bata wahala kuma ninasa boka ahanata zuwa gidannan dawuri Dan uwarta tadamu barinaga yatakoma
umma nafita mutuwar tsaye tayi ganin Kayan da yacika tsakar gida Kayan abincine kalakala zasu dade basunemi komaiba kokayan gara sedai Haka
budar bakin umma secewa tayi mansur shago zakubudene Baku fadaminba saboda bakudaukeni komaibako
kowa shuru yayi ana sauraranta
marsur yace aa umma najip ne da heedaya sukakawo muku tsaraba malamma fada yaketayi Kayan sunyiyawa ga mamima nanata fadan
Mami takalleta tace Yaya kiga yarannan dawannan siyaiya Haka karaso kitayamu yimasa fada Kayan sunyiyawa
umma se hawaye Baki narawa tana nuna Kayan da hannu Batasan lokacin da takaraso wajan kayanba tace duwayannan Kayan
akacemata eh setakasa magana najip da heedaya suka gaishita heedaya Harda zuwa ta rungumeta
tace umma nayi kewarku wlh Ashe Yar uwata tahaihu baafa daminba nazo suna
can tagano kareema nahawaye heedaya tajeta rungumeta tace Yar uwata kwana dayawa wlh nayi kewarki gashi bani da number ki
Kareema Dakar tabudi Baki tacewa heedaya sannunkiu da zuwA kunzo lfy ygd
Heedayace taamsa najip bece komaiba se harara da yake sakarwa kareema bawanda yakula dasu
Najip yace umma inakwana ygd
Kawai baseganin umma akayi tazauna dirshan akasa tana kuka tambayar duniya ammata taki magana
Mami tace wai meyasameki Yaya kobaki da lftne
Tadada fashewa dawani kukan abin yatabawa su Adam Rai sosai Wai meyasa umma take musu Haka batakama girmanta wannan wana irin bakincikine Haka agaban sirikinsu seyagane matsalar gidansu
Adam azuciya yacigaba da magana yace kodayake aiyasan halinta shi najip din
Malam yakalli heedaya da najip yace kutashi kushiga daki muzo mugaisa sosai karku damu wannan tasaba mutanantane sukatashi kwanannan Haka take fama dsu
Atare heedaya da najip sukace Allah yabata lfy
Heedaya azuciyarta tace haryanzu umma batacanjaba halinta nanan abin yatabamata zuciya yake kawai takeyi
Su najip nashiga dakin Mami
Da ranrafe umma takoma dakinta tana rusa kuka Harda ihu
malam yabi bayanta yace wlh kinji kunya mahaukaciya Allah yashiryeki kinyinisa bakyajin Kira de addu'a wlh yau kinci darajar yarannan dabadan hakaba abin da zanmiki agidannan wlh sekinraina kanki karkidamu zamuhadu nangaba Bari yatafi Dan heedaya babakuwa bace tasan halinki ga isharanan kalakala kinagani Amma kinki ganewa bare kishiryu
BAYAN an gaigaisa dasu heedaya anatahira heedaya tagano kwano arufe tabude tanaganin abinda yake ciki tahau murna
tace har yawuna yatsinke Kai Amma naji Dadi Mami kamar kinsan inajin marmarinta
wainar fulawace akwanan ansoyata da manja suyar tayikyau heedaya datafaraci tana dangwalar yajin harwani rufe Ido takeyi Ido suka zubamata suna dariya najip yaga cinyajin nata bana hankalibane yasa hannunshi ahankali yadauke yajin yasaboye abayanshi du idanta arufe cikwai takeyi tadada gwutsurowa zata dangwali yajin taji wayam bakomai
dasauri tabude Ido tace wayadauke murya gamar zatayi kuka take maganar
suka dada samata dariya sukace yakarene kincinye yajin duka
tace Kai wlh wanine yadauke Mami kingansuko zatayi kuka cantakalli najip tace mesanyina hardakaiko tace Kai wlh kaikadauke Dan Allah kabani
yace aa bazan bakiba ze illataku keda abin cikinki bazan bakiba
