gama sauraran tilon d’an nata, a hankali ta janyo shi jikinta ta rungume, ta fara hawaye, cikin karyewar zuciya tace
“I’m soo sorry son, ba zan iya taimakonka akan wannan al’amarin ba!.”
Murmushi yayi wanda yafi kuka da ihu ciwo
a hankali ya zaro ta ajikinshi kafin yace
“I know, kawai ki tayani addua, thats all I need maybe zan samu sauk’in rad’ad’in da nake ji, please Mommy.”
Wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauk’e
kafin yace
“Maybe i’m not destined to be happy, a duniyar nan!! Haka Allah yake son ganina, if not
why?
Tayaya zan kasa cire......”
Da sauri ta sa hannu ta toshe mishi baki, tausayinshi yana sake shigar mata zuciya…
Ahankali yasa hannu ya zare hannun nata sannan yace
“Pls Mommy ku barni In tafi, dan Allah.”
Tana shirin bashi amsa, Dad ya shigo..
Kallonsu yayi kamar zai yi magana sai kuma yayi shiru ya juya kawai, yace
“Ku zo duk ku biyun gidan Granpa, yana son ganinmu, an dawo da su Adama!”
Yana gama fad’in haka ya juya ya fice........
Sanye take cikin bridal gown, peach colour anyi kwalliya da white stones masu shek’i da d’aukar ido a gabad’aya k’irjin
da kuma half d’in k’asan rigar ta tsaye har ta bayan side d’in inda yake flowing….
Ta d’aura jewelry’s white,
yayinda takalmi, tauban, mayafi da head d’inta suka kasance peach….
Fuskarta ta sha casual makeup simple!
Dan cewa tayi itama ayi mata casual d’in inyaso ranar wuni, traditional day d’in da Shuwa
da su Mama za suyi
sai ayi mata bridal d’in.
Tayi masifar yin kyau kuwa
gashi kwalliyarta ta tafi da shigarta matuk’a.
Bridesmaid d’inta su 10 har da Sakina 11, Khadijah bata zo yau ba tace sai gobe zata fara zuwa saboda tana laulayi kuma jikin ya d’an motsa.
Kusan duk Sakina ce ta gayyatosu (bridesmaids d’in)
Y’an makarantar su ntic
kuma aka ci sa’a suka karb’i gayyatar aka shirya anko da su kasancewar ta fad’a musu da wuri…
White gown ne a jikinsu,
sai peach head, takalmi da jewelry’s sai vails d’insu white..
D’inkin su iri d’aya sak dan
saboda ma gudun samun mishkila dama tailor d’aya ne yayi d’inkunan ( bama anan ba )
Makeup d’insu komai iri d’aya.
Tana tsaye Sakina tana yafa mata mayafi Mama ta shigo,
suna had’a ido kawai suka fara hawaye a tare!
Sakina wadda itama taji idonta ya cicciko ne tace “Mama dan Allah ku daina” sai kuma ta fara kuka itama, ahaka Ummu ta shigo ta samesu, itama tana ganinsu ta hau kuka.
Da kyar friends d’insu suka lalllashesu aka d’an yi musu hotuna suka yi abunda ya kawosu, suka juya suka fita.
Sai da aka sake gyarawa Hudan da Sakina makeup d’in su
Allah yaso mai makeup d’in bata riga ta tafi ba.
Ana gamawa, mai makeup d’in ta fara had’a kayanta, tana shirin tafiya kiran Auwal ya shigo wayar Sakina.
Taso tayi ignoring amman kawai sai fa daure ta d’auka, albarkacin biki dan
ta lura yafi kowa zak’ewa, so dole ta san sai ta had’u da shi one way or the other sannan
ta lura da yanda shi kuma Ya Arshaad ya sakar mishi komai , it’s like ya ma manta da abunda yayi mishi akan Jalila..
a k’asan ranta kuma sai tace
“Ko da yake ba’a shiga tsakanin y’an uwa dama m, blood is thick!”
Da wannan tunanin ta d’auka wayar ta kara a kunnenta
tace
“Assalam akaikom”
Yana zaune cikin motar shi,
a Ahankali ya lumshe idanunta da jin muryarta!
Sai da ta cire ran za ayi magana tukun taji a hankali taji yace
“Sakeena..”
