Mami Dan Allah abin da naji kicemin ba gaskiyabane abin da naji kicemin mafarkine
Mami tace kiyi hakuri heedaya kimikawa Allah lamarinki kiyiwa mahaifinki biyaiya saudakafa insha Allah zakiga riba arayuwarki kiyihakuri zabin Allah muka nema Kuma ya zabamana semu godemasa insha allahu wannan auran seya zamemiki alheri arayuwarki kinji heedaya ta yargidan Mami yarinyar kirki meyiwa iyayanta biyaiya
heedaya tace nagode Mami Amma abin da yake damuna Mami najip fa shine mijin da Abba ya auramin Mami kinfasan komai banasanshi wana irin Zama zamuyi dashi Kuma har i KIRARI yayi akaina Kuma yafaru banyarda da najip ba inazarginsa Mami kiyi wani Abu akai Dan Allah
takara fashewa da kuka Nan Mami tadada kwantar Mata da hankali
Mami tace heedaya tashi kije kiyi wanka kiji kwarin jikinki kafin malam yashigo garuwan zafican ankaimiki
Anahaka sukaji Sallamar ango da abokansa sunzo gaishesu harkasa suka sunkuya sukagaishe da su Mami suka ammasa cikin girmamawa najip bakihar kunne buri yacika yasamu masoyiyarsa inkaganshi yaukasan yanacikin farinciki setsokanarsa abokansa sukeyi
Dr addul yace eye kaga angwan heedaya alkawarin Allah yacika heedaya tazama ta najip abidai ahankali kar aragargazamusu yarinya dannaga kanka narawa Kuma kar akirani bananan
dukan wasa najip yakaimasa yace kaifa dan iskane kafiya tsokana
Dr addul yace aigaskiya nafada
najip yace kufa tsiyarku kenan gwauraye sa idanku yayi yawa
Dr yakalkale da dariya yace eye kaga masu Mata yaushe Kai auran mumadai Allah yakusa yayemana mushiga daga ciki
najip yace hm Dr zanso Naga kalar matar da zaka aura kaida kowace mace kagani seka gwaleta gayanmata nabinka kaki kulasu
Dr yaidariya yace zakaganta kuwa Kuma kasanta kawaidai bakasan itabace mu soyaiyarmu cikin nutsuwa mukeyinta bakowa bane yasani seahankali zamu baiyana kanmu karka damu
. najip yace hm Allah yakaimu lokacin zanyi kallo zatasha tsokana awajena
.Dr yasa dariya yace inzaka iyaba kaidai Allah yakaimu lokacin
najip yace ameeen
Najip yadaga Kai yakalli Dr yace abokina inacikin damuwa inatinanin irinzaman da zamuyi da heedaya kasan komai Kuma kasan irin rashin kaunar datake nunamin gakuma wasu kalar maganganu da take fadamin gashi kwatakwata banagane metake nufi tsanar da takemin yanzu tafi tada tinda tabata tadawo tsanar da takemin tafitada yanzufa kamar takasheni Haka takeji Kuma gashi bazato batsammani andaura Mana aure da ita Kuma batataba sanin nizaa bataba dawancen yamutu seyau taji mijin da akabata Kuma seda nacewa babanta yafada Mata yanemi raayinta intayarda shikenan Amma yace bakomai naje nafara shiryeshirye Kuma nasan inta raayin heedaya zaabi wlh bazatataba yardaba
Dr addul yace haba abokina kakwantar da hankalinka kaifa namijine Kuma jarimi komai zezo da sauki insha Allah
Nan Dr yadada kwantarmasa da hankali haryasamu nutsuwa
Malam bayan yagama sallamar baki yashigo cikin gida yacewa Mami takiramasa heedaya
Nan malam yadaga Kai yakalli heedaya yace heedaya
tace naam Abba
