Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels [12:17PM, 02/02/2017] 🙆🏼‍♂@lh@ji🙆🏼‍♂: [1/6, 9:06 AM] A A Dboy: *YAR TALLAH NEW EPISODE* *CHAPTER 1* Tafe tAke tana rusa kuka wiwi,,,,,wiwi Duk ta hada miyau majina da hawaye ta dame fuska gaba daya Rungume take da tiren tallan tata wanda ba komai a cikinsa sai ihu take kwararawa tana kiran wayyo kudina wayyo ni kudina Mutane sai kallonta sukeyi masu tausayi daga cikinsu su kirata suji abinda ya faru su lallasheta ta tafi A haka taita saqawa ta lunguna harta iso layin gidansu Tunda ta iso layin rabi,u wanda bai wuce dan kimanin shekara goma sha huduba kejiyo sautin kukanta yana duqe yana faman wanke wanke Yai niyyar miqewa karaf sukai ido hudu da inna laure Ta watsa masa wani irin kallo simi simi ya koma yaci gaba da wanke wanken Tace munafuki dan iska wlh ka sake tashi baka gama wanke wankennaN ba saina karya maka qafafu Ta qara jan tsaki ta hankade labule ta shige Daki Rabi,u yai saurin tsame hannunsa daga wanke wanken ya kwasa yai waje da gudu A bakin kofar zauren sukai kicibus yace waya tabakine saude? Ta qara fashewa da wani kukan wanda yafi nada sauti Rabiu ya qara janta jikinsa kiyi haquri saude fadamin meke faruwa? Tadan sassauta da kukan tace kudina yaya kudin tallah na wani ya kwaceminsu Rabiu ya dafe kirji ido waje yace garin yaya saude? Kinsan halin inna laure kuma dukanki zatayi Ta qara fashewa da kuka wayyo yaya dan allah ka roqeta karta dakeni Ya danyi jimm kiyi haquri saude babu yaddah zan iya kixo muje kawai ta dakekin Ta qanqameshi wayyo yaya wlh yankani zatayi Idanunsa suka kawo kwallah ya cije yace zo muje saude insha allahu bazata dokekiba kinji? Kai kawai ta daga masa tana share hawaye yaja hannunta suka shiga ciki Tsaye take a kofar daki da alamun ta cika ta tumbatsa jira kawai take a tabata ta bashe Saude ta qara fashewa da kuka wayyo allah na wlh yaya dukana zatayi Inna laure ta zaburo tayo kansu In dokeki don ubanki laifin me kikayi? Hala kin dawomin da sauran raguwar alalen ne ko?ta fada lokacin data shaqo wuyanta Ina kudun suke in gani? Ta qara fashewa da kuka tace wani ya kwace kutumar ubannan wani ya kwace? Aiko yarinya yau zaki daku a gidannan don wlh saina lahira ya fikijin dadi. Ta jata kiyyyyyyyy..... A qasa har zuwa bakin rijiya ta janyo igiyar guga zaki fadamin ina kudina suke ko saina miki dukan mutuwa da igiyar gugannan? Cikin kuka tace wlh wani ne ya kwace ya ruga tace lallai yarinya aiko jikinki zai gaya miki ni zaki kawowa zancen banza zancen wofi Tasa qafarta ta tureta ta fadi ta dinga lafta mata igiyar gugar kamar badan mutum take duka ba Hankalin rabiu ya tashi yaddah yaga qanuwar tashi keyi gashi tasa qafa ta take mata ruwan ciki. Wani irin kuka ya kwace masa ya duqa a wurin yana bata haquri Inna laure tace au har kanada bakin magana munafiki xonan daman ai jiranka nakeyi ta shaqoshi ta hadesu guri guda taci gaba da jibga tamkar zautacciya Hankali tashe inna mai dan wake ta zagayo gidan ko lullubi babu a tare da ita Kai jama,a lafiya maike faruwane a gidannan? Inna laure ta tsaya da dukan tana huci. Barni da yan iskan yarannan mai danwake nema suke su samin hawan jini. Niqi niqi ina fama dasu inkai gwauro inkai mari wai dondai a samu a rufama kai asiri amman yan iskan yaran basu gani kawai an mutu an barni da jaraba yanxu ace kamar saude wai har tasan taje tallah ta boye kudin wai tace wani ya kwace sbd mugun hali irinna wannan munafukin annamimin dake koya mata Inna mai danwake tace eh kam gaskia baku kyautawa kankuba. Yanxu ku