"Alhaji barka da zuwa ya hanya
"Alhamdulillah y Gida da yara
"Lpy kalau
"Nagansu Sun girma sosai kinsan badan kowa yasan ninaje Istanbul ba da nace kece kikaje kinyi jiki kinyi kyau kamar kina can daga ke harsu
"Alhaji banda tsokana
"Ba batun tsokana gaskiya nafada yauwa basiru ya shirye shiryen biki kasan fa abin da ya dawo dani kenan
basiru ya sunkuyar dakai
hajiya tace ananan anayi dake ma abin ya zama 2 yanzu idan ka huta Zanfada maka komai
"to Masha Allah kardai Najib ma auren zeyi
"shine mana Alhaji
"Allah ya temaka
sama-sama Yasmeen tajiyo su suna wasa da dariya ta fito rai a hade taje gaban su ta rungume hannunta ta juya musu baya
"daddy ka tabo auta auta rai ya baci daddy be nemetaba daya shigo Amjad ya fada yana dariya
"Amjad ka bari bana sofa kaida Zaka rarrasarmin ita Yasmeen zokiji
Taki juyowa
"A min afuwa mana shalele yanzu nakeso nace ina kike se gaki kinfito tin a mota naketa yimusu maganarki kinga harsu amjad na dariya kibashi kunya kinji kice kin hakura kijuyo naga fuskarki auta
ta juyo tana dariya "daddy sannu da zuwa ina wuni ya hanya
"Lpy kalau y kike ya shirye-sharyen bikin basiru da Najib da fatan dai harda naki za'a hada
"daddy tace ta tabe fuska tana niyar kuka
ya isa baki kaiba ko shalele
"haka zakice dama zaki fada da kanki kose na fadawa daddy cewar Amjad
"mekake nufi babu komai daddy kaje kayi wanka Bari na shirya abinci a dining table
tafada tana kallon mamanta daki suka dinga tafiya yarage daga Najib sai hajiya naja'atu a falo
"Najib ina fatan dai baka manta da zuwa gidan su shaheeda ba ko
"eh ina sane
Ta daga mishi kai ta tashi tabar falon
Kareema ta goge hawayan fuskar ta ta tashi ta iba da gudu ta nausa cikin dajin wani irin Kuka taji da bata san kona wana dabba bane da kanta ta dawo inda yake
"hahhhh kingama guduwan ina sane na kawo kinan
yajuyo tareda cire abin da yasa ya rufe fuskarshi dashi
Kareema ta Saki baki ta zare ido
"kaine ta fada tana nuna shi
"Zaki baby mekike shirin yi bayan kinsan kina dani waye shi wannan mutumin da na Kaiki gurin shi ina
son sani ina fata dai shine wanda ze aureki ina farin ciki da haka kice shine zeji abin kunyar da zaki aikata
"bazakaji komai a bakinaba duk wannan barazanar da kake min da wani *I KIRARIn* ka baze bani tsoroba baka isa kamin komai ba nafi karfin ka
"Haka kikace
" eh da manyan baki makuwa
yataho inda take yaja mayafin jikin ta Kareema taja da baya ya fusgota yana kokarin rabata da kayan jikin ta saiga Kareema a
kasa ta kara tsorata kirjin Kareema nata dukan uku-uku tin Kareema na ihu harta dena ta saddakar
"hahhhh baby kinyarda nayi Kenan bazan yiba nadai gwada miki cewa aduk sanda naso zan anshi hakkina
bana saba alkawari
kamar yanda nace
miki se ranar aurenki bazan taba canza waba tashi ki gyara mu tafi amma
kisani duk inda kike ina wajan bazan barkiba sai randa na cika alkawarina
Kareema jiki na rawa ta gara rigarta tayafa mayafi "ni na bika Allah ya sauwake bunsuru dakai dabba wanda besan darajar Mace ba Allah ya shiga tsaka nina da kai
"baby ki dena wahalar da Kanki bakece ta farko da kika taba gaya min haka ba kiyi shiru karki bata bakinki mu tafi
