Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
mata mai cike da tsana yace “never. Koda matan duniya zasu k'are ace ke kad'ai ce ki ka rage I will rather die. Ina da matar data fiki a komai Aya so why ki ke tunanin zan sake son ki? Koda banda Ajwa kina tunanin zan sake dawo dake cikin rayuwata ne? Get out from my office. Kuma wlh ki ka sake biyoni duk inda nake sai kiga true colour d'ina. Get out” Ido ta zuba masa ranta na suya. Har ita ta durkusa tana masa magiya ya wulak'antata? Ajwa. Ta sake kiran sunan cikin ranta. Shine sunan matar tashi? To walahi basu isa su zauna lafiya ba inhar tana raye. Yanzu hakan a shirye tazo ta fara zuwa ne kawai ta gani ko zai k'arbi lallashin ta amma tunda ya dage zaiyi mata taurin kai zata bishi da taurin kan ita ma. A zafafe ta miƙe fuu ta fice daga office Asad ya bita da mugun kallo yana jan wani dogon tsaki. Taba fitowa ta samu guri cikin asibitin ta rabe. Wayarta ta ciro ranta na suya ta dannawa wata number kira. Bugu biyu aka d'aga babu b'ata lokaci tace “kije yanzu maza a binne karan kar ki bari wani ya ganki kinji kashedin da Zalmula ya mana. Idan kin gama kuma ina so ki koma kice masa ina so ayi wani amma matarsa nake so ayiwa. Ita ina so ayita tsorata har sai ta bar gidan ta rabu dashi har abada. ” Dan Jim tayi tana sauraran abunda ake cewa sai kuma ta sake cewa “na safa turaren amma baiyi aiki ba. Dama ai cewa ya yi in turaren baiyi aiki ba saboda k'arfi tsari dake jikinsa a binne karan. ...........to shikenan” Kwashe wayar tayi tana kwafa tace “mu zuba nida kai Asad. Baka isa wata mace ta mallake kaba ina numfashi a duron k'asa. ” Fuu ta fice daga asibitin. ──────────────────────── Maza biyu a kansa sai ihu suke da gurnani daga can gefe Michael ne shima tare da wani saurayi. Tun daga can UK Michael ya yi hayarsa suka biyo jirgi saboda uban makudan kud'i da Babaah ya saka kansu. Wani uban gurnani Babaah ya sake jikin msa na jijjaga yana kiran suna Asad ya juye kaf abunda ke mararsa kan yaran dake kansa. Numfashi ya sauke duk ya had'a gumi yana jin kansa kaman kan gajimare. Bai tab'a jin tsananin dad'i irin na yauba. Tabbas Michael daya ce yaran hatsabibaine baiyi k'arya ba. Na d'an wani Ya manta da duk damuwar yake d'auke da ita dawowar sa daga can Abuja. Miƙewa ya yi ya jingina da bango yaran suka bishi suka kwanta a k'irji sa. Hannu ya kai ya tsiyaya giyar dake ajiye gefen gado ya k'urba yana kallon Michael da yaron sa sai ihu suke. Suna gama masha'arsu shima Michael ya taso gaban Babaah ya zauna yana shafa k'afar yace “plan namu yana tafiya bisa tsari Darling. Umarnin ka kawai muke jira” Saida Babaah ya k'urbe giyar dake hannunsa ya ajiye cup d'in ya wani d'ago fuskar sa babu wani annuri yace “good. Nan da wani d'an lokaci zan baku go ahead. Very soon burina zai cika.” Miƙewa ya yi shige banɗaki duk suka bishi da kallo kaman su had'iye. har yanzu ransa na suyan abunda Mom tayi masa. Gefe kuma yana jin kaman ya ajiye wani katon nauyi na rabuwa da ita da ya yi. Yanzu zai masu daman aikatar da burin sa babu shakka bare tunanin akwai abunda zai masa shamaki wajen cikar burinsa. Idan ta Ajwa ne bai damuwa sam don akwai abunda ya shirya mata. 