Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Yanzu tayi sa'a wayan na gabda tsinkewa ya d'aga da wannan muryar tashi so deep. “yes?” Sosai kirjin Ajwa ya buga amma tayi saurin kaudashi da sauri tace “yauwa ni ce” D'an shiru ne ya ratso wayar kafin ya yi magana cike da rainin hankali “ke ce wa? Aljani ne ni da ki ke so na san ko ke wace?” Wayyo Allah Ajwa kaman ta had'iye zuciya. Wani irin taune harshe tayi yanzu tasan laifin tane tunda ba sanin ko wacece ya yi ba kuma ba sanin number ya yi ba. Gyara murya ta sakeyi tace “ni ce Ajwa” Wani irin shiru wayan ta d'auka har tana zaton ko ya kashe ne ta cirota daga kunne ta duba sai taga wayan tana aiki katin ta nata tafiya a banza a wofi. 🥲pyuuuu. . °•★|•°∵ TAURA BIYU ∵°•|☆•° . * ®𝓐𝓼𝓱𝓪𝓷𝓽𝔂 𝓵𝓸𝓿𝓮 08140754777 𝐜𝐡𝐚𝐭 𝐦𝐞 𝐮𝐩 𝐤𝐮 𝐬𝐚𝐦𝐮 𝐥𝐢𝐭at𝐭𝐚𝐟𝐚𝐢𝐧𝐚 𝐛𝐢𝐬𝐚 𝐫𝐚𝐡𝐮𝐬𝐚 𝐦𝐚𝐢 𝐬𝐚𝐮𝐤'𝐢. 𝐒𝐔𝐋𝐓𝐀𝐍𝐀𝐀𝐇 / 𝐆𝐔𝐃𝐔𝐍𝐀 𝐀𝐊𝐄/ 𝐊𝐀𝐈𝐃𝐈𝐍 𝐌𝐀𝐂𝐄/ 𝐒𝐀𝐔𝐘𝐈𝐍 𝐋𝐀𝐌𝐀𝐑𝐈/ 𝐙𝐔𝐁𝐀𝐑 𝐇𝐀𝐖𝐀𝐘𝐄/ 𝐌𝐔𝐋𝐊𝐈/ 𝐙𝐔𝐂𝐈𝐘𝐀𝐑 𝐌𝐔𝐓𝐔𝐌/ 𝐍𝐎𝐎𝐑/ 𝐒𝐈𝐋𝐀𝐇/ 18+ No edit🥲❕ 【Pg13&14】 “Hello” Ajwa ta sake cewa jin shirun ya yi yawa. Still Asad yaki cewa komai harta sama da minti biyu harta cire wayar zata kashe taji yace da firm voice. “what did you want?” Ajwa kaman tayi hauka saboda yanda ranta ke wani irin tafarfasa. Laifin tane data kirashi shi yasa yake mata iko da isa har yake gaya mata magana.kwafa tayi da k'arfi wanda tasan babu tantama yaji tace cikin zafin rai “na kira ne dama don na ja maka kunne saboda hoton ka yana gabda lalacewa idan mutane Mr, Dr idan sukaji abunda d'an uwanka ya yi ” Asad dake kwance kan wata hadad'd'ediyar cushion sanye da gajeren wando da irin singlet d'in nan mai wawakeken hammata, gashin kannan nasa ya zubo goshinsa kaman an kifa masa hula. Yunk'urawa ya yi ya miƙe zaune rike da wayan a kunne wani irin murmushi ya subuce ta gefen bakinsa jin maganan da Ajwa tayi. Wato blackmailing d'in sa zatayi kenan? Da rainin hankali yace “really?” Haushi ya sake turnike Ajwa tana ji tsab aka bata wuk'a zata dama masa babu shakku. “Mr. Doctor. Ina gaya maka ni ba abun wasa bace ka gayawa d'an uwanka ya janye maganan auren nan nashi dani.” “idan naki fa, me zakiyi?.” Asad ya mayar mata cike da rainin hankali yana wanna murmushin nashi na gefen baki. Yanda kasan ta shiga cikin wayar ta shek'i shi tace murya har wani rawa take saboda bala'in “to walahi kun tarowa kan ku march daga kai har shi sai kunga bala'in da tashin hankalin da baku tab'a gani ba.” A hankali ya koma ya wani kwanta lazily ya kai hannu cikin gashin sa yana yamutsawa tare da lumshe ido. “ko?.ok To ni yanzu da ki ka kirani me zan miki? Far'aan ya dage ke zai aura babu abunda zai canza masa ra'ayi, so call him ki gaya masa mana why zaki kirani?.” Wani irin rike wayan Ajwa tayi tana wani irin cije bakinta