Kunyace takamata tarufe Ido tadau kwanan tabar wajan tashige can cikin dakin
Su mansur sukace haba kodamunji wannan cinyaji Haka su heedaya angirma Allah yaraba lfy
itadai Mami dariya kawai takeyi tinshigowarsu tagane yarinyar Tata nada karamin ciki azuciyarta semurna takeyi takusa samun jika
najip yatashi yace Mami zantafi sedayamma zandawo nadauketa kuyi hakuri wataran zatazo takwana bamuje mungaida su mommyba shiyasa zatatafi yau
godiya Mami tayimasa sosai tace bakomai tinda kakawota mungaisa hakanma yayi Allah yakara Baku zaman lfy amma Dan Allah nangaba inzakuzo karkukuma irin wannan siyaryar Haka kaji
shidai dariya yayi yatafi yanamurna azuciyarshi da Allah yabashi sirikai nagari wayanda abin duniya berufemusu idoba
Mamice takoro heedaya taje sukayi sallama da najip
asoro tasameshi atsaye tace Kai mesanyina yaakayi kasan zanzo muyi salam kajirani
yace nasan maminmu zata koroki kizo dannasan take bazakizoba tinda kishigo cikin yan uwa kinshareni gakuma waina komenene kinsamu wlh karkikara cin yajinnan mamima tace bazaki Kara cidayawaba nasan bazata barkiba
dahaka sukayi sallama yaja mota yatafi sedagawa junansu hannu sukeyi
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama*πβ€π€©
*Me 'YAR KWALLIYA* β€π
*Me HADARIN So* β€π
*Me NAFI GANE ARO*β€π
ππππππππππ
π π π π π π π π π π
ππ
*HEEDAYA* π
π
*(I KIRARI)*
ππππππππππ
π π π π π π π π π π
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@Real Husba'ahfama*
89-90
Heedaya nakomawa ciki tafito da tsarabar datayo musu tarabawa kowa se murna suketayi anakaiwa umma nata tace bataso bazata karbaba malam yace akyaleta su Mami sukwashe Kayan itakuwa Kareema daakabata takarba tayi godiya umma tahauta da fada setamayar itakuma tace wlh bazata mayarba Kayan sunyima ranar heedaya srdare najip yazo yadauketa tadawo gida da kewar yan
uwanta
adaran Dr Abdul yakira najip yacemasa gasunan zuwa gobe yafadawa heedaya najip yafadawa heedaya suna da Baki gobe zasuzo suyini murna heedaya tahauyi
Washegari dawajan shadaya nasafe su Dr Abdul da amjad da yasmeen dakuma bahijja matar da najip yakeso zeaura dasallma sukashigo suna murna heedaya tana falo da kofina ahannunta na tangaran zatakai kicin
tabude Ido taga Wanda suke tare takurma wani irin ihu tace asheyau zakuga kaura agidannan inbakusan da itaba yau zakusani
tawani zuba dagudu sewajen ajje motoci taga wata doguwar sanda kamar gora tadawo da gudu dauke da sandar ahannunta tashigo kofinan dataajje Akan hanya sutadauka tahau jifa dasu cikin falan seda sukafashe uuka akasa tazagayesu tashige taikansu Dr Abdul zata kwadamusu sandar
tace rainini hankalin yayiyawa kunzata banida wayoko kunyimin a asibiti yauma kunzo hargida kukuma yimin
najip cewayakeyi meyehaka heedaya kisauraremu kijimana
tace wlh hardakai zanhada kaizanfara dokewa dagani har ita muhakura shikuma wancan mebaka shawar yau Sena gotarmasa dabaki Naga dabakin da zakana bashi shawara kai wlh dukanku Sena hukuntaku tadada dokamusu sandar suka kauce sukayi bayan kujera dagudu
Dr Abdul yace Dan Allah kitsaya kiji Dame mukazo kiyihakuri
sabo da tsoro yasmeen da bahijja hanyar dakin heedaya sukadosa zasushiga gabadaya sunrude
lokacidaya taburkice musu idanta yayija yacanja kala tabisu bahijja dagudu tace auuu dakinama zaashiga hakanma yayi