yace bawani abubane yasa nakiraki sedan nadada yimiki nasiha Akan auran da naimiki Allah yanufa najip ne mijinki Kuma kafin nabashike sedanai biccike akansa bansameshi da wani matsalaba yaran arzikine da Allah beyi auranku da Dan amininaba shine nayanke shawarar hadaku da najip sabo da nasan irinsan da yakemiki Kuma insha allahu wannan auran bazaki tabayin danasani akansaba
Nan shi da Mami sukayimata nasiha kanzaman aure sekuka heedaya taketayi Nan malam yace ajeashiryata dadandare zaakaita
Bangaran umma bakaramin tashin hankali tashigaba dabakinciki namijin da malam ya aurawa heedaya harkukan bakinciki sedatayi
Umma tace kareema kincuceni wlh kingama dani yanzu inaji inagani Yar makiyiyatace zata shiga wannan daular dayanzu kareema kema kinacikinta Amma gashi kinyiwa kanki Nima kinmin gashi yanzu bani da wani karfi agidannan bani da wata daraja a idan malam bare da naje nahada wani makircin baabin da nasani Akan harkar gidannan sedai Naga anayi Kuma bakowa bane yajaminba seke dabaki aikata wannan abin kunyarba dahaka bata faruba yanzu kinaji kinagani Yar uwarki cikin wannan daular gashi yanzu bama tare da naja'atu bare naje nazigata yanda heedaya zatasha wuya agidan yanzu bahali ko kofar gidan ban isa najeba abin duniya yamin yawa Ni hauwa'u inazansa kaina
kareema idadai takasa cewa komai ko itama tajizafin auran aranta Amma bayanda zatayi
kareema tacewa umma bayanda zamuyi sedai muzuba Ido hakuri kawai zamuyi Nima wlh naji bakincikin abin
umma tace munafuka yimin shuru koma menene bakekika jaba kareema kinbani kunya kinzubamin kasa a Ido kin kaso auranki gashinima kinkusa kashemin nawa nazama hoto acikin gidan mijina Kuma nice uwar gida Amma yanzu hafsa itatake da karfi agidannan itatake mulki yanda taga dama malam sewani rawarkai yake akanta munafiki shima malam din asheyana Santa da yake nunawa kamar bedamu da itaba sosai amma yanzu seabi da tace yakeyi niyanzu kokarinama nasamu nakarbi girkina dayahana naringayi nasamu nafara shiga dakin malam Amma abin yagagara kwatakwata bashi da lokacina gashi bawani kudi gareniba bere da nashiga malamai da bokaye
Anahaka sukaji anshigo da lefen heedaya anata Buda
Mami taleka dakin umma tace kufito kuga lefan heedaya kina uwar amarya guda Amma kina daki kinki fitowa haba Dan Allah tace kareema kema hardakeko kinki fitowa kina daki kifito kiga lefan kanwarki kisamata albarka
Jiki amace sukafito zuwa ganin lefe umma batasan lokacin data dafe zuciyartaba sabo da bakincikin lefen da tagani ankawowa heedaya akwatina goma shabiyune kowanne shake yake da Kayan alfarma aciki karamin nakarshe nankune da sarkane da awarwaro na daham kowa yayi mamakin irin dukiyar da akazubawa heedaya
wata kanwar Mami tarangada Buda tace Allah yayarda yarinya tayi goshi kaga heedaya farar aniya barar zuma farar alheri yarinya kinyi goshi sedai muce Allah ya Sanya alheri kowa yace ameeen
dantsokana kanwar Mami takalli umma tace babbar uwar amarya bakice komaiba kinyi shuru kema bambar Yar amarya kinki cewa koma
atare umma da kareema suka hada baki sukace Allah yasanya alheri Kaya sunyi wlh Allah yaba da zaman lfy
umma tajuya zatakoma daki
kanwar Mami Fatima tace inakuma zakije haba Dan Allah uwar amarya
umma tace bani da lafiyane yauda ciwan ciki natashi