Ya shiga mota babu yanda ta iya sedai ta bishi haka ta shiga gaba daya a tsorace take dashi sai zukar tabarsa yakeyi yana tuki harya maidata gida
Dasaurin ta takai hannu zata bude kofa yaki buduwa
"saurin me kikeyi baby bari nai miki tini zankarbi hakkina ranar aurenki kirubuta ki ajiye
l KIRARIn kA ya koma kanka ta fada a zuciyar ta
Yabude mata ta fita kowaige bata yiba ta shiga gida
Yaja mota ya tafi
Umma na ganin shigo warta ta Saki guda lubabatu ta tayata Gaba dayansu suka shiga daki
"Kareema hakonmu ya cimma ruwa cewar lubabatu
Kai ta daga musu dan har lokacin a tsorace take
"Kareema kisaki jiki ki gaya mana abinda ya faru lubabatu kawo mata ruwa Tasha
lubabatu ta dauko tabata Kareema tasha sai lokacin ta dawo dai-dai
Tasanar dasu yanda sukayi da Alhaji da kudin daya bata
umma takarayin wani gudar
"Kareema abin da ban ganeba shine waye ya kiraki a waya a matsayin kawarki daga madina cewar lubabatu
"ina ta tinanin wanda zankira saiga kiran company layin da nake amfani dashi Sun kirani suna
nasu jawabin ina nawa dana gama fadar abinda zan fada sena kashe wayar yauwa yace zezo ya gaida keda abba
Umma tace abu ya kankama
Kirane ya shigo wayar Kareema taki daga wa azatonta zakine saida akadameta da kira sanna ta daga a tsorace taki cewa komai
"Kareema nine Alhaji Ibrahim gadara y kika isa gida
"lpy klau kaifa Alhamdulillah kira nayi na fada miki bazan samu zuwa yauba se gobe insha Allah
"To ba komai Allah yasa haka shiyafi alkhairi Ameen
"Ameen Kareema zan kiraki anjima indan kin huta
To tace ta kashe waya
umma ta ciri dubu goma taba lubabatu taita godiya
"umma wannan duk ni kadai ai dole mukara zakewa indai zan dinga kama farare bugun Abuja ai dole nayi ruwa nayi tsaki ni zan tafi idan na tashi dawowa zandawo dawasu gaggagaggan aiki
Umma tace yauwa lubabatu
bangaren Najib Kuwa bayan sungama cin abinci hajiya naja'atu ta dameshi akan yaje gidan su shaheeda badan yaso ba haka
ya shirya ya tafi tinda shaheeda ta samu lbr zuwan shi take ta gyare-gyare tana gaban madubi haryazo bata gama
kwalliya ba yana zaune a falon baki shaheeda tashigo tana mishi murmushi
"dama dena dariyar nan kikayi kokyau baya miki muni kikeyi yafada a zuciyar shi
Barka da zuwa ina wuni
Kallon banza ya mata
muna fuka ya fada a zuciyar shi
da taga be amsa ba setayi shiru
harararta yake tayi "mtsww nizan tafi tinda bakida abin da zaki fada mommy ce ta turoni tinda kin ganni shikenan
Zatayi magana ya daga mata hannu "natafi
Tana kallo ya fita tana binshi a baya mahaifiyarta yaje y gaisar sannan ya tafi makarantar su heedaya ya wuce
kai tsaye yasamu antaso su ya faka motar shi yana jiran fitowar ta yana ganin ta ya fito ya hade rai
"heedaya zoki wuce
"Inje ina kuma
"mota zaki shiga mu tafi idan kinki takarfi zan daukeki intafi dake
fuskar shi ba alamar dariya hankalin mutane ya fara dawowa kansu heedaya ta shiga motar ba musu yaja motar suka tafi heedaya na kallon inda ze kaisu faka motar yayi
"kifito
"me zanyi a nan
"asibiti ne Kizo muje idan kina min muso raina ya baci akwai matsala
heedaya ta fito suka shiga asibitin tare yana gaba tana binshi a baya
New writer's
Hakan Take
*husba'ahfama* 😍❤🤩
*'YAR kwalliya*❤💋
WhatsApp number 📱 07036891952
👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠👠👠👠
💄💅 *HEEDAYA* 💅💄
*(I KIRARI)*
👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠👠👠👠
Written by *husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
Facebook *Real husba'ahfama*
17-18
Dakin ganin likita ya shiga tabi bayan shi ya nuna mata kujera bece Komai ba heedaya ta zauna
Najib Yayi gyaran murya "heedaya bana kawo kinan danki tausayin bane nakawo kine dankiji halin da nake ciki saboda ke
Najib y mai da kallon shi ga likita "Dr Abdul HEEDAYA ce fada mata meyake damuna meya jamin wannan ramar da nakeyi
Dr Abdul ne a zaune da farin glass a idon shi ya gyara zaman glass din "heedaya maganar gaskiya zan fada miki amma da farko ina zuwa nasan ke nurs ce kafin nace komai duba wannan maganin da yake shane kuma kinsan wayanda suke sha na hawan jini ne
Ya gaya mata abin da yake damun Najib da suman da yayi
"dakam abin bekai haka ba suman da yayine yasa muka gano abin yafi da yanzu yana kan magani gasunan kina gani kuma munbashi shawara dai-dai gwar-gwado wannan kenan
"Kinji ko kullum ina gaya miki sanki ya zame min goba duk abin da yafada magani shawara bazasuyi Komai ba heedaya kece magani kezaki warkar dani
heedaya ta tashi tsaye ta cewa Dr Abdul se amjima ka tashi lpy
Ya daga mata kai
heedaya tayi waje Najib yabi bayan ta bude mota tayi zata shiga ya maida kofar ya rufe
"me kike nufi heedaya bakida tausayi sanki na niyar hallakani amma ko a Kanki
"to meya shafeni da rayuwar ka Najib inada wata halaka da kaine dazan damu da abin da yake damun ka a inda naji anan na barshi dana san abin da zaka kawoni kasa a fada min Kenan daban biyo kaba duk hada Randa zakayi kazo Ka maidani gida
kalamanta suka taba masa rai juwayaji tana ibansa yabude mota ya zauna tareda dafe kai nayan mintuna
"heedaya karkimin haka mana ki dubeni kidubi halinda zan shiga ki tausaya min
"Kadai tausayawa kanka ni meye nawa a ciki na fada maka gaskiya amma kaki ji
tsaye y mike duk da juwar dake iban shi "heedaya indai ina raye bazaki auri waniba Indai ba niba dan saina *Saceki* munje wata duniyar munyi aure ina so kisan da wannan
"hmm Najib Allah ya baka sa a kasaceni idan hakane zesa na soka *I KIRARI* da kakeyi hujja ne a kanka kasan da wannan
"kome ze zama sedai y zama heedaya indai akan kine
yashiga mota itama ta shiga gida ya maidata a kan idon malam nazifi da umma y ajiyeta a mota Najib yaje ya gaida su sannan ya shiga mota ya tafi gida
heedaya na shiga mami ta riketa tana tambayan ta daga ina take
"ina kika shiga heedaya yau Kin dade sosai duk kin daga mana hankali
Umma dake shigowa cikin gida caraf taji maganar a kunnenta " tadai daga miki hankali mu inaruwan mu yarinya ta zabi yawon bariki fiye da komai jita fa ko ajinkin ta nawa yabaki ina kudin me kikeyi dashin yanzu sakaiyar da zaki mana kenan heedaya meye ba a miki a gidan nan idan aure kikeso ki fito da miji meye a ciki
"hauwa'u dan Allah kirufemin baki ban kasa dake ba wannan tsaka nina da 'yata ne ba abin da ya shafeki kida Kanki kikace nina damu keko a jikinki kuma inaso ki sani irin wannan shedar da kikeyi a kan heedaya be dace ba fadi alkhairi ko kayi shiru ina jeye miki randa zakiga yawon bariki a dakinki a kwaryar shanki