🤔 to fa Asad ka shiga uku oo. Wannan jaraba haka duk a kan ka, kai kad'ai?,Allah sarki bawan Allah baisan ana yi ba. To ku FANS dai kuyi ta saka Asad da Ajwa cikin Addu'a 🫥. 𝗧𝗔𝗨𝗥𝗔 𝗕𝗜𝗬𝗨 ®𝐀𝐬𝐡𝐚𝐧𝐭𝐲𝐥𝐮𝐯 /No edit! 'Come and join exclusive already an fara payments free page's are counting! 'Join exclusive @500 to 8140754777, Aisha Sani Hassan. Opay. 【Pg31&32】 Yau haka ta wuni a gidan shiru kaman wata mayya. Ko falo tak'i ta fito in kaga ta fito to yunwa ce take nukurkusarta. Wajejen Azahar su Mom suka kirata sun sauka lafiya. Ai nan Ajwa ta sake lalace tana ta rera musu kuka sun tafi sun barta. Saida sukayi ta rarrashinta da yi mata alkwarin zasu Asad ya kawota kodan taga dangi. Suna kashe wayan kiran Asad na shigowa nan ta d'an k'ara samun relief har barci ya d'auke suna wayan bata sani ba. Yana jin yanda numfashin ta ke sauka a hankali ya d'an saki murmushi bakin sa ya d'an motsa can k'asan mokashi ya fara furta “I love...” sai kuma ya yi shiru yana tunanin me yake son cewa ne? Kai ya girgiza yana murmushi yace lokaci bai yi ba tukun da zaka furta mata wannan kalman. Gwanda ka furta kana kallon kyakkyawar fuskarta kaga wane action zata bayar. Kwanciya ya gyara yana sake manna wayan cikin kunnen sa saboda yanda yake jin saukan numfashin nata so peaceful. A haka shima barci ya kwashe ba tare da ya kashe wayan ba. To gab da margirba ta fara firgice da wani irin mummunan fad'uwar gaba saboda motsi da taji alamun kaman an shigo gidan. Jiki na rawa ta sakko daga gado ta tawo da sand'a ta tsaya bakin k'ofa jikinta zuciyarta na harbawa da bala'in gudu. Sosai taji alamun tafiya an tsaya bakin k'ofar d'akin ta ta sake rudewa matuk'a tayi maza ta kalli wayanta dake kan gado. Ji tayi an tab'a mukullin ana juyawa kaman za'a bude can kuma sai aka daina. Sai kima taji an buɗe d'aya daga cikin kofofin an mayar an rufe. Wayyo tsaida zuciyar Ajwa ta daina bugawa na d'an wani lokaci. A guje da sand'a ta matsa bakin gado ta d'auko wayarta. Tsabar yanda jikinta ke rawa wayan ta fad'i ta sake bi da rawar jiki ta d'auka. Asad ta dannawa kira wanda yake can cikin emergency da aka yiwa kira na gaggawa yana barci. Haka wayan tayi ta ringing bai d'aga ba. Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Menene yake faruwa ne a gidan? Kardai ko barayi ne suka samu hanyar shigowa? Dum-dum k'irjinta ya sake wani irin bugu saida wata zufa ta karyo mata. Yanzu wa zata kira? Kii taji an buɗe k'ofar kaman an fito tana ji aka wuce wanda shine bata san inda akayi ba. Bakinta dake d'an rawa yana yin duk addu'ar data zo bakin ta d'an cije. Dole tayi jarumta taje taga waye ya shigo gidan har ya iya wuce maigadi kuma tasan tabbas Asad ya masa kashe kar wanda ya shigo saida izni. Hannu na rawa ta buɗe k'ofar a hankali rike da wayarta data sake kankamewa cikin k'irjinta. Kai ta d'an leko dashi a hankali tana duba corridor d'in taga babu kowa sannan ta sanyo jiki kaman wata ninja jikin bango tana bi. Koda tazo falo ma