Fatima tace Allah sarki aibamu saniba Allah yasawake
umma tai shigewarta daki kosauraransu batayiba tanashiga tadura hannu aka tafashe da kuka tace yau heedaya akakawowa wannan dukiyar inaji inagani Amma bayanda zanyi hafsa ce yarta tasamu wannan daular ko kareema lokacin da zata auri alhaji baa kawomata hakaba Daman najip nada irinwannan arzikin bansaniba Ni babansa nakewa kallan shine mekudin ashebahaka bane shima najip nadashi danasanima da kareema nahadasun ga alhajin ma munyi biyu babu kareema kincucemu kin datsemana hanyar arziki munaji managani makiyanmune zasuci
tadada fashewa da kuka anahaka kareema tashigo
umma batasan lokacin data wankawa kareema Mari afuskaba
umma tace inkika kuskura kikayimin wata magana anan wlh nalahira seyafiki jindadi
itadai kareema kunci taruke tana ta kuka
umma tace gashi wancan shegiyar figangiya harhabaici take yadamin zamu hadune dukanku karku damu indai inaraye yanda kareema tabar wannan arzikin heedaya dolekema sekinbarshi karyane nazuba Ido nabarki awannan gidan dolene nanemi hanyar da zamu shirya da malam
Dadandare yan daukar amarya sukazu tafiya da amarya bakaramin kuka heedaya taringayiba mamima Haka Dakar suka rabu da heedaya akasata amota
Kaitsaye gidan hajiya naja'atu aka shige da ita akabawa hajiya naja'atu amanar heedaya hajiya takarbesu hannu biyu har kyauta tayiwa yanrakiyar amarya heedaya kuwa sarkar daham hajiya naja'atu tabata du abin da ake umma nacikinsu tarufe faskarta dankar hajiya naja'atu taganeta umma tayi mamakin gyaran da akayiwa gidan hajiya naja'atu du ancanja komai na gidan Nan wani bakincikin yadada lullube umma harwani zanzabine yakamata sabo da bacinran da take ciki da danasani
Daga gidan hajiya naja'atu akashege da heedaya gidan da najip yagina gidane bana wasaba Dan kareran gidane nagani nafada fadar kyansama Bata bakine
Nan umma tadada shiga tashin hankali kafin tagama farfadowa daga bakin cikin da take ciki taji anata sakin Buda ana shewa Ashe yasmeen ce ta dankawa heedaya makullalin mota ahannunta tace daddy yace abata shine tukwicinsa Yana Mata sannu dazuwa cikin iyalinsa
Kowa yayi mamakin wannan hidima da dangin augo sukayiwa heedaya umma suman zaune tayi har akagama komai zaataho batasaniba Nan wata Yar uwar malam tagargizata tace hauwa'u lafiya zaatafifa kitaso dakar tatashi suka tafi serawar sanyi takeyi
ana komawa gida tashige dakin kotakan su Mami batabiba sekuka take tayi kareema du tarude tarasa meyake damun umma tambayar duniya tamata taki magana haka ta hakura takwanta
zuciyayar umma burikane kalakala aciki da zanzabi mezafi umma da kwanta
Heedaya kowa yawatse sekuka take gidan itakadai anahaka abokan ango suka rako ango
Nan sukahau tsokanar amarya itadai heedaya kanta arufe yake taki bude fuskarta dahaka sukamusu nasiha da addu'ar samun zaman lafiya najip yarakosu suka tafi
Dr addul ne macemasa adaiji nasihar da mukaimaka abi yarinyar mutane ahankali dannasan akan gwuwa kake
najip yace bazan kulakaba kayi kaikadai
sauran abokan sukasa dariya Nan sukayi sallama yarufe falo yatahu dakin heedaya zuciyarshi nadukan UKU