sukasuba dagudu suka kollo dakin
kome tasamu afalan jefomusu takeyi suna kaucewa najip cewa yakeyi Dan Allah my love karkiyimin asarar babyna nasha wahala kan nasameshi kitsaya Dan Allah karki lahanta kanki
sunkuyawa najip yayi tabayan kujera yabi bayan heedaya batakulaba taji ankamota tabaya anrike yakama hannun yakwace sandar sukazube kasa sehaki sukeyi
amjad kwanciya yayi akasa yana dariya yace kut Daman munada kaura dagaske ayan uwanmu bamusaniba seyau agaisheki anty heedaya kiyihakuri kizauna kiji Dame mukazo hakakawi koruwa baabamuba serotsemu daake niyaryi
Dr Abdul yace Wai Daman anagotar dabaki
sukasa dariya dukansu
najip dai matse heedaya yayi atsakiyar kafarshi yanda bazata tashiba
amjadne yakwallawa su yasmeen Kira kufito matsorata kubude kofar kufito sunsauka
atsorace sukafito bahijjace me tambayar Daman dagaske Yaya tanada aljanu baku fadaminba
heedaya tace bulukiyace akaina bakisaniba kuma insuntashi shake mutane sukeyi se harararsu takeyi takalli yasmeen tace kema hardakeko zamuhadu bazakiyi wuyar murkushewaba
Yasmeen tace inkinganniba
Dr Abdul yafara magana
Yace kanwata munzo gaishekine dakuma yimiki bayani yau
kinsan andaga auranmu nida yasmeen dakuka tafi hutu bawani abubane yakawo hakaba sedan anaso ahada auranmu danasu amjad ayishi lokaci daya akayanke shawarar cewa abari sannanma su yasmeen sungama makaranta itada bahijja shikuma amjed yakarasa gininshi dayakeyi mungayawa najip kar agayamiki Wanda amjed zeaura sumunhadu gabadayanmu bawatabace matar da amjad zeaura se bahijja Kuma bahijja dakikegani bawatabace kanwatace uwadaya ubadaya tintana yarinya sunshaku da najip hartagirma mumunyi zatanma najipne zeaureta asha bahaka bane jininsune kawai yahadu batanan akai bikinku danhaka bakisantaba tanacan inda take karatu shiyasa Kuma insunyi hutu batafiya zuwananba acantake zamanta saboda akwai yan uwanmu acan rabon aure tanadawowa soyaiya mekarfi tashiga tsakaninsu da amjad Kuma bawanine yahada wannan abinba ninenan daga ita har najip din dakyar nashawo kansu sukayarda daabin danasasu Kuma alhamdulillah burina yacika kunsasanta dalilin Haka toyau munzone musanardake dankisan wacece bahijja Kuma najip bawanda zeaura kekadaice azuciyarshi yanzu kinganeko Kuma bikinmu Nanda satibiyu masuzuwane zaayi sekishirya kece kirjin biki kiyihakuri daabin da mukamiki munmukune danmugyara zanan auranku Amma badawata manufa mukaimikiba kaura dafatan kingane
kunyace takamata tarufe Ido taboye fuskarta ajikin najip tahau dariya Suma dariyar sukakamayi
amjad yace caucau sa'a dai kaura agidan Yaya najip dake bawata Allah wlh yaimaganar irinna kauraye
dariya kawai dateyi
Dr Abdul yace to atemaka abamu koruwane musha irinwNnan gudu daakasamu Haka
heedaya tace kuyihakuri Dan Allah wlh bansan hakabane
sukace bakomai ranar yinisukayi agidan su najip seyamma sukakoma gida
BAYAN SATI BIYU
Rana batakarya sedai uwardiya tajikunya Allah yakawomu bikin Dr Abdul da yasmeen amjad da bahijja ansha biki bakadanba najip da heedaya sunyi rawargani bakadanba ankai amare gidajansu lfy anyibiki cikin kwanciyar hankali angama biki da sati daya sukatafi kaaar waje hutu nawata daya
BAYAN WATA SHIDA
Malam yayanke hukuncin aurawa Kareema zaki