harkunfi son aita jibgarku irin haka idan kun boye kudin kuci me dasu fisabilillahi Tadan numfasa tana kallonsu kafin ta qara zaro ido a,a laure yaya nake ganin yarcan kamar bata motsine"" Ta qara matsawa tana tattabata ta dago da sauri hankali tashe tace wlh laure bata motsi. Tace kai haba mai dan wake da gaske kike? Inna mai danwake ta daga hannun nata ta saki taga ya tafi ragwaf alamar ba rai Inna laure ta kwasa da gudu tana gyara daurin zani fadi take iya karfinta na shiga uku ni laure Dis is just d begining [1/6, 9:06 AM] A A Dboy: 📚📚DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100📚📚 [1/7, 5:48 PM] A A Dboy: *YAR TALLA* *CHAPTER TWO 2* Inna laure ta kwasa a juge tana fadin na shiga uku ta isa bakin randa ta ciko tasa da ruwa taxo ta sheqa mata gaba gaba daya yarinyar ta firgita ta tashi tana fadar wayyo inna kiyi haquri mai dan wake ta riqeta ke yi shiru da allah aita kyaleki Inna laure ta sauke wani nannauyen numfashi ta shiga zare na mujiya Mai dan wake ta miqe tana fadin ni na tafi amman dan allah laure ki dinga kula kisan irin dukan da zaki dinga musu don karkije ki daure kanki da kanki Inna laure ta sake jan kwaron numfashi kafin tace insha allahu zan kiyaye mai dan wake ta fice abinta Laure ta juya ta shige dakinta ta barsu a nan Saude ta rarrafa ta nufi dan uwan nata Wanda ke zaune ya hada kai da gwiwa yanata faman kuka Saude ta raba jikinsa ta kwanta ya qara janta a jikinsa sosai Bata jima da kwanciyaba barci ya dauketa sai faman jan ajiyar zuciya take Akai akai Malam bala yayi sallama ya shigo gidan nasa hannunsa saqale dana iklima yarinyar da bazata wuce yar shekara goma sha daya ba Qanwar saude ce don ita yanxu tana shekara sha biyu ne a duniya Malam bala ya shigo tsakar gidan tare da miqama iklima baqar ledar dake hannunsa ta karba ta shige dakin mahaifiyarta tana tsallen murna Malam bala ya kalli rabiu fuskarsa ba yabo ba fallasa yace bakin munafiki kallon uwar me kakemin? Me mugun halin tsiya hala wani abun kukai aka dakeku ko? Inna laure ta hankado labule ta fito kamar an bankadota ai daman jiranka nake malam wallahi yau saika biyani kudina in dorama yarinyarnan tallah ta boye kudin wai tace an kwace Na rantse da allah ban daukar asara Malam bala yace ai daman tunda na gansu zazzaune anan nasan wata ta'asar sukayi Yan iskan yara masu tsinannan hali wanda sukai gadon Halin tsiya niko yarannan dada inda zan kai Su wallahi dana kaisu na huta da bala,in su Tace ahto nidai kudinane sai an biyani Babu mai doramin asara alalata ta murtala biyuce da goma Malam bala yace toya zanyi ai dole na biyaki tunda allah ya hadani da jarababbun yaya Kiyi haquri idan na dawo daga kasuwa gobe saina biyaki miqomin buta nayi alwala Laure taja kwafa ta juya ta koma dakinta ta dauko masa butan ya nufi bayan gida Ta watsama rabiu harara sannan ta wuce dakinta ta samu iklima ta zazzage baqar ledar sai diban kilishinta takeyi Ta miqa hannu zata dauka yar tasa kuka tana tirje tirjen qafafuwa inna laure tayi saurin ajiyewa Ga abinkinan sarkin rigima. Ai nasandai duk cinki baki iya cinye wannan kilishin Yarinyar ta turo baki irin na shaqwababbun yaya taci gaba tacin abinta Duhun magaribane ya fara ketowa sauro suka fara duduma a jikin rabiu ya lallaba ya kwantar da saude saman siminti Ya lallaba ya nufi dan akurkin dakinsu ya shinfida musu yar yagalgalallan tabarman kaba irin mai cin jikinnan Sannan ya dawo ya lallaba ya dauketa da qar Ya kaita dakin ya kwantar da ita ita kadai ta mamaye tabarman don haka shi saman simintin dakin