New writer's
Hakan Take
*Husba'ahfama*πβ€π€©
*'YAR kwalliya*β€π
ππππππππππ
π π π π π π π π π π
ππ
*HEEDAYA* π
π
*(I KIRARI)*
ππππππππππ
π π π π π π π π π π
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@Real Husba'ahfama*
Godiyaπ€π ta musamman
*Hassana lawan* β€π
Inajin dadin kwarin gwiwar da kike bani
Allah yakara kauna π
Wannan shafin nakine gabab dayaππ
*Nasadaukar Miki* dashi
Nagode π€ Allah yabar zumunci
*Ameeen* π€²π€²
66-67
Kaitsaye najip dakin da heedaya take yaje yasa hannu zebude ya shiga yaji dakin a kulle yaita buga kofar Yana Kiran sunanta taki budewa
yace heedaya bawani Abu zanmikuba Dan Allah kibude magana zamidake
ko tankamasa batayiba Haka yahakura yakoma nasa dakin
da safe wajan shadaya heedaya tabude dakin tafito shima yunwar da taji tana da muntane yasata fitowa tana xuwa falo tahau dube dube batasan lokacin datace Masha Allah sabo da tsaruwar da falan yayi tana cikin dube duban taga wata kofa tabi wajan tana shiga taga kicinne awajan nantahau dube dube taga akwai komai na abinci awajan
tace wahalanle komai yasiya kanemo medafama kaci Amma badai niba wlh sedai wata Dan bazama nazoyi gidankaba
Nan tahada abin da zata karya tafito falo tazauna tanaci anahaka najip yafito Yana baza kanshi tanajin kanshi tinkan yakaraso tasan shine ko dagakai bataiba takalleshi tacigaba da karyawarta da sallam dauke abakinshi yakaraso wajanta yazauna azuciyarta taamsa sallamar da yayi
Najip yace my love heedaya kintashi lfy yasaban waje shine jiya Kika kullemin dakiko cikin shagwaba yake fadamata
taikamar batajishiba
yace ina nawa abincin kotare zamuci
Taikamar Bata jishiba
kicin yaje yadauko cokali yadawo yazauna yasa hannu zeci kafin yakai bakinshi tadoke cokalin yafadi kasa sauran na pletdin tazuba Masa ajikinshi tamike tsaye tadaka samasa tsawa tanunashi da danyatsa
tace kafita idona najip karka ganni araha agidanka kayizatan komai zezomaka da sauki to kabude kunnanka kaji wlh bahaka bane ka auro tashin hankali da hannunka kaida kwanciya hankali harse ka sakeni in bahakaba wlh bazan barka kaji dadin rayuwarkaba Kai Wai wana irin mayene amayunma Kai da banne wlh mara zuciya Wanda zuciyarshi Kare yacinye Kai inkana da hankali harkazo indanake da sunan aure Amma dan baka da kunya kazo kayiwa mahaifina dadin baki ka aureni dannasan mahaifina abinduniya berufe Masa idoba daharzaka rudeshi dakudi sedai inko gungiyarkuce taimaka aiki akansa kuka aikaceshi yayarda yabaka Ni
shidai najip yayi mutuwar zaune sauraran mugayan kalaman heedaya yakeyi
tacigaba da cewa sabo da kungiyarku baabin da bazata aikataba tunda kun iya kashe mutane tinda Allah yakwatoni wancan karan shine yanzu sukabaka shawarar ka auroni to wlh dagakai harsu nafi karfinka bazaku iya da niba insha Allahu narigaku nace Allah Kuma Yana tare Dani shize kareni daga sharrinku kuma wlh ina gayamaka kagaugauta sakina tinkan najamaka tashin hankali inkaiwasa zanzama ajalinka zandau hukunci ahannuna tinda yansanda haryanzu sunkasa gama biccike akanku
