Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Ba sai kun rufe file ba, zaku iya tafiya kawai…” Yana gama fad’an haka ya kama hannun Mama ya cire mata cannular yana cewa “kuna gama cases d’inku ki tafi asibiti, dan ina jin tsoron jikin nan naki a haka!.” Yana fita Mama wadda daman abunda takeso kenan, ta yafa mayafinta, sannan ta cewa Huda “wuce mu tafi!” ………. Kasa sauk’e kafarta data d’aga da niyyar tafiya tayi jin Abba yana cewa “Babu inda Huda zata bii ki!!” Da mamaki ta juyo tana kallon Abba kafin tace “Ban gane ba!” “Babu inda zata je, tare da ke!!” Abban ya fad’a yana mai k’arasowa inda take sannan ya zuba mata idanuwanshi da ta kasa jurewa kalla tayi saurin yin k’asa da kanta. Cikin tattaro dukkan ragowar k’arfin jiki kuzari da jarumtar ta, ta zagayeshi taje inda Hudan take ta fara k’ok’arin kama hannunta amman kafin tayi hakan tuni Aslam ya juyo da sauri ya rigata, sannan ya tura Hudan bayansa, shi ya zamana yana a gaban Maman!! Da kyar ya iya bud’e idanuwanshi da ya runtse!! Tun lokacin da ya rik’e hannun Hudan ya zubasu a kan Mama! Cikin wata iriyar kasala data dirar masa lokaci guda yace “You have to pass through me first!” Arshaad kam zuwa yanzu ya zo wuya!!! Dan haka cikin fushi ya kalli Aslam d’in yace mishi “Let her go!!” “No” Yace ba tare da ya kalleshi ba! Sannan ya dakawa Hudan wadda take ta k’ok’arin kwace hannunta tana kuka tsawa “Ki nutsu!!”. Wani irin irin kuka Mama ta fashe da shi a take ta durk’ushe a wajen abin tausayi. Abba ne ya umarci Aslam da “Ya kai Hudan mota dan in dai yaci gaba da ganin Maryam a haka tou za a samu matsala!” Da sauri Arshaad yace “babu fa inda zata je ba tare da Mahaifiyarta ba!!! Haba Abba! Ka san kuwa shak’uwar dake a tsakanin y’a da uwa?? Ka san abubuwan da suka yi going through tare, lokaci d’aya kawai kazo kace zaka d’auketa haka nan? Why are you trying to be selfish???” Kallonshi Abban yayi da idanunsa da suka fara rinewa…. He‘s tired so tired of everything!! A yanzu yadda yake jin zuciyar shi tabbas idan ya tsaya kula Arshaad to zai iya yi mishi illa!! So yake yi kawai ya isa gida tare da Huda ya fuskanci kowa da komai! Masu laifi kuma ya hukuntasu dan bashi da tantamar cewa akwai waenda suka san da zaman Huda a dunyia a cikin estate d’in su… Apart from that ma inda ace ya san yanada y’a tun farko to da ko kwana d’aya ba zai barta tayi a gidan Usman ba which definitely ya san anan take da zama… Tabbas ya san bai kyautawa Maryam ba, but she’s not ready to listen!! Baya jin kuma zata yarda ta bashi Huda a cikin sauk’i! Shi kuma a halin yanzu ya kai peak!! Edge!!Limit!! Na tolerance… So yake kawai ya isa gida. Shiyasa cikin k’ok’arin danne zuciyar shi da yake ji tazo masa iya wuya!!! Ya cewa Aslam “Kai ta mota!! Idan tayi tirjiya ka d’auketa!” Yayi maganar ba tare da ya d’auke idanunsa da suka koma tamkar garwashin wuta daga kan Arshaad ba! Yace masa “Do your best ka lallashi Maryam sannan ka maidata gida.” Yana gama fad’an haka ya juya ya bi bayan su Aslam da Huda wadda ta bisa salin alin dan , gani tayi ana cewa ‘ya d’auketa’ ya durk’usa ya fara k’ok’arin ciccib’arta…. Amman fa kukan da take yi still tana k’ok’arin zame hannunta ana Aslam ya sanya