Ranar da Zaki yazo neman izinin turo iyayayansa malam yaamince ranarne Zaki yafadawa malam abin da yace zefada Masa
Nan Zaki yace Abba kwanakican nace Dan Allah damaganar da nakeso naidaku dakai da heedaya da mahaifiyarta sekuma akasamu sabani Allah benufa ranar nazobe tafiya takamani ta gaugawa seyau Allah yayarda zanfadamaka sabo danaga kanada kirki sosai Kai dantijone nakwarai mesanin yakamata Dan Allah kannafada maka kayimin alkawarin innafadama bazakafasa bani auran kareemaba Dan Allah Kuma kayafemin nashiryu gafara nazonema wajanka dakuma heedaya da mahaifiyarta sonake yaunawanke heedaya awajanka dudatayi aure tana gidanta lokacin da nashigo gidanku can shekaru dasuka wuce naso nafarwa kareema bawatabace taaikoni se umma Babar kareema itataaikoni Kuma tace in antambayeni nace heedayace taturoni sekuma fadan damukayi kwanakican akofargidanka Dani dayarana dakuma mage dayaransa du bawatabace tasamu se umma Kuma tace muce musamarintane damuke fasikanci da ita bakaramin kudi tabamuba alokacin toshine yau nace Bari nafadama gaskiya wlh baruwan heedaya du hadin kishiyar uwartace Dan Allah kuyafemin natuba Kuma karkahanani kareema mutuncin da kanunaminne tinda nafara zuwa neman auranta najidadi shiyasa Naga yadace nafadama gaskiya wlh tindanayi abun yake damuna seyau Allah yasa nasauke nauyi itakuma umma danake ganin tasanni zatabani yarinyarta tinda nashiryu itace tanunami tsana da kyama Kuma nabautamata sosai mundade munamata aiki itama tasani akiratama nafada agabanta
malam yace innakirata dasauran yangidan zakafada agabansu sonake suzama sheda
yace eh nayarda wlh zanfada
malam yace inazuwa kajirani zansa ashigodakai
yaceto Abba
malam nashiga yatara kowa atsakargida yace ajeashigo da Zaki akaje akashigo dashi
malam yace aliyu fadi abinda kafadamin agabansu kowa nasauraranka
yace to Abba
kafin Zaki yayi magana
umma tace Wai Dan Allah meyake faruwa hakakawai antaramu Kuma karasa Wanda zemana magana sewannan waikasan wayeshi dahalla kaitashi kafice segumi takehadawa takasa Zama wajedaya
malam yasakarmata harara yace innakarajin bakinkin anan wlh seranki yayi mugunbaci ko Ina sekinnuna halinki
taishuru seraba Ido takeyi
can Zaki yafara bayani yafadi komai kamar yanda yafadawa malam awaje salati kowa nawajan yafara mamikowa kuka tafashe dashi tace Dan Allah hauwa'u me mukaimiki Haka me muka tsaremiki Haka kike tahadamana irinwannan shirrin yanzu wace ribakikaci dakikayi
Adam can yace ehhh wlh natuno akwairanar danaga umma taje wani kango Kuma tambas bakowane mutunbane ze iyazuwa wajannan barekuma mace
yaiwa Zaki bayanin ranar
Zaki yace eh anyihaka ranarma cikwan kudinmu takaimana takuma bamu wani aikin alokacin
umma anyi tsumutsumu ankasa maga segumi dayake taketomata
malam yace aliyu tashi katafi mungode Kuma munyafe maka dagani harwayanda kayiwa lefin naari bakinsu nace munyafe kai kobakomai yanzu munzama daya dakai kazama sirikinmu danhaka yanzu kaje katuru iyayanka atsaida ranarbiki nitawajena bawani lokaci metsawo zaajaba befi acikin satinnan zaayikomai insha Allah
Zaki yayi godiya yatafi yanata murna burinshi zecika naauran kareema
sumansur sebawa mami hakuri suketayi Harda kareema abin itama yatabamata Rai haushin abin da ummanta tayiwa su Mami