Najip yace innalillahi wa'inna'ilaihirrajiun heedaya kinfara maganar taki da bana ganewa Ni wlh daga kinfara irinwannan maganganun naki kikedada sani cikin duhu bana gane mekike nufi Dan Allah kiganar da Ni da irin maganganunnan Wai mekike nufine yace Anya heedaya dakika Bata kwakwalwarki batasamu matsalaba
Heedaya dada da dakamasa tsawa
tace koma meye yasameni waye yaja bakaibane kokana zatan ban sanibane kazo kanamin wani borin kunya anan kana nuna bakasan komaiba waini zakamayar yarinya dabaka aikatamin wannan abinba wlh harzuciyata zanwa mahaifina biyaiya nazauna dakai shima mahaifina besan halin kabane kaboye mugun halinka kabaiyana masu kyau mahaifina yabanka yake Yana ganin kirkinka nankuwa besan harshi kacutaba kasashi cikin tashin hankali besaniba yadauki yarsa yabaka insha allahu akwai ranar da gaskiya zatai halinta ranar zakaji kunya zakai nadama Dan ranar har a gidan TV senasa annunaka ranar sabo da murna har ruwa Sena zuba akasa nasha
Najip yace Dan Allah ya Isa ya isahaka nagaji nagaji kitsaya mufahimci juna heedaya Ina sanki Ina kaunarki kekadaice macan da zuciyata take kauna kiji tausayina kisauraramin kisoni kamar yanda nake sanki Dan Allah wannan fadan da muke ya Isa Haka tinkan muyi aure muke abudaya yanzu yadace mudena kinji mufarantawa iyayenmu Rai suma suji dadi kinjin masoyiyata jeki dafamin wani abin karyawar sekizo muci tare nasan kema baki koshiba zanzo natayaki dafawa muyi sauri mugaba kafin yunwa tawahalarmin da ke yace yanzu kiga yanda Kika batamin jiki my baby
Heedaya tace kadanma kagani abinci Kuma kodawasa karkakuma zuwa katambayeni Danni ba Yar aikinkabace bazantaba dafamaka abicci ba kuma duranar da kakuma ganina inacin abinci kazo kasa hannu zakasha mamaki senajima ciwo dannan gaba da wuka zannazama akusa Dani sabo dakai kanasa hannu nai maganinka
tashige daki tabarshi anan jiki bakwari yatashi yakoma daki Dan gyara jikinshi
Zama yayi bakin gado yayi tagumi yace ya Allah kasausautawa heedaya ranta tasoni kamar yanda nake santa kaganar da ita gaskiya ya Allah kainaroka zabin alheri Akan auranmu da heedaya ya Allah kasamata Sona azuciyarta kamar yanda nake santa wannan maganar da takeyi shine bana ganewa kullin senayi tinani Amma nakasa gane metake nufi
Najip tshiyayi zefita yanemi abin da zekarya yaji kansa namai ciwo gajuwa da take ibanshi jiyayi Yana niyar faduwa dole yakoma kangado yakwanta zanzabi mezafi yarufe Masa jikinshi serawar sanyi yakeyi
Heedaya nashiga daki tafada kangado tafashe da kuka sedatai kuka me
isarta tace Abba bakasan waye najip ba dabaka auramin Shiba najin shine Wanda yai IKIRARIn saceni Kuma yasacenin tinda Naga sheda duda banga fuskarshiba Amma Naga agogun hannunnishi Wanda yataba zuwa guna yanunamin haryanzu Ina zirgin najip seranar da gaskiya tai halinta Abba zakagane Waka aurawa yarka yaboye mugun halinshi yanuna mekyau kuka bashini
Lubabatu ce takawowa su kareema ziyara taji mutuwar auran kareema bayan sun gaisa da umma
lubabatu tace umma Ashe abin da yafaru kenan
azabure umma tace mekikaji
tace mutuwar auran kawata Mana sekuma auran heedaya
umma taja dogun numfashi azuciyarta take Allah nagode maka tinda bataji dayanba
umma tace wlh abin da yafaru kenan