saida ta leko a hankali taga babu kowa ta wuce kitchen da bala'in gudu. Abun farko data fara cin karo dashi ta d'auka. Wato tabarya . Juyowar da zatayi taga mutum tsaye bakin k'ofar kitchen. Wani irin gigitaccin ihu Ajwa ta saka har fitsari na neman kwace mata tana k'ara rike tabaryar hannunta don ta zame mata makari. “Ajwa?” Tasan wannan muryar. Tsananin tsoro ne da ya hanata gane wake tsaye a gabanta, amma yanzu data fara dawowa cikin hayyacin ta fara gane surar dake gabanta da da take ganin sa dishi-dasshi. Ba kaman yanda ta sanshi ba ya d'an rame da ya kuma tara y'ar kasumba kad'an a fuska, haka gashin kansa yanzu ya taru har yafi na Asad tsayi kuma ya rinashi ya yi baki kaman na Asad. Yana sanye da bak'ar hoodie riga da bakin wando.Da tsananin mamaki take kallon sa kafin ta furta sunan sa kaman wacce ta kasa gasgata shine ko gizo yake mata “FAR'AAN? ” Far'aan da ya yi suman tsaye cikin tsananin mamaki da al'ajabin ganin yarinyar da zuciyar sa ta kasa samun sukuni gidan Asad. Kasa juriyar da ya yi yasa ya dawo don neman soyayyar ta da kuma neman gafarar ta ita da Asad, to amma me take gidan Asad da baya gari? . B'angaren Ajwa tayi tunanin zataji zafin ganinsa amma ko kad'an babu abunda taji saima ajiyar zuciya data sauke da mamaki tace “yaushe ka dawo Far'aan?” Saida ya d'an firgita sannan yace cikin rashin yarda da ganin Ajwa “shigowa ta kenan gari. What are you doing here?” Ido ta zuba masa tana tunanin baisan Asad aka d'aura auren dashi ba kenan bayan ya gudu?. Bata bashi amsa ba tace “bari na dafa maka wani abu.” Da ido Far'aan ya bita k'irjinsa na harbawa. Please baya son zargin sa ya zama gaskiya. Asad bazai tab'a yi masa haka ba. In har ba auren ta ya yi babu abunda zaisa ta zauna gidan Asad da daya ya gina ne don matar da zai aura. Jiki babu kuzari ya koma falon ya zauna k'irjinsa na tsananin bugawa. Bata jima ba ta fito da kula da jug. Gabansa ta ajiye ta wuce tayi d'aki don tana ganin babu dalili da zai sata zama falon. Tana shiga d'akin wanka ta fara shiga ta fito d'aure da alwala. Bata wani shafa mai ba saboda zafi da ake sanadin ruwa da ake tunanin za'ayi. Ga mamakin ta tana mik'a hannu zata d'auko kwalban turaren sai taji wushh ta wuce ta fadi k'asa kaman wanda iska ta ta harbata.Bata kawo komai ba saboda window data bari a bud'e ta sunkuya ta d'auka ta fesar turaren mai sanyin kamshi. Kwabarta ta nufa ta d'auka plain doguwar riga ta saka ta dawo ta shimfiɗa dadduma ta tada sallah magriba. Koda ta idar bata tashi ba ta zauna tana lazumi kafin ta rufe da tilawa. Saida akayi isha sannan ta rufe Qur'ani ta ajiye gefe ta mik'e tana ninke hijabin data cire. Can k'asan ranta take tunani ko taje taji ko Far'aan yana buk'atar wani abu saboda tun daz'u bata sake jin motsin sa ba. Tana k'ok'arin fita sai wayarta ya hau ringing ta matsa da sauri ta d'aga ganin sunan Asad. Bata sanda ta saki wani b'oyeyyen ajiyar zuciya ba zuciyar ta na dancing ta d'aga da y'ar siririya murya tayi sallama. Saida ya fesar da numfashi yace “Baby I miss you. Kin kirani ina emergency. I'm sorry