Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
alwala. Lokacin data fito kuwa tuni zazzabin ya rufeta ruf jikinta har rawar sanyi ya fara. Da kyar ta iya yin sallah ta kwanta nan kan danduma. Daga Mom har Suliem duk babu nutsuwa tattare dasu ita kanta Mom zazzab'in ne a jikinta ga hannun ta dake mata masifar ciwo amma ta b'oye bata son Ajwa ko Suliem su fuskanci halin da take ciki musamman ma Ajwa da zata sata a gaba dole taji menene ya faru, wannan kuma wani sirri ne da bazata iya gayawa yaran nata ba don kaman su ta tonawa asiri ne. Ido ta lumshe tana sake hasko abunda ya faru daz'u wasu hawaye suka sake biyo kuncinta tayi saurin gogewa. To daren dai haka suka kwana zaune ita da Suliem suna bawa Ajwa kulawa. ──────────────────────── Koda Babaah ya koma d'akin sa nan ma hargagi ya yi tayi shi kad'ai kaman wani tabab'bb'e yana jifa da kaya. In kaga yanda yake zakayi tunanin yana kan wani abu ne. K'arshe waya ya d'auka ya haye can k'uryar gado yana kira. Tana fara ringing aka d'aga cikin gaggawa. Cikin d'an k'ank'anin lokaci Babaah ya fara juyi kan gado yana fidda nishi hannun sa can cikin wandon sa. Gaba d'aya Babaah ya koma kama wani d'an yaro har magiya yake yana kuka da bin umarni da ake bashi ta wayar. Haka Babaah ya lalace kan wayar nan da wanda suke tare yana biyawa kansa buk'ata duk ya fice hayyacin sa . In kaga yanda ya sadda kai yana bin umarni sai kasha mamaki ko uwarsa albarka. * . °•★|•°∵ TAURA BIYU ∵°•|☆•° . * ®𝓐𝓼𝓱𝓪𝓷𝓽𝔂 𝓵𝓸𝓿𝓮 08140754777 18+ 【Pg7&8】 Washe gari duk haka suka tashi jiki babu kuzari musamman ma Ajwa amma tana k'arfin hali saboda taga yanda suka damu daga Mom har Suliem babu wanda ya yi wani barcin kirki. Mom kam kwana tayi tana sallah bata samu runtsawa ba sai bayan tayi sallah asuba ,shi yasa har gari ya waye bata tashi ba daga ita da Suliem. Ajwa data farka tun bayan tayi sallah ta kasa komawa saboda shi kansa barcin ba dad'in sa take jiba, gaba d'aya jikin ta ciwo yake tana sane tak'i tashin Mom duk da tasan cewa Babaah yana nan kuma hakan babban matsala ne garesu baki d'aya. Saboda mugunta ne yasa yaki kawo musu mai aiki bare mai gadi. Komai su suke yi basu da wani hutu in har yana nan. Ilay kuwa sai ga Babaah kaman wanda aka wurgu d'akin. Bugu k'ofar da ya yi shi ya yi sanadin tashin su duk suka farka a firgice banda Ajwa data maida nata idon ta lumshe. A hanzarce Mom ta miƙe tsaye tana kallon Babaah dake tsaye bakin k'ofa ran nan a matuk'ar bace “wani sabon rashin mutuncin ki ka tsira daya hana ki zo ki bani abun kari bare kizo ki sauke nauyin ki da Allah ya d'ura miki matsayin ki na mataa? Ko kuwa ganin dama ne?.” Saida yaja Mataa d'in ya k'arasa da wata irin calm voice mai saka tsigar mutum tashin. Gaban Mom ya yi wani masifaffen fad'uwa saboda hango tsantsan tashin hankali dake kwance kan fuskarsa da kuma muryar daya yi maganan da ita. Kafin tayi magana Suliem dake mak'ure jikin gado tayi maza tace murya na rawa “Babaah ina kwana?.” “lfy” Ya bata amsa da dakakkiyar murya idonsa na kan Mom. “ke nake jira. .” Nauyayyiyar