lubabatu tace kareema Wai meyafaru ya sakeki
kareema zatai magana
umma taisauri tace makiyane suka shiga zakaninsu sekuma yan bakinciki irinsu hafsa da hajiya naja'atu suka banko nasu surrin harya saketa
lubabatu tace ikwan Allah gashi Kuma Harda ciki kocikin jikinki bedubaba yasakeki Dan rashin imani yanzu cikin watansa nawa
dasauri umma tace yaakai kikagane tana da ciki
lubabatu tasa dariya tace haba ai inmace nadaciki ina ganewa
umma taishuru tarasa mezatace azuciyarta tace shikenan asirinmu yakusa tonuwa a idan duniya dolene nadau matakin zubar da cikinnan kome malam zemin sedai yaimin bazan iya wannan abin kunyarba
jiki amace kareema tace wata hudu yashiga na biyar
Lubabatu tace to Allah yaraba lfy
Anahaka wayar kareema tayi Kara tadauka tace shaheeda bayan sun gaisa tacewa kareema gatanan zuwa kareema tace Kai Amma naji Dadi wlh kamar kinsan kwana biyu balabari Dan Allah kitahomin dasu kema kingane Nan heedaya tace Mata to Nan sukayi sallama taajje wayar kareema semurna take
lubabatu tace wana irin murna kike Haka wacece wannan da kike murna da zuwanta
kareema tace wata kawata ce bakiga yanda take sonaba
umma tace kyafadi Haka Mana nadokeki yanzunnan
kareema taja bakinta taishuru anahaka sukaji Sallamar shaheeda dasauri kareema tafita tatareta suka rungume juna suna murna shuka shiga dakin umma Nan suka gaigaisa lubabatu tinda takalli shaheeda taji Bata kwantamata araiba
lubabatu tatashi tace nizantafi sewani lokacin
umma tace damaganar da zamuyi zannemeki in ankwana biyu
lubabatu tace to umma Allah yakaimu lokacin
Nan sukai sallama dajuna sabo da murnar ganin shaheeda kareema korakiya batayiwa lubabatu ba
Umma Nan tadada musu fada kan abin kunyar da sukayi
shaheeda tace kugode Allah umma ke auranki bemutuba nitawa mommy daddy na yasaketa
Shaheeda Nan tabasu labarin abin da yafaru dasu
umma tace hm Nima kusan hakanne ai gani inakwasar bakinciki bayan da zanyi
umma tabata labarin abin da malam yaimusa bayan sun gama tantaunawa umma tashi tabasu waje
Umma natashi sukahau Hira kasa kasa Dan kar ajisu
kareema tace shaheeda yisauri kiciromin naboye nashiga damuwa da nadade banshaba yanzu abin da yake damuna yanda zanfara fita nasamu muna haduwa acan gashi usi ya dameni da Kira yacemin yayi kewata Nima Kuma du atakure nake gashi abba yahanani fita yawo kibani shawarar yanda zanyi
shaheeda tace zanfada miki yanda zakinayi kawo kunnanki
tana gama fadamata suka tafa Kai kawata nagode kinkawo shawara mekyau
shaheeda tace yanzu abbanki nanan kobaya Nan
tace bayanan seyamma zedawo
Shaheeda tace yaiwa tashi mutafi azaman rakani zakiyi kifadawa umma daganan semu shige kawai Amma kinsan in cikinmu yatsufa zamudena harka semun haihu kofitama denawa zamuyi
kareema tace eh nasani kawata
shaheeda tace umma zantafi sewani lokacin
kareema tace zanmata rakiya
umma tace to karki Dade sabo da malam
tace nasani umma bazan dadeba
tace zonan kareema rakiyarce Kika canja Kaya kikai wannan kwalliyar haka Nan ta hau kame kame bakomai kawai zafi nakeji nacanja kaya semun dawo umma dasauri suka fice