"laaa yanzu me kike nufi nizanyi yawan bariki da wannan tsofan nawa bakinki yasari danyan kashi I KIRARIn ki ya koma kanki
"Daga baya kenan hauwa'u heedaya daga ina kike a ina kika tsaya
"mami zan miki bayani nasan zaki fahimce ni da aka tashemu a makaranta nafito sena
Wuf umma ta katseta "seta hadu da dadironta yace tazo ta rakashi dasuka tafi sheke aya basu ankaraba sai lokaci ya kure kamar haka ina nufin lokacin datadawo yanzu kenan shine yazo ya ajiyeta amota a idan malam ya ajiyeta ya gani da idanshi Hafsat meyasa bakya son gaskiya ne ga abu kiri-kiri a fili kina gani heedaya karfe nawa yanzu idan baki saniba bari na fada miki karfe 6 yanzu malam yaje masallaci idan yadawo zamuji mezece akai
tawuce ta shiga dakinta Kareema na jinsu taki fitowa abin duniya ne ya isheta idan ta tino da abin da ya faru tsaka ninta da zaki abin na tsoratata
mami rai a bace taja hannun heedaya ta watsata daki tarufe kofa
"heedaya kinajin dadin kalaman da ake fadamin a kanki ko heedaya kinajin dadin hakan ina kika tsaya heedaya ina kikaje ina matukar jin zafin abin. da Hauwa'u take dangan taki dashi heedaya Indai abin da hauwa'u da Kareema suke fada yazama gaskiyane bazan taba yafe mikiba Bani bake har a bada kinji na fada miki
mami ta zauna akan kujera tana haki heedaya ta sunkuya a gabanta tana kuka "mami dan Allah kiyi hakuri wlh ba halina bane bazan taba aikata hakaba Umma zata iya fadan komai a kaina nina sani tana bakin ciki da karatun da nakeyi daga ita har Kareema narasa me aka fada miki mami kinsan halina namiki alkawari bazan taba canzawaba ina kan tarbiyar da kikabani
Nan ta sanar da ita abin da yasa ta dade tana fada tana kuka harta gama fada mata
Mami tayi shiru tana nazarin "heedaya waye shi najib din meyakeso dake idan aurenki zeyi da gaske ya turo iyayansa ayi magana mana
"bana sanshi mami Najib mutumne na gari halayansa masu kyaune saidai yanada nakaso 1 dane ga Alhaji Ibrahim gadara mahaifiyar sa kuma hajiya naja'atu kawar umma
Zunbir mami ta mike tana kaikawo a falo "heedaya karma ki fara banshirya ba naja'atu ba mutuniyar arziki bace ayanzu dai bazan iya hada jini da itaba saidai idan nangaba inta canza hali batada mutunci ko Kadan kimanta dashi heedaya
"ban taba sanshiba mami ko kadan
"yauwa Allah ya miki albarka karya kara cewa kizo ya Kaiki wani guri ki bishi kinji
Sukayi shiru a dakin kamar ba mutane
"mami bakisan I KIRARIn da yakeyi a kaina bane banaso na fada miki dan karna daga miki hankali heedaya ta fada a zuciyar ta
mami ta kalli heedaya "nasan bazaki aikata ba heedaya ina kara samiki tsanar hakan a zuciyar kine inaso kibawa hauwa'u kunya ta fada a zuciyar ta
Mami bari nayi alwala nayi sallah
Kaita daga mata
Umma najin dawo War malam nazifi daga masallalaci tirakarsa ya wuce umma tayi kwafa ta ciji yasa "dani kake magana sai na sa ka budi baki kayi maganin yarin yarcan nasa kayanke mata hukunci cikin fishi nice fa hauwa'u