ajiyar zuciya ta sauke murya nad'an rawa tace “kayi hak'uri Babaah, wlh jikin Ajwa ne ya yi tsanani jiya bamu runtsa ba sam sai bayan munyi sallah shi yasa na makara bansan gari ya waye haka ba..” Ido kawai ya zuba mata Allah kad'ai yasan meke cikin ransa. Can kuma ya d'an jinjina kai yace “ok” Ba Mom da Suliem ba, har Ajwa da idonta ke lumshe saida ta buɗe ta kalli Babaah dake k'ok'arin juyawa ya fice. Da azama Mom ta bishi bayan ya fice don da ta kasa motsi. D'akin sa ya koma yana k'ok'arin rufe k'ofar Mom ta dafa k'ofar ya juyo ya watsa mata idonsa da bazaka iya karantar abunda ke ciki ba. Baya kad'an Mom taja bayan sun had'a ido. “me za'a dafa ma?” Zuba mata ido kawai ya yi bai bata amsa ba duk ta kagu ji take kaman har hanjinta yake gani. “shigo ciki ” Ya buɗe k'ofar sosai yana kallon ta. D'agowa tayi ta kalli fuskarsa gabanta na fad'uwa. Bata san abunda ya faru jiya ya sake faruwa. Gira ya d'aga yana kallonta yace “ko bazaki shigo bane?” Mom kaman ta fashe da kuka ta rab'a a d'ad'are ta wuce ta gefen sa ta shiga d'akin. Maida k'ofar ya yi ya rufe harda saka key ya juyo fuskarsa babu wani d'igon rahama yace “ni da ke yau, zanga wanda ya isa kuma yake sama tsakaninmu. Abunda baki so shi zanyi tunda kince ke ya'ya mata ki ke so mu zuba nida ke. Wuce muje ciki” Wasu hawayen bak'in ciki ne suka wankewa Mom fuska tace “wai kai me yasa ne ko na sakan d'aya baka san a samu kwanciyar hankali bare zaman lafiya Babaah?. Yaran nan fa Allah ne ya bamu su bamu muka bawa kanmu ba. Kaji tsoron Allah kana masa butulci baka san abunda yaran nan zasu zama ba nan gaba. Ya'ya mata rahama ne fa. Wlh ka guji duniya Babaah babu komai ciki sai wulak'anci da rashin daraja wajen ALLAH(S.W.T) domin da tana da darajar fika-fika sauro wajen mai duka, to da tabbas ko d'igo kafirai bazasu samu ba na ruwa. Duniyar nan fa kaman inuwa ce ga matafiyi don yada zango, da zarar ya barta shikenan fa Babaah ” “ok. To yi min wa'azi tunda ga jahili ko Measha? Har zaki gayamin duniya. Ki fara yiwa kan ki wa'azin tukun tunda kinsan hukuncin matar dake kaurawacewa mijinta. Ke bakiga wannan laifin ba shine zakimin wa'azin banza da wofi . Wlh yau sai nayi abunda baki so sai dai ki had'iye zuciya ki mutu ” Tun daga nan falon d'akin suka fara zuba dambe kaman wasu k'ananan yara daga bisani ya d'agata chak ya yi d'aki da ita yana hargagin. “inga uban da ya isa ya kwace ki a hannuna yanzu, in kuma y'ar iskar y'ar taki ce zatazo ta kwace ta gwada na gani” Bayan koma ya lafa ya mik'e ransa tas yana maida kayansa idonsa kan Mom dake chukwikiye cikin bargo tana wani irin kuka mara sauti. Kuka tayi shi harta gode Allah baki ya tab'e cikin rashin damuwa yace “akwai yaro dana zab'awa Suliem matsayin miji mun gama magana da iyayen yaron. Ina tunani wani satin d'an uwansa zaizo suzo yaganta su daidai ta . Da zarar sunga juna zamu saka lokaci ayi komai a gama. Ina sanar dake saboda kina da iko da kuma hakk'i ki sani amma da sai ranan auren zakiji da ace hakan naso.” Juyawa ya yi zai fice har ya