Da sauri cikin fad’a fad’a tace
“Menene!!?”
Dan jikinta ya fara yi mata abunda yake mata a duk lokacin da suke tare wanda
ta tsana fiye da tunani..
Murmushi yayi kafin yace
“Mun iso,
ku fito mu wuce, ko?”
Bata bashi amsa ba ta kashe wayar….
After kamar 10 minutes haka suka fara fitowa..
Tunda suka fara fitowa camera man da mai video coverage suke d’auka.
Sakina da k’anwar Ashraff saurayin Sakina da Hudan ne suka fito a k’arshe.
Motocine a jere tun daga farkon layin har zuwa k’arshe!
Gaba daya irin su d’aya bak’ak’en benz!
Sai ta tsakiya da aka d’ora wata y’ar k’aramar peach flower a gaban glass d’in
ce kawai ba bak’a ba instead ita fara ce ta sha tint!
Amman itama k’irar ragowar motocin ce kawai kalar ne ya bambanta, kana gani ka san itace ta Amarya da Ango
dan haka su Sakina suka ruk’ota suka nufi motar da ita.
Suna zuwa bakin motar Arshaad yasa hannu ya bud’e seat d’in baya inda yake zaune ta gefe…
Wata zazzafar suite ce a jikinshi white, hatta neck tie d’in shi white ne da takalmi,
sai wani d’an kyalle da ya d’an d’aura a jikin aljihunshi na suite d’in nasa d’an mitsitsi peach.....
Lokacin da yace mata kar su damu ya gama order da had’a komai kayan da za ayi using, aranta ta gama aiyyanawa ‘ba wani kyau za suyi ba’ dan tayi tunanin maza ba su iya zab’e ba amman yau kam ta tabbatar Ya Arshaad k’arshe ne wajen zab’a, had’a kaya da colours.
Murmushi Sakina tayi
kafin tace
“Ango irin wannan kyau haka?”
Dariya ya d’anyi
sannan yace
“Ai ban kaiki ba.
K’anwar Amarya”
Yana mata magana idanunshi na kan Hudan!
Da kyar ma ya amsa gaisuwarta ita da k’awarta.
Lura da Sakina tayi hankalinshi baya kansu yasa ta saka mishi Hudan a motar ta rufe a ranta tace
“Gata nan ai sai ka cinyeta da kallo”
Tana d’an murmushi.
Ba dan hancinta ya jiyo mata k’amshin turaren Auwal ba da ba abunda zai hanata afkawa kanshi In ta tashi juyowa
domin barin wajen.
A hankali ta d’an juyo jin k’amshi da mutum a bayanta daff!
Suna had’a ido kuwa ta zabga masa wata uwar harara..
A wajen k’anwar Ashraff kawai ya samu gaisuwa, bai
damu ba ya amsa ta kafin ya juya ga Sakina yace
“Kin yi kyau over!”
Yad’an yi mata alamar perfect da hannunshi yana murmushi..
White suite ce shima a jikinshi da d’an ratsin black, yayi masifar yin kyau
sai dai askin sa da yayi yau d’in ne ya b’ata mata rai.
Hannu yasa ya bud’e gaban motar, kafin yace “Bismillah” yana kallonta still da murmushi akan kyakkyawar fuskarshi.
A hankali ta d’auke idanunta daga kanshi, daman tun d’azu da ta sunkuya suna magana da Arshaad ta ganshi zaune a mazaunin driver!
A tunaninshi zata yarda ta zauna kusa dashi kenan, tab!
Ai ko hauka take ba zata yarda ta zauna kusa da shi ba
ita da take k’ok’arin ganin ta kauce mishi ta kowacce hanya,
besides Ashraff ma yana jiranta tare za su tafi..’
Da wannan tunanin ta kamo hannun k’anwar Ashraff ta saka ta a cikin gaban motar ta rufe, ta yi gaba abunta.
Guiwa a sace Auwal ya bita da kallo har ta isa inda motar Ashraff d’in take a chan gefe bama a cikin convoy d’in nasu ba, ta shiga.
Da kyar ya iya dedeta kanshi ya juya yaje ya shiga ya kunna motar
dan har an fara yin gaba...
Suna isa inda za ayi event d’in
ya bud’e motar shi ya fito.
Sai hotuna ake d’auka amman shi bai damu ba, neman ta kawai yake yi..
