muradi zaka kashe min kanka ne kalli yadda ...ai ganin jini ya fara diga yasa mumy yin shiru tare da rudewa cikin tsananin soyayya ta tsinka masa marin da sai data ji saukansa a zuciyarta kana da sauri ta yaga gefen zaninta, kisna ta matso kusa dashi tana kokarin taba hannunsa ya dakatar daita da hannunsa sannan ya runtse idanunshi gam dan baya son ganinta bai ji zafin marin da momy tayi masa ba illa gyara tsayuwarsa da yayi cike da jarumta, ahankali ya dinga motsa labbansa yana furta kalmar "kiyi hakuri momy kiyi hakuri ...." "karka sake cewa zakayi wani abu kaji na fa?a maka ka manta da komai "no mommy "no I can't ",wallahi mommy abinda Kika fa?a min nayi banyi wani abu dana san ba daidai ba ".muryarta a raunane tace "mommy me yasa mesa dan Allah kice masa ya dinga sawa zuciyarsa salama ya dinga bin komai a hankali idan wani abu ya sameshi ban san yadda su aryan zasu ji ba ......."
"har ke kanki zakiji babu dadi dan duk abinda ya samu uban ya'yanki ya sameki "a hakan da bai daukeni da daraja ba , bai san mahimmancina ba ,sannan bai damu da damuwata ba tayi zance a zuci "shima kuma bazai so wani mummunar abu ya sameki ba amatsayinki na matarsa kuma uwar ya'yansa inji cewar mumy , aliyu ya sake runtse idaunshi yana ciza gefen lip's d'insa da karfi mumy ta kamo sa ta zaunar dashi akan kujera "karka sake min irin wannan ganganci dan rayuwarka nada matukar muhimmancin gareni ta kalli inda kisna ke tsaye "kin wani tsaya kina kallon mu ki je dakina ki dauko min akwatin first aid ,juyawa tayi a sanyaye ta bar d'akin ko cikakken second biyar bata yi ba ta dawo ta ajiye ta sake fita dan dauko tsinyaya ta gyara gurin ta cigaba da tsayuwa tana kallonsu dan ko tace zata taimaka masa bazai yarda ba
mumy ta bude laulausan tafin hannunsa gabanta na wani irin faduwa ,shiru tayi tana kallon raunin daya ji ,tausayinta ya kamata taji kamar ta cire ciwon ta dawo dashi jikinta wanke masa hannu tayi da hydroxy da auduga, tana wanke raunin tana duba ko kwalba ya shiga naman hannunsa .
Bayan ta gama ta rufe akwatin ta janyo kisna tare da zaunar daita gefenta bayan kamar minti goma " kisna taga gara ta aiwatar da nufinta tunda gasu tare , ta kira sunan mumy a hankali "mumy ina neman wani alfarma agurinki saboda kece mutun ta farko a duniya da kike son zamana da ya Aliyu tun ada can baya har zuwa yanzu ,sai gashi har yanzu babu wani cigaba a rayuwar aurenmu.
"da cigaba mana me yasa zaki ce haka "? Mumy tayi mata tambayar a dan kufule dan yaji haushin maganarta "allah babu wani cigaba mommy saboda har yanzu ya Aliyu bai daukeni a matsayin matarsa ba me zai hana mu saukakawa juna ya sawakemin idan zaki wuce na biki mu koma tare dan wallahi zuciyata ta gaji da wannan zaman idan kuma hakan bai samu ba wata rana labarin mutuwa zai riskeku a lokacin da kuke tsananin bukatata ta karasa maganar hawaye na gangaro mata mumy ta damki tsintsiyar hannunta jikinta na rawa numfashinta na barazanar daukewa "ki kwantar da hankali mumy Allah rabuwar mu zai fi kwantar miki da hankali zucoyoyinmu zasu fi samun natsuwa Allah ya raya mana su Aryan "abinda ta fa?a gaskiya ne mumy nima ina iyakacin kokarina naga cewar na manta baya na inganta relationship din dake tsakaninmu amman na kasa idan dai har zai yiwu mu sawakewa juna ......."