Kareema ta kalleta ta dauke kai Alhaji Ibrahim gadara kwana yayi yana kiran Kareema a waya anan ya sanar da ita kudirinsa a kanta bajan aji Kareema ta amsa masa yaji dadi sosai yasa tasanar da mahaifinta zezo suba yara bane da zasu bata lokaci a soyayya hajiya naja'atu zazzabi tibiran har rawar sanyi takeyi tarasa dawa Alhaji Ibrahim gadara yake waya duktabi ta daga hankalinta kota kanta baya yi wayarsa yakeyi yana tintsira dariya duk yanda hajiya naja'atu tayi dan sanin dawa yake waya fur yaki gaya mata fatanta Allah yasa ba Kareema bace idan itace shikenan nata ya kare a cikin gidan danko ruwa bazata shaba
Washe gari hajiya naja'atu ta zuba sammako zuwa gidan hajiya saude mahaifiyar shaheeda tana zaune a falo ta zuba uwur tagumi Kana ganinta kasan tana cikin damuwa ga wani rama sadidan da tayi dukta fita haiyacinta
"hajiya naja'atu mafita zamu nema duk wannan ba aikin ta gumi bane ta ina zamu fara duk abin da suke ta kama dashi gidan suka zo cewar saude
"hajiya saude ya zanyi banida wata mafita nifa bansan ta inda zan fara ba kinsan Allah hanyar zuwa gurin bokama ban saniba addu'a kawai nakeyi Allah ya shiga tsakanina dasu a yanzu kome akace nayi zanyi indai zesa hauwa'u ta fasa aurawa Alhaji Kareema
"hmm karma ta fasa nibana fatan mata fasa wlh ta inda aka shigo tanan ake fita hanyar da sukabi shi muma zamu bi kuma zamuci nasara
"Allah yasa yanzu ta ina zamu fara ina zamuje dan dazafi-zafi akan daki karfe
"gurin zuwadai a kwashi bari na dauko mayafina niko keda inda zan kaiki
"kai amma naji dadi akalla na samu na maida kibata ko yayane
Ta dauko mayafi da key din mota ta fito "hajiya naja'atu mu tafi ko
naja'atu ta mike zasu tafi Alhaji shafi'u ta gani ma haifin shaheeda ta sunkuya ta gaida shi
"lpy klau naja'atu y Yara da megidan naki
"suna lpy
"Masha Allah hajiya saude fita za ayi
kallon banza ta mishi "kanada matsala da hakanne
"a'a ko kadan a dawo lpy
"na Dauka hanani zakayi ido baya iya gani yayi shiru kullum ina fada maka bana san haka bana so kakiji amma tam
"Allah ya baki hakuri hajiya bazan sake ba
"kama sake idan kasake kaga matakin dana dauka bani kudi na kara wayanda suke gurina bazasu kaiba
"rafar kudi ya ciro a aljihun shi yafara kirgawa cikin bacinrai ta fisge kudin
"meye haka shafi'u dan zaka bani kudi seka kirga matar taka kaga abinnan da kakeyi yana bata minraifa tom hajiya naja'atu mutafi
Allah ya huci zuciyarki tuba nakeyi
duk mamaki ya ishi naja'atu bakinta faltam baya
New writer's
Hakan Take
*husba'ahfam* 😍❤🤩
*'YAR kwalliya* ❤💋
WhatsApp number 📱 07036891952
👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠👠👠👠
💄💅 *HEEDAYA* 💅💄
*(I KIRARI)*
👝👝👝👝👝👝👝👝👝👝
👠👠👠👠👠👠👠👠👠👠
Written by *husba'ahfama*
*IG officiall_husba'ahfama*
facebook *Real husba'ahfama*
19-20
Suna tafe a mota kowa yayi shiru hajiya saude ta Kalli hajiya naja'atu tayi murmushi
"Naja'atu Kardai haryanzu baki dena tinanin Kareema ba nice da kaina nace ki kwantar da hankalinki zakisha mamaki idan muka dawo daga inda muka je
"hmm kokadan ba wannan bane yake damuna hajiya haryanzu baki dena juya Alhaji shafi'u ba
"hahhh nasan abin da kike tinani Kenan ina sane nace tinanin Kareema kikeyi banida wata hanya sena kafe shi so kike nasakeshi ya cika min gida da da kishiyoyi dakam da kika bani shawara naji nayanke shawarar hake abin da na binne dana hake washe gari yakemin wani isa da takamar da bazan dauka ba nadaure cikin sati daya segashi yasa anata shigo da akwati da aka gama shigo dashi natam bayeshi na menene kinsan budar bakinshi meyace