gaba d’aya hankalin duk mutanen da suka wuce ta gabansu ya dawo kansu, da yawa tunanin su rasuwa aka yi mata, shiyasa ba wanda yayi k’ok’arin tsaidasu! Sai dai ‘Allah ya ji k’an rai’ kawai da wasu mutanen suka dinga cewa Wasu kuma kallon tausayi suka bisu dashi. Aslam yana isa bakin motar yaiyi mata key ya bud’e ya dannata a ciki ya rufe sannan ya zagaya mazaunin driver ya shiga ya bata wuta, ba tare da ya jira Abba ko Arshaad ba ya d’auki hanyar MT estate da ita........ Arshaad gaba d’aya ya tsorata da ganin yanayin Abba Dan tabbas bai tab’a ganinshi a irin wannan yanayin ba! Duk inda bacin rai ya kai b’acin rai to yau ya hango shi a kwayar idanun Abba! Shiyasa ya kasa tsaidashi. A hankali bayan fitar shi yaje inda Mama ke durk’ushe tanata faman kuka shima ya durk’usa gaba d’aya ranshi ba dad’i! A hankali yace “Mama dan Allah k.....” Kallon da ta d’ago tana yi mishi ne ya sa ya had’iye ragowar maganar sa! A hankali ta mik’e ta gyara mayafin jikinta sannan tace “Arshaad mai yasa kayi mana haka?” Da mamaki yake kallon ta kafin yace “Mama ni kuma mai nayi?” So da Buri Free Book 39 Da sauri Sakina tace “Mamaa” sai kuma ta k’arasa wajen da sauri ta hau tattab’a ta, ganin bata motsi yasa ta sa hannu ta juyo da ita! “Innalillahi wa innailaihirrajiun” Shine abinda Sakina Ummu da matar dake gefen Mama suka fad’a a tare, dan a yadda Sakina ta juyo da ita haka ta biyo hannun Sakinan ta taho yuuu ta zube wanwar kwanciyar rigingine. Ummu mutuwar tsaye tayi a wajen, so take ta k’arasa inda suke amman ta gagara sakamokon ganin y’ar uwartata da tayi kwance tamkar gawa! Ta kasa tab’uka komai banda hawaye ba abunda take yi. Sakina wadda ta rikice tanata tattab’a Maman ne ta juyo tace “Ummu ki zo ki kamata mu mik’ata emergency.. Mama ce amman bata numfashi.” Jin hakan ba k’aramin sake rikita Ummu yayi ba, ita dai kawai ta ganta a gabansu a tsaye amman bata san ya aka yi ta isa wajen ba. Matar nan ce ta matso itama ta hau jijjiga Mama tana cewa “kumafa yanzun nan muka gama magana da ita, tun jiya muke nan tare da ita. In banda kuka ba abunda take yi, nayi tambayar duniyar nan tak’i kulani… Sai dai kawai taje tayo alwala tazo tayi ta sallah. Sai d’azu ne da naga kamar batta lafiya nace ‘tazo muje in rakata taga Likita’, shine na samu ta d’an kulani ta inda take ce min ‘bara ta d’an yi bacci, idan ta farka sai muje’.” Ita dai Sakina cicib’arta ta fara k’ok’arin yi hakan yasa suma suka sa hannu suka taimaka mata suka yi waje da ita..... Su Madu suna tsaye a k’ofar shiga emergency.. Kana ganinsu ka san hankalinsu ba a jikinshi yake ba! Ga tsananin gajiyar da suke tare da ita Dan ma Allah ya taimaka Abokin Junaidu ne ya biya musu kud’in jirgi su kuma suka biyawa Baba Saboda yaga yanayin tsufansu gashi da ya kira Baban ma a hanya ya jisu suna dawowa daga wata tafiyar…. Ba dan haka ba da gajiyar ba zata yi musu da sauk’i ba. Suna tsaye suna tunanin abunyi next suka hango su Ummu d’auke da mata suna nufusu, sai da suka matso su sosai sannan suka gane Mama ce. Basu samu damar tambayar su ba dan da sauri mai gadin k’ofar ya wangale suka shige kawai dukkansu… Ana ganin su aka karb’esu bayan an kawo gado an d’aurata, aka tura ta ciki don