kai k'ofa ya juyo yana kallonta. Tun daz'u ya lura kaman hannunta na damun kuma damben da sukayi daz'u ya lura da hannun ya kuma san sanadin abunda ya faru jiya ne. “zan kira Dr yazo ya duba ki. You're a wise woman. Idan ki ka fad'a wani abu da zasu fuskanci wani abu har a tafi damu a baki, kar ki manta kan ki da yaran ki ki ka tonawa asiri. Ni na fita.” Ya sakai abunsa ya fice ko wanka baiyi ba. Sakkowar sa kasa kitchen ya wuce ya kwashe duk wani d'anyen abinci dake ciki ya mayar store ya gark'ame da katon kwado bai bar ko kwayar shinkafa ba. Yana fitowa kuwa waje y'an neman taimako sun cika k'ofar gida. Haka ya dinga binsu d'aya bayan d'aya yana musu shatara ta arzik'i, mutane sai shi masa albarka suke da Addu'oi. Sosai Mom ke kuka idanuwanta sunyi luhu-luhu kaman wanda suke ciwo. Da kyar ta yunk'ura ta mik'a ta saka kayanta ta fito tayi nata d'akin. Saida tayi wanka ta chanza kaya zuwa atamfa d'inkin doguwar riga ta d'an shafa hoda a fuska sannan ta d'ura hijabi kan kayan sannan ta fito falo ko kad'an bata yarda ta koma d'akin Ajwa ba don tasan sata zasuyi a gaba da tambaya musamman Ajwa. Yanda take jin fuskarta da hannun ta bata son su fuskanci mugun raunin daya ji mata. Tana fitowa kuwa sai ga kiran Babaah yana kara ja mata kunne ga likita nan zuwa zai dubata ita da Ajwa. Batayi zaton zaice ya duba har Ajwa ba amma taji dad'i da Allah yasa yace ya dubatan don dama tayi niya tasa sai dai ya yi fad'an da zaiyi. Tana kashe wayar doctor ya buga gate sai ita ta fita ta buɗe masa. Sosai ya duba hannun ya bata magani. Yanayin Dr ya nuna yana son ya tambayi ba'asi yanda tayi wannan mugun bugewa haka har ya so ya saka mata gocewar k'ashi , amma Mom sam bata bada fuska ba yana gama dubata ta haura dashi sama d'akin Ajwa. Cirko-cirko suka same su zaune kaman wanda aka aikowa da sakon mutuwa. Ai Ajwa na ganin Mom ta fara yunk'urin miƙewa da k'arfin hali zata tashi tsaye Mom tayi saurin k'arasowa ta maida ita. Bayani tayiwa likita abunda ke damunta itama ya bata magani da zai mata allura yace a fara kawo mata tea mai kaushi ta fara shara. Da sauri Suliem ta fito kitchen d'in don had'a Tea sai dai tana zuwa taja tunga ganin store a gark'ame da katon kwad'o. Turus ta tsaya tana kallon k'ofar ta rasa me zatayi. Wani irin sanyi jikinta ya yi ta juya ta buɗe fridge tana Addu'a Allah yasa ta samu d'an drink. Allah da ikon sa kuwa sai ga fresh milk da Babaah ya siyo shekaran jiya ya manta da ita a ciki. Da sauri ta d'auko ta ta d'auki cup ta haura sama harda d'an gudunta. Tana shiga d'aki daga Mom har Ajwa kallonta kawai ya sanar dasu akwai wani abu. Mik'awa Ajwa madarar bayan ta zuba a cup ta d'an k'urba kad'an ta ajiye. Haka dole likitan ya mata allura ya tafi. Ba'a dad'e dayi mata allurar ba barci ya yi awon gaba da ita, sai a lokacin Mom ta iya tambayar Suliem abunda yasa bata dafa shayin ba. Hawaye ne suka wankewa Suliem fuska tace “Babaah ya rufe store d'in Mamaa. Ya kwashe komai ya mayar cikin store ya kuma rufe da kwad'o .” “ya rufe store?wace magana ki ke yi