duka. Ji take kaman ta buga wayan a k'asa saboda takaici. Numfashi ta fesar da k'arfi tace “haka kace? To ka bani number nashi ni zan kira shi da kaina.” Tana rufe baki ko numfashi bai bari ta shak'a ba yace “No” sai kit ya kashe wayarsa. Wayyo zuciyar Ajwa wani irin ihu ta saki ta d'aga wayar zatayi jifa da ita ta fasa sai tayi wurgi da ita kan dago. Kaman mahaukaciya ta hau jifa da kayan ta dake jere kan mirro tana ihun kaman wani sabon kamu. Karshe gadon ta hau tana ta tsalle da zuba ihu sai abun ma ya baka dariya. Irin b'acin ran nan da in aka maka laifi ka rasa ma me zakayi ka huce. Kiran sallan la'asar da aka fara ya d'an sata nutsuwa ta miƙe fuu ta shige banɗaki ta d'auro alwala. Bayan ta idar da sallah ta jima tana Addu'a kan Allah ya kawo sanadin da wannan auren zai lalace kafin ta rufe da salatin Annabi(S.A.W) ,sannan ta miƙe ta fito saboda cikin ta dake kukan yunwa. A falo ta samu Mom da Suliem suna kallo duk sunyi wani jugum-jugum. Batace musu komai ba tayi kitchen duk da tasan ba lallai ta samu abun kirki ba. Tayi mamaki data ga wainan shinkafa da miyar taushe taji nama da busheshesn kifi ga had'in zubo cikin fridge yasha kayan itatuwa. Tasan Babaah ne ya fito dashi a masa tunda har yanzu store d'in a rufe yake. Sosai ta kwashi abincin ta fito ta zauna tana ci kaman bata so. Daga Mom har Suliem kallon ta kawai suke babu wanda yace mata komai don sun san halin Ajwa. Idan tana cikin b'acin rai shirun yafi mata kwanciyar hankali. Suna zaune Babaah ya fito yasha manyan kaya sai zuba kamshi yake. Kallo d'aya ya musu ya saka kai zai fice Mom tayi saurin miƙewa ta bishi “fita zakayi ne Babaah?” Wani irin juyowa ya yi ya watsa mata harara “eh ko ban isa na fita bane sai na nemi izni?” D'an fesar da numfashi tayi tace “aa dama ina so ne muyi magana.” “bani da lokacin magana dake yanzu. Idan har kan maganan aure ne, babu fashi inshaAllahu .” Bai jira ta sake cewa komai ba ya juya da sauri ya fice saboda wayarsa data fara ringing. Da ido Mom ta bishi ranta na suya can k'asan ranta kishin da take b'oyewa ya taso. Hak'ika tayi k'arya idan tace bata son Babaah, halinsa sane ya danne wannan son. To ance miji dai miji ne kaman yanda uba yake uba. Dole ko yane zataji wani abj a ranta musamman data san babu shakka Babaah wajen wata zashi yanda yake zuna kamshin nan. Shi ya girma amma kullum sai abu yake kaman wani yaro. Fesar da huci tayi ta juyo jiki a sanyaye idanta sai cikin na Ajwa tun tashin Mom ta maida full control nata kansu. Murmushi tayi mai kaman da yak'e wanda aka ce yafi kuka ciwo ta wuce da sauri ta haura sama. Da ido Ajwa ta bita tana jin wani irin kunan rai. Kuma a haka yake so ta auri wanda yake so?. Ita gaba d'aya ta sani maza ne