yin bincike.. Ba a jima ba sosai, Dr ya fito! Likitan dai da ya karb’eta jiya shine, magana d’aya ce ya maimaita musu “hawa da jininta yayi over ne ya janyo komai..amman this time around har eco za suyi” Nan yake ce musu “ba yadda bai yi da ita jiya akan ta zauna ta shanye drip d’inta ba amma tak’i, ta biyewa wasu suka dinga hayaniya suna fad’a! Yayi yayi akan suyi shiru suka k’i, shiyasa shi kuma ya sallameta, so suma in sun san hayaniyar za suyi gara karma su shiga inda take, dan zai sake korar su ne!”. Yana gama fad’in haka ya nuna musu inda take sannan ya wuce........ Bayan kamar awa d’aya, Kaka da su Baba suka wuce aka bar Sakina da Ummu. Su Kaka na fita Hudan wadda take kiran Sakina a kai a kai ta kira, nan Sakina ta gaya mata “sun ganta suna tare ma yanzu haka” Sai a lokacin hankalinta yad’an kwanta. Nan itama Sakinan take tambayarta “tana Ina?” Hudan tace mata “tana wajen Gwaggon su Aslam, amman still Abba bai san tana gidan ba, dan a b’oye ma Arshaad ya kawo mata wayarta data bari a gidan Gramma, so in shaa Allah gobe da sassafe za ta san dabarar da zata yi ta gudo.” shiruu, Sakina tayi chan tace “ki bari mu yi magana da Ummu tukunna, kar ki yi komai, kinji?” Ummun ce tasa hannu ta karb’i wayar suka yi magana da Hudan ta d’an kwantar mata da hankali, kafin suka yi sallama. Da kyar suka samu bacci ya kwashesu wajen k’arfe 3 na dare. Da sassafe su Madu da Baaba Talatu suka zo kawo musu breakfast, har lokacin Mama bata farfad’o ba. Sama sama take jin hayaniyar su dan haka ta fara k’ok’arin bud’e idanunta. Sakina wadda take a kusa da ita ce ta lura dan haka ta maida gaba d’ayan hankalinta gareta, ganin Sakina ta k’ura mata ido ne ya sanya suma duk suka taso suka zagaye gadon suna tambayar “mai ya faru?” Basu ida tambaya ba Mama ta k’arasa bud’e idanunta… Tsantsar farin ciki ne ya baiyyana a fuskokinsu gaba d’ayansu, cikin murna suka hau furta “Alhamdulillah” suna tambayarta “ya jiki?”. Da kyar Baaba Talatu ta taimaka mata ta mik’e ta zauna.. Tana zama suka had’a ido da Ummu! Kawai sai ta fashe da kuka abun tausayi…… Duk shiru suka yi. Da kyar Madu ya samu ya k’araso inda take ya dafa ta sannan ya d’an fara bubbuga bayanta alamun lallashi. Farin ciki ne ya mamaye zuciyoyinsu gaba d’aya, duk sai suka hau murmushi Kaka har da y’a kwallarshi, ya sa hannu share ba tare daya bari kowa ya lura ba. Ita kanta Mama duk da yanayin da take ciki hakan sai da ya sanyata zubar da kwallar farin ciki, dan rabonta da Madu ya nuna kulawarshi a kanta kaman haka, yau yau shekaru ashirin da bakwai kenan!. Share hawayenta tayi sannan ta d’ago ta kalleshi, shima itan yake kallo, ba abinda ta hango a idanuwanshi sai tsantsar tausayinta, bakinta na rawa cikin kuka tace “Abba, ya raba ni da Huda! Dan Allah ku karb’o min ita, wallahi mutuwa zan yi in ba y’ata, na shak’u da ita sosai, ba zan iya yarda in bar mishi ita ba.” Da sauri Ummu ta k’araso ta rungumeta, sannan cikin tsananin tausayinta tace “Ki yi hak’uri ki huta, munji komai, in kika warke sai a san abun yi, ki kwantar da hankalin ki dan Allah.” Cikin jujjuya kai Mama ta zare Ummu a jikinta kafin tace “Bilkisu ba zan iya yin hak’urin nan ba!! Abba ya zama wani irin mutum! Mugun