Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Allah

Toshikkenan Allah yakaimu
Tashi yayi, be Iya cemata komai ba, yatafi part dinsa
Har dare de magana tana cinsa Arai, Daga qarshe yaje wajan momy yace momy dama inaso zamuyi magana ne

Tace inajin ka, wacce iri?

Momy Tunda daddy yace bazai sake samomin me aiki ba, kifadawa anty jiddah tadawomin Dame aiki na🤣

Yanzu Kai Alhaji shazali Ina kataba ganin anyi haka? Itama fa Acan din aiki yarinyar take mata

Hade hannayen sa yayi waje daya 🙏🏻 please momy nah

Tace to shknn, tadauki wayarta takira anty jiddah

Bugu daya ta Daga, Bayan sun gaisa momy tace jiddah babu me gyarawa Haneef dakinsa fa yanzu, yakamata ki dawo da yarinyar Nan haka, taci gaba da gyara masa, yaro duk yanata mita anbar masa dakinsa da datti

Anty jiddah najin haka cikin ranta tace wannan ba aikin kowa bane saina Haneef
Shegen yaro ni zaiyi wa wayo? Tanan ya bullomin kenan🤣








Sharhi, comment, share, Dan Allah 🙏🏻









Amnah El Yaqoub ✍🏻

💕SHALELAN BABA💕
(Romance)

Writing by Amnah El

27&28

Amma momy yarinyar nanfa school nakesan maidata tareda Sajida

To yanzu jiddah Tunda shi wanda yayi silar zuwanta yace a dawo masa da ita basai abar magana ta wuce ba ita Kuma yarinya tadawo bakin aikinta

Momy meyasa kikesan biyewa wannan Yaron ne Dan Allah?

Ba biye masa nakeba jiddah kawai quruciya ce take damunsa 🤣

Quruciya de momy, yanzu Haneef dinne me quruciya? Yaron da kuke shirin liqa masa mata biyu

Yanzu de jiddah Kinga babu wani tone tone Dan Allah kihado mata kayanta tadawo gida, sai anjima, qit takashe wayar saboda kada ma anty jiddah tasake Cewa komai

Yanajin Yanda wayar ta qare wani farin ciki ya mamaye Zuciyar sa, yace yawwa momy to yanzu ba shikkenan ba, kema Yan biyunki sun huta

Kallansa tayi, to kaima Kuma Haneef saika kiyaye gaba, banasan wannan kore koren dakake wa masu aiki

"nikwa momy inani Ina korarta? "

Kallan rashin fahimta Tayi masa me kake nufi?

A a momy babu komai, Bari inje daki na huta, sum sum yatashi yayi part dinsa yana gudun karyaci gaba da zama Kuma momy ta harbo jirginsa

Yana Zuwa part dinsa yafada kan gado, ya janyo computer sa yafara aiki cikin kwanciyar hankali, haba ai Gara haka, Gara tadawo insata agaba ina kallanta San Raina, yafi ace kullum Ina zarya a gidan anty, Tunda inada ikon dawo da Mai aikina, (tofa kaga masu yar aiki😃🤣)

********
Sister Kinga wannan brezia din na siyo mana su a school dazu da safe, Kinga wannan babbar zata Miki

Sajida wacce irin brezia Kuma? Kofa candy ba muyi ba

To brezia sai anyi candy ake sakawa? Nikam saka abata zanyi wallahi

Shalele tace a a nikam babu ruwana, bazan sakaba, aisai inji kunya ma, kowa Yana ganinka yasan me kasaka

Au kunya Ko? To shikkenan ai sai ki zauna da Abu turu turu babu Rigarsa

Anty jiddah ta turo kofar Dakin nasu ta shigo, gefen gadon ta nema ta zauna, tace Haneefa kinason Zuwa gidan su momy?

Mama gidan su momy Kuma? Aiken mu zakiyi?