ko nan da shekara talatin gaba bata hango kanta karkashin ikon wani d'a namiji, saj rana tsaka Babaah ya canza mata wannan kudurin? Kai abu ne da bai yiwu ba. Suliem ta kalla data k'ara zama wani so silent kallon take amma sam hankalin ta da tunanin ta baya nan. Kwafa Ajwa ta sake yi duk sunbi sun sake burkita komai daga jiya zuwa yau. Basu tashi daga falon ba sai wajen magriba kowa ya wuce nashi d'akin don yin sallah. Tunda tayi sallah magriba take zaune tana tilawa saida akayi isha ta rufe ta miƙe tayi sallah. Tana idarwa ta haura gado ta janyo wayarta ta sake dannawa Asad kira. ──────────────────────── Lokacin da kiran ya shigo yana zaune kan gado sanye da wasu jayan barci bakake masu laushi rike da laptop nashi yana duba wasu case na majinyata da aka turo masa wanda zai duba gobe idan yaje Mexico. Su'ad nacan falo yana kallon ball. Tun safe Far'aan ya fice har yanzu bai dawo ba ya yi kiran number nashi har ya gaji wayan a kashe. Sosai kuwa ransa ya b'aci don yasan bazai wuce yana can tare da wata ba. Me yasa Far'aan ke son lalata rayuwar sa ne da yawace-yawace banza da wofi? Yana bin mata suna kashe masa kudi kaman ba namiji ba. Kusan effort nashi kan aikin nan saboda Far'aan ne don yaga ya bashi dukkanin abunda yake buk'ata tunda shi yak'i maida hankali ya yi aikin, amma duk da haka bai fasa k'arban abun hannun yan matansa ba.' Ding' sak'o ya shigo wayarsa ta private number nashi da bakowa ya sani ba. Da d'an mamaki ya buɗe sak'on yana tunanin waye kuma yake da private number nashi banda Far'aan da Su'ad? '𝘈𝘴𝘴𝘢𝘭𝘢𝘮𝘶'𝘢𝘭𝘢𝘪𝘬𝘶𝘮. 𝘯𝘢𝘴𝘢𝘯 𝘻𝘢𝘬𝘢𝘺𝘪 𝘮𝘢𝘮𝘢𝘬𝘪𝘯 𝘨𝘢𝘯𝘪𝘯 𝘢𝘯 𝘮𝘢𝘬𝘢 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘥𝘢 𝘱𝘳𝘪𝘷𝘢𝘵𝘦 𝘯𝘶𝘮𝘣𝘦𝘳 𝘯𝘢𝘬𝘢. 𝘴𝘶𝘯𝘢𝘯𝘢 𝘑𝘈𝘝𝘈𝘙𝘐𝘈 𝘢𝘯𝘢 𝘬𝘪𝘳𝘢𝘯𝘢 𝘈𝘳𝘪𝘢. 𝘋𝘰𝘯 𝘈𝘭𝘭𝘢𝘩 𝘪𝘯𝘢 𝘴𝘰 𝘪𝘥𝘢𝘯 𝘬𝘢 𝘴𝘢𝘮𝘶 𝘥𝘢𝘮𝘢 𝘬𝘢 𝘬𝘪𝘳𝘢𝘯𝘪 𝘢𝘬𝘸𝘢𝘪 𝘮𝘢𝘨𝘢𝘯𝘢 𝘮𝘢𝘪 𝘮𝘶𝘩𝘪𝘮𝘮𝘢𝘯𝘤𝘪 𝘥𝘢 𝘯𝘢𝘬𝘦 𝘴𝘰 𝘮𝘶𝘺𝘪 𝘥𝘢 𝘬𝘢𝘪 𝘨𝘢𝘮𝘦 𝘥𝘢 𝘥'𝘢𝘯 𝘶𝘸𝘢𝘯𝘬𝘢 𝘍𝘢𝘳'𝘢𝘢𝘯. 𝘕𝘢𝘨𝘰𝘥𝘦' Da tsananin mamaki ya sake karanta sak'on yana tunanin wacece haka, kuma menene take son cewa game da Far'aan? Bai jira wani abu ba ya fara k'ok'arin kiran number sai kuma kiran Ajwa ya katseshi. D'aya wayar tashi ya kalla ya d'an ware manyan idanuwansa ganin number Ajwa da ya yi saving da LITTLE TIGER yana yawo jikin wayan. Murmushi ya d'an kwace masa ya zubawa wayar ido tana ta ringing harta katse bai d'aga ba. Komawa ya yi ya kwanta rik'e da wayar ya hard'e hannu a k'irji. Ido ya zubawa wayar yana kirge sai ga wani kiran ya sake shigowa. Murmushin gefen baki ya sake saki ya zubawa number ido saida ta kusa tsinkewa sannan ya d'aga cike da kasaita yace “yes, who's this?” Harshe Ajwa ta taune saboda bak'in ciki. Eh lallai wato ma bai gane number nata ba kenan?to taya zai gane Ajwa? Zuciyanta yace. Y'ar kwafa tayi rai a cunkushe tace “nice