ya kwanta babu ko filo balle abun rufa Ga duhun dakin. Ya runtse idanunsa dukda yanada yakinin yunwace ke kwankwasarsa bazata barshi yayi barci ba Tunanin mahaifiyarsu ya fado masa kamar yaddah kullun yakeyi kafin ya kwanta Wasu hawaye suka cika masa idanu masu zafi tabbas yasan wahalar da sukesha somon tabice Akan wanda mahaifiyarsu tasha a gurin mahaifinsu Nasiharta gareshi itace ta dawo masa tamkar yanxu take masa su tace Rabiu don allah don annabi ko bayan raina. Ka kula da rayuwar qanwarka karkabar rayuwarta ta gurbata a duk halin da kuka tsinci kanku a ciki kaga ita mace ce dole tana buqatar taimakon wani wanda zai jibanci lamarinta Nasan kaima kana buqatar taimako amman a duk yanda rayuwa taxo rabiu yinta ake Nasan kodani ko bani dole ku rayu bakuda mataimaki sai allah. Rabiu kuyitayimin addu,a in rayu kodan saboda ku. Nima inason in rayu sbd ku Baisan sanda kuka ya kwace masa ba saida yaji saude jikinsa tana jijjigashi. Tace yaya kuka kake? Yayi saurin hadiye kukan tare da goge hawayensa Ya lalubo hannunta ya riqe kafin yace ba kuka nakeba dariyace nake na tadaki ko? Tace a,a yaya yinwa nakeji cikina sai cixona yakeyi tun safe banci komaiba na tafi tallah har yanxu Ya salam ya fada a fili sbd rashin sanin abinyi Saude ta kwantar da kanta a kan cinyarshi tace kaji cikina sai kuka yake ko yaya? Bai tanka mataba ta qara girgizashi cikin muryar kuka tace yaya abinci zanci Rabiu ya kwantar da murya yace dakinyi haquri kin kwanta kinga da safe ba saiki karya ba Tace wlh bazan iya barciba yace to lallaba ki kwanta ina xuwa Ta zame daga jikin nasa sai shi kuma ya miqe ya fita Duk suna kwakkwance a tsakar gida cikin gidan sauro sbd lokacin zafine Sai radio ce keta faman babatunta a banza Rabiu ya lallaba sadab sadab ya isa har inda suke ya dauko langar fura ya lallabo ya shigo Dakin ya zauna yana fadin tashi saude ga fura na samo miki kisha Ta tashi da hanzarinta ya lalubo bakinta ya kafa mata langar furar tasha iya shanta sannan shima yasha kadan ya rage sauran ya lallaba ya tafi don mayarwa Yana qoqarin ajewa kenan iklima ta farka tana fadin laure zansha fura Rabiu yai saurin durkusawa a wurin jikinsa nata faman bari Inna laure ta tashi tana haska fitila da niyyar dauko langar furar Taga mutum a durkushe wuri guda Ta fasa wani uban ihu wayyo allah malam baraw barawo Malam ya tashi a firgice ya rarimo adda yana ina yana ina ? Kafin ya fito daga ciikin gidan sauron rabiu ya kwasa a guje yayi dakinsu yana famar rawar jiki Malam ya fito yana ina barawon yake laure? Tana rawar murya tace nan nan na ganshi duqe wlh Malam bala yaja tsaki to idan nan kika ganshi yana ina ? A,a ka. Haska mana ya dauko touc light ya tafi yana haskawa har zuwa zaure ya dawo yana fadin kedinnan Wallahi kinada matsala. Yanxu haka inuwa wani tsuntsun kika gani kinxo kin rikita mutane da wani barawo Laure tace malam nifa mutun na gani anan duqe Yace to idan da mutum kika gani da ban ganshiba ko laya yayi ya bata? Don allah ki koma ki kwanta kinji Laure tace niko malam wlh bazan iya rintsawa ba don da idona naga mutum nan tsugunne Malam bala ya shige gidan sauransa yana fadin ai saikiyita zama ke kadai Sai a lokacin hankalin rabiu ya kwanta ya saki wata ajiyar zuciya ya lallaba ya kwanta abinsa Bai jima da kwanciya ba bacci barawo ya sacesa Qarshe shida na safe laure ta hankado kofar dakin nasu ta gansu sai sharar barcinsu kawai sukeyi wani takaici ya kamata ta juya ta debo ruwa cikin kwanon sha ta daga labulen ta sheqa musu a firgice duk suka tashi sukai wuqi