Ba aikenku zanyiba Haneefa, inaso ne kikoma can gaba daya, dazu munyi waya da momy tace Haneef dakinsa yana zama da datti, shikuma Kinga Baisan qazanta, shiyasa tace kikoma

Sajida tace Amma mama karatun dazata fara fa?

Wannan babu damuwa akan haka, zanyi magana da Haneef yasama mata lesson teacher din dazai dinga yimata karatun, kokuma shi yazauna yayi Mata, Bayan wata daya sainayi masa maganar karatun inji Yanda zamuyi dashi

Ahankali Shalele tace Amma mama ni Bansan rabuwa dake

Kiyi hakuri Haneefa Nima akwai dalilin dayasa zan barki kikoma can din, insha Allah zakiga ribar Hakan agaba, yakamata ku kwanta yanzu dare yafara yi
Taja musu kofar tayi dakinta, dalilin dayasa zatabar Shalele tatafi guda daya ne, tanaso yarinyar ta kusanta da Haneef, yakasance a kullum tana kusa dashi, ta hakanne zaisa ta cimma burin ta akansu
Doctor Sulaiman ma dayaji dalilin nata sosai ya gamsu

Wajan sha biyu saura Sajida ta dubi Shalele data fara bacci tafara tashin ta
Cikin magagin bacci tace Sajida lafiya?

Tashi sis magana zamuyi

Haneefa ta tashi zaune, tace meyake faruwa ke baki fara bacci ba?

Sister shawara zan baki, duk lokacin dakika koma gidan momy, kada ki yarda ki nunawa uncle kina sonsa
Kinsan halin maza, idan sukaga mace tana sansu tofa babu zaman lafiya Daga ranar zasu dinga tashin Kai (🤭 nikam ba ruwana Sajida ce tafada)

Sannan koda wasa kada kisa aranki Cewa Wai bazai Iya sanki ba, a kullum anaso Bawa yasa aransa Addu'ar dayake yi ta riga da ta karbu
Kawai kisa aranki uncle nakine ke kadai

Maganar kina sonsa kuwa kiyi biris ki share shi, kiyi Kamar bakisan komai ba

Ajiyar zuciya ta sauke, gaskiya Sajida maganr ki Hakan take, Kuma naji dadin shawarar dakika bani insha Allah zanyi amfani da ita, Amma yanzu please ki kwanta, dare yafara

Sajida tace to shknn gud 9yt, Daga nan sukaja bargonsu suka kwanta

********
Washe gari da safe anty jiddah da Sajida suka tayata tahada kayanta, momy tace ta turo iliya direban yara zaizo ya dauke ta

Iliya dayazo Shima waje yasamu yazauna yana jiransu
Anty jiddah ta dubeta, Haneefa kiyi hakuri kinji, insha Allah zansa Haneef yana kawomin ke da kansa, Sajida ma Ko weekend ne zansa ta dinga Zuwa Miki

idanunta suka cika da qwallah, ni mama banasan rabuwa dake, Dan Allah kice musu nide su barni awajan ki

Haneefa nafada Miki inada dalilin dayasa banyi musu ba akan komawarki gidan, nan gaba kadan zaki gane dalili na, tashi muje iliya tun dazu yana jiranki
Haka suka futo Har wajan motor sa, Suka sake sallama, sannan ta shiga suka tafi, Sajida ta zauna tayi Shiru Kamar marainiya, dama haka ne sabo yanada dadi rabuwa babu dadi

Suna shiga gidan ta harari part din Haneef, aranta tace a kanka gashinan ansa narabu da Sajida ta

Momy da yara Suna falo, huzaifa yana cinyar Samah yanayin game awaya, tayi sallama tashigo gidan
Momy tace sannunki da Zuwa
Ahankali tace Yauwa momy nagode

A a babu komai, kije kihuta kici abinci, da yamma kyaje kiyi masa gyaran, yanzu Kam jeki huta