Ganin ba ita ba dalilin ta yasa ya zaro waya ya hau kiranta!
Kowacce mota ta k’araso, har ta masu d’aukar hoto amman tasu bata iso ba..
Arshaad ne ya d’an kira sunan shi dan haka ya juya,
da hannu Arshaad d’in ya yafito shi, yana zuwa yace “Ana ta hoto babu kai, me kake nema?”
D’an murmushi kawai yayi ya tsaya aka yi musu, daga nan
aka fara k’ok’arin shiga hall d’in.
K’awayen Amarya, a baya Abokan Ango a gaba
Auwal da Jamil su ne daf da Ango da Amarya dan sune suka saka suit kamar Angon
ragowar mazan kowa kayan shi ya saka.
Shi dai Auwal har aka shiga bashi da nutsuwa dan haka Amarya tana zama ya juya ya fita yana mai
cewa Jamil yayi jawabin da da shine zai yi, yana da uzuri.
Arshaad bai yi mamakin rashin ganin Aaima da Aslam a wajen ba! Amman tabbas ranshi ya sosu, baya son b’ata wannan ranar ta musannan dan haka ya kawai sai ya basar ya ci
gaba da huld’ar gabanshi.
Tsarin wajen ba k’aramin had’uwa yayi ba
Tebur da kujeru uku a zagaye wajen guda ashirin!
Sai chan wajen sit d’in Amarya da Ango gefen dama da hagun su kuma akwai kujeru goma goma da dogon tebur
a lamun nan ne wajen zaman best friends dan har ma sunje sun zazzauna matan masu anko mazan kuma waenda suka zo tare.
Kwata kwata friends d’insu da suka tarar a wajen ba sufi ashirin ba!
Cool music ke tashi ba wani hayaniya..
Cocktail ne da cake da sweet da hot chocolate da kuma menu mai d’auke da abubuwa daban daban akan tebur d’in, sai waiters a gefen tebles d’in a tsattsaye su wajen 30 da uniform, duk
abinda kake buk’ata sai ka kira ka gaya musu a menu d’in aje a kawo maka
In ka gama su d’auke.
After kamar 20 minutes da fitar Auwal, motar su Sakina ta shigo wajen..
Ranshi a mugun b’ace ya k’arasa inda motar take!
Bai yi wata wata ba yasa hannu ya bud’e side d’inta ya kamo hannunta ya fito da ita.
Da kyar ta iya tsayawa ta gyara mayafinta wanda yake k’ok’arin zamewa…
Ko lura da guy d’in da ya fito shima ya zagayo inda suke Auwal d’in bai yi ba ya fara magana
“Ina kuka tsaya??
Kin san mintunku nawa kuwa?
Almost 30 minutes kowa ya k’araso banda ku, Ina kuka biya haka?”
Ya k’arashe maganar cikin tsananin b’acin rai, kamar wani ubanta…
Kallon shi take yi kawai.
Sai da ta barshi ya kai aya tukun ta fara k’ok’arin wuceshi ba tare da tace uffan ba!.
Tafarfasar da zuciyarshi keyi ba kad’an bane dan
haka cikin zafin nama ya sake sa hannu ya fincikota ya dawo da ita unintentionally ta bugu da jikin motar.
Da sauri Ashraff ya k’araso inda suke ya juyo da shi ya cukumi wuyan rigar shi!
Cikin tsananin b’acin rai yace
“Meye ne matsalar ka?
Who the hell are you?
A iya sani na bata da yaya!
Ka fito kawai ka fara yiwa mutane hauka..
Ka godewa Allah ni ba mahaukaci bane Irin ka dan wallahi da sai na gyara maka zama a wajen nan!”
Ya k’arashe maganar yana sakin mishi kwala da k’arfi.
Auwal ya taso kenan yana shirin yin magana a zafafe
Idanuwansa suka sauk’a kan Sakina wadda ta fara hawaye.
A take yaji duk jikinshi yayi sanyi…
Tun lokacin da ya tura ta jikin mota har yanzu bata motsa ba tana a yanda take sai dai
hawayen da ita kanta ta rasa na menene waenda suke zuba
akan k’uncinta.
Kamar an tsoma shi a ruwan sanyi haka yaji, ya kasa motsawa zuciyarsa na dukan uku uku, gashi tak’i yarda ta kalli inda yake.