Nan malam yayi gyaran murya yace kareema nayanke hukunci nasa aliyu yaturo iyayanshi kanmaganar auranku dudanasan bawani sanshi kikeyiba nidai nayaba da hankalinshi danhaka nace yaturo Kuma inhar na isadake Kuma Ni mahaifinkine najure duwani bakinciki dakikasani to Nima inaso kiyimin biyaiya kiyarda da auran wannan yaran kodan mahaifiyarki yazama darasi agareta Kuma in Allah yayarda komai daran dadewa zakiga ribar biyaiyar dakikayimin kinji
tace to Abba nayarda duda banasanshi zanmaka biyaiya kamar yanda Yar uwata heedaya tayi Kuma tagariba arayuwarta nagode Abba Allah yashigemana gaba
kowa yace ameeeen
tace to Abba yazaayi da magaji
yace eh shinayanke hukunci tinda yanzu yakusa shejara Kuma yafara tafiya duda batayi kwariba Kuma yanacin abinci sosai bedamu dakebama sosai awajan kakarshi zakibarshi itace zataci gaba da rainanshi danhaka daga gobe in Allah yakaimu kiyayeshi kekadai zakitare
tace to abba kome kayanke dedaine Allah yabar girma Dan Allah abba kome nayimaka arayuwata dawanda nasani da Wanda bansaniba kayafemin nadena duwani mugun hali dakasanni dshi
yace nayafemiki Allah yaimiki albarka yadada shiryaminke da sauran yaranmu gabada
yace sekuma magana tagaba hauwa'u nagaji nagaji dahalayanki yau zaayita takare kibude kunnenki dakyau kiji nasakeki saki biyu Kuma wlh kisani kigaigauta barmin gidana kukama kitambatar kintafi da jikanki Kuma wlh inbaki tafiba zankiramiki yansanda suyimiki Koran wulakanci ma nakira kawunki nakyauye tinkan nashigo gida yazoyasaki agaba yatafi dake dannasan inharnabarki kikatafi kekadai bazakije kyauyeba waniwajan zakije wlh yau kisani ko iyayenane sukadawo sukabani hakuri akanki wlh bazan hakuraba karma ki kuskura kikiramin kowa dasunan bani hakuri danhaka kije kihada inaki inaki kibarmin gidana yanazuwa tafiya zakuyi danyace baze kwanaba yau zakukoma hakakawai alokacin kikasamin hawan jini da tashin hankali kinsani adamuwa Kala kala kikasa NASA heedaya da uwarta agaba ni azatona maganarki gaskiyane kikasa nazargi yarinya tanabin maza Ashe bahakabane du makircinkine kindade kinayimin Abu yau natara nazubar kowa yakama gabansa nidake Nima nahuta Ina zargin yarinyar danahaiface Yar iska Ashe bahakabane matatace Yar isar tsohuwar banza inba tsohuwar banzaba Kuma Yar iskaba wacece take Hulda da yandaba keatinaninki Allah bazetoni asirinkiba Kuma baze sakamusuba to Allah ba azzalimin bawansabane Kuma baya bacci Kuma bayasan mezalinci
su Adam sunbude Baki zasuyi magana yace sutashi subashi waje ba maganarsu bace mamima zatayi magana yace baruwanta intayi seranta yabaci
umma tashakuka bakadanba tayi nadamar abinda tadade tana aikatawa taringa tsinewa Zaki hakatashiga tahada kayanta raibesoba baadadeba kawu nakyauye yazo malam yayimasa bayanin komai beyi mamakiba
yace nasani zataaikata finhakama batada mutunci kokadan bakaramin hakuri kayi da itaba yau karya takare zatakoma inda tafito tamanta damu gaba daya tadena zumunci damu dandai hannunka baya rubewa kayarne wlh shiyasa zankarbeta natafi da ita yanzu dabadan kaiba dakake lekomu akaiakai koyaranta bazamusaniba ammakai kayikokarin nunawa yaranta danginta itakuwa koakanta batamasan yaranta dakai kunazuwaba tana inane tafito mutafi ga akori kuracan nataho da ita afara zuba kayanta