Cikin girmamawa tace godia nake momy, tayi cikin dakinsu itada baba Hanne 🤣

Samah tace oh momy kuwa radau abakinta, Kamar ita tasaka Miki

Safah tace to laifi ne danta fadi Hakan? Kede da neman magana kawai

Tana shiga dakin tafada jikin baba Hanne
Cikin murna baba Hanne tace wanake gani Kamar yata? Baba nice, Allah yadawo Dani

Baba tace Kai amma naji dadi alhmdlh, sannu yata, sannu da Zuwa

Tace amin baba, tana ajiye truly dinta yar qarama Daga gefe
Baba wallahi nagaji, Kuma wai momy Ina shigo wa Wai inzo in huta anjima naje nayi masa aiki
Ni wallahi aikin nan ya isheni, gidan mama jiddah yafi nan dadi wallahi

Baba tayi Murmushi to kiyi hakuri mana yata, nan dinma abinda yasa bakya jin dadinsa saboda Yan biyu basa janki ajiki ne, can Kuma akwai Sajida, Sajida Kuma sauqin Kai Gare ta
Kiyi hakuri zakiji dadin nan dinma wata Rana, harma ki zauna din din din

Baba me kike nufi?

Yata nifa Tunda naganki Naga kinfi dacewa da Haneef, Amma iyaye duk sunje sun hadashi da wasu yanmata masu budadden ido, to baka Isa kayi magana ba, kinsan Yan boko

Baba Kenan, nikam inani Ina shi?
Bari inyi Dan bacci baba, idan ankira sallar la'asar ki datani Daga bacci

To yata a tashi lafiya

Momy dake falo wayarta tayi qara, tana dauka tace Haneef Ina jinka

Momy yarinyar Nan tazo kuwa?

Wacce yarinya?

Kansa ya shafa yace
Ina nufin me aikin nan

Cikin ranta tace meyake damun Yaron nan ne?

Afili tace tazo Haneef, tana dakinsu tana hutawa, nace taje tahuta, anjima saitaje tagyara ma dakin, kokuma abarta sai gobe?

Dasauri yace a a a a momy, tana hutawa taje tayi aikinta, yawwa Takoma bakin aikinta 🤣

Momy tace yaushe zakaje wajan yarinyar? Lokaci daya annurin fuskarsa ya gushe, yace yanzu ma Ajmal nake jira Yazo Daga office dinsu saimuje

Yauwa to Allah yayi ma albarka

Sai da ta idar da sallar la'asar sannan tatafi part din nasa
Tana saka kafarta aciki taga duk yayi wani iri, ita kanta tasan gyaran be gamshe taba
Kujerar falon tahau tayi kwanciyar ta, wannan uban aikin wallahi bazan Iyaba saina huta, Dade da Bansan ciwon jiki naba nayi 🤣
Aikuwa Kamar a gidan anty jiddah tayi kwanciyar ta, Bata tsoron ma yashigo ya sameta ahaka

********
Suna hanyar Zuwa gidan su qawar momy wayarsa tayi ringing
Anty jiddah yafuto baro baro ajikin screen din
Dasauri yadaga yace anty nah ya gida yayarana

Yara lafiya Haneef, yau ba za'a zominba? 🤣

A a anty Zuwan nan de da sauqi

OK da sauqi Ko, to shikkenan dama nakira ne infadama inada niyyar saka yarinya a school momy tace a dawo ma da ita, Dan haka alhakin karatun yarinyar Nan yana kanka, idan anshiga sabon term ka tabbatar ka maidata makaranta

Sannan akwai lesson teacher dayake Zuwa gida yayi musu karatu

Yace to yanzu anty me kike nufi Kenan? 🤔

Kamarya menake nufi Haneef? Tanaso taqara tabbatar da abinda take zargi Dan haka dasauri tasake Cewa
Nifa Haneef aikin nan ba dole, yanzu saina sa hijabi na inzo in dauke yarinyar Nan, babu zafi

Dasauri yace a a anty, basai kinzo ba, za'a nema mata (🤣)

Meza ka nema mata?