ban d'aga ba ina fatan ba emergency ne yasa ki ka kirani ba daz'u ban d'auka ba?” Gaba d'aya sai taji wani irin quilt. Ashe gwanda da Allah yasa ma bai d'aga ba data d'aga masa hankali yana tsaka da ceton rayuwar wasu. Jinta take kaman wacce ke kan gajimare ashe. A d'an shagwabe da ita kanta bata san tayi ba tace “babu komai dama Far'aan ne ya dawo” Wani irin shiru Asad ya yi har tayi tunanin wayar ta tsinke zata cire a kunne taji yace da wata irin murya data kasa tantancewa “me ki ka ce?” Saida ta janye wayan ta kalle ta kafinnta kayar kunne .bata san me yasa amma sai zuciyar ta ke gaya mata kaman ranshi ya b'aci da jin maganan. To b'acin ran na menene? Kwana bawa Far'aan d'in baya nan suna neman sa ruwa a jallo, amma yaznu ya dawo kuma tanaji kaman ransa ya b'aci?. A hankali ta sake cewa “Far'aan ne ya dawo daz'u yana falo” Yanzu ma wani irin shiru Asad ya yi har wajen sakan biyu kafin taji yace da kyar da wata irin murya mai kaushi. “kai masa wayan Ajwa” ah lallai zargin ta ya tabbata tunda ya kirata da sunan ta ba Baby da yake kiranta dashi ba daga jiya zuwa yau. To b'acin ran na menene? Tana k'ok'arin miƙewa ta fice k'ofar toilet nata tayi wani irin k'ara Bamm kaman wacce aka bugota da mugun k'arfi . Zabura Ajwa tayi ta saki y'ar k'ara k'irjinta na bugawa da mugun k'arfi saboda tsoro. A firgice ta kalli k'ofa dake rufe sai kuma ta saki ajiyar zuciya. Lokaci guda yanayin muryar sa ta chanza da wani kulawa da damuwa yace “menene Baby? Meya faru?” D'an murmushi tayi jin canjin sa cikin d'an k'ank'anin lokaci. “babu komai. Toilet ne na manta ban rufe ba dana fito shine iska ta bugo k'ofar” Ajiyar zuciya ya sauke ta relief “ok be careful. Jeki kai masa wayan. Ajwa” “hmmm” D'an shiru ya yi kafin yace “kinsa Hijabi?” tambayar tashi ma taso ta bata dariya. Wato shida d'an uwansa ma bai yarda dashi ba kenan?. Zuciyar ta na furta kice masa aa kiga mai zaiyi amma saita tsinci harshenta na cewa “eh” Ajiyar zuciya taji ya sauke kafin ya sake cewa “Alright jeki kai masa wayan zan sake kira” D'an Murmushi tayi ta cire wayan daga kunne kafin ta juya ta d'auki hijabin ya data ninke. Tabbas da baiyi mata magana hijabin ba da haka zata fita. Inda ta barshi nan ta sameshi kwance kan doguwar kujera ya yi matashi da hannun kujerar ya rufa fuska da hannun d'aya. Babu alamun ya tab'a abincin data ajiye masa. Kafin ta k'araso wajen nasa wayanta ya sake k'ara a karo na biyu wanda yaja hankalin Far'aan ya d'an farka a firgice yana kallonta tana nufoshi da wayan fuskarta babu yabo babu fallasa. Ido kawai ya zuba mata zuciyar sa na harbawa. Yanzu daya sake ganinta ya sake yardar wa kansa masifaffen so yake mata. Da d'an murmushi kan leɓen ta mik'a masa wayan tana cewa “Asad ne yake son magana da kai” Kaman mara laka a jiki ya k'arbi wayan yana kallonta ta juya ta koma d'aki. Saida ta b'ace idansa ya sauke wata wawuyar ajiyar zuciya yana jin k'irjinsa ya masa wani mugun nauyi. Kiran ne ya katse wani ya sake shigo ya d'an ja numfashi ya fesar .harta wayan kamshin turarenta take. Saida ya taro jarumta sannan