mutun.. Shi ne fa ya turo Arshaad wajen Huda, Arshaad cousin d’inta ne! Suka dinga yaudarar mu, idanunsa akan mu yake all this time amman bai baiyyana kanshi ba sai yanzu? Saboda ko nace ba zata koma wajenshi ba ya san ai Arshaad zata aura, kenan ko? Wanne irin ubane zai yiwa y’arsa haka? Bilkisu gaba d’aya kaina ya kulle, a baya yace ‘baya buk’atar ta’, yanzu kuma yazo ya raba ni da ita a lokacin da nafi buk’atar ta, mai yasa zai yi haka? Laifin me na yiwa Abba da zafi haka??”. Ta k’arashe maganar tana mai fashewa da kuka. Lallashinta Kaka Baaba Talatu da Ummu suka hau yi, amman furr!! Tace “ba zata hak’ura ba! Ba zata iya yin hak’urin da suke so tayi ba, yanzu zata je ta taho da y’arta, barinta a hannun Abba danger ne! Tunda har ya iya turo wani wajenta saboda son zuciyarshi bai damu da yana sonta tsakani da Allah ba ko akasin hakan ba Tou tabbas zai iya yin komai. Ko bayaga haka ma idan duk duniya zata taru a kanta tofa ba zata d’auki y’arta wadda Abban yace ‘bayaso ta fad’a mata ko da sunan shi ne’ ba, ta bayar a shi yanzu! Sai dai duk abinda zai faru ya faru. Suyi mata kwatancen gidan ko kar suyi mata zata tafi ta nema, tunda Allah yasa taji kwarin jikinta yanzu, daman jiya ma jiri ne ya hanata motsawa daga inda take.” Gaba d’aya Mama ta hargitse musu, data ga ma ba zasu bata goyon baya ba, Sai ta fara k’ok’arin sauk’a daga kan gadon sannan tasa hannu zata cisge cannular hannunta. Madu ne ya rik’e hannun nata, kafin cikin lallashi yace “Maryam koma ki zauna muyi magana.” Cikin sheshshek’ar kuka ta koma ta zauna tana share hawayenta. Sai da yaga ta d’an sassauta kukan nata, sannan ya fara magana “Ki kwanta ki huta, baki da lafiya. Koda kin fita za ki sake fad’uwa ne, saboda baki gama dawowa normal ba! Ki zauna ki shanye allurai da magungunan ki, da ni da Babanku Bashir za muje mu samu Abba, in shaa Allah, kinji ko??” Da sauri Kaka yace “Za muje a yau! Ki kwantar da hankalin ki kinji?” A hankali taji kad’an daga cikin nauyin da zuciyarta tayi ya d’an sauk’a, dan haka ta d’aga musu kai alamar ‘to’ kawai, tana sharar hawaye. Ajiyar zuciya Baaba Talatu ta sauk’e, sannan ta nufi wajen kulolin da suka kawo ta zubowa Mama abinci ta kawo mata. Sakina ce ta karb’a ta fara k’ok’arin bata, amma sai ta kauda kai gefe tace “ta k’oshi” Cikin turo baki Sakina tace “haba Mama ki ce mana, kin ganki kuwa yadda kika koma? Gashi duk kin yi wata zuru zuru kamar…” Dukan da Maman ta kawo mata tayi saurin kaucewa, duk kuwa sai suka hau murmushi…. Da naci da komai hakanan sai da Sakina ta d’urawa Mama abincin nan, ta kuwa ci sosai, dan sai da su Madu suka sa baki tukun Sakina ta hak’ura. Sai wajen 11 na safe su Sakina suka fara shirin tafiya don suke suyi wanka suyi girki, ita da Ummu. Baban su Sakina ne yazo d’aukar su! Ya d’auka Mama ko wani zai yi mishi maganan Arshaad amman yaji shiru shiyasa shima yana yiwa Maman ‘ya jiki’ ya fita, dan baya so suyi mishi d’in, but ya tsara a ranshi zai gayawa matarshi, duk abinda ya sani, da kuma dalilin yin shirun da yai, saboda kar ayi mishi kallon munafuki. Sai da suka biya duk wani bill sannan suka tafi a lokacin an tafi da mama yi mata eco. Su Kaka ma shirin tafiya gidan su Abba suka