Haka akakira almajiran unguwa sukazo sukaringa fita dakayan umma gabadaya tanatakuka koyaranta suntausaya Mata kareema tasha kuka bakadanba tanaji danagani umma tatafi ita da magaji tana kokekoke mehali bayafasawa kantatafi seda tazage Mami tas kafin tabar gidan Mami batakulataba indasabo tasaba
Acikin satin aka daura auran kareema da Zaki tatare dutana cikin tashin hankali ga umma batanan gashi Kuma taauri Wanda bataso
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama*πβ€π€©
*Me HADARIN SO*
*Me 'YAR KWALLIYA*
*Me NAFI GANE ARO*
WhatsApp numberπ±
07036891952
ππππππππππ
π π π π π π π π π π
ππ
*HEEDAYA* π
π
*(I KIRARI)*
ππππππππππ
π π π π π π π π π π
Written by *Husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad
*@Real Husba'ahfama*
91-92
Yau heedaya tatashi jikinta badadi kawai daurewa takeyi harta phadamusu abin karyawa Koda sukazo ci takitaci tin najip bekula da halin datake cikiba harseda yakula
yace my love waiyau kowa lfy kike tinjiya da zamu kwanta nake tambayarki sekicemin bakomai gashi yanzu munzo garyawa kinkici serufe Ido kikeyi
tace nacema bakomai
yaishuru Yana kallanta shima yakasa cin abincin
ranrashinshi tayi yaci tukunna
tace masa Bata da lfy tintana Kan kujera takoma kasa dasauri yakira Dr yafada Masa yacemasa suyimaza suzo asibiti nakudace dasauri yasata amota yahada komai daake bukata sukatafi sunazuwa akashiga da ita najip hankali yatashi yarasa inda zesakansa yakasa Zama addu'a bawanda bayayi heedaya anacan ana nikan kaura da tsakowa tawahala najip kasa jurewa yayi yakira hajiya naja'atu awaya tataho kafin takaraso Allah yasauki heedaya lfy tasamu santalelan danamiji damurna akafito akayiwa najip albishir zokuga murna wajan najip mukullin motar hannusa yamikawa me fadamasa haihuwar yacemata gatukwici takandun motar sunacikin motar yabata duka haba itama murna takamayi Harda rawa takoma ciki dagudu zeshiga shima aka cemasa yajira afito da ita anahaka Sega hajiya naja'atu dagudu najip yaje yarungumeta yanamurna yafadamata itama murna tafara lokaci guda yanuwa da abokan arziki sunji haihuwar anfito da heedaya da yaro fas inkunga heedaya bazakuce itace tahaihuba sabo da gayun datasha najip naganinta yaje yarungumeta dagata sama yayi Yana juyawa
hajiya naja'atuce takaimai duka tacekai lfykake sauketa Bata dakwari
akahau dariya
momi dasu Adam Suma segasu
hajiya naja'atu tace kema kinzo ganin megidan damani nabarmiki ragone tinda yafito bacci yaketayi malalacine
nansu yasmeen sukahau taremasa
Mami tace kagamasu da to munbarmuku bayanma hancinnashi amanne
yasmeen tace Su mami anga yaro kyaikyawa anrude yaranmu wlh mekyaune
sukahau dariya kwanan heedaya daya a asibiti akasallameta kaitsaye gidan hajiya naja'atu akashige da ita aikuwa najip besoba hajiya naja'atu Bata fadamasaba suna karasawa
yace mommy yahaka
taharareshi tace auu dakai kaima ita gidanka zaayi sabo da danyankai totananan setayi arbain Harda yankai
yace wlh Nima nanzandawo
tace kaikasani yarinyata Kuma bazakaringa ganintaba dakanka zakakoma naka gidan
yakalli heedaya yagatana dariya tanarufe Baki
yace mommy kingantako tanamin dariya
Tace tome kakeso taimaka