Ajwa.” “ok. Why ki ke sake kirana?.” Can k'asan makoshi tace 'd'an rainin hankali dani ka ke zancen. Shegen isa da ikon banza da wofi' abunda bata sani ba kaf yaji abunda tace. Wani irin murmushin ya sake yi. “number Far'a....” “No” kafin ta k'arasa ya tare numshin ta. A zafafe tace “kai namiji ne Mr,Doctor. Kuma duk halin ku d'aya na rashin kulawa,son kai,wad'anda kawai suka damu da kansu. Ka jira ka gani. Walahi ka kuskura ka bari Far'aan ya aureni sai na zame masa musiba da tashin hankali. Sai na lalata rayuwar dumb brother naka. Ka jira ka gani ” Kit ta kashe wayar tayi jifa da ita. Wani irin shiru ya yi da wayan a kunnen sa. Yanda take maganan zai tabbatar maka da bawai wasa take ba, amma a matsayin ta na mace me zata iya yi? What will she possibly do da zai lalata rayuwar Far'aan?me yasa take kiransa da wad'annan sunayen? Wai take jerashi cikin irin wannan mazan data lissafa?me yasa ta tsani auren haka. Ya fuskanci bawai auren ne kad'ai ta tsana ba su kansu mazan basa gabanta. To amma why?dole akwai abunda yasa take acting haka. Numfashi ya fesar mai zafi ya miƙe ya shige toilet don watsa ruwa saboda kansa da yaji ya fara chaji. Duk uban sanyi da ake haka ya sakarwa kansa ruwan sanyi. ──────────────────────── Tana kashe wayar tayi jifa da ita ranta na suya. Menene zatayi ta kashe wannan auren? Haka ta kwanta da kyar ta iya barci a daddafe babu dad'i saboda damuwa. To watsan kwana biyu sosai Ajwa ke cikin damuwa gashi tun ranan data kira Asad bata sake samun shi a waya kullum ta kira wayan a kashe. Babaah dai har yanzu bai sake cewa komai ba game da auren kuma kwana biyu baina cika zama a gida ba bare ya musu tijarar sa. Kudin da Asad ya bawa Suliem dashi suke amfani suna buk'atan su na gida da cefane. Yau Juma'a suka wayi gari da kiran mutanen Saudiya. NONNA(kaka) ta kira zancen auren kaman yanda Babaah ya sanar dasu. Ajwa kaman tayi hauka saboda Nonna tace akwai yayyen Mom da zasu taso gobe da asuba saboda Babaah ya sanar dasu gobe iyayen Far'aan zasuzo da yamma. Ita data ga Babaah baya zama ta d'auka ko abun ya d'an kwanta ashe yana can yana shirya komai basu sani ba. Kad'an ne ya rage Ajwa bata fad'i irin cin kashin da Babaah yake musu ba ko Allah zaisa Nonna tace za'a fasa auren, to amma idan ta fad'a ina take da hujja ko misali da zai tabbatar da halin sa bayan duniya tana masa kallon wani mutum na daban? Ko a cikin dangi ana jerashi cikin wanda suka fita daban saboda hali nasu mai kyau. Ranan kwanan zaune Ajwa tayi ,tayi kiran number Asad kaman zatayi hauka amma abu d'aya take ji duk sanda ta kira, wato switch off. Asubar fari Babaah ya dira a gidan dan bai kwana ciki ba. Yana shigowa kuwa ya fara hargagi maza su fito su fara durawa bak'i