Kince asamo mata lesson teacher, shine nace za'a samo mata

Babu wanda zaka samo mata Haneef, Kai zata yiwa aiki, danhaka Kaine zaka koya mata karatu Har Zuwa lokacin dazaka sakata a school

Amma anty....

Dasauri ta katse shi,
Kaga Haneef nifa abin nan babu zafi, Ada kun dauke ta ne batada uwa, yanzu kuwa tanada ita, aiki zata maka me lasisi

Cikin damuwa yace shikkenan za'a mata

Za'a mata Ko zaka mata?

"zanyi "

Tace ok sai anjima takashe wayar, Murmushi tayi Wai zanyi, bazai cede zanyi mata ba, saide zanyi, wannan miskilanci na Haneef yana Bata mamaki

Yanzu ne tasake tabbatar wa Haneef ne yasa momy ta kirata akan Haneefa, afili tace Haneef kakira wa kanka, Kuma Nima ka ragemin aiki, domin kuwa zamanku waje daya, zaisa yarinyar taqara shiga ranka fiye da yanzu
Kafara son yarinya baka saniba, sannan ka gagara baiyyana kowa, ba irin wannan soyaiyar nakeso ba Haneef, nafison kaso Haneefa ta Yanda zakaji aranka Cewa zaka Iya baiyyana wa kowa, ciki harda iyayenmu, rashin budurwa ne yasa suka hadaka da wannan yaran, aganina kawo musu Haneefa zaisa su janye wannan maganar yanmatan

Ajmal yana ganinsa Kuma yaji duk wayar da sukai, Amma be tambayeshi akan menene ba, yanaso dakansa yayi masa maganar, idan abinda yake damunsa yakai intaha dakansa zaizo yayi masa magana

Har suka je gidan qawar momy, Shima gida ne Dan madaidaici haka, Amma bazaka kirashi da gidan talaka ba, Afalo akayi musu iso suka zauna

Snacks aka kawo musu da lemuka da ruwa
Da sallama tashigo falon, fara ce Amma ba sosai ba, gaba daya haka tatafi babu wani shape, siririya ce sosai Kuma doguwa, dasuka gaisa, sai tayi Shiru

Ajmal yace to ita Kuma wannan nata tsarin kenan🤣

Gyaran murya yayi yace, Hajiya barka da futowa, ni Sunana Ajmal, abokin Haneef Shazali, tun muna yara
Wannan shine angon naki, munzo mu ganki ki ganmu, Ko za'a samu fahintar juna

Murmushi tayi tace Sunana hajara, Allah ya tabbatar mana da alkhairi
Baku sha ruwa ba

A a karki damu babu komai

Shide Haneef babu um bare um um, kallansa tayi tace Kai baka magana ne?

Inayi mana, kawai de dake dinne banasan... Ajmal ne ya zungureshi Daga gefe jin baran baramar dazai musu

Ya Kalle ta yace to Mungo de mu zamu tafi, ga katin sa na waya, Ko zaki Iya nemansa

Tace a a barshi, yanzu zaku wuce ne?

Wannan karan shazali da kansa yace eh

To kujirani awajan Dan Allah minti uku

Basu kawo komai ba suka ce to shikkenan
Suka fice, Ajmal harda Cewa kya gaida hajiyan

Suna fita harabar gidan Ajmal yace Allah sarki, wannan saliha ce wallahi 🤣 babu ruwanta, hajara duniya ba zafi

Haneef yace nikaina nayi mamaki wallahi, qila itama bataso Kamar ni, shiyasa Ko katin ma Bata karba ba

Suna wannan maganar suka hangota tana Jan truly qatuwa
Ajmal yace Bari muga Ko gift ne takawo maka
Tana zuwa wajan tace kuyi hakuri fa na tsaida ku, kayana naje nahado kawai zan bishi gida, Dan muji dadin fahimtar juna, shiyasa ban karbi katin ba🙆🏻‍♂🤦🏻‍♂🤣