haka Suliem ” “wlh Mamaa ya rufe store d'in ya barmu mu zauna da yunwa. Anya kuwa Mamaa, Babaah shine mahaifi..” Kafin ta k'arasa Mom ta sauke mata mari da ita kanta bata san sanda ta fidda hannu tayi shi ba. Rai a b'ace Mom tace “kina so ki cemin a yawon banza na haifeku kenan ko Suliem? Idan bashi ne uban kuba waye uban naku. Nace waye ubanku? .” Suliem na wani irin kuka ta rungume Mom tana girgiza kai. Ita tasan tsabar b'acin rai ne da bak'in ciki yasa tayi haka. “aa kiyi hak'uri Mamaa. Wlh ba haka nake nufi ba. Don Allah kiyi hak'uri .” Ajiyar zuciya Mom ta sauke ta janye Suliem daga jikinta ta sakko k'asa don ta gasgata maganan Suliem. Tabbas kuwa ya rufe store d'in. Waya ta ciro ta danna masa kira saida ta kusa tsinkewa sannan ya d'aga. “lfy menene kin dameni da kira ina cikin muhimmin abu.” Sassauta murya tayi tace “Abban Suliem nace ko mantawa kayi ka rufe store d'in tunda kasan dole zamu d'ura abinci?” Da wani irin iko yace “dasani na na rufe naga daman hakan ne. Tunda har kina mantawa da dafamin abinci to kowa sai ya daina ci duk sanda naga dama a dafa sai a dafa.” Bai jira tace wani abu ba ya kashe wayarsa. Ido Mom ta zubawa wayar wasu hawaye suka biyo kuncinta. Hak'ika d'an ragowar imanin da take tunanin Babaah nada shi babu yanzu. Allah ya kawo musu sauk'i ya kuma shiga ciki lamuransu. Allah ya nuna mata lokacin da Babaah zaiyi nadaman abunda yake musu ya shirye shi idan mai shiryuwa ne. Sama ta koma ta kira Suliem d'an chanjin dake hannun ta bata taje kasuwa ta yi musu cafene suka dura abinci. Tsawon kwana biyu Babaah bai dawo gidan ba ,bare ya buɗe store sai Mom ke bada chanjin hannun ta Suliem na musu cefane a b'oye basu so Ajwa ta sani. Yanzu kam jikin nata alhamdulillah ta d'an warware don tana d'an fita waje wajen yara in taji hayaniyar su ball. ──────────────────────── Misalin k'arfe had'u na yau laraba jirginsa ya sauka babban birnin tarayya Abuja. Sanye yake da k'ananan kaya bak'ar riga mai gajeren hannu do bak'in wando ,ya d'ura irin k'atuwar jacket d'in nan a kansu. Kanshi sanye da farar p-cap data shiga da farin cambus dake k'afarsa. Yana goye da k'atuwar jaka ta matafiya fuskar nan b'oye cikin mask. Tunda ya fito daga jirgi duk wani atmosphere ya chanza duk inda ya wuce komai tsayawa yake cak. Tafiya yake da wannan izzar tashi kaman baya son taka k'asa,Su'ad na biye bayan sa shima yasha kyau cikin Ash shadda . Duk inda suka wuce sai an juyo an sake juyowa sai sun b'ace idon mutane sannan kowa ke kama harkar gabansa jiki a mace. Suna fitowar harabar wajen Su'ad ya ajiye Jakar sa ya rik'e kugu yana kallon wajen “yanzu da kace kar na gayawa Far'aan zuwan mu, a me ka ke so muje gida kenan?.” Maimakon ya bashi amsa sai ya nufi wata k'aramar Toyota dake fake can gefe da number airport's jikinta. Kai tsaye bayan motar kawai ya buɗe ya fad'a babu tambaya ko ciniki da mai mota zaije ko aa. Mai mota kuwa ya juyo a sukwanne zaiyi tijara jin an fad'a masa mota babu neman izni. Yawu ya had'iye ya zubawa Asad ido girma da kwarjinin sa yasa