Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ashe ragowar kayantane na jiya aka kawo/ Cikin girmamawa maid d’in ta gaidata sanann ta hau shigo mata da kayan leda leda. Godiya Huda tayi mata bayan ta gama, ta juya ta fita. Ita kuma ta tura k’ofar taja kayan zuwa bedroom. Tana gama ajjiyewa a closet ta fito kenan ta zauna akan gado Abba ya shigo cikin jallabiya mai k’aramin hannu rik’e da hannun Sudais wanda shima yake sanye cikin kayan bacci. Da sauri Sudais d’in yazo ya rungumeta sannan yace “Abba just told us that you are our big sister, i’m so glad that we’ve a big sister” Ya k’arashe maganar yana sake hugging d’inta. Murmushi tayi itama tayi hugging nashi back kafin tace “I’m so glad to have cute brothers too.” Da sauri ya d’ago yace “Monday idan anje school zan gayawa Ashraf da Sultan da Kareem nima nayi big sister, dariya suke yi min kullum suna tsokanata! Yanzu kema kice Abba ya kaiki school d’inmu a sakaki a ss2 dan Allah so that i can come and see you during break time just like they do, and also....” Abba ne ya dafa kanshi yana dariya, kafin yace “Sudais wai har yanzu baka san ka girma ba? Ya kamata fa ace ka daina wannan shirmen And Big sis ta gama secondary ai,,kar kayi mata adduar komawa baya mana. School d’in su Aaima zata tafi, ko?” Yayi maganar yana kallonta yana murmushi. D’an zamowa tayi ta gaidashi, a hankali ya amsa yana mai dafa kanta yana kallon idonta da tashi d’aya ya fahimci taci kuka. A kan Kujerar gefen gadon ya zauna yana kallonta kafin yace “Me ya saki kuka? Mama kike son sake gani?”. A hankali ta sunkuyar da kanta k’asa kafin tace “ina jin ba dad’i ne akan abunda nayi mata jiya, Ummu ta kirani nace mata mun dawo, inaga haushi suka ji dan I’ve been calling them since last night amman ba wanda ya amsa.” Ta k’arashe maganar tana sakin kuka. Ajiyar zuciya Abba ya sauk’e kafin yace “A kawo miki Sakina? Ku zauna tare?” Da sauri ta d’ago tana kallonshi, sai kuma ta hau d’aga kai tana share hawayenta. Murmushi yayi kafin yace “Ok, but no more crying, in ba haka ba in fasa.” Da sauri ta cigaba da goge hawayenta, da kyar kuwa ta samu suka tsaya…. Abba bai kira Baban Sakina ba sai da ya sakata tayi murmushi kala uku! Sudais yana tayashi da yi mata cakulkuli. Bayan sun gaisa ya tambayeshi akan “Dan Allah ya bar Sakina ta zo ta d’anyi kwana biyu da su tunda basu fara school ba yanzun, maybe Hudan ta d’an sake in ta ganta.” Nauyi da kunyar Abban ne suka hanashi yi masa musu dan haka yace “yanzu an sallami Mama ne suna kwashe kaya, amma zuwa anjima in shaa Allah zai kawota. Ya tura mishi adress kawai.” Godiya yayi sannan ya kashe wayar, ya tura mishi da adress d’in. Yaji dad’in yadda ta saki ranta sosai. Cikin murna ta tanbayeshi “me zata dafa?” Murmushi kawai yayi yace mata “koma me ne in ta dafa yayi” Kafin ya tambayeta adress d’in su Sakina, tayi mishi kwatance, daga nan suka fita shi da Sudais........ Wanka tayi ta sa wani silk gown, A shape, colour d’in emerald green, an d’anyi kwalliya ta k’asan k’irjin da igiya mai stones ya zagaye, daga gefe ta gaban an tufkeshi yayi kmr ribbon babba. Bai matsetaba kuma bai yi mata ruwa ba dai dai jikinta, tayi masifar yin kyau, ta gyara gashinta ta tufke a k’eyarta sannan ta d’auko d’ankwali kayan ta nad’a wanda kasancewarshi k’arami, yasa ta d’anyi normal d’aurin kai dashi ta kuma bi da edges d’in dankwalin ta kan gashin data tufke ta sake zagayewa da shi d’ankwalin. Sannan ta d’auki turare ta fesa duk a cikin kayan da tayi order jiya. Tayi kyau sosai kuwa abunta. Wayarta ta d’auko ta kira Ummu still bata d’auka ba, Sakina kuma a kashe. Jiki a mace haka ta sauk’a ta shiga kitchen. Ga mamakinta har an gama breakfast, maid d’in jiya da wani shima da uniform a jikinsa irin nata (maid d’in), Sun gama hada komai, kuloli wajen uku, kitchen d’in sai tashin k’amshi yake yi. Sai da ta k’araso tsakiyar kitchen d’in tukunna suka lura da ita, kamar zasu kifa haka suka hau gaidata cikin girmamawa.. Itakam kunya da mamaki ma da kyar suka barta ta amsa. Ta riga tayi niyyar yiwa Abba girki shiyasa ta tambayesu me suka dafa? To dai d’ayan abincin itakam ba ma ta sanshi ba kuma bata tab’a ganinshi ba ma, sai shawarma a d’ayan kulan, farfesun kayan ciki kuma a d’ayan, sai ruwan zafi a flask ga mai buk’ata. A hankali cikin nutsuwarta ta k’arasa ta bud’e inda suka nuna mata a matsayin store d’in ta shiga.. Babu abinda babu a ciki, dan haka ta d’auko, dankali kad’an da kwai da Mayonnais da su albasa sai su green beans da macaroni. Sun so su tayata aikin amman tak’i, da kanta ta had’a mishi potatoe salad mai d’ankaran dad’i da kyau! A dining d’in taje ta ajjiye bayan ta juye a cooler. Tana shirin barin wajen Auwal ya shigo… Suna had’a ido da shi ya b’ata rai! Fuskarnan tamau haka ya nufo dinning d’in. ita dai Huda ta lura kwata kwata wannan baya k’aunarta ya tsaneta! A hankali ta gaidashi amman kamar wanda take magana da dutse ko kallon inda take bai yi ba! Kujera kawai yaja ya zauna ya hau had’a tea. D’aga sagaggun k’afafunta tayi ta fara takawa don barin wajen dai dai Abba yana sauk’owa, bata ma lura dashi ba sai da ta kusan tsakiyan falon suka yi kicib’is! Murmushi yayi ya dafa kanta sannan yace “har an gama girkin?” Itama murmushin ta mayar mishi tace “Eh” “Ok, muje.” Yace sannan ya kama hannunta suka juya. Suna zuwa Auwal ya mik’e ya gaidashi, cikin kulawa Abban ya amsa mishi sannan ya cewa Huda “kun gaisa da yayan naki?” A hankali ta d’aga kai alamar ‘eh’ Harararta yayi sannan yace “Daddy ne yace kuzo muyi breakfast.” “Ok” Abban yace sannan ya cewa Huda taje taga ko su Shuraim sun gama shiryawa. Har ta juya taji yace “Ina abincin da kika dafa?” Da sauri taje ta d’auko kular ta mik’a mishi, karb’a yayi sannan ya mik’awa Auwal yace masa “fara yin gaba da wannan, gamu nan zuwa.” A k’afar bene ta had’u da Yaran dan haka suka juya tare. Suna k’arasowa parlourn suma suka wuce side d’in Daddy. Ita dai tana mamakin tou wanchan uban abincin, da aka dafa musu waye zai ci!? Kasa hak’ura tayi ta cewa Abban “Ko ta koma ta d’auko kulolin chan, masu aikin fa sun yi girki”. Murmushi yayi yace mata “Karta damu anjima da yamma idan anyi na sadaka za a had’a a kai tare da wanchan d’in.” BULAMA ✍️ So da Buri Free Book 42 Yadda side d’insu yake, haka na Daddy shima yake, komai da komai iri d’aya, kawai de akwai k’ofofi da corridors d’in da suke a nasu wanda babu a na Daddyn. A parlourn suka tarar da Daddy d’in da alamun su yake jira. Abba ne