A hankali Ashraff ya k’arasa inda take ya fara yi mata maganar da Auwal d’in baya jin me yake cewa.
Goge hawayenta tayi ta gyara tsayuwarta.
Sannan Ashraff d’in ya bud’e bayan motar ya d’auko k’aton cake d’in da suka tsaya karb’a.
Daganan suka zo suka wuce shi ba tare da sun ce mishi komai ba!.
Sam ya kasa motsi ya kasa yin komai.
Kawai iya hawayen da ya gani daga idonta ne ya kashe mishi guiwa ya sanyaya mishi jiki.
Yafi 10 minutes a wajen
kafin da kyar ya samu ya wuce ciki, yana zuwa ya nemi waje ya zauna..
Ba abunda ya iya ci a wajen yana nan zaune a wajen shi kad’ai amman dukkannin hankalinshi na a kan Sakina wadda itama ya lura bata da sukuni ga Ashraff a gefenta wanda yake ji kamar yaje ya rufe da duka, sai wani shishshige mata yake yi.
Su y’an matan wajen a tunanin su tsabar kyau da had’uwar sa ne yasa yake shan k’amshi yak’i shiga mutane
basu san shi kuwa zuciyarshi ce take shirin tarwatsewa ba!
Gashi ank’i a tashi daga wajen.......
Sai after kamar 2 hours tukunna aka ce Amarya da Ango su yanka cake!
Bayan sun yanka Huda na k’ok’arin durk’usawa ta bashi yayi saurin tarota ya karb’a shi ya durk’usa ya bata!
Ai kuwa aka hau tafi ana ta videos da pictures.
Daga nan masu bada gifts suka bada aka yi addua aka tashi a lokacin already Auwal ya dad’e da komawa cikin mota su kawai yake jira.
Suna fitowa kowa ya fara kama gabanshi….
Bai yi tunanin Sakina zata shigo motar ba!
Dan haka ya fara k’ok’arin tada motar bayan su Hudan sun shigo
Arshaad ne yace
“Wait Auwal, bara mu d’an jira Sakina”
Yana juyawa yaga sun yi sallama da k’awarta da wanda ya gansu tare sun tafi..
Sai da taga wucewarsu, tukunna ta zo ta shiga a lokacin ita kad’ai ce ma ta rage a harabar wajen.
Har suka isa gidan su Mama bai ko kalli inda take ba
Motar shiruuu sai hirar su Arshaad da suke yi k’asa k’asa ba wanda yake jin me suke cewa..
Sallama Sakina tayi da Arshaad
Hudan kuma ta cewa Auwal sun gode, daga nan
Arshaad ya dawo gaba su kuma suka wuce cikin gida.......
Dad, Mommy, Gramma, Aslam Arshaad sai Aaima
kawai Granpa ya buk’aci gani tunda a ganinshi ya riga ya cire Dad da Abba da su Hudan acikin zuriarshi…..
Mammy da Mom kawai suka tarar a parlourn dan Ummi kusan a sume ma aka kawota, shiyasa Granpa ya kira Doc akai d’akin Gramma ma da ita domin bata taimakon gaggawa.
Aaima tana shigowa da suka had’a ido da Mammy sai tayi
kanta ta gudu ta rungume kawai tasa kuka.
A hankali Aslam yaje ya gaida Granpa tukunna ya dawo wajensu ya gaidasu yana mai shafa kan Aaima alamun lallashi, haka itama Mommy bayan ta je ta gaida Granpa d’in ta dawo wajensu….
Gaba d’aya hankalinsu yana ga Aaima, wani abun mamaki kwata kwata basu lura da
Mommy ba har sai da muryarta ta yiwa dodon kunnuwansu dirar mikiya!
A firgice duk su biyun suka d’ago suna kallon ta!
Itanma su d’in take kallo da murmushi akan fuskarta
especially ma Mammy wadda
bakinta yake rawa ta kasa furta uffan!
Mom na shirin yin magana Granpa yayi gyaran murya.
Duk nutsuwa suka yi suka maida hankalin su a kanshi bayan sun d’an gyaygyara zama..
Kallonsu yayi d’aya bayan d’aya, kafin yace
“Ina Muhammad?”