yi, aka bar Baaba Talatu. Sai a sannan ne Baba yazo, ganin Maman bata nan yasa suka gaisa da Baaba Talatu ya wuce kasuwa akan zai dawo da azahar in shaa Allah. Su Kaka basu samu damar zuwa gidan su Abba ba, sai la’asar, a sakamokon kiran da aka yi musu akan results d’in da ya fito, dangane da case d’in Junaidu......... Yadda Hudan taga rana haka taga dare, Gwaggo Asabe har mamakinta take yi dan duk juyi in tayi sai taga idonta biyu! Gaba d’aya ta kasa bacci ta k’agu Safiya tayi taje taga jikin Maama, da taga safiya ta k’i yi k’arshe kawai mik’ewa tayi taje ta d’auro alwalla, tazo ta fara jero nafilfili. Tana idar da sallar asuba kuwa bayan ta gama Azkar ta d’anyi karatu, ta shiga tayi wanka. Tana fitowa ta tarar Gwaggo Asabe bata d’akin, hatta sallayar data barta akai ta nad’e. Doguwar rigar da Gwaggo Asaben ta bata jiya had’e da Maclean da brush sabbi ta d’auka ta sanya, luckily ta samu comb a d’akin cikin drawer, dan haka ta goge shi da tissue sannan ta sa hannu ta zare ribbom d’inta ta hau ware tufkar da ta yiwa dogon gashinta wanda yanzu har ya kai tsakiyar bayanta….ita kanta tana mamakin yadda ya tofo a cikin shekara uku! Bayan askin dolen da Ya Jalila tayi mata… Tunawa tayi da Jalila wadda Sakina tayi mata k’us k’us d’in Khadija tace mata ‘kamar ciki ne da ita( Jalilan)’ amman Umma tayi k’arya tace ‘ta tafi jinyar Hansai’. A hankali ta sauk’e ajiyar zuciya a ranta tana adduar ‘Allah yasa ba cikin ne da ita da gaske ba’ ….abunka da zuciya mai kyau! gaba d’aya duk sai taji tausayin Yayar tata ya lullub’eta, don haka ta hau yi mata addua da fatan alkhairi, tanayi tana taje kanta. Sai da ta gama tsaf, ta d’auko ribbon d’in ta tufke gashin a d’an k’asan tsakiyar kanta kad’an! Ganin yadda jelar take reto ne ya sanya ta kanannad’e gashin waje guda ta tura ta had’e da ribbon d’in, d’ankwalin doguwar rigar ta d’auko tayi style d’in V da d’aurin very simple amman ba karamin kyau tayi ba, ga gashin data duk’unk’une ana iya hango santsi da kyallin shi da uban yawa dan d’ankwalin k’aramine sosai so bai gama rufewa ba. Ta d’auko wayarta kenan zata kira su Mama ta ganta a kashe, ba chargi. Ajiyar zuciya ta sauk’e, daman ta san za ai haka, dan tun jiya chrgin ta yayi low sosai. Zama tayintana jiran Gwaggwo Asabe ta dawo ta ari wayarta ta kira su Mama don duk ta haddace nambobin su. Kusan minti arbain taji shiru.. ga anxiety yana neman kashe ta! Shiyasa ta yanke shawarar mik’ewa, ta hau nemanta. Bata wani sha wahalan neman nata ba, dan tana fitowa daga d’akin taji k’amshi ya cika ko Ina a gidan wanda hakan ne ya tabbatar mata da inda take(Gwaggwo Asaben), dan haka ta nufi k’asa. A k’ofar kitchen d’in suka had’u da Gwaggon, da tray a hannun ta, da kuma tea flask da ta rik’e da kyar. Sai da Hudan da d’an rissinar da kai tukunna ta gaisheta. Da kulawa Gwaggo Asabe ta amsa… Har ga Allah ta dad’e bata had’u da Yarinya mai hankali da nutsuwa irin Huda ba, ga kyau tubarkallah…shiyasa lokaci guda suka saba, taji ta shiga ranta sosai! Har k’asan zuciyarta take yiwa Aslam d’insu kwad’ayin auren Yarinyar saboda ta had’a komai ga kyau ga hankali ga nutsuwa gata y’ar uwarshi! Sai dai kuma yadda taga Arshaad yana shige mata