ya fara gaidashi tukun su Huda. Yana jin Yarinyar a jikinshi matuk’a dan haka bayan ya amsa ya hau tambayarta “ya take? Tana jin dad’in zaman? Akwai abunda take buk’ata?” A hankali tace “komai Alhamdulillah. “Ma shaa Allah” yace sannan suka k’arasa….. Nan d’in ma abinci wajen kala hud’u akayi. Cikin nutsuwa da nishad’i sukayi serving kansu suka fara having breakfast d’in. Basu dad’e da fara cin abincin ba, Hudan taji yanayin bugun zuciyarta ya chanza! A hankali ta runtse idanunta tana k’ok’arin saita kanta, da kyar ta samu ta bud’e idanunta tana mai jin wata nutsuwa tana sauk’ar mata sakamokon k’amshin turaren da ya sakarmata da kasala lokaci guda! Basuma lura da shigowar tasa ba, sai da ya matsosu sosai da k’amshin turarenshi ya yi musu sallama, tukunna suka lura da shi. A hankali yace “AsSalama alaikom” “Wa’alaikassalam, d’an albarka!” Daddy yace yana mai ja mishi kujerar kusa dashi. Zama yayi, a lokaci guda kuma yana mai amsa gaisuwar su Shuraim sannan yace Daddy Ina kwana” Da kulawa Daddy ya amsa haka shima Abba bayan ya gaidashi. Sannan ya juya ya mik’awa Auwal hannu, sukayi musabaha. A hankali Hudan ta gaidashi ba tare da ta yarda sun had’a ido ba! Juyowa yayi ya kalli inda take, sai kuma da sauri ya kauda kanshi, a hankali yace “lafiya” Hira suka d’an fara sama sama, kusan rabin hirar akan maganan company d’in da Aslam da Abba za su bud’e ne. Ita dai Hudan kasa ci gaba da cin abincinta tayi, tun lokacin daya shigo! Bata san daliliba amma in dai yana waje to sai ta dinga jin kanta uncomfortable, ga yadda k’irjinta yake yi mata shima, wanda ta rasa dalili. Abba ne ya cewa Aslam “Ina Arshaad ne? Ban ganku tare ba.” “Ya tafi d’aurin auren wani Abokin su, and wai za su kai amarya Kaduna, around 2 haka.” Aslam d’in ya bashi amsa. “Ok” Abba yace kafin ya kalli Huda yace “Ko a bari sai gobe kuje park d’in ko? Tunda yau Arshaad d’in yana busy.” Kafin ya rufe bakin shi Auwal yace “Bani da aiki sosai yau, zan kaisu.” Hudan ta d’anji sauk’i saboda daman ba zata so su fita itada Arshaad ba, kuma ba zata so ace Aslam ya kaita ba! Amman kuma ba ita kad’ai ba hatta su Daddy sai da suka fahimci akwai wani abun da Auwal ya shirya duba da yadda baya son ta yanzu kuma lokaci guda yace ‘Zai kai ta’ Daddy wanda ya san halin kayanshine yace “a’a! Ka barshi goben Arshaad d’in ya kaisu” “Daddy i volunteered fa.” Auwal d’in ya fad’a yana kallonshi. Cikin d’an fad’a Daddyn yace “And i insist akan ka barshi Arshaad ya kaisu.” Murmushi Abba yayi kafin yace “Daddy tunda ya nuna zai kaisun a barshi mana ko? Please.” Baya son jan magana dan haka yace “ok” kawai ….dukda ya san Auwal bai Isa yayi mata komai ba tunda tare za su tafi ita da su Shuraim amma baya so suje Auwal d’in yayi mata wani kalar rashin mutuncin da zai ja yaji kunya ne. Murmushi Auwal d’in yayi ya kalli Hudan kafin yace “Ki shirya around 2:30pm haka” Yana gama fad’an haka ya mik’e yayi hanyar sama, da alama ma ko “to” d’in data ce mishi bai ji ba. Shuraim ne ya mik’e, yace “Abba zanje in yi assignment d’ina kafin mu fita” Da sauri itama ta mik’e daman hanya take nema saboda sam bata k’aunar zamanta waje d’aya da Aslam kwata kwata, gashi ta lura sai faman kallonta yake tayi, sannan anyi rashin