"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un " mumy ta shiga furtawa jikinta na tsananta rawa ..."
Inshallahu ku saurari 14 zuwa an jima
Mmn sudais
????????????
CUTAR DA KAI
????????
????????????
Free page 14
~TRUE LIFE STORY~
*PAID BOOK*
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
"Wannan littafin na kudi ne ,mai bukata karanta shi zai tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number alert +234 803 238 4602 domin tabbatar da an tura , ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 ,kada ayi vtu a number MTN sannan kada a Kira number mtn ba'a kira dashi only chart ne . "domin sauraran littafaina sababbi da tsofaffi za'a iya tuntu'bar Channel dina ta Hausa bakwai,sannan muna bada sarin Lagos lace da kamfala ,Lagos rapa , jaka da takalma, getzner na cotonou da chiganvy, volyal lace duk akan farashi mai sauki ,ga mai bukatar siyan ?aya ko sari yayi magana ta wannan number 08059623096,yauwa har ma da agwalumar cotonou mai dan Karan zaki muna turawa kowani gari ...????
....Wani irin kyarma jikin mumy yake batare da sun fahimci haka ba saboda idanuwansu daya rufe, sai faman ya'bawa juna bak'ar magana suke cikin kunar rai ,
A matukar fusace Aliyu ya katsewa kisna hanzarin "na fiki son rabuwa dake mumy nima na amince da tsarinta mu rabu kawai kowa ya huta , dan Allah mommy ki sanyawa zuciyarki salama kiyi hakuri ki bari mu bar rayuwar juna mu cigaba da zumuncinmu shima idan zai yiwu idan kuma bazai yiwu ba kowa ya kama kansa ya fada yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa , wannan maganar data sake dokan kunnuwan mumy yasa taji wani mummunar faduwar gaba ya sake ziyartar jikinta , qirjin mumy ya dinga baguwa da tsananin karfi , duk wani tashin hankalin da take kokarin dannewa acikin zuciyarta sai daya fito fili saboda babu abinda ta tsana a rayuwarta kamar taji maganar rabuwa a bakin Aliyu dan na kisna mai sauki ne tunda sakin ba a hannunta yake ba ...."
Aliyu ne ya fara lura da yadda jikin mumy ke karkarwa kamar mazari yayi saurin rikota cikin tsansnin tashin hankali yana kiran sunanta "mumy !mumy!!! dan girman Allah mumy ki kwantar da hankalinki ".a hankali ta kai hannu ta dafe daidai qirjinta da taji yana mata wani irin zafi da bugawa " Please Karki min haka wallahi bana son na rasaki bana son wani abu ya sameki a dalilin rabuwata da kisna idanunta suka fara rufewa sakamakon kalmar rabuwar daya sake maimaitawa "mumy Please ki tamaineni ki bude idanuki me kike so ayi yanzu ? " duk abinda kike so a shirye nake zan miki matukar zai sakaki farinciki cikin tsananin tashin hankali kisna take furta mata haka kafin daga baya Aliyu ya kwantar daita akan katifa ya mike cikin sauri gaba-daya ya rud'e ya gigice hawaye sun cika masa kwarnin idanunshi tamkar ba wannan Aliyu mai karkarfar zuciya ba ya fita daga d'akin , itama kisna hankalinta yayi matukar tashi dan kusan tafi shi shiga tashin hankali, take ta fara data sani maganarta da bata furta kalmar su rabu da mumy bata shiga damuwa ba ,wani sabon hawayen ne yazo idanunta ya fara zuba akan kuncinta tamkar an bude fanfo , a hankali ta fara rera kuka mai ban tausayi ,ta sake ri?e hannun mumy dake cikin nata gam yayinda hawayenta yaki tsayawa sai faman kuka take da kiran kalmar "na shiga uku cikin tsananin tashin hankali "mumy na tuba bazan sake ba, bazan sake furta kalmar rabuwa da ya Aliyu ba tunda bakya son rabuwarmu , " ki taimakeni dan Allah karki mutu ki barni a gurinki kawai nake samun farinciki da kwanciyar hankali idan kika mutu kika barni rayuwa zata min muni, sosai take kuka tana rike da hannun mumy itama mumy ta rike hannunta gam hawaye na gangaro mata ... ....."