wuqi kamar ya,yan zakaru Inna laure ta taba baki cikin masifa tace Hmmmmm Ya labarin [1/7, 5:49 PM] A A Dboy: 📚📚DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100📚📚 [12:17PM, 02/02/2017] 🙆🏼‍♂@lh@ji🙆🏼‍♂: [1/8, 4:40 PM] I love my mum: *YAR TALLA* *CHAPTER 3* Inna laure ta tabe baki cikin masifa tace nan har lokacin barcin safe gareku? Sannunku yayan hutu to saiku tashi Kai kaje ka jido mana ruwa ke kuma kije ki share mana gida ki tafi kai markadan waina Ta saki labulan ta juya tai gaba Babu wanda yace komai cikinsu rabiu yadau jarka ita kuma tadau robar markaden ta fice babu alwala bare wanke ido Rabiu ya jido ruwa yafi jarka goma Saida ya ciccika komai na gidan sannan ya fara gyaran gidan Saude ta dawo daga markaden tana hada wuta iklima ta fito riqe da kofin shayi da qaton biredi a hannunta Saude tai saurin tashi daga hura wutar Da take ta kalli iklima tana miqa mata hannu sanmin zo indan gutsira kadan kinji? Rabiu yai saurin kwAbarta ke da,ala kyale mata abinta Saude ta bata fuska nidai don allah zanci Yace toki bari idan na samu kudi zan siyo miki Ta qara bata fuska nidai zanci Kullum saikace zaka samu kudi kuma ba samu kakeba Rabiu yadan kura mata ido kafin yace insha allahu yanxu zan samu kinji? Kai kawai ta daga masa yana juyawa ta miqama yarinyar hannu iklima tace ban badawa Ta juya ta shige dakin nasu tana fadin laure wai kinji wai in san mata biredin ni kuma nace ban badawa Laure ta hankado daki tana fadin au biredin yar tawa kike sama ido Wato ta kawo miki keme cikin ci ki cinye ita kuma ta fadi ta mutu kenan ko? Ta shaqo wuyan rigarta tana fadin dan ubanki kin sabacin irin wannan ne ? Ko sAlon kici kiyita zawo yar banza kawai wuce ki bama mutane wuri ta hankadeta saidata fadi Ta zuya ta kalli rabiu kai kuma zakaci gaba da aikin gabankane ko kuwa?ko zaka rama matane? Bai tanka mataba ya duqar da kansa yaci gaba da sharar da yake Ita kuma taja kujera ta zauna taci gaba da hada kullun wainarta Malam ya kwalama rabiu kira. Ya ajiye tsintsiyar ya tafi Ya watsa masa kallon banza kafin yace. Ungo ka bata munafuki wanda yai gadon mugun hali Rabiu ya amsa jiki na rawa ya fice Dan guntun biredi ne wanda bazai wuce gutsira biyu ba. Sai dan ruwan shayinda ba ko madara Rabiu ya miqa mata ta karba cikin rawar jiki Ta tura biredin duk a baki tana tauna da kyar sbd yaddah ya cika mata baki Rabiu ya kalleta yace kisha a hankali kar kiyi amai bata kulashiba ta Ta kafa kai ta shanye ruwan shayin tas tana lashe kofin Inna laure ta kafa mata dundu wanda yasata amayo duk abinda taci yayo waje cikin takaici tace shegiyar yarinya mai kama da mayyah maqerin kofin zaki tando duk wanda kikasha bai isheki ba? Munafuka tashi kibar wurin kona haureki Ta saka kafa ta tunkudeta Saude ta kwasa da gudu ta nufi dakinsu tana kuka mai sauti Rabiu ya rakata da kallo inna laure ta daka masa tsawa zakaci gabane kokuwa binta zakayi Dan iska mai kama da igiyar shanya Rabiu ya durkusa. Ya soma kwashe aman sautin kukan nata na tsinkulansa a kirji Laure ta gama tuyar wainar ta kukkulla a farar leda naira. Biyar biyar ta zuba mata a cikin bokiti ta dauki ta goma ta miqama rabiu sannan ta kwalawa saude kira Ta fito tana matsar hawaye laure taja tsaki au kukan kike har yanxu kenan? Baki bugu bane shiyasa tashi ki dauka gatanan ta murtala huduce kiyi maza ki dawo kinsan alala nanan tana jiranki Saude ta durkusa ta dauki bokitin tana fadin ina tawa? Inna laure tace eh lallai ai dadin sai yayi miki yawa kisha shayi kici waina ai dadin sai yayi miki yawa yar