sa a ya zauna a kujerar da take opposite d’in tata ne….a hankali cikin nutsuwarta tace “Abba nima bara inje” sannan ta juya ta yiwa Daddy sai anjima. Sudais shima binsu yayi, suka fice a tare…. Da murmushi Abban ya bisu da kallo yana jin wani tsananin farin ciki a ranshi.. Gyaran muryar da Daddy yayi ne ya juyo da hankalin su inda yake. Ganin yanayin shi yasa duk suka maida hankulansu a kanshi. Cikin rauni yace “Abba jiya da daddare naje wajen su Mammy, and thier situation is bad! Very bad!! Na san abunda suka yi was wrong but anyi saurin yanke hukunci cikin fushi gaskiya.. Thou they deserve it, but matsalan shine they can’t survive in there most especially ma Ummi, dan a yanzu inda zaka je ka kalla jikinta to ba zaka so ka k’ara kalloba sakamokon k’uraje da borin jinin da suka fito mata ta koina! Ka san dama ita tanada allergy tun tana y’ar k’arama tanada kyankyami sosai! Ko fa 1 week ba ai ba amman in kaje ba lalle ka iya gane ta ba! I don’t think zata iya kai 2 months a wajen nan gaskiya, jiya da naje ruwa ake k’ara mata, amai da gudawa take yi, gashi ko abinci mai kyau in mutum ya kai musu Granpa sai ya sab’a maka. Kar garin punishing d’insu kuma muje mu shiga hakkinsu, after all they are our wives..” Ajiyar zuciya Abba ya sauk’e kafin yace “Daddy inda case d’innan a hannu na yake, tou da zan iya sassauta musu, not because of wai na yafe musu ko na huce, NO! Only because of maganan da kayi min yanzun… Amman Granpa ke rik’e da case d’in, already ni da kai masu laifine a idanunsa a yanzu, Ina tunanin In muka yi interfering, za a iya samun matsala…” Cikin katseshi Daddy yace “Ba interfering za muyi ba! Gramma za muyi wa magana, na san ya san yanda za tayi ta d’an shawo kanshi, at least a d’an sassauta musu, ya bari a dinga kai mu su abinci daga nan, sannan a ajjiye su a tsaftataccen waje, dan gaskiya jikin Ummi ya bani tsoro jiya.” Numfashi Abba ya fesar, sannan yace “ba komai zan kira Gramma d’in a waya zuwa anjima in shaa Allah.” A hankali Aslam yayi k’asa da kanshi sannan yace. “Zan yiwa Granpa magana, in sha Allah zai sauk’o, zan lallab’ashi.” Shiruu, suka d’an yi, chan kuma Daddy yace “ok, hakan zai fi.” Abba yana shirin mik’ewa, Daddy yace “akwai wata maganar still fa. Jiya bayan mun rabu Arshaad ya kirani, wai yana son yin magana dani, i think kunyar ka yake ji shiyasa ya bari sai da na koma.” Da mamaki Abba yace “Arshaad? Kunya ta kuma? Ikon Allah!” Murmushi Daddy yayi, sannan yace “Bayan yace ‘yana son magana dani’ shine nace masa ‘ya zo tou muyi face to face’ Mun dad’e tare dan tare ma muka je station d’in da shi.” D’an kallonshi Abban yayi sosai ya bashi dukkanin hankalinsa alamun yana buk’atar k’arin bayani… Murmushi Daddy ya sake yi, kana ganinshi ka san yana cikin farin ciki da jin dad’in al’amarin, fuskarsa cike da annashuwa yace “Good news ne, Ashe wai ya san Huda, for the past 3 years, and suna dating ne, ita ce Yarinyar da muke da shirin zuwa nema masa aurenta! So yanzu ya same ni ne akan ko za a fara maganar tasu tund........” Kwarewar da Aslam yayi ne ya hanashi k’arasawa. Da sauri Abba ya mik’a mishi ruwa dan haka ya karb’a ya d’an kurb’a yana tarin kad’an kad’an still, su kuma sunata jera mishi “sannu!” D’aga kanshi