Zuciyar Aliyu na matukar zafi ya dawo d'akin hannunsa rike da goran ruwa bai tsaya tsiyaya ruwan a cikin cup ba ,ya ?alle murfin goran da karfi wani zafi yaji ya ratsa tafin hannunsa inda yaji ciwo sai dai bai tsaya kallon tafin hannunsa ba ,ya soma shafa ruwa a fuska mumy yana kiran sunanta , naunayen ajiyar zuciya ta sauke sannan ta dinga sauke numfashi a hankali a hankali "sannu mumy suka hada baki gurin furta mata haka da kyar ta gyada musu kai idanunta na runtse ,Aliyu ya kamo kanta ya kai goran ruwa bakinta "ki sha ruwa mumy " .
Ta girgiza masa kai alamun bazata sha ba "dan Allah mumy ki rufa min asiri ki kwantar da hankalinki ya kalli kisna da idanunsa da suka rikice suka canza kala tamkar garwashin wuta ya soma magana cikin zafin rai "wallahi Idan wani abu ya same mumy a dalilin furucinki bazan taba yafe miki ba , kuma wallahi bazan cigaba da zama dake ba dole na yakiceki ta karfin tsiya daga jikina domin nafi bukatar rayuwa mahaifiyata akanki ya karashe maganar yana wurgi da rabon ruwa ......."
kuka kisna take sosai tamkar ranta zai bar gangar jikinta tana rike da hannun mumy Sun yi matukar tausayawa halin da mumy take ciki , bazasu iya daukar halin da zata shiga a dalilin cikar burinsu ba .......
Aliyu ya mike da hanzarin zai fita daga dakin domin kiran Samir dan sukai mumy asibiti ta rike hannunsa ya dawo da sauri ya daura hannunsa akan nata tare da zubawa mata idanunshi kamar zai yi kuka "mumy zanje na kira Samir ne mu kai ki asibiti" sake girgiza masa kai tayi ta zuba masa ido cikin sarewa tace "karku wani kai ni asibiti alhalin magani na gida , kune damuwata muradi , idan zanganku cikin farimciki da kwamciyar hankali wallahi nima zan kasance haka"bazan ta?a yarda da tsarinaku ba ,rabuwarku wani babban tashin hankali ne gareni bansan me yasa nake son kasancewarku tare da juna ba amma kafin na cigaba da magana ku amsa min wannan tambayar "?
ta soma yunkurin mikewa zaune daga kwance da take jikinta na daukar zafi Aliyu da kisna suka kai hannuwansu da sauri domin taimaka mata hannun Aliyu ne ya riga na Kisna sauka a gadon bayan mumy sannan hannunta ya sauka akan nashi saurin kallon kwayar idanun juna suka tare da jin faduwar gaba mai tsanani zuciyarsu ta dinga bugawa a tare , zuwa wannan lokacin ko'ina ajikin Aliyu rawa yake yayinda zuciyarsa ke dokawa da sauri sauri fiyye dana Kisna , gabad'aya gabobin jikinsa sun yi sanyi, a hankali Aliyu yayi saurin janye kwayar idanunsa a kanta itama tayi kokarin dauke hannunta dake kan nashi suka yi shiru a tare suna satar kallon kwayar idanun juna ,karamin bakinta ta turo masa tana kashe masa idonta d'aya ..
abinda tayi ya bala'i bashi haushi sosai and he don't want any dilemma with her ko sake kallon inda take bai yi ba dan gani yake bata damu da halin da mumy take ciki ba kukan munafurcinta data saba ne ...