abincin don sun taso. Kafin su taso suka kura zasu shiga jirgi. Haka Ajwa ta fito kaman wata zombie saboda yanda kanta ke masifar ciwo kuma ta hana kanta yin kuka don taci alwashi ta daina kuka a kan Babaah. ──────────────────────── 2 days back. Mexico. Tun ranan da sukayi waya da ita washegari Asubar fari jirginsa ya d'aga zuwa Mexico. Sosai ya tafi da damuwar Far'aan don koda suka rakosa Airport shida Su'ad saida sukayi fad'a kan yawon da yake. Haka suka rabu kowa ransa a bace. Daya sauka kuwa yana sane yak'i kunna duka layinsa don bayan sanma Far'aan d'in ya kirashi ya bashi hak'uri. A hankali ya faka motar da aka bashi musamman kirar Lexus saboda buk'atunsa yau da kullum gefen wani restaurant dake cike mak'il da costumers. Bak'ar riga ce a jikinsa mai wuya data kama faffad'an k'irjinsa da bak'in wando . Farin glass ne kan fuskarsa da gashin ya dan zubo gefe da gefen goshin sa ya tufke ragowar a keya. Sosai ya yi kyau hannun sa d'aure da hadad'd'en silver watch. A hankali ya Sanyo jiki ya fito da k'afarsa dake boye cikin farin cambus kafin ya Sanyo jiki gaba d'aya waje. Kusan yana fitowa yaja hankalin mutane da yawa musamman matan dake wajen tuni suka fara tura k'irji suna jifansa da flirtatious kallo. Kurar data debosu bai kalla ba ya fara k'ok'arin saka kai zai shige cikin restaurant d'in. Wata baturiya ce tasha gabansa sanye da wani gown mara hannu irin na yan kanti da adon flowers sai blue jacket data d'ura a kanta tayi rolling da blue k'aramin mayafi. Yarinyar tana da kyau babu laifi. Baya kad'an Asad yaja yana kallon ta da fuska a yatsine musamman yanda take ta zuba masa murmushi. “hi, sorry na tare ka. Nasan baka gane ni ba. Sunana JAVARIA ” Javaria? Ina ya tab'a jin sunan nan? Ahh yes, ita ce yarinyar data yi masa sako? But tana tasan inda yake? Wacece wannan yarinyar? Kaman tasan tunanin da take ta sake murmushi da ita kad'ai tasan ma'anan sa kafin ta sake cewa “nasan zakayi mamaki yanda akayi nasan inda ka ke. Ba abun mamaki bane saboda na dade ina bibiyar ka. Da farko dai ina so mu shiga ciki muyi magana ” Ta dad'e taba bibiyar sa? Saboda me? Wace irin yarinyar ce wannan Far'aan ya yi huld'a da ita? Lallai mutum abun tsoro ne. A tuhume yake kallonta kafin ya jinjina kai ya wuce ya shige restaurant d'in ta biyoshi tana murmushi. Can Vip ya samu ya mak'ale Javaria sai wani d'aga kai take saboda yanda mutane suke ta kallon Asad. Wannan wani damane ta sake samu. Suna zama waiter ya matso ya kawo musu ruwa da menu. Murmushi Aria tayi ta d'auki cup d'in da wani iyayi ta d'an k'urba ta ajiye tana d'an sauke fuska k'asa saboda kaifin idon Asad d'in da take ji har cikin ruhin ta. Why bata fara haduwa da Asad ba sai Far'aan? Ta tambayi