kawai ya iya yi Idanunsa sun yi jaaaa! Alamun ba kad’an ba yaji azabar kwarewar… Sai da suka ga ya d’an nutsu tukunna Daddy ya kalli Abba yace “ya ake ciki?” Shiruu, Abba yayi, kamar mai nazari, kafin yace “all those years kuma bai gane ta ba?” “Abun mamaki ko? Suna tare amman basu gane junan su ba!” Daddyn ya fad’a, kafin ya ci gaba da cewa “Ya yiwa Dad ma maganar! Wallahi baka ji yadda lamarinnan yayi mana dad’i ba! Ni kam na riga ma na bashi ita.” Ya k’arashe maganar yana murmushi mai kama da dariya wanda ke baiyyana tsantsar farin cikin da yake ciki. A hankali Abba yayi k’arfin hali ya d’an k’ak’alo guntun murmushi kafin yace “Tou Allah ya zab’a mana mafi alkhairi” Ameen Daddy yace sannan ya juyo ya kalli Aslam wanda ya runtse idanunsa ya kwantar da kansa da bayansa a jikin kujerar! Cikin zolaya Daddyn yace “wannan azumin da kaina zan buga maka wak’ar gauro!! Arshaad yayi maka wayo..” D’an murmushi kawai yayi ba tare da ya bud’e idanunsa ba. Abba baya son maganan shiyasa ya sako wata maganar daban dan haka suka hau tattaunawa…… Shi kam Aslam mik’ewa yayi yayi musu sallama ya kama gabanshi. A b’angaren Hudan kuwa bayan sun gama dabdalar assignment d’insu dasu Sudais ta tafi d’akinta, tana kwanciya bacci mai nauyi yayi gaba da ita. Sai wajen 1:30 ta samu ta farka. Alwalla tayi tayi sallah, sanin da tayi ba a gida za tayi sallar laasar ba ya sa ta karanta izu hud’u, tayi doguwar addua ta tofa, itama ta shafa. Tana idarwa Shuraim yazo ya kirata yace “taje inji Abba, yana parlour” Jikinta ba kwari ta fito, dan still ta sake gwada number Ummu tana shiga amman tak’i d’auka! Gashi har yanzu Sakina itama bata kunna wayarta ba, ba kuma ta k’araso ba, Allah yasa ba hanata aka yi ba!. Tana wannan tunanin tana tafiya domin amsa kiran Abban nata. A parlourn saman inda sides d’insu yake ta sameshi. Tun daga yanayin ta ya fahimci tana cikin damuwa.. Ajiyar zuciya ya sauk’e bayan ya amsa gaisuwar ta kafin yace “Zauna, i want to talk to you” Zama tayi, a one seater d’in parlour da yayi mata nuni da. Ba tare da b’ata lokaci ba , ya fara magana “D’azu Daddy yake cewa wai Arshaad ya sameshi akan maganar ku!” Da sauri ta d’ago ta kalleshi, a zuciyarta ta hau mamakin Arshaad da kalar nerve d’inshi! Despite abunda yayi da kuma fushin da suke yi da juna amman shine yaje ya samesu da maganan! Me kenan yake so? Auren yakeso ayi ko tanaso ko bataso kenan ko me!?…. A hankali ta sunkuyar da kanta k’asa, jin Abban ya sake cewa “Yace wai you two knew each other for a while ko?” Sai da ta taushi zuciyarta, tukunna ta iya d’agawa Abba kai alamar ‘eh’ sannan ta bashi labarin yadda Arshaad d’in ya kaisu makaranta… Hatta wayoyin daya siya musu sai da ta fad’a mishi bata b’oye komai ba a labari da tarin alkahairan da yayi musu tun daga had’uwar su har kawo yanzu. Dan ita bata kasance mai manta alkhairi ba kwata kwata. Tanaso ta fad’a mishi issue d’inshi da Jalila amman sai ta kasa. Ajiyar zuciya Abba ya sauk’e bayan ya gama jin bayaninta ya na k’ok’arin fassara lamarin Arshaad amman ya kasa! Tabbas akwai abinda Arshaad ya sani tun farko kuma yayi shiru wanda shi kad’ai ya san dalilin yin shirun da yayi! Dan a cikin labarin da Huda ta bashi yanzun yaji inda Arshaad ya