Tinda kareema tafita har yamma Bata dawoba du hankalin umma yatashi tarasa inda zatasa kanta
Batagama rudewaba sega malam yayi sallama
umma tace nashiga uku Ni hauwa'u kareema kindada jamin wata matsalar gashi malam yadawo haryanzu baki shigoba yanzu inyaga dawowarki mezamuce Masa kareema sokike zuciyata ta muga akanki
Har akayi sallar Isha i ba kareema babu alamarta umma sezarya take zuwa kofar gida Mami dunakula da ita su Adam har tambayarta sukayi meyake faruwa tacemusu bakoma Shan iska take
har karfe goma nadare ba kareema seji sukayi umma takurma ihu dagudu kowa yafito zuwa wajanta har da malam suna tambayarta meyake faruwa Nan tafada musu abin da yake faruwa Sunshiga mamaki da tashin hankali malam kuwa koajikinshi
Dagakai malam yayi yakwalleta cikin tsana yace kema kinsan inda taje meye nawani tada hankali shin banhanata fitaba
Umma takasa cewa komai se kuka take Nan mazan gidan suka bazama nemanta haka suka hakura suka dawo basu gantaba
Har wajan karfe goma shabiyu da rabi nadare suna tsaye akofar gida sunyi curko ccurko
Malam ne yace tinda takai wannan lokacin Bata dawoba kushiga gida segobe Kuma
Sunjuya zasu shiga sukaga wata mota tafigo da gudu tayi fakin akofar gidansu
Fasa shiga sukayi suka tsaya kallan ikwan Allah segani sukayi wasu maza sunfito daga cikin motar dushigarsu bata arziki layi sukaga sunayi Basu gama mamakin abin da suka ganiba can sukaga ana janyo mutun daga cikin motar Nan suka dada mutuwar tsaye kareema sukaga anjanyo daga mota wani daga kikin mazan yasabata akafada suka doso kofar gidan sudukansu kafin su malam suyi magana segani sukayi sun danna kansu cikin gidan cikin zafin nama mazan gidan suka rufamusu baya zuwa cikin gidan umma akofar gida tazuba tazauna dirshan sabo da tashin hankalin da tagani
New writer's
Hakan take
*Husba'ahfama*πβ€π€© ce
*'yar kwalliya* β€π
WhatsApp numberπ±
07036891952
ππππππππππ
π π π π π π π π π π
ππ
*HEEDAYA* π
π
*(I KIRARI)*
ππππππππππ
π π π π π π π π π π
Written by *husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real Husba'ahfama*
Follow me on Wattpad *@Real Husba'ahfama*
68-69
Mazan gidan nashiga suka tarar da sunkwantar da kareema a tabarmar da take tsakar gidan ashinfide sukajuya zasufita suna layi ko magana basuyiwa kowaba acikin su malam
sabo da tsabar zuciya data Kama su Adam basusan lokacin da suka rufesu da dukaba dako Ina dukansu suke sabo da abuke suke sunkasa karbar kansu dakar malam da Mami suka hanasu dukansu
malam yace kukyalesu balefinsu bane lefin kareema ne da mahaifiyarta
Haka suka fice sunajan jiki suna cewa su Adam zamu hadune Kuma yarinyarku yanzu muka fara harka da ita bayanda zakuyi Adam yadada yunkurawa zebisu su Mami suka rikeshi Haka suka shige umma azaune komutsi batayi akofar gida Haka suka shiga mota sukaja da gudu sukabar kofar gidan
mansur yatashi yawankawa kareema Mari ina koajikinta batamasan yanayiba
Mami ce tace akyaleta setadawo hankalinta zuwa gobe
Nayi Batan suna ashafina nabaya wajan sunan bamban Dan hajiya naja'atu ba
mansur sunansaba basiru sunanshi shikuma dangidan umma bamban shine mesuna mansur
Du bidirinnan daakeyi su Mami basusan umma nawajeba suatinaninsu tana daki