Cikin sanyin jiki ya kamo hannu mommy cikin laulausan tafin hannunsa tare da matsowa gefenta sosai itama kisna ta sake matsota suka sakata a tsakiya ya d'ago kanshi a hankali ya watsa mata harara itama batayi sanya a gwiwa ba ta mayar masa tana murgud'a masa baki yaji tamkar ya buge mata baki ko janyo ta ya yaryarfa mata maruka masu rai da lafiya sai dai ya kasa aiwatar da ko daya saboda shi a yanzu babu abinda yafi bukata kamar samun natsuwar mumy muryarsa a ?ausashe yace "malama ki dan matsa can mumy ta samu wadataccen iskaa kin wani manne mata kina kokarin ....."
"kai ma ka matsa mana cikin ni da kai wa ya hanata sha?ar wadataccen numfashi ? ta kasheshi tana zabga masa harara " nifa bana son damuwa dan Allah kowa yayi lamarin gabansa kawai zai yi magana mumuy tayi saurin d'aga masa hannu alamun yayi shiru umarninta yabi bai sake cewa komai ba ,mommy ta numfasa sannan ta cigaba da magana a tsanake" banason jin wata magana bayan amsar tambayar da zan muku yanzu "tsakanin kai da kisna idan kun rabu zaku iya manta junanku har duniya ta nad'e"?shiru ne ya sake biyowa baya , hatra d'akin ya sake daukar shiru tamkar babu wasu halitta acikinsa kisna ta d'ago idanunta a hankali ta kalleshi dan ganin yanayinsa wani kallo ya watsa mata wanda yasa take hantar cikinta kadawa , ta tabe masa baki qirjinta ya bugawa da karfin gaske .
"ina tambayarku kun min shiru zaku iya manta junanku har abada ? Still shiru suka yi suna kallon mommy "Ni nasan bazaku iya manta junanku ba har duniya ta nade da tunanin juna zaku mutu amman idan amsarku ta kasance "eh zaku iya manta juna sai nasan abun yi ........"
Jin yadda suka yi shiru yasa ta waigo gefen da Aliyu yake da gefen da kisna take makale daita tamkar zata mata numfashi taga suna kallon juna tayi murmushi irin nasu na manya "mai yasa kuke kallon juna ku bani amsar tambayata mana kun min shiru suka sake yin shiru kowanensu na jiran yaji abinda d'an'uwansa zai furta "nasan baza ku iya amsa min wannan tambayar ba bari na fa?a muku abinda zai sa ku shiga hankalinku wallahi muddin kukayi kuskuren barin juna karshenku wahala mai tsanani ,kuma sai ta shafi rayuwar ya'yanku saboda zaku raba musu hankula , saboda kai Aliyu wata matar zaka aura kema Kisna wani mijin zaki aura kuma duk wanda zaki aura bazai kai uban ya'yanki ba ,hakazalika kai ma nawal bazata zama tamkar Kisna agurin su Aryan ba ,da zaran ta samu nata zata manta dasu ba kowace matar uba ke rike masa yaya tsakani da Allah ba ta karashe maganar tana sauke numfashi da kyar Aliyu ya sake tashi ya dauki goran ruwan da yayi wurgi dashi yaga da sauran ruwa aciki ya mika kai bakinta ta kurba tana lumshe ido "na gode muradi Allah yayiwa rayuwa albarka Allah ya yaye maka zafin zuciya ".
"gara kan kina yi kina masa addu'a, wannan zuciya kamar ta mutanen farko ,zuciya a wuya kamar kuturu ba'a jin rarrashi bare hakuri kallonta kawai yayi ya furzar da iska tare da jan tsaki ,ta watsa masa harara tana hura masa hanci dan ta sake tunzura shi ,a ranshi yace kiyi duk iskanci da kika ga dama ganin idon mumy ne zamu hadu ne .."