" a'a sekin fada
"hmm cemin yayi kayan fadar kishiyane kuma bama daya ba uku zemin ranar nashiga damuwa washe gari nakoma gur bokan dazan Kaiki yanzu akaimai mugun dauri dabaze sake maganar aureba koda asirin ya karye dan haka nadauki alkawari duk wanda ze auri 'ya'yana kafesu za ayi saboda namiji bashida tabbasa
hajiya Naja'atu ta jin-jina kai
"Ko kinga laifina
"A'a wlh kokadan banga laifinki ba hajiya saude
Gidan Alhaji Ibrahim gadara
Yasmeen ce taketa shige da fice tana neman hajiya naja'atu amma bata gantaba falo ta dawo tarike kugu tana cije yatsa
"Mommy ina kikaje kuma waime kike shirya wane
"shirye shiryen biki sukeyi kokin manta kemafa bedace kizauna ba ki shirya kije gidan Kila suna bukatar temakonki cewar Alhaji Ibrahim gadara
"daddy ina kwana
"lpy klau y kike
"lpy klau mommy nacanne daddy
"Eh Tana can sammako tayi kayan dakin maryam da Yasmeen aka kawo kije ki gani
"bashi zekai mommy gidan nan ba akwai ma tsala Yasmeen ta fada a zuciyar ta
Daddy bari naje
To kijira basiru ya kaiki yanzu ze fito
Ok bari na dauko jakata
Yasmeen ta dauko jaka da mayafi ta fito tada motar da tajine yasa tasan basiru yana waje wajan taje itama Tabude ta shiga motar
"yaya ina kwana
"lpy klau y kike
"lpy klau
"ke nemamki nakeyi kince maryam tabaki sako kibani baki baniba
Yasmeen ta shiga tinanin abinda zata fada Mai "idan nace bawani sako karya nayi yaya baze barniba ta fada a zuciyar ta cikin kwarin gwaiwa take
cewa bata baniba na tino tace zata baka da kanta muna murna yaya da Anty maryam zasuyi aure kowa ya huta yau saura kwana5
murmusawa Yayi Yaja mota ya tafi a kofar Gidan su shaheeda ya ajiye ta sukayi sallama ta shiga Gidan a falo taga Alhaji shafi'u yana kallo tayi sallama ya amsa har kasa ta sunkuya ta gaida shi ya amsa
"Yasmeen maraba ya kike y karayu
"Alhamdulillah
"Masha Allah shaheeda na ciki fa Amma mahaifiyarta bata nan sunfita tare da mamanki
"to dama gurin shaheeda Nazo bari naje dakin nata akofar dakin ta tsaya tanata bugawa taki budewa ba alamun mutum a dakin tatura kofar ta bude tana shiga tasaki sallati ta riketa
"shaheeda meye haka kekadai kina niyar faduwa nakula kamar bakya iya tsayawa da kafarki meya faru
Ta zaunar da ita a kujerar dake dakin ta sai juyi takeyi tana daga mata hannu batare datace komai ba
"Allah me iko kodai shaheeda tabi layi ne Allah karka tabbatar da abinda nake tinani shaheeda kai tadinga girgizata
"Yasmeen tafada cikin wani irin murya dake cike da ayar tambaya kece kikazo barka barka dai ta sauko daga kujerar ta sunkuya a gabanta tace ina wuni Yasmeen ya gida ya love dina karki ganni haka lpyta kalau garau nake
Yasmeen ta rike kai batare da tace komai ba ta kara kare mata kallo"dan Allah mommy me kika gani a jikin shaheeda dubi abinda zaki debo kikawo mana gida
Wuf shaheeda tace zan gyaru karkice komai ina sanshi zan aure shi Nakawoshi gidana
"eh bashi ze aurekiba ke zaki aure shi kuma ki kaishi gidanki wana irin kwaya kikesha shaheeda daya haukataki lokaci daya