gidan uban waye ke a garinnan? Batace komaiba ta lallaba ta wuce rabiu dake kusa da ita ya kamo hannunta ya damqa mata nashi wainar ta fice tana murna Inna laure taja tsaki tace matsalarkace nidai ko suma zakadingayi sbd yinwa wlh tallah saika gamamin duk ayyukana dondai na rigada na fita haqqinka Zakara kawai mai neman suna ka bada kwaya kaci tsakuwa Bai tanka mataba yaci gaba da aikin nasa Yana gamawa inna laure ta tattaro kayan iklima masu himilin yawa ta watsomasa ta wurgo masa kullin omo maza ka sabe mata kayannan Rabiu ya durkusa yana tattare kayan bayansa na faman cijewa ya nufi bakin rijiya ya soma wankin Malam bala ya fito daga dakin hannunsa riqe da wani dan takurerren buhu na zuwa kasuwa harya wuCe yadan dawo kadan yace kai rabiu idan ka gama wankin ka shiga daki ka tattaro nawa ya wurgo masa naira hamsin ga wannan nan kasai omo Kuma banason wankin banza don wallahi na dawo naga basu fitaba komin dare saika sake wankesu kanajina ko? Ya karba da hannu biyu gamida daga kai alamar eh Saidaya kammala na iklimar gaba daya sannan yaje ya siyo omon talatin garin goma sugar goma Yaxo ya jiqa saidaya kumbura sannan yasa suga ya fara sha Baiyi cokali biyuba ya tsaya gamida kafama kofin garin idonsa ya cikoda hawaye Wata rayuwa can ya tuno lokacin da mahaifiyarsu ke jiqa musu gari ta tasasu gaba shi da saude susha. Ita kuma ta zauna a gefe tana kallonsu Ko cokali daya ba zatayiba duk kuwa da yinwar da zata tashi da ita ta wuni da ita Tausayin mahaifiyar tasu ya dirsar masa ya tuno yar uwarsa saude yanxu haka yasan da yinwar a cikinta Yaja numfashi sannan yaci gaba dashan garin Laure ta giftashi kamar zata wuce don taka me yakeyi ganin garin rogone yasa ta wuceshi kawai ba tare data tankashiba Shima kuma bai tankataba yasha garinsa ya rage sannan ya tashi ya tattaro kayan mahaifin nasa yaci gaba Karfe daya na rana saude ta dawo daga tallar wainar tana aje bokitin laure ta miqa mata tiren alale idon yar ya ciko da hawaye wahala ya isheta Ga wahalar yawo ga azababbiyar rana ga uwa uba yunwa ita kenan tallah ba dare ba rana Har yaran unguwa sun nada mata suna da YAR TALLA ina kika fito tallah ina zaki tallah ina kika dawo tallah Saude ta daura tiren saman kai wasu hawaye suka gangaro kuncinta laure ta tafa hannuwa na shiga uku Muhammadu dan Abdullahi mezan gani ni laure ? Tallar ce bakyason zuwa to dawo ki ajiye ki zauna ki huta yar hutu zoki ajiyemin tunda baki zuwa Saude ta wuce tana faman sharbar hawaye laure tace uhm hum yarinya kenan ai dama kin adana hawayenki don tallah yanxu kika fara alalata ta murtala hudu ce da goma ki dauki ta gomar kuma wallahi ragin sule idan kikayi a jikinki zan fanshe sannan ko kanxo bance ki dawomin dashiba [1/8, 4:41 PM] I love my mum: 📚📚DAGA GROUP OF HYPE HAUSA NOVELS BOOK WHATSAPP 08064400100📚📚 [1/8, 4:42 PM] I love my mum: *YAR TALLA* *CHAPTER 4* Tace kuma wlh ragin sule kikayi a jikinki zan fanshe sannan ban yarda da ki dawomin da ko kanxo ba anan muka tasaya Saude dai bata kulataba ta wuce tana sharbar kwallah Rabiu dake wanki ya tsame hannunsa daga cikin ruwan wankin ya dauko kofin garin ya bita da gudu Ya jawo hannunta ya kaita kan dakalin wani kofar gida ya zaunar da ita gamida sauke tiren tallar a gefe ya zuba mata idanuwansa Kukan me kike? Tallar ce bakyason zuwa? Saude ta girgiza kai alamar a,a tana share hawaye da bayan hannunta Rabiu yace idan ba tallar bace bakyason zuwaba to menene? Taja majina tanata faman sheshsheqa kafin tace na gaji yaya kafata ciwo take gashi banida takalmi ga zafin