"Kana magana ne ? tayi maganar cikin jan hankali ."
"ke kisna ban son iskanci sa'anki ne"? tayi shiru "ki shiga hankalinki dan kice kika fara kawo zance rabuwa a tsakaninku da muradi bayan kuma kece za kiyi hakuri dashi domin kin zo gyara kuskurenki ne a gurin mutumin da yake tsananin fushi dake dan iskanci sai kina fada masa magana "kiyi hakuri mumy , "bani zaki bawa hakuri ga wanda zaki sake bawa hakuri nan kuma yanzu a gabana saboda ko babu aure a tsakanin ki dashi d'anuwanki ne bai cancanci wasu abubuwa daga gareki ba , muryarta a raunana tace "to ..to kayi hakuri ".
"haka ake bada hakuri ki hada kalamanki guri daya ki bashi hakuri ta shagwabe fuska kamar zatayi kuka tace "kayi hakuri ".. shiru yayi yaki magana dan zafin da zuciyarsa keyi ba zai bar shi ya amsa mata ba .."Kisna na kiraki da babban murya karki sake zance rabuwa tsakaninki da muradi saboda ina matukar sonku tare bana son ku rabu, rabuwarku daidai yake da shigata damuwa "Ni kuma zafin da zuciyata take akan shi fa mumy ni kadai fa nasan abinda nake ji kar a waye gari a iske bana numfa........" Da ikon Allah babu abinda zai sameki idan kika zauna dashi tsakani da Allah zaki samu lada mai dimbin yawa sannan zaki jiyar da mahaifiyarki dadin da bata bata jin irinsa ba ,zata sake magana mumy ta dakatar daita kana ta maida hankalinta kan Aliyu .....
"aliyu wacece ni agurinka "? da kyar ya iya bude bakinsa muryarsa can kasa yace "Mother " yana riko hannunta cikin nashi "tabbas ni uwarka ce shiyasa ma nafika jin haushi akan abinda kisna ta maka ,abinda tayi ya balain tsaya min a rai ya dameni ya daga min hankali saboda na fahimci halin daka shiga a lokacin amman duk da haka yana da kyau ka yafe mata a karo na biyu dan Allah ku fahimci mahaifiyarku ina son ganinku cikin farinciki dan Allah ku zauna lafiya dan kwanciyar hankalina shiru suka yi zuciyarsu na dokawa da sauri iska ya furzar yana Kallon Kisna itama shi take kallo "mai yasa mommy zata masa haka akan kisna "? "Mai yasa zata sa igiya ta daureshi akanta ? "Aliyu ta sake kiran sunansa muryarta a sanyaye kamar zata zubar da kwalla ," ka saki ranka nasan halinka kana da tsananin fushi da riko a cikin zuciyarka wanda ba'a son muslimi yana yin haka ta kamo hannu kisna ta saka cikin na Aliyu ta dunkule guri daya " ka yafe mata wannan alfarmata ce na nema agurinka nasan ko numfashinka nace ka bani zaka mallaka min bare kalmar baki ,Shiru yayi har kusan second biyar "kayi shiru muradi kace ka yafe mata ? Da kyar ya sake bu?e baki yace "na yafe amman darajanki ne mumy wani sanyayiyyen numfashi Kisna ta sauke tana mai godiya ga Allah da ya furta ya yafe mata mumy tace "nasani darajana taci kuma na gode ko alahira wani nacin arzikin wani Allah yasa muci arzikin Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama "ameen suka hada baki..."Sai abu na gaba Kisna zan baki wata biyar ki dawo da Aliyu daidai ,kaima Aliyu zan baka wata biyar ka dawo daidai da matarka idan ba haka ba zan ?auki mummunar mataki akanku wanda a karshe bazai muku dadi ba, tana gama fadar haka ta mike da kyar ta soma kokarin barin dakin Aliyu ya mike zai taimaka mata tace "yi zamanka muradi na gode zan iya takawa da kaina ya koma ya zauna yana furzar da numfashi .."