kanta. Harde hannu ya yi kan kujera ya wani zuba mata mayun idansa babu wasa yace “yes ke nake saurara. Don't West my time” Ya yi mamaki ma da yaga tana jin hausa don Baturiya ce ciki da waje babu wani sirki. Tunda har tace tayi huld'a da Far'aan to dole zataji hausa. Murmushi tayi da kunyar munafurci tace “sunana Javaria kaman yanda kaji, Baturiya ce ni ciki da waje amma had'uwa ta da Far'aan ya canza abubuwan da yawa cikin rayuwata. Saboda Far'aan na karb'i addinin musulunci saboda soyayyar. Na rabu da komai da kowa nawa kowa ya guje ni saboda shi. Abunda ban sani ba ashe shi ba haka bane cikin ransa. Soyayyar sa ta karye ce a gareni ya yinda zuciyata take hannun sa.” D'an shiru tayi sai kuma ga hawaye shar sun wanke mata fuska. “Far'aan ya yaudare ne da sunan So ya saka na gujewa rayuwata ,dangina da ahalina sanadin hakan suka yanke alaka dani. Ashe abunda ban sani ba Far'aan yana tare dani ne saboda dukiyar iyaye na. Bayan sun gujeni saboda addinin gaskiya dana k'arba sai ya kasance duk wata hanya da zan mallaki arzik'i su sun yanke min ita. Na koma bani da komai sai Allah da soyayyar Far'aan da nake fama da ita. A ganina babu abunda zai rabani da Far'aan saboda abubuwa da yawa da nayi sacrifice saboda shi. Ashe nayi zabin tumun dare domin Far'aan shima sai ya gujemin lokacin danafi buk'atar sa cikin rayuwata. Ya gudu ya barni da takarda da kuma... .” Kuka ne yaci k'arfi ta ta kasa k'arasa maganan da take. Sosai jikin Asad ya wani irin sanyi zufa ta fara karyo masa. Baisan abun Far'aan haka ya yi worst ba. Just why? D'agowa Javaria tayi tana face majina da jan ido ta k'arasa cewa “abunda nake so nace shi ne. Far'aan ya aureni ya kuma sake ni bayan bani da komai ya gudu ya barni da cikin sa..” Wani irin dum. Maganan ta doki kan Asad wanda aka kwadawa guduma. Kai duk iskancin Far'aan bazai tab'a yin aure a b'oye basu sani ba. Taya ,a kuma ina? Anya kuwa gaskiya ce take fad'i? Yasan matan yanzu babu abunda baza suyi ba don suga sun lalata rayuwar mutum musamman ma su turawa. Kaman tasan kokwanton da yake ta bud'e y'ar Jakarta dake rataye a k'afad'ar ta ta fito da wasu hutuna ta ajiye gabansa tana cewa “nasan cewa ba lallai ka yarda da abunda nace ba amma ga evidence da proof nan. Wannan hotun ranan auren mu da bayan munyi aure. Sai wannan takardar aure ce kaman yanda muke yi al'ada saboda sanin halin ku hausawa baku da amana sai gashi Far'aan ya tabbatar min da hakan. Ka duba ka gani ga saka hannun sa nan da nawa .” Tsananin shock daya shiga gaba d'aya ya kasa motsi sai gumi kawai da yake ta karyo masa. Miƙewa tayi tana goge fuska da tissu tace “naji labarin cewa zaiyi aure. To ina mai tabbatar maka da zarar ya samu abunda yake so zai zubar da ita gefe. Don wanna shine game din Far'aan. Wannan V-card din shi yake wa da zarar kuma ya same shi she's just like us. .” A hankali ta juya ta fice tana murmushi hakanta ya cimma ruwa. Saura kai Far'aan. I'm coming for you. 