heedaya tanasamun kula wajan hajiya naja'atu ranar suna yaro yacisunan baban su najip wato ibirahim sunakiranshi da Kalil anyi shagalin sunasosai fadama Bata bakine Haka heedaya tacijaba da wanka tanasamun kula itada yaranta hartayi arbain Tasha gyara wajan hajiya da yasmeen tazaga dangi sosai hargidan kareema taje taji tausayin halin dataganta ciki taimata nasiha sosai tabata kudi masu yawa tace kojarine taja Haka heedaya takomo gida dajin tausayin Yar uwarta tadau alkawari azuciyarta naseta temaketa kareema
heedaya ankoma gidan najip zokuga rawarkai wajan najip heedaya tadawo Daman damadu atakure yake sabo da hajiya takasa tatsare
KAUYE
BAYAN SHE KARA DAYA
Umma ankode anrame kamar ba itaba inkunganta abin tausayi ga inuu baya tausaya Mata wahala kawai yakebata irin yarannanne masu kiriniya gabarnar tsiya gashi gidanyawa suke kananan yaran gidan haka yakebi yana dokesu Haka iyayan yaran suyita dukanshi anafada da umma tintana mayarwa har tahakura tadena sabo da anfi karfinta Haka wani lokacin zata goyashi gajikin tsufa inhar tanasan zaman lfy to sedai tagoyashi ga aikin gidan har da ita akaraba sunce bazasu dafamata girki tanaciba da ita akekomai duranda batayiba Bata da abinci gagori datakesha kusankullin yaki karewa ga bangaran malan yahana kowa yaje wajanta yace duwanda yaje beyafeba har yaranta yace akwai lokacin daya iba inyayi zebari aje dole Haka suka hakura kolabarinta basaji tinyaranta nadamuwa harsun hakura tanayin surfen kudi sekuma zuwa roran wake agona dahaka tatara Dan kudinta rannan tataho gidan kareema halin da tazo taga kareema hankalinta yatashi bakadanba
zuwatayi tasamu Zaki yamata dukan tsiya umma nazuwa suka rungume juna sukahau kuka
umma tace kareema Kinga yanda Allah yaidamuko dagani harke wlh yanzu nagane komai nayi nadamar rayuwa wlh nagane kuskurena nagane daukan hakkin mutanan danadauka arayuwa zanje nanemi yafiya wajansu suyi hakuri suyafemin naje Naga rayuwa alhakin heedaya da hafsa kadai ya ishemu gakuma naja'atu
Nan kareema tagayawa umma du irin zaman datakeyi dakuma temakwan da heedaya takeyimata Amma se Zaki yakwashe
tace umma bacinraine yaimin yawa yashigo dakayan maye nadauke masa nashanye besaniba shine yadawo beganiba yaimin wannan dukan
umma tace haryanzu bakidena shabako
tace wlh nadena heedaya tahanani Kuma sabo dabana samu Kuma bahalin naje nasamo nadena sha koyashigo dasu bana kallama rainane yabaci yaudinma nadauka nasha
Nan umma itama tadada Mata nasiha tacemata Dan Allah kartakuma Sha Haka sukarabu da juna suna kewar juna
kaitsaye umma gidan malam taje takwayi sa'a kowa nanan basuma ganetaba maganarma Tata tacanja sabo da hakoranta sundada zubewa su Adam dasuka ganeta daga baya kuka sukasa suka runguta sukahau bata hakurin rashin zuwansu
tace bakomai banji haushinkuba shima Wanda yahanaku zuwan shima banji haushinshiba
tabawa Mami hakuri Mami tacemata tahakura Kuma tayafemata malam kuwa anshafama kanyahakura harkome taroka wajan malam
yace aa baze maidataba
tace hafsa sabaki kozeyarda
itama beyardaba mamice takwantar Mata da hankali
tace zatashawo kansa yahakura Kuma zasuzo Suma taje gidan hajiya naja'atu tabata hakuri itama tayafemata su mansurne sukakaita hargida nansukaga inda takekwana harkuka se dasukayi aikuwa kwana sukayi agarin sukaje kasuwa suka siyomata katifa daduwani abinda
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 21