Mommy na tashi daga mazauninta Kisna ta mike cikin sanyi jiki ta biyo bayanta ,mumy dake kokarin zama ta dubeta a tsanake tace "me kuma kika zo yi ? " Maza ki koma gurin mijinki ki soma aiwatar da aikinki Allah ya baki nasara akanshi muryata a shagwabe tace "mumy wannan dan naki fa akwai wuyar sha'ani kanshi kamar kwakwa yake wallahi "ungo nan haka zaki daure , tun farko da bakiyi abinda kikayi masa ba kema kinsan yadda kike so zakiyi a gidansa ,hakuri zaki kara akan wanda kike yi , ki sanyawa ranki ibada kike yi kin san kuma duk abinda akace ibada ne dole sai an d'aure tare da sanyawa zuciya hakuri inshallahu ina ji ajikina zakiyi nasara akansa bazai sake wining zuciyarki ba "shikenan mumy adduarki ta Kara min karfin gwiwa daga sarewar dana yi da lamarinsa dan wallahi har na cire tsammani a kanshi "ba'a cire tsammani da rahmar Allah mamana ,kuma inshallahu sai kinyi alfahari da mijinki wata rana mumy ta dan dauki lokaci tana bata shawarwari daga karshe sukayi sallama ta koma dakin yana nan zaune a inda ta barshi yayi tagumi
ta matsoshi sosai kamar zata shige jikinsa sauran ka?an ta kwanto jikinsa tace " maganar mumy gaskiya ne bazamu iya rabuwa da juna ba sai dai wallahi na gaji da irin rayuwar da muke ka saki ranka mu zauna lafiya , ni dai nasan a halin yanzu babu abinda nake son kasancewa dashi kamarka bazan iya rayuwa babu kai ba , ina sonka aliyu kaima nasan kana sona "? tayi maganar tana murza tafin hannunsa dake cikin nata ..."No i can't ya fada atakaice yana furzar da iska mai zafi tare da jan dogon tsaki , shiru tayi jikinta na ?aukar rawa "you mean you don't love me "? "yes I do ya sake bata amsa a takaice ,ta sake matsoshi tare da sanya kwayar idanunta cikin nashi, d'ayan hannunsa ta kamo ta mikar dashi tsaye "come with me ta nufi jikin bango dakin dashi bai mata musu ba yayi shiru yana biye daita kamar wani karamin yaro suna karasawa ta tsaida shi tana fuskartashi tare da kai hannuwanta duka kan wuyansa ta zagaye tana jifansa da wani irin kallo mai kashe gabobin jiki "meye haka kuma "?yayi magana yana kai hannunsa zai cire hannuwanta dake zagaye da wuyansa "tsaya mana ranka shi dade ka ga wani abu , ta cire hannuwanta dake zagaye da wuyansa ta zuge zip din gaban rigarta take dukiyar fulaninta dake cike bammm sunyi wani luhu luhu dasu ga kyau ga haske ga taushi suka bayyana a gabansa "wowwww is beautiful yaushe rabon na gansu ya fa?a acikin ranshi amman a zahiri tsaki yaja yana kawar da fuskarshi gefe kamar yaga mugun abu ,ta kai hannunta ta dawo da fuskarsa gareta ya sake dauke idanunshi akansu "duk fa wannan kayan marmari is for you Aliyu muradi ".... "for me"? ya furta yana watsa mata harara "Yes of course is for you don't you like it ta sake turo masa su daidai bakinsa kasancewarta doguwa sosai ka?an ya rage bata kamoshi ba yayi saurin runtse idaunshi qirjinshi na wani irin bugawa da karfin gaske "stop all this nonsense Kisna it not look beautiful ",kinsan wani abu "?ta girgiza masa kai tana tura hannunta cikin vest d'insa har tayi nasarar kife yatsunta a qirjinsa ya bude baki da niyyar zai yi magana ta muzra kan nipple's d'insa duka tana wani irin narke masa ajiki ... ...tsarkewa yayi ya soma tari kamar wanda yaci wani abu mai yaji take ta rude tana masa sannu "na kawo maka ruwa "?Kai kawai ya girgiza mata alamun a'a ya zare hannunta daga jikinsa ya nufi gaban mirrow yana magana yana kwance agogonsa sai lokacin ya samu damar fadar abinda yake son fad'a mata " duk wannan abinda kike yi basa burgeni saboda bana jin komai ajikina ji nake kamar namiji ne a kusa dani ,wallahi na gaji dake bazan dai iya fitowa na fad'awa mommy bane dan ita kadai zan iya gama rayuwata dake ba dan ina sonki ba,idan son samuna ne ma wallahi nayi nisa da rayuwarki zai fiyye min kwanciyar hankali.."