ya d'aga wayar don tsoron yiwa Asad d'in magana yake. Gaba d'ayan su shiru sukayi sai hucin numfashin da sukeji. Ohh how much Far'aan ya yi missing his blood and flesh. Sai shar ga hawaye sun biyo fuskarsa muryar sa na rawa yace “Hussein, I'm sorry. Don Allah kiyi hak'uri ka daina fushi dani haka” Duk yanda ran Asad ke b'ace saida zuciyarsa ta karye. Murya shima a d'an raunane yace “why ka aikata abunda ka aikata Far'aan? Kasan fushin da Dad da Mamee sukayi?. Kasan abunda ya faru bayan b'acewar ka?. Har akwai abunda zai dameka ka ki gayamin Hassan? Na d'auka duk duniyar nan baka da wani daya wuce ni da zaka gayawa damuwar ka?. Na d'auka ni ne d'aya barin ka Hassan amma ni kad'ai ne nake wannan tunanin tunda har zaka yanke hukunci baka gayamin komai ba” Yana kuka sosai kaman wani k'aramin yaro yace “duk abunda zaka fad'a ka gayamin na cancanci hakan. Laifina ne dana saka kayi wannan tunanin na cewa kai ba komai bane a wajena. Don Allah kayi hak'uri wlh sharrin shedan ne da kuma gushewar tunanin yasa na aikata abunda na aikata. Nayi alkwarin idan ka dawo zan gaya maka komai don magana ce mai tsayi bazai tab'a yiwuwa ta waya ba” “Alright stop crying. Kaje wajen Dad?” “Aa” Yace a hankali yana share hawaye duk sukayi shiru. Can k'asan ransa yana tsoron tambayar da ya riga da yasan amsarta amma duk da haka yace kaman mai tsoron amsan da za'a bashi. “uhmm. Ajwa me take yi a nan?” Shiru Asad ya yi kaman mai tunanin abunda zaice kafin ya fidda numfashin ya kira sunan Far'aan. “Hassan, hukuncin daka yanke ya canza abubuwa da dama ciki harda auren Ajwa dani. She's my wife now Far'aan. Sanda ka gudu Dad saboda b'acin rai yasa aka d'aura auren dani. It a very long story wanda dole sai mun zauna. Yanzu you should go and see Dad ka nemi yafiyar sa ka kuma kunna wayan ka zan kira later” Da sauri Asad ya kashe wayan don sai yaje ji kaman bai kyautawa Far'aan d'in ba. To amma rashin kyautawar menene tunda shi Far'aan d'in ko a da can bawai sonta yake ba yana son kauda kwad'ayin sane kawai kanta. Gaba d'aya zuciyar sa tayi shattering ta tabbacin zargin sa da Asad ya gasgata. Wau Dad zai yanke wannan hukuncin saboda ya yi laifi? Shima Asad d'in ai ya sgaya masa zai dawo ya aureta saboda me ya amince da hukuncin da Dad ya yanke. Duk sukayi betraying nashi. Bai tab'a son abu rayuwar sa ba da kuma son ganin ya mallakashi kaman Ajwa. Hawayen dake fuskarsa sosai suka k'ara yawa yana jin zuciyar sa na mada wani irin ciwo. Saboda soyayyar Ajwa ya daina huld'a da mata. Duk wasu dabi'u da aka sanshi dasu marasa kyau ya daina saboda yana so ya dawo mata da kyakkyawar niya. Yana so yazo mata a matsayin mutum na kwarai amma sai gashi Dad ya wargaza masa wanna burin. Anya kuwa yanda yake jin Ajwa zai iya hak'ura da ita?. Kaman wanda aka tsikara ya miƙe da sauri ya nufi corridor. K'ofar daya fara tsayawa dazu saboda bashi da shamaki da gidan nan ya tsaya nan zuciyar sa ta bashi shine dakin Ajwa saboda daz'u yaji alamun an kulleta, sai dai ya kasa buga k'ofar ya sake damke wayar a hannunsa. Wani irin kuka ne yazo