Tashi tayi tana dube dube a dakin taleka karkashin gado ta daga kadan ta zazzake pillow bataga komai ba wata jaka ta gani a fefe shi kadai taje gurin jakar ta bude sai da ta tsorata da abin da ta gani ta mayar ta ajiye
Ta dawo tasata a gaba tana kalla
parking din motar hajiya saude tayi a wani gefen kango
"Hajiya naja'atu kinga gidan nashi can Allah yasa yana nan saboda iyanzu yana can yana ganawa da mutanan boye
"Shidin
"Eh kinsan tareda Su yake aiki ki fadi gaskiya idan munje idan kinyi karyama ze gane
"To muje
suka fati suka karasa wata bukka hajiya saude ce tashiga ta fito
tana magana a hankali kinci sa'a yana nan
"Alhamdulillah Allah nago kanta karasa hajiya saude tarufe mata baki
"Ke kirufa mana asiri karkija yace ya fasa ai tinda kikazo nan sedai ki kira shedan ba Allah ba kinsan dashi kika zonan
"hakane fa
"Dana haka ki kula zomu shiga
"toh muje
Suka Shiga suka zauna hajiya naja'atu ta dinga fada mishi matsalarta harta Gama bece komai ba ya janyo kasar dake kan fai-fai yanata zane daya gama ya ture shi gefe yana kare mata kallo
"Naja'atu kike ko meyasa kikayi jinkiri bakizo nan da wuriba gashi abu na nema yafi karfina Maganar gaskiya aure dai za a yishi ba fashi kuma yarin yar da koma waye a tsaye suke kuma me yi musu aiki aiki yakeyi da gaski nagano ranshin sa'a da azaba da zaki sha sedai badaga gunta ita kadai bace su2 ne gashi nan ina gani
Bata bari ya karasaba tace yanzu ya za ayi kar hakan ya faru
"babu tin farko kekika jawo komai tinkafin sufara yadace kekirigasu tashi
Hajiya saude tace ba wani abu da za ayi yanzu aduba sosai konawane zamu iya biya
Eh to bari na sake dubawa
Yasake zana kasa yace hanya dayane tak amma me kamar wuya
Hajiya naja'atu ta Kalli hajiya saude
hajiya saude tace ayi ko meye tabude jaka ta ciro kudi gashi wannan somin tabine
"to shekenan kuje zakuga koma meye
Hajiya saude ta kama hannunta suka fita saida suka kai jikin mota naja'atu ta tsayar da saude
"mezeyi yanzu saude niduk na kidime wlh hauwa'u shu'umace ta innalillahi
"shima haka naja'atu kisa ranki a innuwa seyaGama aiki yake fadan me yayi shiga mota muje gida
Haka naja'atu ta shiga mota suka tafi tanata tinani a zuciyar ta
Yasmeen nakan shaheeda harta fara dawowa dai-dai
"Gashi kisha lemo ta mika mata ta sha
Nagode Yasmeen kinsan me kainane
Yasmeen ta daga mata hannu "base kince komai ba zoki rakani tafiya zanyi
"kai bazaki jira kiga kayanba inkika tare nagani
"OK fine muje tana tafe tana hada hanya harsuka karasa bakin kofar fita sai kuma ta dawo baya sauti takeji yana tashi taje har gurin
"daddy me kake kalla haka newai yamin yawa a kunne Ka rage karage dan Allah kunnena ze fashe
Yasmeen na bayanta "shaheeda a haka kibari mana zomuje ta kama hannunta
shaheeda ta fusge taje ta kashe TV "daddy ka hakura tinda bazaka rage karar ba narasa me kakeyi a gida
Murmushi Alhaji shafi'u yayi"ayi hakuri a kunna min zanrage karar kinji shaheeda
"daddy bazan kunnaba bazan kunna komai ba ka tara a gaba kona tafi idan kakunna sena gayawa mommy muje Yasmeen
Yasmeen ta kasa daga kafa daga inda take hannuta shaheeda ta
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 4 Chapter of 21