rana fasona sai jini yake famanyi Wani irin abu ya tsikari zuciyar. Rabiu ya tsirama kafar ido Wasu hawaye suka cika a idanuwansa gashi bashi da ikon iya taimaka mata Don shi kansa kafar tashi babu takalmi. Tabbas da tausayawa qaramar yarinya kamar saude tayi tafiya babu takalmi Yaddah ake tsala rana yau ga uwa uba kafar duk ta tsatstsage da faso Rabiu yasa yatsa ya goge kwallar data tarar masa muryarsa a sanyaye yace Kiyi haquri kije insha allahu zan samar miki takalmin da zaki dinga sakawa dakin dawo kinji? Ta daga masa kai ya miqa mata kofin garin ta karba ta shanye ta miqa masa kofin Ya amsa ya karbi tiren ya dora mata ta tafi Yana tsaye yana kallonta harta bace Sannan ya juya ya koma gida Laure ta watsa masa harara tace ni naci uwar zariyama ballentana bita zaizai Bai tanka mataba ya duqa yaci gaba da wankinsa harya gama Ya shanya wankin sannan ya nufi kofar dakinta ya durkusa daga waje Inna na gama ina alalata Inna laure ta dago daga kwancen da take saman katifa ita da yarta Ta watsa masa wani kallo tace abincima wato har kaso biyu zaka dinga ci kenan Koba dazun na giftaka naga naga kanacin garin kwaki ba? Dallah ni tashi ka bani wuri ta doka masa tsawa Rabiu ya miqe tamkar almajiri ya nufi bakin rigiya ya janyo ruwa guga guda yayi alwala ya nufi dakinsu yayi sallar asuba da azahar a hade Sannan ya kwanta nanfa gajiyar daya kwaso ta rufeshi Saude tasha yawon tallarta harta godema allah amman alalar ko rabi bata samu ta saida ba nanfa idonta ya ciko da hawaye ta soma bin jama,a tana hadasu da Allah su siya Danladi ya tabo abokinsa ilu kai baba yarinyar canfa tana cikin matsi ina yawan ganinta a cikin tasharnan anya ba zamu far matAba kuwa? Ilu yace nimafa na dade ina wannan tunanin to amman abinda ke tsoratani yarinyar karamace sosai karkaje ka balloma kanka ruwa Danladi yace kaiko da mugun baki kake idan zakaxo muje mu fasa kawai kaxo muje malam Mu jata kangon alhaji sani Ilu yace kuma hakanefa to taro mana ita ni bari naje na duba mana wurin na tabbatar da tsaro Ya dire daga kan teburin da yake ya nufi gurinda saude take duqe gaban wani direban j.5 tana zazzage masa alala a kwano ilu ya iso waje yace ke yarinya idan kin gama sayar masa kikaima wancan gashi can zai siya tace to ta miqama direban alalan ya karba ya somaci ita kuma ta rabe gefe tana jiransa ya gama ya bata kudin da kwanon ta qara gaba Direban ya soma ci gaya dago sai yaga ta kura masa ido ji take dama bakinta yakekai alalar sbd tsabar yunwar dake cinta Direban yadan daga murya yan mata ya kike kallona ko na miki ne ? Saude tayi saurin dauke kanta yayi daria yaci gaba da cin alalarsa Karen matar dake can gefe yace sai oga baka tambayeta ko tana ciki bane Yace kai share wannan bata inda ke mata dadiba Karen motar ya sake bushewa da daria yace sai oga allah yabar mana kai Baice masa komaiba ya qarasa cinye alalar ya wurga mata robar ta zabura ta miqe gamida saka kwanon cikin tiren ta qarasa inda yake domin karban kudin ya kura mata ido yaya akayine? Tace kudin zaka bani Ta nawace? Saude ta numfasa kafin tace ta murtala daya da gomace Yasa hannu a aljihu ya ciro kudi masu yawa ya dubeta Yace yanxu idan na baki wadannan kudin zaki barni nayi lalata dake Saude ta zaro ido tana kallonsa Ya sake maimaita mata a karo na biyu Idonta ya ciko da kwalla alamar zatayi kuka Yace a,a meye abin kuka yanmata karbi kudinki kisan inda kikai kuma karna sake ganin kafarki ta tako inda nake Idankuwa ba hakaba saina turmusheki A wurinnan ya miqa mata kudin karbi

Chapter 1 of 26