ya kasa cewa komai yana jiran umarni. Da sallama Su'ad ya buɗe gaba ya shigo ya zauna fuskarsa d'auke da murmushi ya mik'a masa hannu suka gaisa. Ganin Su'ad mai taxi ya d'an ji sauk'i ya d'an saki jiki. Ko kafin su kai inda zasu sauka tuni mai taxi ya ware suna ta hira da Su'ad da kwasar dariya kaman cikin sa zaiyi ciwo. To koda suka k'araso k'ofar wani matsakaicin stairs da aka kashewa dukiya, Asad sa kai ya yi ya fice daga motar babu ko waiwaye. Su'ad shiya sallami mai mota dake ta mamaki irin wannan izza ta Asad. A guje yabi Asad wanda tuni ya shige gate don maigadi dake zaune kan benci da y'ar radio nashi, yana hango fitowar Asad daga cikin motar ya wani tashi da bala'in gudu ya buɗe gate sai zuba masa sannu da zuwa yake kaman zai ari baki. Dad dake zaune harabar wajen cikin wani kebantaccen garden dayasha furranni. Sanye yake da cikin doguwar riga y'ar dubai mara nauyi gabansa d'an k'aramin tebir ne na glass da aka shak'e da kayan marmari sai jarida ta DAILY TRUST dake hannunsa yana dubawa. Da d'an mamaki ya d'ago jin murya maigadi nata sannu da zuwa Alhaji. Cikin matsanancin mamaki ya mik'e da sauri ganin Asad ya sawo kai ciki yana k'ok'arin wucewa duk da cewa ya gansa. Da sauri ya nufeshi suka hadu tsak'iyar wajen bakinsa ya kasa rufuwa. K'afad'un Asad ya rik'e daya zuba masa idonsa da ake gani kawai saboda mask ya jijjaga yana cewa “MashaAllah My Boy. Look at you Asad. Hak'ika tsark'i ya tabbata ga Allah daya bani ku matsayin ya'ya. Kaga yanda ka k'ara zama wani giant? MashaAllah .” Rungume shi ya yi kaman zai maidashi ciki Asad kuwa ya wani sandare kaman gunki sai ido da yake bin mahaifin nashi da shi. Wannan abu ne da basu saba dashi ba. Wato soyayya daga wajen mahaifin su ko nuna damuwa da lamuran su. Janye shi Dad ya yi daga jikinsa yana cigaba da duban sa tun daga sama har k'asa ya cigaba da cewa “ashe kana hanya amma baka sanar ba?. Daka fad'a ai da Mamee taku ta d'ura muku wani abu, muje maza ku hutu kuci abinci.” Shi dai bai motsa ba har zuwa lokacin gani yake kaman mafarki ne yake. Hannun sa Dad ya kama ya juyo ya kalli Su'ad da shima ya cika da mamaki ya yi wani shiru kaman ruwa ya cinye sa. “Su'ad, sannunku da zuwa kunsha hanya. Muje maza ciki ku huta kuci abinci ” Haka suka bishi salo-salo kaman marasa laka a jiki. Hadad'd'en main falon gidan suka shiga da aka k'awata da kaya na kece raini. Mamee(Hajiya Rukayya) matar Dad ,cousin nashi ce. Bayan rasuwar mahaifiyar su Asad aka had'a auren saboda su. Da fari sun d'auka itama kaman Dad take mutum mara damuwa dasu da lamuran su don tun bayan mutuwar mahaifiyar su ,damuwa da al'hini Dad ya daina basu kulawa har ya kasance sun tashi babu soyayya da kulawar mahaifi kansu. Su suka gina kansu kuma suka tarbiyartan da kansu da taimakon Mamee data tsaya tsayin daka wajen gani ta maye gurbin uwa a garesu,to amma sud'in sunki bata wannan damar saboda Dad. Halin ko in kula da yake nuna musu kusan yana da nasaba da rashin jin Far'aan. Mamee dake zaune falon cikin kwalliyarta hannun ta rik'e da