"look I understand what's in your heart ,ba Sai ka fa?a min ba saboda idan da sabo na saba da wannan kiyayyar ko zan iya baka tukuici akan wannan kiyayyar "?yayi shiru yana Kallonta ta cikin mirrow zuciyarsa na tsalle kallon wawiya yake mata ita kuma tana masa kallon mara wayo "bana bukata kuma karki dameni da shirmeki na banza on-expecting yaji ta sumbaci kumatunsa ta juya tana wata irin shegiyar tafiya tana kad'a masa jiki wanda ya zame mata jiki a tsorace ya juyo yana kallon bayanta "kina hauka ne kike irin wannan tafiyar "? "Haukan sonka ba ta bashi amsa tare da juyowa suna fuskantar juna "me kuma ya samu tafiya ta ? tayi magana tana matsowa a hankali ta karaso gabansa ta tsaya kirjinta na kadawa shiru yayi tare da tsura mata ido kamar zai cinyeta ganin taki ?auke idanunta akanshi ya cire vest dinsa yabi gefenta zai wuce Kawai yaji ta rungumeshi a jikinta , hannuwanta ya sauka a daidai kan nipple's d'insa wani irin shock yaji a ilahirin jikinsa "dan Allah ka bani wata biyar kamar yadda mommy ta fada ina tabbatar maka kafin lokacin soyayyata zatayi tasiri a cikin zuciyarka am very sure zaka soni kafin lokacin "no ya furta a zuciye "ya Aliyu Ni dai ka bani dama dan Allah nayi maka alkawarin muddin baka soni ba zuwa lokacin zan daina sonka gaba-daya zan rufe babin wani Aliyu a rayuwata zaka rabu dani batare da sanin kowa ba, zanyi nesa da rayuwarka a hankali take masa magana cikin rada tana shafa qirjinshi tana manna masa kiss a wuyansa, juyo wa yayi daita a hankali aiko ta fada cikin faffad'an qirjinsa mai kwance da kashi sai kamshi yake zubawa " wayyo my world best wallahi bazan iya rayuwa babu kai ba sonka yayi mugun kamani ta karasa mgnr tana mirza kan nipples d'insa yayi saurin runtse idanunshi shi kadai yasan yadda yake ji a lokacin ,a hankali ta cigaba da murza nipples dinsa tana sauke ajiyar zuciya sannan tana lumshe masa idanu, ta zaro harshenta daga kwance da take ajikinsa tana lasar tsakiyar qirjinsa yayinda hannunta ke kan nipples dinsa tana zagayewa tana fitar da numfashi tana jin wani mugun feeling na taso mata a gaba-daya ilahirin jikinta kamar yadda shima yake ji ,gaba-daya gobobin jikinsa sun soma macewa saboda amsar sakonninta, jin yanayinsa yana neman sauyawa yayi sauri
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 15 Chapter of 21