Yanda kasan an doka masa guduma haka yaji, ashe ita Naga abin na gaske ne, ita harma tafi waccen

Ajmal kuwa kasa magana yayi 😱

Ganin sunyi Shiru yasa ta bude Bayan motar ta shiga tasaka Jakarta ma, tace ku shigo mutafi mana 🤣

Ajmal ya kalleshi Shima ya kalli Ajmal, babu damar magana
Suna shiga motar yakasa hakuri yace aida kinyi hakuri kin koma idan kina buqatar ganina sainazo, tace a a my Haneef, nida gidan qawar mamata kada kadamu muje

Haka suka taho, ahanya babu me magana acikinsu saide ahada ido ayi shiru🤣😃(maganinku Kenan, yau kun hadu da wadda tafi ku tsiya)

Suna Zuwa gida cikin bacin rai yayi part dinsa, Ko kallanta Bai sake yiba itama kuwa taja Jakarta tayi part dinsu momy

********

Saida tagama hutawa sannan ta tashi tafara gyara falon, riga da sket ne ajikin ta Yan kanti
Yana shigo wa falon yaganta tana mopping Ahankali yasauke Ajiyar zuciya duk da yana cikin bacin ran wancen jarababbiyar Saida yaji sanyi aransa

Zuba mata ido yayi yana Kallanta, Yanda take mopping din yake kalla saide ko'ina ajikin ta rawa yake, musanman qirjinta
Dasauri yadauke idonsa akansu
Masha Allah manya dasu, Zuciyar sace tasake bashi shawara, babu wata wata kuwa yabi shawarar Zuciyar sa yasake maida idonsa kansu
Dama haka nakowa yake atsaye?
Alamu Taji Kamar Ana kallanta, ahankali ta dago kanta ta kalleshi, suna hada ido duk da duburbuce Amma tana tuno shawarar Sajida saita saki jikinta
Tace uncle sannu da Zuwa, Ina yini?

Fuskar nan atamke yace lafiya, Daga nan yashige dakinsa yafada kan gado, niktile dinsa yacire yayi wulli dashi qasa, Allah yasa de yarinyar Nan bataga abinda yake Kallan mata ba ta Raina shi

(um kagama kalla sannan kazo kahade rai? 😱)

Itama kafada ta dage tace kome aka masa oho, taci gaba da aikinta

Saida tagama gyaran falon sannan Takoma tagyara kitchen dinma

Hanyar dakin ta nufa, kafin ta shiga Saida tace nutsu Shalele, karki ji tsoro ki nutsu kishiga ciki kawai

Ahankali ta tura kofar Dakin ta shiga, yana kwance akan gadonsa Amma kafafunsa Suna qasa, idanunsa a lumshe, Amma Sarai yana ganin duk abinda take, ita kuwa tayi zatan bacci yake, ta wuce toilet ta wanke shi, tasaka abin Qamshi
Sannan tadawo cikin dakin, kallansa ta tsaya yi, taga bacci yake sai kawai tafara aikinta
Harta gama shara, taje wajan data ajiye masa photunansa tadauka ta goge su sannan tasake gyara musu zama

Shide yana kallanta, yana ganin irin wannan baiwa Tata, gata qarama Amma tana wannan uban aiki saikace inji🤣

Wani iri takeji hau gata gashi a daki daya, duk Bata cikin hayyacinta dande ta dake ne kawai🤣

Mopar ta ta dauko tafara mopping dakin, cikin sauri, tanaso tagama tafice tabar cikin dakin nan
Duk yana kallanta, cikin ransa yace to ai Gara haka, Gara tadawo nan din Yanda zai sata agaba yayi ta kallo