had’u da Mama ba so d’aya ba, and in dai Arshaad ne ya tattare mishi d’akinsa kwanakin baya da za suyi parking ya kai personal kayayyakinshi gidanshi na kwandila, tou tabbas ya san wacece Huda! Ahankali yaji tace “Amman Abba yanzu bama tare mun yi fad’a sosai..” Ta k’arashe maganar ta na kuma yin k’asa da kanta. Murmushi Abban yayi kafin yace “Ai kuwa ke kad’ai kike fad’anki! Don shi gashi yazo yana binmu one by one yana expressing how much he loves you.” Da sauri tasa tafukan hannayenta ta rufe fuskarta… Tashi d’aya Maryam ce ta fad’o mishi arai, yanayin kunyarsu iri d’aya ce, kalli fa fad’a tace sunayi amman kuma anyi magana ta hau jin kunya…. Murmushi yayi kafin yace “Kije ki shirya dan na san yanzu Auwal zai zo, Shuraim yace min “zai bada hadda yau a islamiyyarsu da suke zuwa duk asabar da lahadi so nan zai je shi ba zai samu daman binku ba. Sai kuje da ke da Sudais kawai.” “To” tace, sannan ta mik’e, har tayi gaba sai kuma ta juyo Tace “Abba Allah da gaske nake yi munyi fad’a dashi, fad’an gaske!” Dariya ta bashi ganin yanda ta dage akan ita fa sun yi fad’a, amman ko a cikin bayaninta, yadda take yabon Arshaad d’in, ya sanya ya fahimci still tana son abunta. Murmushi kawai ya sake yi yace “Tam na yarda kun yi fad’a, shikenan.” Ahankali ta juya ta wuce don taje ta shirya. Lumshe idanunsa yayi ya kwantar da bayanshi da kanshi jikin kujerar... .....Zai fara yin magana da Arshaad first! He just hope yanada kwakkwaran reason ba munafuntar su yayi ba all this time.. Saboda in dai hakane tou gaskiya zai murzawa idanunsa toka, ya hanashi Huda! Dan ba zai bari y’arsa ta rayu da Namiji mai b’oye b’oye ba. Ya lura da tana sonshi, so yana adduar Allah yasa Arshaad d’in ya zamana yanada reason d’in da zai kare kanshi kwakkwara! Zai yi farin ciki da hakan domin kuwa ya san that’s wat she wants.. Dukda kuwa yana da wani buri da ya d’aura akanta tun lokacin da ya fahimci yanada y’a mace mai shekarunta amman tunda he’s late ta riga ta zab’i Arshaad, shikenan ba komai, yana yi mata fatan alkhairi….. BULAMA ✍️ So da Buri Free Book 43. Cikin nutsuwa ta shirya ta d’auki y’ar k’aramar jaka da wayarta ta fito. Bata samu Abba a wanann parlourn ba! Dan haka ta sauk’a chan k’asa cikin nutsuwarta… Tun kafin ta k’arasa ta hangoshi shi da Sudais wanda shima har ya shirya da alamun ita yake jira. Har ta sauk’o Abba bai lura ba, yana nan ya dulmiya duniyar tunani….surutun Sudais ne ya d’an dawo da hankalinshi parlourn, dai dai nan kamar had’in baki Auwal ya shigo.. Riga da wando ne a jikinshi, rigar maroon mai dogon hannu da black jeans asalin crazy! Ga wani had’add’en takalmi sau ciki mai mugun kyau black! D’azu uban gashi ne a kanshi amman yanzu yayi sabon aski an aske gefe da gefe da k’eyar an bar tsakiyan (saman kan) lallausar sumar ta taru a kanannad’e iya tsakiya sai shek’i take yi, gefe wajen kunnenshi na dama ta sama inda aka aske an sake bi anyi wani style kamar zigzag, asalin farar fatar kan nashi ta baiyyana ta fito da design d’in radau!! Ga wani bracelet kamar sark’a a hannun daman shi, sannan ya maka wani arnen bak’in glass mai shek’i wanda kana gani kasan mai mugun tsada ne…… Yana shigowa k’amshin turarenshi ya gauraye ko ina. Tafe yake yana danna