'Wannan V-card d'in shi yake wa. Da zarar ya same shi shikenan ta shiga sawun mu' maganan dake ta masa amsa kuwa kenan cikin kunne. No bazai bar hakan ya kasance ba. Wani irin miƙewa ya yi da sauri ya fito ya fad'a mota. Yana k'ok'arin tada ita zuciyar sa tace 'amma why ka ke so kayi protecting yarinyar da baka sani ba? Far'aan ya kamata ka kare shine flesh and blood naka. Why?.' Shi kansa bashi da amsan wannan tambayar. Wani huci ya fesar mai zafi ya maida kanshi ya kifa jikin sitiyari. A fili yace “Hassan. Why ka aikata haka, just why?.” A hankali ya ciro wayarsa ya kunna aikuwa sak'on Far'aan ya dinga shigowa babu kakkautawa. Lumshe manyan idanuwansa Asad ya yi yana had'iye wani abu daya tsaya masa a makoshi. Far'aan yana neman jawo musu tsak'iyar da babu ruwa. Yaja neman tada musu zaune tsaye. Maimakon ya kira sai kawai ya shiga neman ticket duk da cewa aikin nasa bai k'are ba a nan. ──────────────────────── Wajen shad'aya da rabi mutanen Saudiya suka sauka garin Bauchi. Babaah da Mom da kansu suka je suka tarosu a airport's. Mutum hud'u ne suka zo. Yayar Mom da kuma k'anwar Mamanta sai babban yayen Mom da kuma wan Babaah da yake bi. A gida suka bar Ajwa da Suliem dake ta kai kawo babu matsakar tsinke suna ta girki kaman babu gobe. Suna jin k'arar motar a guje suka fice gaba d'aya ita da Suliem suka tare su sai ihun murna suke. Aunty Raihana(Yayar Mom) da Ammi kanwar maman su sai dariya suke haka Baffa( Alhaji Yusif Babban wansu gaba d'aya daya zame kaman uba cikin family) sai kawu(Alhaji Munir wan Babaah ). D'aya haka duk suka had'u d'aya bayan d'aya suka rungume cike da murna kafin suka rankaya gaba d'aya cikin gida. Nanma baiyan gaishe gaishe anjima ana ya bayan saduwa kafin Suliem da Ajwa suka cika musu gaba da kayan ciyeye. Haka suka lalace a falon ana ta hira da yaushe rabon saduwa har wajen azahar kafin duk suka tashi aka nuna musu da k'unan da zasu sauka. Zuwansu yasa Ajwa ta d'an manta da damuwar da take ciki plan nata ya koma yanda zata tonawa Babaah asiri kafin su koma Saudiya. Wajen la'asar Alhaji Sultan ya yi waya gasu nan suna gab da shigowa garin Bauchi. Wayyo Ajwa kaman tayi tsuntsawa ta bace. Da gaske dai abun nan ya kankama sai anyi kenan? To bayan sunzo bayan gaishe-gaishe da ban gajiya babu wani b'ata lokaci suka bada kudi da kuma saka rana. Alhaji Lurwan kanin Dad da suka zo ya d'an gyara zama yana kallon Babaah da Baffa yace “alfarma ce dai muka zo da ita. Dama cewa mukayi saboda ku mutanen