carbi ta tashi da azama ta taresu cikin matsanancin farin ciki. Cikin d'an k'ank'anin lokaci ta rasa ma inda zata saka Asad don ma bai wani saki jiki ba amma ba kaman yanda yawa Dad ba don Mamee yana ganin kimarta sosai da girman ta. Dad da kansa ya zuba abinci ya zauna kusa da Asad zai bashi suka zubawa juna ido. Kallon da Asad din ya masa sosai yasa jikinsa yin sanyi. Duk abunda ya gani wajen ya'yan sa laifin sane, amma yaci alwashi zai gyara abunda daya b'ata. Zaija yaransa a jiki ya nuna musu soyayyar daya gagara nuna musu lokacin da suke buk'atar sa. Murmushi k'arfin hali ya yi yana kallon idon Asad yace “shi wannan abun fuskar ba'a cireshi ne?, ka cire ka ci abinci mana Asadu. A cireshi a huta haka ko? ” Maida idanuwansa ya yi ya lumshe ya kawar da kai daga kallon Dad kaman baisan magana yace “am not hungry” Baki Dad ya buɗe zai sake magana Su'ad ya yi saurin cewa “munci abinci ne Dad muna gab da sauka daga jirgi. Bari muyi sallah tukun zuwa d'an anjima ma sake ci” Kai Dad ya jinjina “to shikenan kuje kuyi sallan bari nasa a kawo muku abincin sashes naku sai ku huta. Wannan ja'irin yaron nasan ya gyara b'angaren naku ko ina yake ma oho. Ko ka sanar masa da zuwan naku ne?” “no” Kawai yace ya miƙe ya yi waje abunsa. Da ido Dad ya bishi yana murmushi mai ciwo zuciyarsa nace masa duk laifin ka ke bakaji haushi ba. Su'ad daya kasa tashi ya miƙe shima jiki a d'an sanyaye yace “bari muje Dad , Mamee sai anjima” “to shikenan a huta lafiya” A tare suka amsa fuska d'auke da murmushi. Koda ya shiga b'angaren nasu ko ina kal'kal sai shek'i yake. Kabar Far'aan da shak'iyancin sa amma akwai tsabta ko mace albarka. Kai tsaye d'akin sa ya wuce yana shiga ya yi jifa da jakarsa ya fara cire kayansa yana jifa dasu ya shige toilet. Sanda Su'ad ya shigo yana wanka kai ya girgiza yabi kayan da Asad ya zubar ya kwashe ya ninke ya zuba masa cikin kwaba kafin ya yi tsalle ya d'ane kan gadon. D'aure da tawul ya fito a kugunsa da wani k'arami hannun sa yana goge gashin kansa. Wani uban fito Su'ad ya yi yana kallon Asad zaiyi magana ya watsa masa wani mugun kallo. Y'ar dariya ya yi cikin ransa yace ' duk abunka wannan jikin wata rana na watane sai yanda taga dama shi'. Miƙewa shima ya yi ya shige toilet d'in dan watsa ruwa. Bakin gado Asad ya zauna ya d'auko wayar ya turawa Far'aan sak'o da kalma biyu kawai 'I'm here' Miƙewa ya yi ya d'auko doguwar riga mara nauyi mai hula ,ya feshe jikinsa da turare kafin yaja daddamu ya shimfiɗa musu yana jiran Su'ad ya fito suyi sallah. ──────────────────────── Doguwar ajiyar zuciya ta sauke tana sake kai mayafi ta goge gumin goshinta. Gaba d'aya ranta babu dad'i don yau jarabawar ba k'aramin zafi tayi mata ba ko nace tayi musu. Kwana biyu rashin dowawar Babaah ya d'an sama musu nutsuwa da kwanciyar hankali har suna fata dama kar ya dawo yanzu. Saboda rashin Babaah a gida ne ya bata dama ta d'an samu daman karatu hankali a d'an kwance tunda ta sami lafiya. Yau exams d'in nasu masu matuk'ar zafi ne sukayi CALCULUS da PHYSICS. Tun safe