Garin saurin datake wajan mopping santsin tiles yajata zata fadi qasa, da karfi tace Auch!!! Asukwane yatashi zaune yace lafiy... Kafin Yarufe baki tasowar dayayi zaune ita Kuma zata fadi qasa yasa jikinsu ya hadu
Aikuwa lokaci daya tafada kansa
Wadannan abubuwan guda biyu dasuka sauka akirjinsa yasa jikinsa yasaki yaji baida kuzarin dazai tareta haka yanaji yana gani suka fada kan gadon

Atake ya lumshe idonsa, wannan karan Kam bawai yana ganin nata bane, da gaske lumshe idon yayi

Ita kuwa tsoro yasaka runtse idonta,tana tunanin faduwa aqasa, jin ajikinsa tafada yasa tafara bude idonta Ahankali, harta bude shi fes akansa, taga ya lumshe ido, ta sauri ta janye jikinta Daga nashi

Shima sai a lokacin yabude idonsa yace "are you OK?

Daga masa Kai tayi, tazari Mopar dazata fice Daga dakin

Ahankali yace" bakiji ba "

Juyowa tayi ta kalleshi

Yace ki shirya gobe za'a fara yi miki karatu inji anty

Qasa tayi da idonta tace to, sannan taja masa dakin tafice dasauri gabanta na faduwa, yau itace ajikin Haneef? Oh ya Allah

Tana fice wa cikin ransa yace meyasa Bata saka wannan abin ne? Yanzu Kuma inda wanine tafada kansa haka Shima fa zaiji irin abinda yaji yanzu Ko?
Nan da nan kishin Yan maza yatashi 🤣🤣

Key din motarsa ya Zara yafuto waje, a lokacin Ana Kiran sallar magrib, Saida ya tsaya akai sallah sannan yashiga mota da kansa yafice da gudu

********
Tana shiga dakinsu tafada duniyar tunani, meyasa bataji Haushin abinda yafaru tsakaninsu ba yanzu? Kodan San datake masa ne? Haka taita murmushi Baba Hanne tana kallanta, tasan Kuma Sarai Daga part din Haneef yarinyar take, Ko menene ya wakana take wannan farin cikin oho musu, yaran zamani de ba'a iya musu 🤣🤭

********
Wani babban boutique yaje, yayi parking yadauki ATM dinsa yashiga ciki

Wadanda suka sanshi sai kallansa suke Ana nuna shi, haka yafara zagaye wajan yana dube dube, to abinka da mutumin dabai sababa, saide yayi waya yabada umarni ayi

Daqyar yagano wajanda kayan mata suke, wata budurwa yagani awajan yaqaraso wajanta "sannu fa"

Tana Juyowa taga Haneef Shazali, ai tuni tafara fara'ah, tayi tunanin ko zaice yana sonta ne, tace yawwa, yace am Dan Allah inane ake Saida vest na mata, tace laa kaga wajan can, gashi can

Yace ok, yayi gaba, ganin yatafi baice mata komai ba Kuma tasan basake ganinsa zatayi ba saitasha Gabansa tace Dan Allah Ko zan Iya yin selfie dakai?

Yace why not?

Yatsaya sukai, baisake kallanta ba yayi gaba, ita kuwa tace jeka de, inma bakace kana sona ba ai de munyi photo 🤣🤣

Yana Zuwa wajan yadebi panties da brezia dozin biyu, yatafi yaje yabada ATM Dinsa suka ja kudin su, Daga nan yayi gida

Yana Zuwa gida yayi parking motarsa yafuto da kafarsa daya yazuba wa ledar hannunsa ido, brezia din dake ciki ya kallah latest ne shegen masu kyau, aransa yace Ko zasu yi mata? To Wai ma tayaya zai iya Bata? Yace mata me? Karfa tayi masa wata fassarar, Kuma shi gaskiya idan yana ganin wadannan abubuwan ahaka gaskiya akwai babbar matsala 🤣

Haka de yafuto Daga motar, yayi part din momy, inyaso kawai ya ajiye mata ledar agaban ta yajuya, yana ganin kawai Hakan shine mafita 🤣🤭

*********
Hajara na zaune Afalo ta Dora qafa daya Kan daya tana kallo, a lokacin Shalele na daki tacewa baba Hanne baba Bari inje kitchen in dauko ruwa, qishi nakeji
Tafito Daga dakin taga baquwar fuska a falon, wannan Kuma wacece yaushe tazo gidan? Kosu momy baquwa sukai? Dazu Bata ganta ba
Hajara na Juyowa taga Shalele atsaye, ta miqe dasauri tace iyeee kece Anan gidan?