Saudiya daba zama zasuyi ba mai zai hana Juma'a mai zuwa a d'ura aure don mu b'angaren mu bamu da matsala. In yaso idan akwai wani abu ma za za'ai in Allah ya kaimu daga baya sai ayi komai a nutse. Kunsan yaran zamani babu kunya shi yaron ne duk ya hanamu sakewa ya matsu ayi auren cikin d'an k'ank'anin lokaci shi yasa mukace bari mu nemi alfarma idan da hali in hakan zai yiwu.” “to Alhamdulillah. Allah ya nuna mana da rai da lafiya” Haka duk suka tashi kowa cikin farin ciki da annushawa banda Ajwa da take ji kaman zata had'iye zuciya ta mutu. Kullewa ma tayi a d'aki ta ki bud'e kofa duk bugun duniya da Ammi suke tana ji daga baya suka kyale ta don a zaton su kunya ce irin tasu ta larabawa. Duk tana jinsu daga baya wayan Asad ta shiga kira amma har yau a kashe take. Haka tayi jufa da wayan kaman zatayi hauka. ──────────────────────── “Wayyo Far'aan , dad'in ka ya yi yawa ” Babbar matace dake zaune kanshi tana ta sukuwa ita kad'ai duk ta firgice kaman mahaukaciya. D'an yatsina fuska ya yi don gaba d'aya dakiya yake saboda mugun nauyi ne da ita. Irin matan nan ne da suke da uban hips da uban nono daya zube kaman faranti. Sam bata cikin jerin matan da yake bi saboda ita d'in hamshakiya matar ce tsohon mijinta daya mutu wanda ya tab'a yin minister ya bar mata uban dukiya ita da yaranta kaman hauka ne, inba haka ba sam ita ba ajin sa bace. Kugunta ya rike saboda wani mugun tashi da tayi zata koma ta zauna da sauri yace “ke kina da kai? Kashe ni zakayi?” Bata amsa ba bata kuma daina rawan da take ba jikinsa nasa har wani yawu yake biyo gefen bakinta saboda duniyar taurarin da take jin kanta a ciki. 'Ding' wayansa ya yi kqrar shigowar sak'o. D'an juya kai ya yi gefe ya mik'a hannu ya d'auko wayar. Ganin Number Asad yasa ya wani tashi da sauri ya d'auke ta cak ya ajiye gefen sa. Da azama ya buɗe sak'on '𝑘𝑎𝑛𝑎 𝑖𝑛𝑎? 𝑐𝑜𝑚𝑒 𝑎𝑛𝑑 𝑝𝑖𝑐𝑘 𝑚𝑒 𝑖𝑛𝑎 𝐴𝑖𝑟𝑝𝑜𝑟𝑡 ' A guje ya yi banɗaki matar sai kwala masa kira take amma ko juyowa baiyi ba. A gurguje ya yi wanka ya fito yana saka kaya Hajiya Zuwaira tace “ina zaka je ne haka kana ta sauri bayan kuma kasan ban samu nutsuwa ba” Mugun kallo ya watsa mata yana cewa “brother d'ina yazo zanje na d'auko shi airport's ” Da sauri ya juya zai fice wayan sa hau k'ara yana jin Zuwaira ma cewa sai yaushe zamu sake had'uwa amma bai bi ta kanta ba. Sunan Kawun sa daya gani jikin wayar ya d'aga da sauri yana cewa “kawu ya ya sun amince?” Daga d'aya b'angaren dariya ya yi yana girgiza kai yace “sun amince Hassan. Juma'a mai zuwa iwar haka ka zama ango. Don Allah ka nutsu ka ajiye duk wannan shiritar aure ba wasa bane kaji” “inshaAllahu Kawu.” “to Allah ya yi muku albarka. Sai mun dawo” Da amin Far'aan ya amsa ya kashe wayar.

Chapter 6 of 15