sosai, watak’il shi ne zai fara cewa yana sonta, dan jiya ta lura har wata y’ar hira suka tsaya yi a parlour, sai wani nan nan yake yi da ita….. Hannu Huda ta saka tana k’ok’arin karb’ar tea flask d’in dake hannunta wanda hakan ne ya katse mata tunanin ta! Ba musu ta sakar mata , dan itama tana jin yadda ya kusan fad’uwa. A tare suka nufi hanyar sama, tana gaba Hudan na biye mata baya, wata hanya suka kuma d’auka bayan sun shanye stairs d’in, nan ta sake hango wani bene, benen suka bi suka hau, suna kaiwa k’arshe suka tarar ta wata y’ar k’ofa A bud’e k’ofar take hakan yasa suka shige, dogon corridor ne sosai, sai k’ofofi biyu, d’aya a farko farko hanyar dama, d’ayar kuma a kusan k’arshen dogon corridor d’in ta hannun hagu, Wadda itan taga Gwaggwon ta nufa, sai da suka iso bakin k’ofar, tukun suka tsaya! Rik’on tray d’in Gwaggwo Asabe ta gyara sosai a hannu d’aya sanna tasa hannu tayi knocking, tukun taja ta tsaya, ta gyara ruk’on tray d’in. Kusan minti biyu tukunna suka ji ance “come in” Hudan ta kalla tace “tayi amfani da empty hand d’inta ta bud’e musu.” Hakan tayi, bayan ta murd’a handle d’in a hankali ta d’an tura sai kuma ta matsawa Gwaggo Asabe don ta fara shiga.. Murmushi Gwaggon Asabe tayi sannan ta shige Itama Hudan ta bita a baya. Sai da ta rufe k’ofar tukun ta juyo ta fara kallon d’akin…. “Ma shaa Allah” tace, a ranta. Ba zaka kirashi d’aki ba kuma ba zaka kirashi da parlour ba, ga set d’in kujeru har da k’aramin dining, da makekiyar tv d’in da bata tab’a ganin irin ta ba, ga kuma set d’in gado shima komai akwai, royal, light blue da fari haka colour d’in kujeru da gadon suke, hatta pentin d’akin haka yake. Ga kuma wani glass door, wanda kana iya hango swimming pool da shuke shuke da kujerun shak’atawa. K’auyanci ta fara, don a ranta ta hau rayawa “daman ana pool a sama? saman ma ta biyu! Ita tunda take bata tab’a ganin d’aki mai girma sosai da kyau irin wannan ba!”…… Tunanin ta ne ya katse jin Dad yana cewa “Hudan k’araso mana ya kika tsaya a k’ofa?”. Sai a lokacin hankalin ta ya kai kan Dad, da wata mata a zaune a gefen shi yana rik’e da hannunta. Ji tayi kamar ta rusa kuka!! Da ta san gurinshi Gwaggo Asabe zata zo da bata biyo ta ba, kenan ita duk b’uyab da takeyi ma a banza, tunda gashi a gidanshi ma ta kwana ba tare data sani ba, kuma yadda ya nuna it’s like ya san tana nan d’in, shikenan ta san yanzu zai kira Abba shi kuma ya hanata zuwa taga Mama. Gwaggo Asabe ce ta katsemata tunani jin ta sake cewa “Huda k’araso mana.” A hankali take takawa izuwa bakin gadon inda suke… Taji Dad yana cewa “Ashe da gaskiyar Abba, daman ya ce tana wajensu Aslam ni ban yarda ba, sune suka kawota jiyan ko?” D’an murmushi Gwaggo Asabe tayi kafin tace “Eh jiya lokacin da ka kira ni, Arshaad bai dad’e da kawota ba, shi ya rakota.” Hudan dake jin su duk sai taji jikinta yayi sanyi, ashe ita kad’ai take ta shirmen ta. A hankali ta k’arasa wajen, kanta a k’asa. Har k’asa ta durk’usa ta gaida Dad, wanda cikin tsananin son yake yiwa y’ar d’anuwan nasa yayi saurin kamo ta ya zaunar da ita a kan d’an stool d’in da yake facing d’inshi, cikin kulawa ya amsa kafin ya hau tambayarta “ya kwanan bak’unta?” “Alhamdulillah” kawai ta iya