Tafidda hannu ta wanka mata mari, tace dama nafada Miki inde nasake ganinki, wallahi sai jikinki yagaya Miki
Rannan ma dakika ga na qyale ki, ba tsoron ki nake jiba 🤣🤣

Shalele Taji zafin mari tuni tafara hawaye tace Mena Miki zaki mareni?

Au ni kike tambaya me kika min? Tasake Daga hannu zata sake mata wani Marin

Cikin tsawa Hajara!!!

Juyawa sukai Dukansu, Haneef ne atsaye abakin kofar falo, duk abinda yake faruwa akan idonsa

Shalele ta juya tayi daki da gudu (nace jeki dama rabon shan mari ne yafuto dake🤣🤣🤣)

Haneef yana Zuwa wajan Hajara babu tambaya babu komai, Kuma dama ga Haushin ta da yakeji tunna dazu Shima yadaga hannu ya watsa mata mari

Tace nika mara Haneef?

Kobe ishe ki ba?

Meyasa bazaka tambayeni abinda tamin ba? Yarinyar Nan awajan shopping naganta tayimin rashin kunya, na qyale tane kawai saboda tana tare da bodyguard Yan Sanda

Shine yanzu saboda na rama zaka mareni?

Kansa yadafe da hannunsa 🤦🏻‍♂yayi gaba yabarta anan, Hajara tanason saka masa ciwon Kai (um ahakan zakayi mata biyune?)

Itama cikin fishi tayi dakin da aka sauke ta aciki

(wata sabuwa, mude asaninmu Shalele Bata taba Zuwa shopping da Yan Sanda ba Ko fans🤔

Wai Yaya makomar kyautar Haneef ga Haneefa? Taya zai Bata?

Zaku samu amsoshin ku Zuwa jibi insha Allah, gobe babu posting 🤗 ranar hutu ce, Nima hutawa zanyi inyi karatun novel Kamar kowa ehe😃😃😃

Zan huta na kwana daya, muhadu jibin kawai my fan's 💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻 ngd sosai

Sharhi, comment, share, Dan Allah 🙏🏻

Amnah El ✍🏻

💕SHALELAN BABA💕
(Romance)

29&30

Tana shiga dakin dakuka baba tace subhanallah yata keda wa daga fitarki yanzu?
Jikinta tafada cikin kuka tace baba watace afalo ina fita ta mareni wai tataba ganina nayi mata wulaqanci

Baba tasa hannu tafara bubbuga bayanta kamar qaramar yarinya kiyi hakuri budurwar haneef ce ,kina can part dinsa tazo dazu

Baqin ciki goma da ashirin ya kamata ,lokaci daya taji batasan ta,daga kukan mari sai aka wuce Dana kishi(😂🤣)

********

Zama yayi aqasan kafet din dake malale afalonsa yadafe kansa🤦🏻‍♂,su mata akoda yaushe inde suka hadu su biyu tofa ransu bayayin fari harsai sun saka mutum cikin damuwa ,yanzu ita wannan banda Neman fitina me wannan qanqanuwar yarinyar zatayi mata hartayi mata irin wannan hukuncin ?ai marin yayi mata yawa irin haka ai sai yataba lafiyarta(😃)
Kuma koba wannan bama ai shi duka kangarar da yara yake,bawai ya shiryasu ba