masa ya matsa ya jingina da bango ya durkushe a gurin ya had'a kai da gwiwa. Anya zai iya hak'ura da Ajwa ya barwa Asad?. Ta k'asan k'ofa ya tura mata wayan ya matsa can gefe dafe da zuciyar sa da yake jin tana barazanar tarwatsewa. Ajwa dake k'ok'arin kwanciya don har ta haye gado ta hango wayarta ta k'arshin k'ofa. Bata motsa ba saida ya gama turo wayan ta tabbatar ya matsa daga wajen sannan ta sauka ta d'auko wayan ta koma kan gado. Addu'a ta fara tana shafawa wayan ya sake k'ara ta d'an yi murmushi ta d'aga da muryar barci tace “Hello” Yanda muryar nata ya ratsa dodon kunnen sa saida tsigar jikinsa ta tashi. Ya wani lumshe ido yana fesar da hucin numfashi. “kin kwanta?” “uhmm” D'an cije leɓen sa ya yi. Sam bata san yanayi data jefashi ba da yanda take amsa masa. “kina ji Ajwa. Nasan Far'aan is my brother amma idan zamansa ya takura ki a gidan ki gaya masa ya tafi kinji. Kar kice wai don d'an uwanane shi. Tell him to leave.And please idan zaki fita ki dinga saka hijabi a jikinki kinji?” Saida ta kwanta tana murmushi da ita kanta bata san na menene ba can k'asan ranta da wata y'ar murya tace “tohm” ji tayi yaja wani irin shakekken numfashi ya fesar murya so husky yace “are you testing my patience?” Dariya ce ta kusa kwace mata tayi saurin shanyewa ta d'an turo baki tace “Me kuma nayi yanzu?” “Ajwa. Kinsan abunda ki ke fa ki ke playing dumb. Tunda haka ne nima bari na gaya miki halin dana shiga. I want to f#ck you so bad.....” “aaaaahhhhhh” Bata bari ya k'arasa ba ta saki ihu mai had'e da dariya ta kashe wayar da sauri ta cusa kai cikin fillow duk kunyar duniya ya isheta. Lallai ta yarda maza basu da kunya. Nashi b'angaren murmushi ya yi yana gyara doguwar rigar dake jikinsa ta barci ash ya miƙe daga kwancen da yake . Rigar mai madauri ce da dogon wando duk k'irjin sa a waje. Fitowa ya yi don had'awa kansa coffee saboda safiya ce. Yana tafe ya kama mad'aurin rigar ya d'aure ta gefe sai dai kafin ya shiga kitchen d'in doorbell nashi ya yi k'ara. Dan tsaki yaja don har yanzu hankali sa bai kwanta da saukan Far'aan gidan ba sa. Tunanin ajiye aikin ma ya ke ya koma a yau d'in nan ko gobe. Yasan waye Far'aan da mata musamman ma kasancewar sa cikin gidansa tare da matar su kad'ai. Yana buɗe k'ofar saida ya yi dana sanin buɗewa saboda Aya dake tsaye wujiga-wujiga da kayanta duk a yage fuskarta gefen bakinta duk ya kumbura. Tana ganin ya bud'e ta sake rushewa da wani irin gurgushen kuka tace “Asad don Allah ka taimake ni. Wasu ne suka biyo ni zasuyi raping d'ina ” Bai yarda da maganan ta ba saida ya hango inuwar maza sun fice daga compound d'in a guje saboda ruwa da ake tsugawa baka gani da kyau. To uban menene ma ya kawota gidan sa? Ya akayi tasan inda yake?. Yanayin daya ganta ne yasa bazai iya barinta ra fita titi ba kusan tsirara. Wani irin frustrated numfashi ya sauke ya matsa mata yaba kallon fuska a murtuke yace “get in” ai a guje ta rab'a shi ta shige ya bita da mugun kallo. Wai menene yake faruwa da rayuwar sane kwana biyu? Me yasa lokaci da komai yake tafiya perfectly suke k'ok'arin