suke bugawa sai yanzu suka gama wajen biyar na yamma. “anya kuwa zamu samu nape Ajwa. Kinga fa titin kaman anyi ruwa an d'auke ga magriba tana kawo kai” Cewar Moon k'awarta tak, kuma aminiyar ta. D'an tsaki Ajwa ta sake ja ita bama wannan ba yanda garin keta had'ewa lokaci guda shine yafi d'aga mata hankali. Aikuwa aka fara iska mai k'arfi mutane suka fara neman mafaka. Hannun Moon ta kama tana cewa “kinga zo kawai mu koma cikin makarantar wannan ruwan idan ya sauka baza muji da dad'i ba. Idan ya tsagaita sai mu tafi ko a kafa ne mu fara takawa. Saboda wannan hadarin shi yasa babu motocin su kansu” Har sun juya Allah ya taimakesu mai nape dake k'ok'arin fitowa daga makarantar ya d'auke su. Moon aka fara saukewa sai Ajwa. Tana sauka Suliem itama na sakkowa daga nape nik'i-nik'i da kayan abinci. Shinkafa data siyo musu kwano sai taliya da wake sai kuma kayan miya. Saida gaban Suliem ya yanke ya fad'i ganin Ajwa na fitowa itama daga nape dake gabanta. B'oye-b'oye da suke tayi gashi yau asiri ya tono. To ai dama ance ranan b'oye cibi ba'a wanka. K'arasowa Ajwa tayi cike da d'an tuhuma kan fuskarta ta taimaka suka fito da kayan. Saida ta bari Suliem ta sallami mai nape sannan ta d'ibi kayan suka shiga ciki. Kaman jira aka kuwa su shiga ciki aka tsuge da ruwa kaman da bakin kwarya. Zaune falo suka iske Mom na kallon a Taswira. Kai tsaye gaban Mom ta ajiye kayan ta zauna kan tebir tana kallon Mom tana jira ta fito da abunda Suliem d'in ta siyo. Kallon su gaba d'aya Mom tayi da d'an yak'e kan fuskarta tace “ya ya jarabawar Bint? Yanzu nake tunanin ki ga hadari ya had'u a gari” “Hmmmm, Mamaa kayan abincin menene wannan. Sadaka za'ayi?” Kallon juna Mom da Suliem sukayi kafin Mom ta sauke ajiyar zuciya ta kama hannun Ajwa ta rik'e. Kaf ta kwashe komai ta gaya mata tun ranan da Babaah ya bar gidan ya rufe store kuma har yanzu da basu san inda yake ba ,kuma bata samun sa a waya. Saida Mom tayi dana sanin gaya mata don lokaci guda idonta ya juye ya yi jazur jikinta ya fara kyama, da wani bala'in gudu ta miƙe tayi sama Mom da Suliem na kwala mata kira amma ina kota juyo. Bata jima ba sai gata a guje ta dawo rik'e da guduma ko ina ta samo tama Allah masani. Kai tsaye kitchen tayi suka rufa mata baya jiki na kyama ta d'aga gudumar ta dinga bugawa jikin kwad'on da dukkanin wani k'arfin ta. Bugu biyu tayi kwad'on ya b'alle ta zaroshi tana huci tayo waje Mom da Suliem nata k'ok'arin hanata sai ihu take “wlh bai isa ya mana huron yunwa ba Allah ya hore mana abunda zamuci, in kuwa yace zai mana huron yunwa saboda rashin imani wlh sai na k'ona kayan abincin kowa ya rasa ” “Allah ko? Ni kuma zan nuna miki ni Uban ki, ni na tsugunna na haife ki kuma ni na isa dake nake kuma da ikon yanke dukkanin wani hukunci da naga dama” Babu zato muryar Babaah ya ratso falon kaman saukan Aradu. Omo, Ga Babaah ya dawo fa. Da alama dai Ajwa tana da rabon shan wani dukan.😬 Thoughts naku a comments. Mu had'u a can🫡 . °•★|•°∵ TAURA BIYU ∵°•|☆•° . * ®𝓐𝓼𝓱𝓪𝓷𝓽𝔂 𝓵𝓸𝓿𝓮 08140754777 18+

Chapter 3 of 15