Nan malam yace sekukira uwarta tadauke yarta
Adam yaleka dakin umma yaga bakowa yace aibata dakin abba
sukace to tana Ina
.Ali ne yace kamar batashigoba munbarta awaje Bari naje. Nadubo daganan Sena kulle gidan
yanafita waje yaga umma azaune komutsi batayi yakira sunanta yaji tayi shiru yatabata yaga Bata motsi dagudu yakoma cikin gida
yace umma nawaje Bata motsi
atare sukabi bayanshi sunazuwa suka girgizata Amma Ina umma batasan meakeyiba
Mami ce tace kuje ku ebo ruwa kukawo
ana kawo Mata tayaiyafamata taja dogun numfashi tazabura
tanacewa suna Ina cankuma seta fashe da kuka kareema kincuceni wannan ba halinkibane wlh asiri akaimiki aka rabaki da mijinki kikashige wannan halin
bawanda yacemata komai Haka aka kamata aka shiga da ita cikin gida duwannan abin da akeyi malam beje wajan umma akofar gida ba tana zuwa tayi wajan kareema tarufeta da dukaka
umma tace kareema kincuceni kingama dani
kanta karasa
malam yace karki kuskura kikara dukanta kodawasa ranki seya baci badan komaiba kekika sata awannan halin wai kinmantane Kona tinamiki alkaba in da Kika ringa fada akan heedaya tinbana yarda harse da kikasa nasoma yarda daga baya danayi bincike bahaka bane shirri kawai kike mata Daman irin wannan ranar nake jiyemiki gashi Kuma tazo shi Allah ba alzalimin bawansa bane Kuma fadace ta Allah duwanda yayiwa danwani mugun alkaba I insha Allah seyakoma kan danka sekayi kuka da idanka to gashinan kinfara inba kituba zuwaga Allah ba kinkuma nemi gafar su hafsaba to kadanma Kika fara gani
Nan umma tadada bashewa da kuka jiki amace tatashi zata tafi daki tatafi yu zata Fadi dasauri mansur yatarota
yace umma yi ahankali zanzabinema jikinki
Haka yakamata yashiga da ita daki
malam yace kowa yaje yakwanta segobe in Allah yakaimu da maganar da zamuyi daku
kowa yace to Nan suka wuce zasu tafi su kwanta
Mami tace yazaku tafi kubarta atsakar gida
atare su Adam suka hada baki sukace bame kaita daki takwana awajan bayanda Mami batayi dasuba sukaki kaita daki Haka suka shige sukeje suka kwanta
dakyar Mami takamata takaita daki umma kokulasu batayiba tana takanta
WASHEGARI
Dasafe bayan kowa ya karya agidan su kareema malam yatarasu adakinsa Harda kareema da umma
Malam yace nakirakune Akan kareema inaso kuzama sheda malam yace kareema
tace naam abba
yace inaso kifada Mana Wanda yaimiki ciki
kafin kareema tayi magana umma tayi sauri
tace alhaji ne aikowa yasani tinda daga gidansa tafito da cikin
kareema tace umma wlh ba alhaji bane
umma bashiri tatashi tarufeta da duka
malam yadaka Mata tsawa yace baki da hankaline dake nake maga karki Kara samana baki amaganar da mukeyi da kareema sheda kawai nakiraki Kuma bakiga cikin dake jikintaba inwani Abu yasametafa
umma takoma tazauna tana nishi
malam yace kareema kemuke jira kifada Mana
kareema tace us ne Abba
malam yace to alhamdulillah tinda kinsan Wanda yaimiki kigayamasa yazo Ina nemanshi Kuma inkinhaihu zaabashi danshi
tace to Abba
malam yace kareema bance karnaganki kinfita ko inaba
tace Abba kafada umma ce tace nafita
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 21