Ledar hannunsa ya kallah ,yanzu damuwarsa daya tayaya ma zai fuskanceta yabata wannan abin nasu🤣?
Shiya koreta saboda ta wanke masa gajeren wando ,yanzu yaje yasiyo mata brezia ,shikuma ayaya yake kenan ?
Allah yasoshi bai futo fili yabaiyana dalilin dayasa yace tatafi ba

Dakinsa yashiga da ledar yaboyeta,daga nan yashige toilet domin watsa ruwa

******

Washe gari yana fita aiki shalele taje tagyara masa part dinsa sosai sai qamshi yake da daukar ido,tadawo daki tayi zamanta tana jiran yadawo taje ta tambayeshi maganar karatu

********

Yana tsaka da aiki wayarsa tayi ringing, new number yagani ,baiyi picking ba ya ajiyeta yaci gaba da abinda yake
Aka sake kira ,yayi rejecting ,bai amsa kiran number dabai saniba ,akaro na uku da aka sake kira cikin masifa yace wai waye?

Hairat is my name

Cikin taqaici yace OK ya'akayi ?

Haneef nakiraka kana cemin ya akai ?sai wani abu yafaru ne sannan zan kiraka ?

Am dan Allah kinga hairat yanzu I'm very busy ,kit yakashe wayarsa

Wayar tabi da kallo,ita wannan gayen zai kashewa waya?
Itada take kashewa wasu?🤣

Gaskiyane ,idan yasan bayasan kiran meyasa zasu bata Katin? Cikin bacin rai take jijjiga kai tana cewa gaskiya ne,gaskiya ne

(🤣😃😂to tsaya nan kina gaskiya ne kin kasa daukar mataki)
********

Saida yagama dukkan ayyukansa sannan yataho gida
Saida yaje part dinsa yayi wanka yashirya sannan yatafi part dinsu momy domin cin abinci
Yana zuwa kuwa yaga momy da hajara afalon, Bayan sun gaisa momy tatashi tayi cikin dakinta cikin farin ciki

Safah ce takawo masa abinci,, ko kallan hajara batayiba tayi cikin dakinsu, ita Dama ta tsani wannan matar wallahi tafison anty hairat , ita Kuma Samah San hajara take 🤣

Ahankali yasa hannu zai dauki spoon yafara cin abincin, hajara tayi sauri ta riqe haannunsa
Haba my Haneef Ina zaune? Kawo nayi saving dinka mana
Kallanta yayi, yasake kallan hannunsa data riqe Ahankali yace waike wacce irin mashirmaciya ne ce?

Sakemin hannu

To laifi ne danna riqe hannunka?
Jikinka na riqe?

Tsaki yayi yagirgirza kansa sannan yazare hannunsa daga nata yace mummunan tunani daga mummunar Mata

Nikake cewa mummuna Haneef?


To sainayi qarya nace kinada kyau Bayan baki dashi?

Cikin fishi tasake cewa nikacewa mummuna de?

Ahankali yace yes

Bata sake cewa komai ba tayi cikin data sauka, Shima cikin nutsuwa yafara cin abincin sa

Shalele da baba Hanne suka futo zasu Dora abincin dare, suna Bude kofar sukaga hajara ta futo da qatuwar truly dinta
Sai suka dakata daga Nan bakin kofa

Haneef na ganin hajara da wannan uwar jaka yatashi ya nufeta, bece Mata komai ba yakama jakar ya riqe

Cikin tsananin masifa tace kaga Haneef kasakar min jakata, wallahi yau yau dinnan gidanmu zan kwana

Still baiyi Mata maganaba yafara Jan jakar

Dasauri ta riqeshi ta qwace Jakarta, nace ma bazan zauna ba bakaji ne?

Ajiyar zuciya yasauke, metake nufi dashi ne?

Afili yace hajara me kike nufi ne? Damafa Naga jakar tayi Miki nauyi ne shine zan Kai Miki ita bakin gate 🤭🤭🤣

Baba Hanne da Shalele me zasuyi inba Daria

Please Login or Register in order to submit comment