cewa kafin ta juya ta hau gaida matar gefen shi har sau biyu amman ba alamun zata amsa kuma ta kafeta da idanuwa! Tana shirin sake gaidata a karo na uku ne Dad ya sauk’e ajiyar zuciya ya d’an dafa Huda tukun yace “Karki damu ba zata iya amsawa bane, amman ta fahimceki, tunda gashi tanata kallonki.” Yana gama fad’in haka ya juya ga Gwaggo Asabe jin tana cewa “ga breakfast, watak’il taci tunda naga yanzu jikin da d’an sauk’i, ko?” Shiru ya d’anyi kafin ya sauk’e wata ajiyar zuciya tukunna yace “Sai addua fa, amman Alhamdulillah, ni fa da Granpa zai yarda wallahi da an hak’ura da wannan theraphy d’in, saboda duk lokacin da akaje aka yi aka dawo ni sai inga kamar abun k’aruwa ma yake yi, kwanaki fa har hira tana yi, amman yanzu kiga gaba d’aya sai a hankali, danfa baki ganta last two weeks ba (Tym d’in da suka dawo. A Abuja), shiyasa ai na hanata dawowa nan, da kyar fa da addu’o’i tukunna abun yayi sauk’i ta dawo hakan.” Ajiyar zuciya Gwaggo ta sauk’e kafin tace “nima dai gaskiya na dad’e da lura, magana ce kawai banaso.” Cikin d’an fad’a Dad yace “Ai kuwa ta gama theraphy! Dan a gaskiya, ko ance za aje, sai dai In kaita Abuja kawai muyi sati mu dawo, abu ba fad’ar Allah ba amman an maidashi kamar dole!?” Kwalla Gwaggo Asabe ta share sannan tace “Ai shima Granpa d’in naji yana cewa ‘daga wannan an gama’.”Cikin katseta Dad yace “ai tun last year yake cewa ‘daga wannan an gama daga wannan an gama’! Amman an kasa gamawa da gasken.” Ajiyar zuciya Gwaggo ta sauk’e ranta duk ba dad’i da yanayin y’ar uwarta ta…. A hankali ta durk’usa ta fara serving abincin cikin mutuwar jiki. Hudan itama duk jikinta yayi sanyi dan haka tace “Allah ya bata lafiya”. A hankali Dad ya d’an juya ya kalle ta sai kuma yace “Ameen” cike da jin dad’in adduar tata. Juyawa yayi ya kalli Mommy, gani yayi har yanzu Hudan take kallo, kamar tanaso ta tuna wani abun.. Bai gama fahimtar yanayin ta ba yaga ta d’aga hannunta sannan tayi amfani da yatsar ta manuniya wajen sai da Huda! Gaba d’aya hankulansu kanta ya koma, cikin rawar murya kamar ta mai koyan magana sukaji tace “Aaa-sllam, ttanna kama ddda Aasllm d’Ina” Ba Dad ba hatta Gwaggo Asabe sai da gabanta yayi wani irin mahaukacin fad’uwa!!! Rabon da Mommy ta kira sunan Aslam, tun kafin ta fad’o daga bene! Gaba d’aya rawa jikin Dad ya d’auka, a hankali ya sa hannu ya juyo da fuskarta, ya kalli cikin idanunta sannan yace “Kina so kiga Aslam d’in naki?” Da sauri ta hau d’aga mishi kai, sai kuma hawaye, shaaarrrr suka zubo mata. “Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!” Shine abunda Dad ya dinga maimaitawa, cikin kid’ima ya mik’e ya fita yana cewa “su Gwaggwon su tsaya gashi nan zuwa, kar kowa yaje koina.” Ba ayi minti goma ba sai gashi ya turo k’ofa, rik’e da hannun Aslam Abba yana binsu a baya! Cikin zumud’i yace “Ga Aslam d’in naki” ya fad’a yana tunkarar ta, yana cewa su Abba “komai yazo k’arshe in shaa Allah, Aslam yau da kanta ta kira sunank.........” Razananniyar k’arar da ta fasa ce ta hanashi k’arasa maganar tashi, ta kuma rud’a duk wani wanda ke a cikin d’akin!! Basu ida dawowa haiyyacinsu ba ta kuma sakin wata k’arar! Wadda kusan rabin estate d’in sai da aka

Chapter 2 of 28