A hankali cikin girmamawa Aslam yace
“Yana wajen event d’insu an fara yau”
Da mamaki Mom da Mammy suka kalleshi, suna shirin yin magana suka ji Aslam d’in ya sake cewa
“Ni da Aaima ma da yanzu zamu wuce
to kuma sai kiranka ya riskemu”.
“Call him! Kace ya bar duk abunda yake ya zo yanzun nan!”
Cewar Granpa.
A hankali Aslam yace
“Granpa plss..”
Cikin d’an fad’a fad’a abunda bai tab’a yi mishi ba yace
“Call him now!!”
Ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace
“Ok, Granpa.”
Sannan ya zaro wayar shi ya hau kiran Arshaad…
Har ta tsinke ba a d’auka ba, ya sake kira nan ma ba a d’auka ba, zai kira a karo na uku Granpa ya d’aga mishi hannu, yace
“Leave him”
Daga nan ya fara magana
“2 months ago!
Adama, Rukayya da Zainab
Sun yi wa wannan family d’in babban laifi wanda hakan ya kai ni ga yanke hukunci a garesu mai tsauri!
Dalilin tara ku a nan da nayi shine
Inaso In jaa muku kunne akan
‘magana ta riga ta wuce!’.
Mazajen su Adama da ita Ummi basa kusa
dan haka kai Yahaya kai ne zaka sanar da sak’ona garesu!
Banaso ko da wasa inji makamanciyar maganar nan ta sake tasowa!
Sun yi laifi an hukuntasu magana ta mutu!!
Duk kuma wanda ya k’etare umarnina ko a fuska ya nuna musu wani abun yi zai
gamu da fushina tabbas.
Su Yusuf kar suga wai basa tare da ni, muddin suka yi wani abun da bai kamata ba a matayensu to tabbas zan yanke musu hukunci mai tsanani!
Ka gaya musu hakan.
Ku kuma”
Ya juya kan su Mammy
“Wannan hukuncin da na yanke muku kuka yi going through for the past 2 months ba komai bane!
Ku k’irga azabar sau ashirin
tou tabbas ita zaku fuskanta muddin kuka bari naji wata matsala daga gareku.
Sai magana ta biyu!
Duk da Muhammad ya b’ata min rai a yanzu, hakan ba zai
saka In chanja abunda na shirya ba…
A kwanaki yayi laifi
wanda ya kai ni ga rage mishi matsayi
Auwal ma haka.
Tou yanzu Alhamdulillah naga progress da ci gaba a tare da su, dan haka ranar Monday
Auwal ba dan halin ubansa ba sai dan kwazon shi zai koma
assistant md
tunda Aslam ne md yanzu
shi kuma Muhammad ya koma matsayinshi, treasurer.
In shaa Allah
Nan da shekara d’aya za a fidda wanda ya chanchanci a malllakawa MT gaba d’aya na uk da na Abuja da na nan Kano, a tsakanin su uku.
Yahaya In Zainab ta warke ka mik’a ta gidan Mijinta inda ya k’aura ya koma, amman yanzu ka fara kai Adama tukunna ta samu ta huta, Mammy kema ki wuce d’akinki.
Allah ya bamu alheri.”
Yana gama fad’in haka ya mik’e, ya shige d’akin shi.
Shiruu, d’akin ya d’auka.
Da kyar Mammmy ta iya mik’ewa dan jikinta ba energy
ta isa inda Mommy take tana zuwa kawai ta fad’a jikinta ta fashe da kuka tana cewa
“Alhamdulillah!!
Na ji dad’in ganinki a haka y’ar uwa ta, Alhamdulillah Alhamdulillah”
Mom ita ma rarrafawa
tayi inda suke, ba yabo ba fallasa ta d’an rungume Mommy kafin tace
“Alhamdulillah,
Allah ya k’ara mike lafiya”
Ba wadda Dad ya k’urawa ido irin Mammy!
A hankali yace musu “ku taso mu tafi”
kawai, ya mike.
Aaima ce taje ta kansu ta tayasu mik’ewa, dan ko kuzarin kirki babu a jikinsu!
Duk sun yi bak’i sun rame sun kod’e sun k’anjame!
Banda kuka ba abunda take yi.
Aslam tare suka tafi da Mommy kamar yanda suka zo tare.