dawowa cikin rayuwar sa shida Ajwa. Ita nan ta hanashi sakat can yauma ga dawowar Far'aan? What is happening? ──────────────────────── Zan ciya cewa barcin da take mai tsananin nauyi yasa bataji sanda aka fisge bargon data yi rufa dashi ba can gefe. Lokaci d'aya itama y'ar fitilar data haske dakin ta d'auke dif d'akin ya gauraye da wani uban duhu. Kaman a mafarki taji an fisgi yatsan k'afarta ta farka a d'an firgice tana salati. Mamaki ne ya kamata sosai ganinta cikin uban duhu ita data san ta bar side lampa kunne. Hannu takai tana laluben wayar ta jita da kyar ta jita can k'arshen gado. Da azama ta fara k'ok'arin kunna torch babu zato taji saitin kunnenta na hagon anyi tafi abu ya wuce wushh kaman iska. Bata san sanda tayi wani uban wancakali da wayar ta saki wata gigitacciyar k'ara ta dire daga gadon a guje zatayi waje kafin ta kai k'ofar an bud'eta ta waje d'an hasken corridor ya shigo d'akin. Tsananin gigicewa da tayi sai idanta ke nuna mata Asad don haka ta nufeshi a guje tana kira. 😨wannan shi ake kira chakwakwiya mai zafi. Ana wata ga wata inji y'an caca. To ni kam yau kaina ya kulle na rasa ma ina yafi zafi. Anya Aya bada wata manufa taje gidan Asad ba? 𝗧𝗔𝗨𝗥𝗔 𝗕𝗜𝗬𝗨 ®𝐀𝐬𝐡𝐚𝐧𝐭𝐲𝐥𝐮𝐯 /No edit! 'Come and join exclusive already an fara payments free page's are done! 'Join exclusive @500 to 8140754777, Aisha Sani Hassan. Opay. 【Pg33&34】 LAST FREE PG! Kujera ya nuna mata fuska babu walwala ta zauna a d'an rabe tana k'ara chukwikiye gaban rigarta daya yage har bra d'in ta kana hangowa. Harshe ya d'an taune ya wuce kitchen ya zuba mata d'an tea da ragowar cookies daya shigo dasu jiya ya ajiye mata kan table. D'agowa tayi da d'an yake fuskarta da har yanzu hawaye yake gudu tace can k'asan mokashi “Nagode” Baice komai ba ya wuce d'aki zuciyar sa na zafi abincin ma yaji ya fice masa a rai. Wanka kawai ya shige yana tunanin hanyar da zaibi ya raba Aya da rayuwar sa. Can b'angaren Aya tana ganin wucewar sa ta saki wani mugun murmushi ta koma ta sake bararrajewa kan kujera. Tarkonta ya kusa kamawa sauran kiris. Wayarta ne ya hau ringing ta fito da wayan da sauri daga cikin y'ar Jakarta tana kallon hanyar da Asad d'in yabi. Da alama kiran take jira don ko duna number wanda ya kira batayi ta d'aga da sauri. “ya ya an samu nasara?” “Aya aiki ya b'aci, walahi an ganni ina k'ok'arin bunne Karen nan kinga yanzu haka ma gudun tseratar da rayuwa ta nake” A zabure Aya ta miƙe k'irjinta na harbawa da mugun k'arfi. Innalillahi wa Innalillahi raji'un. Akwai matsala idan aikin nan baici ba. Yanda numfashin wacce suke wayar da ita ke fitowa ta cikin wayan zai tabbatar maka da abunda take fad'a kuma ba k'aramin gudu take. K'asa da murya Aya ta sake yi taba rawa tace “na shiga uku Emeka idan aikin nan baiyi ba ina cikin matsala fa. ” “aahhhhh, ina yaran da ki ka biya su miki duka kaman sunyi raping naki? Su aikin ya yi Asad d'in ya yarda ” A zafafe Aya tace “wane aiki ina gaya miki ina cikin matsala idan ba'a binne karan nan ba. Duk abunda zancewa Asad bazai yarda dani ba” Ihun Emeka ne ya

Chapter 14 of 15