waya, har ya k’araso cikin parlourn bai ma lura da su Abban ba. Da Hudan ya fara lura kasancewar ta a tsaye sai kuma sudais wanda ya k’arasa wajenshi da sauri yace “Ya Auwal har da wannan wajen nan zaka kaimu ko? Wanda ake sa glass ayi game..” Dariya yayi ya d’an sa hannunshi akanshi ya hautsina y’ar sumar data d’an tarar mishi ba sosai ba sannan yace “Ashe yau za asha ihu kenan” Dariya dukkansu suka yi, sannan ya dago ya kalli Huda.. Three quarter riga mai fad’i ce a jikinta wadda ta wuce mata har gaba da guiwowinta peach colour, sai pencil trouser white, ta yi mopling da white vail, sai y’ar k’aramar white bag d’inta. Kwalli kad’ai ne a idonta sai d’an pink d’in jam baki data shafa amman tayi masifar kyau! A ranshi yace “Yarinyar akwai kyau kamar aljana” sai dai shi ko sau d’aya bata tab’a burgeshi ba, asalima shi haushin ta yake ji! Ko dan ita tayi sanadiyyar zuwan su Mom da Mammy cell ne, oho! Duk da ba wani shiri yake yi da Mom d’in tashi ba amman yayi mugun jin zafin abunda aka yi musu ata dalilin y’ar k’aramar Yarinya. Gyaran muryar da Abba yayi ne ya katse mishi tunani.. Bai ma lura da shi ba, sai yanzun. “Abba ashe kana nan.” Ya fad’a yana d’an murmushi. A b’angaren Abba kuwa yanda yaga ya kafe mishi y’a da ido ne ya sanya yaji kamar yace su fasa fitar! Ajiyar zuciya ya sauk’e yayi saurin kawar da tunanin daga zuciyarshi, sannan ya sake kallon Auwal d’in yace “Kallo d’aya tak! Duk wani mai isheshen hankali zai yi maka ya fara yi maka zargin gudowa kayi daga gidan mahaukata!!Kalli wandon ka kamar wanda aka yi maka gorin kaya, kalla nan” Abban ya mik’e yana nuna mishi wandon da hannunsa kafin yace “har cinyarka ana iya hangowa! Wannan d’an iskan askin shi kuma an hanaka amman naga abun naka gaba yake yi dan na yau ma yafi na kullum! Sai kace wani zakara. Harda sark’a a hannu!! Wai ni auwal mai kake son ka zama ne? Eh??” Yayi mishi tambayar cikin b’acin rai, bai jira jin amsar shi ba yace “Wallahi ka tabbar ka seseta wannan d’an iskan askin kafin ku dawo gidannan inba hakaba kowa sai ya ji kanmu!” Yana gama fad’in haka yayi hanyar sama ranshi a b’ace… Gaba d’aya In ka kalli Auwal ba zaka tab’a kiranshi da musulmi ba, ba abunda yafi b’ata mishi rai kamar sark’ar hannunshi ya lura harda wata sark’a a wuyanshi wadda ta b’uya a cikin rigar kawai shiru yayi masa dan in yaci gaba da kulashi zuciya zata jashi ya fella mishi mari!! Anyi maganan anyi har an gaji amman saboda ya raina mutane sam bai fasa ba. Auwal kuwa kamar ya had’iye zuciya… Tunda Abba ya fara fad’a ya had’e rai! Ba abunda yafi b’ata mishi rai irin tijarar da Abban yayi mishi a gaban Yara, don haka ya ja hannun Sudais suka fice ba tare da yabi ta kan Hudan ba. Ganin da tayi ranshine a b’ace yasa kawai ta bishi wajen, bata biye sa ba. Sudais yasa a gaba, amman dake Yaron ya fishi hankali yana ganin Hudan ta taho ya bud’e mata motar shi yayi saurin tsallakawa baya. Kamar zai yi magana sai kuma kawai yayi shiru. Ko ida rufe murfin motar bata yi ba ya fige ta da azabar gudu.. Daman masu gadin tun da suka hangoshi ya tada mota suka wangale gate, gudun kar garin saurin bud’ewa idan ya taho yayi gaba da wani! In kuma kayi jinkiri a balbaleka da zage zage! Komin

Chapter 13 of 28