Dad kuwa sai da ya fara kai Mammy gida ita da Aaima
tukunna ya wuce da Mom dan kaita sabon gidan da su Abba suka koma.
Side d’in Daddy ya shiga tana biye da shi a baya..
A zaune suka samu Daddyn a parlourn k’asa yana shan coffee da suit d’inshi a jikinshi ko takalmi bai cire ba da alama yanzu ma ya dawo daga aiki
dan ga suitcase d’inshi a gefe.
Sallamar Dad ce ta jawo hankalinshi gare su, mik’ewa
yayi yana d’an murmushi da muryarshi dake nuni da a matuk’ar gajiye yake yace
“Yaya ina wuni, ai da ka kirani na zo..”
Muryarshi ce ta mak’ale sakamokon ganin Mom wadda ta fito yanzu daga bayan Yayan nashi.
A hankali ya sauk’e ajiyar zuciya, yana kallanta..
Rabonshi da ita wata d’aya kenan, tun last zuwanshi da yaje tayi ta kuka ya yanke shawarar sai dai ya kira police d’in ya had’asu dan ba zai iya jurar ganinta a wannan halin ba!…
Muryarta ce ta dawo dashi daga duniyar tunanin da ya tafi, a hankali yaji tace
“Ina wuni”
Jinjina kai yayi kafin a hankali yace
“Alhamdulillah”
Sannan ya koma ya zauna ya shiga gaida Dad wanda ya nemi waje shima ya zauna.
A k’asa kan kafet Mom ta zauna tana ta sun sunkui da kai!
Tausayinta fal zuciyar Mijinta
dan ya hango tsantsar nadama da shiryuwa a matar tashi, daman chan shi ya san sharrin shaid’an ne!
Ba abunda yafi d’aga mishi hankali irin bak’i da lalacewar da tayi, in shaa Allah nan da 3 days zai shirya musu fita suje ayi mata checkup…..
Muryar Dad ce ta katseshi
jin yana cewa
“Abba ya dawo kuwa??
Inason ganinku ne tare.”
“Eh to i don’t think so but bara in kirashi”
Daddyn ya fad’a yana mai zaro wayarshi daga aljihun wandonsa.........
Da kyar ya iya kai wa 2 yau a waje, duk da tarin aiyukan da suke a kanshi haka nan ya baro su birjiki! Ya dawo gida.
Yana d’aki shi kad’ai sallah kawai yake iya fita yayi…
Anya bai yi gaggawar aurar da Hudan ba kuwa?
Kar yaje garin gudun b’atawa su Yaya da Daddy rai ya cuci kanshi fa!
He just knew her
amman har ya d’auketa d’ungum ya bama wani
kuma bama a Kano kusa da shi da anytime yaso zai je ya ganta za su zauna ba!
A Uk za su zauna, sai
after 4 ko ma 5 years tukunna za su dawo!.
Da k’arfi ya sauk’e ajiyar zuciya
A ranshi ya raya zai nemi Alfarmar Arshaad akan su d’an zauna anan gidanshi for some time, ko da ace duniya za tayi mishi kallon the most selfish father ne!!
Tsaki ya jaa tunawa da yayi Arshaad d’in har ya biya mak’udan kud’i na course d’inshi da zai yi da kuma karatun da Hudan zata fara…
Yana wannan tunanin yaji kira ya shigo wayarshi..
D’auka yayi ba tare da ya kalla sunan ba ya amsa ya kara a kunnenshi, sai da Daddy yace
“Abba”
Tukun ya fahimci wanene
dan haka ya gyara zama yace
“Ina wuni, ya aiki?”
Amsawa Daddy yayi daganan yace masa “yazo ya samesu ga Dad ya zo yana son ganinsu”.
“Ok” kawai yace,
sannan ya kashe wayar ya mik’e ya fice jikinshi duk a sanyaye.
Ko mintuna hud’u cikakku bai rufa ba, ya k’arasa parlourn.
Waje ya nema ya zauna
suka sake gaisawa..
Ba tare da b’ata lokaci ba, Dad ya fad’a musu sak’on Granpa!
Shi ababa wallahi har k’asan zuciyarshi yama manta da wata halitta wai ita Ummi!
A hankali ya sauk’e ajiyar zuciya, ya koma ya kwantar da kanshi a jikin saman kujerar
ba tare da yace da su komai ba!
Dan in ya cewa Dad zai iya yin abunda Granpa yace a yanzu dai tou gaskiya k’arya yake yi,
sai dai maybe ko in gaba.
Mom ce ta katse mishi tunanin shi ta hanyar cewa
“Abba Ina mai baka hak’uri game da kuskuren da muka aikata maka!
Bisa ga biyewa son zuciyoyinmu, ka yafe mana dan Allah.”
Shi sai a lokacin ma ya gane ita ce a wajen.
Mik’ewa kawai yayi ya cewa su Dad
“Bara inje in sha magani In d’an kwanta kaina yana min ciwo, sai da safe.”
Daga nan kawai ya nufi hanyar fita….
.....inda ace Mom ta san tunzurashi d’in da maganar ta tayi, da ba zata soma ba!
Kawai wani sabon haushin su ne ya sake lullub’e shi..
Hudan is soppose to get married at this age duk wani uba zai so hakan
amman dalilin su ya sanya har yake having second thoughts akan abunda ya san shine farin cikin ta, yakamata ace yana taya ta murna yana sopporting d’inta d’ari bisa d’ari amman because of them gashi har yana son aikata abunda za aganshi kamar selfish,
kuma ya san inba da kyar ba, su Yaya za su iya jin haushin sa wanda hakan abunda bai tab’a
faruwaba ne…
Daddy yana shirin yin magana da sauri Dad ya dakatar dashi ta hanyar d’aga mishi hannu!
Har Abba ya fice ba wanda yace komai.
Yana fita shima Dad d’in ya mik’e yayi musu sallama ya fice.
Mik’ewa Daddy yayi daga inda yake ya koma k’asa wajen Mom. Tun kafin yace wani abun ta fad’a jikinshi ta fashe da kuka tana rok’on shi akan “yayi hak’uri shi da y’an uwanshi, in shaa Allah ba zata sake ba! Sharrin shaid’an ne
dan Allah kar ya dinga kallonta da abun ya taimaka mata ya goge komai a ranshi…”
Lallashinta ya shiga yi yayi hugging d’inta yana jin tausayin ta na sake shiga zuciyarshi..
Da kyar ya samu tayi shiru daganan yace “tazo taje tayi wanka ta huta”
Dan da gani tana buk’atar ta tsaftace jikinta da kuma hutu ba na wasa ba..........
Hatta kujerun personal parlour d’inta na chan sama, sabbi dal Daddy ya saka mata
Bedroom ma ya saka mata sabbin furnitures
duk don ya dan rage mata zafi.
Har k’asa kuwa ta durk’usa ta kama k’afafunshi tayi godiya sannan ta sake bashi hak’uri.
Shi kam Daddy
tausayinta kawai yake ta ji,
yaga duk tayi sanyi ta koma kalar tausayi, sai wani nan nan yake yi da ita....
Ko da Auwal ya dawo bai san da labarin dawowarta ba, gashi kuma ranshi a mugun b’ace yake ga gajiya, dan haka direct side d’inshi ya nufa, yayi wanka yayi sallah ya bi lafiyar gado, da kyar sai da yayi da gaske tukunna hoton Sakina da Ashraff yabar idanuwanshi
sannan ya samu bacci ya d’auke shi.
Auwal yana ajjiye Arshaad ya shiga gida shima.
A mugun gajiye yake dan haka tun a hanyar shiga ya zare suite d’in shi ya rik’eta a hannu
kafin ya fara k’ok’arin zare necktie d’in! Kana ganinshi ka san bacci kawai yake buk’ata.
Ko kallon cikin parlourn bai yi ba ya nufi side d’inshi….
“Ango!!”
Yaji muryar Mammy.
Da sauri ya d’ago yana kallon setin inda yaji muryar tata ta fito, “ai kuwa ita d’in ce”
ya fad’i hakan a ranshi.
Da murna ya k’arasa inda take zaune ita da aiima…
Ita kam ko wankan ma bata samu tayi ba! Tana nan a yanda ta fito a cell! Yo
ina zata iya wanka, ko sama bata samu ta hau ba tun da Aaima ta fad’a mata mummunaan labari take zaune take jiran dawowar Arshaad.
Huggin d’inta yayi
kafin ya d’ago
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 22 Chapter of 28